Saturday, 27 January 2018

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN SHIRKA DA NAU'OINTA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#SHIRKA_DA_NAU'O'INTA

BAYAN mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka hakika banban abunda ALLAH yafi kauna shine riko da tauhidi, Kuma babban abunda ALLAH yafi kin shine shirka!!

ALLAH madaukakin na cewa "KU BAUTA MA ALLAH KADA KU HADA SHI DA KOWA"

lallai yan uwa musulmi mafi girman zunubi shine yin shirka da Allah....

ALLAH madaukakin na cewa yayi "DUK WANDA YAYI SHIRKA DA ALLAH MAKOMAR SHI WUTA (idan ya mutu bai tuba ba)"

Sannan kuma Allah na cewa "LALLAI ALLAH BAYA GAFARTAWA IDAN AKAYI SHIRKA DASHI AMMA YANA GAFARTA WANI LAIFIN WANDA BA SHIRKA BA GA WANDA YASO"

Yan uwa musulmi hakika Allah ya tsoratar da dukkan annabawan da ya aiko game da Shirka,  ALLAH yana cewa "MUNYI WAHAYI GAREKA DA WADANDA SUKA GABACE KA IDAN KAYI SHIRKA LALLAI DUK AYYUKAN KA SUN LALACE"

Yan uwa musulmi mu duba girman Annabawa amma Allah yace masu idan suka yi shirka ayyukan su sun lalace balle mu, Wannan kiran fa ba Allah yana nufin Annabawa ba!!

A'a ana nufin mu, Domin annabawa basu yin shirka...

Yan uwa musulmi idan muka diba musulmi fa yawa sun fadawa shirka da sanin su wasu kuma bada sanin su ba!!

ALLAH madaukakin sarki na cewa "DA YAWAN SUNYI IMANI AMMA SUN HADA ALLAH DA WANI"

Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya gargade mu gargadi mai tsauri yana cewa "lallai abunda nafi tsoratar maku a rayuwar Ku shine shirka karama"

Wata rana Abubakar assidiq radiyyallahu anhu yaje wajen Manzon Allah sai Manzo Allah yace mashi lallai shirka tana nan cikin musulmi, Lallai shirka tafi boyuwa a cikin Ku Sama da tururuwa a saman bakin dutse cikin dare "

Amma ga wata addua da zaka rika karanta wa domin neman kariya kace" YA ALLAH INA ROKONKA KA GAFARTA MANI KA KARENI DAGA SHIRKA "

NAU'OIN SHIRKA

*Rokon kabari, Sau da yawa zaka ga wasu masu karancin islamiyya suna zuwa rokon kabari, Ko aljanu ko waliyai ko annbawa Alaihis salam

Alhalin Allah madaukakin sarki ya haramta hakan har ma ya fada cikin suratul ahkaf cewa" BABU BATACCE IRIN MAI KIRAN WANIN WANIN ALLAH "

Kuma duk musulmi mai imani ya amince cewa kiran WANIN Allah shirka ne, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Roko ibada ne " Dan haka duk wanda ya roki WANIN Allah dan neman biyan wata bukata ko neman kariya hakika yayi shirka!!

* Kudurta cewa wani  na cutar wa...

Sau da yawa idan wani abu yafaru da dan Adam sai ya dora laifin bisa wani abu, Ko dora shi ga wani dalili ko kuma cewa ai wane ne dalili da sauran su...

ALLAH madaukakin sarki yace "IDAN ALLAH YA KAWO MAKA CUTA BABU MAI IYA DEBE MAKA ITA SAI SHI"

*SHIRKA TA HANYAR YIN MAGANA...

sau da dama wasu na fadar wasu maganganu alhalin shirka ce, Kamar cewa 'Taya Allah kiwo yafi Allah na nan'!

Kamar cewa Idan Allah ya yarda tare da wane, Ba' a cewa hakan nan cewa ake yi idan Allah ya yarda sannan wane ya yarda, Kaga dole sai ka fara sanya Allah farko.

Sannan masu cewa mun dogara ga Allah mun dogara gareka,  Huzaifa ya ruwaito cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada Kuce abunda ALLAH yaso da abunda wane yaso"

* JINGINA NI'IMAH GA WANI ABU....

jjngina samuwar Ni'ima ga wani abu kamar aiki, Ko sana'a ko, Alhali yin haka sanya wa Allah kishiya ne, Allah kuma yace "KADA KU SANYA MA ALLAH KISHIYA"

* SIHIRI...

Yanzu yawan yin sihiri ya yawaita cikin musulmi, A yanzu yadda sihiri yazama ruwan dare ya koma wa wasu kamar jini, Saboda yawan yin sihiri har sanya wasu anan Zamfara na Jefa Alqur'ani Mai tsarki cikin makewayi (Toilet) subhannallah...

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yaje wurin boka ko dan sihiri ya karyata abunda aka saukar wa Manzo Allah (Alqur'ani)" 

* YIN RANTSUWA DA WANIN ALLAH...

wasu nada tabi'ar yin rantsuwa da, kaddara ko lokachi ko iyaye da sauran su, Har munzo zamanin da akafi yarda da rantsuwar da akayi ba Allah a ciki...

* IZGILI DA WANI ABUN ADDINI....

wasu kuma nada tabi'ar yin izgili da Abubuwan addini kamar, Gemu hijabi, aswaki, Yawaita sallama da sauran su.

* RATAYA LAYA KO KARHU

Daga cikin musulmi akwai masu tabi'ar daura laya ko karhu ko guru ko qaho da sauran su, Da sunan samun kariya ko wani abu, Wannan duk shirka ne.

*JIBINTAR KAFURAI
wasu nada tabi'ar jibintar kafurai fiye da musulmai, Alhali basu son Allah kuma basu son Manzon Allah.

Tabbas duk wanda ya fada shirka tabbas ya halaka, Duniya da Lahira.

ABUBUWAN DAKE SAMUWAR MAI YIN SHIRKA

- Rayuwar mai shirka tana lala cewa.

- Kullum cikin tashin hankali mai shirka ke kasancewa.

-Cirewar natsuwa daga rayuwa.

- shiga cikin batattu domin Allah yace "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA BACE"

-Rosa ayyukan bawa, Duk wanda yayi shirka ya roza ayyukan shi.  ALLAH madaukakin sarki ya cewa Manzo Allah cewa "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA LALATA AYYUKAN SHI"

-DUSHE HASKE.

duk mai yin shirka Allah zai sanya wa rayuwar shi duhu, Baya taba ganin hasken alkahri.!!

Yan uwa musulmi hakika shirka tana tauye imani, Lallai yazama wajibi garemu muyi watsi da duk abunda zai kowa mana tangarda a cikin imanin mu, Domin samun tsira gobe Kiyama mu da iyalan mu da yan uwan mu baki daya.
. Allah ka albarkaci rayuwar mu baki daya.

Allah kayi mana kariya daga shirka, Ka biya mana bukatun mu na alkhairi, Ya Allah Muna tawasuli da sunayen ka ka biya mana bukatun mu na alkhairi baki daya, Ya Allah kara albarka ga garuruwan mu kabamu lafiya da cikakken zama lahiya ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 01-5-1439
Friday 19-January - 2018 AB

HUDUBAH MAI TAKEN MATSAYIN TAUHIDI GA RAYUWAR MUSULMI

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#MATSAYIN_TAUHIDI_GA_RAYUWAR_MUSULMI

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

BAYAN mukaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka kamar yadda kuka gani kan abunda khudbar mu zata yi magana, Yan uwa hakika shi tauhidi shine rayuwar bawan Allah kacokan..

Yan uwa musulmi hakika hakika Allah madaukakin sarki ya halicce mu baki daya dan mu bauta mashi, Babban dalilin halittar mu baki daya shine dan yin bauta ga Allah ga Allah mahallici.

Allah madaukakin sarki ya halicce mu kuma yabamu umarnin bauta mashi, A cikin suratul zariyat Allah madaukakin sarki na cewa "BAN HALICCI MUTUN DA ALJANI BA SAI DAN SU BAUTA MANI"

Bautar Allah ga kowane mutun da aljani dole ne kuma wajibi ne, Mafi girman abun bukata ga bawan Allah shine kadaita Allah ba tare da sanya mashi kishiya ba a ko ina..

Hakika cikin imaninka da tauhidinka dole ne sai kazama mai furtawa da kaskantar da kai da kwadayin rahamar sa da tsoron azabar sa, Da kuma kasancewa mai sujjada gareshi da cikakken tsoron sa!!

Yan uwa musulmi masu albarka hakika domin kara tabbatar da tauhidi Allah ya wajabta mana karanta suratul fatiha a cikin kowace sallah da zamu yi, A ciki muke cewa "IYAKA NA ABUDU WA'IKA NAS TA'IM"

IDAN HAR BAWA YAKI YIN BAUTA GA ALLAH HAKIKA YAYI ASARAR DUNIYA DA LAHIRA!!! 😨😨😨

Yan uwa musulmi hakika Allah ya aiko mazannin shi baki daya domin su tabbatar da tauhidi da musulunci a kasa, Kuma Allah ya aiko littafan baki daya dan tabbatar dan tauhidi a kasa '

ALLAH madaukakin sarki ya fada cikin suratul nahli cewa "WALLAHI MUN AIKOWA KOWACE AL' UMMAH DA MANZO DOMIN SU BAUTA MA ALLAH KUMA SU KAFURCEWA DAGUTU"

Yan uwa musulmi hakika wannan ayar kadan ce daga cikin ayoyin dake tabbatar da dole ne yin bauta ga Allah da kuma kare yin tauhidi.

Yan uwa musulmi masu albarka lallai da tauhidi ne rayuwa ke natsuwa kuma ta samu kwanciyar hankali, Hakika idan rayuwa ta kasance babu tauhidi a cikin ta tabbas dabba ta fishi,

Duk wanda keda tauhidi to hakika shi rayayyene, Idan kuma baida tauhidi komai mulkin sa da duk wani gata nashi to matacce ne.

Allah madaukakin sarki yana cewa cikin suratul an'am cewa "WANDA YA KASANCE MATACCE MUKE RAYASHI MU SANYA MASHI HASKE"

hakama Allah madaukakin sarki na cewa "KU KARBA KIRAN ALLAH DA MANZO IDAN AN KIRAKU GA RAYUWA (TAUHIDI)

Yan uwa musulmi wallahi duk wanda baisan Allah ba baida banbanci da dabbah, Har ma dabba tafi shi domin kuwa ita dabba babu wani hisabi da za'a yi masu.

Idan har muka yi imani lallai ALLAH zai samar mana da jindadi, Allah yana fada cikin suratul nur cewa "ALLAH YAYI ALKAWARI IDAN KUKAYI IMANI DA AIKI NA KWARAI ZAMU KHALIFANTAR DAKU DA SHARADIN KUN KADAITA ALLAH"

kafurcewa Allah lallai shine babban jigon samun zaman lafiya mai dorewa.

Riko da tauhidi shine jigo na samuwar arziki, Allah madaukakin sarki na cewa "DUK WANDA YAYI IMANI DA ALLAH YA AIKATA AIKIN KWARAI ZAMU AZURTASHI"

Arziki na nufin wadatar zuci, Koda kaga kafuri da kudi da dukiya zaka same shi babu kwanciyar hankali da natsuwa.

Amma idan kana da cikakken imani da Allah zaka ji natsuwa da wadata koda baka da kudi 😀

Yan uwa musulmi masu albarka hakika Riko da tauhidi na kawo natsuwa daga shaidanu,Bai yiwuwa shaidani ya tsaya idan ake gudanar da tauhidi.

Duk inda ake kiran sallah shaidan yakan tsere da gudu, Har sai an gama sannan idan za'ayi ikama haka, Saboda a cikin kiran sallah da ikama akwai tauhidi a cikin su.

Hakama ayatul kursiyu aya ce mai girman gaske, Wanda duk ya karanta ta kafin ya kwanta Allah zai turo mala'iku su rika gadin shi wannan duk dalilin tauhidin dake ciki ne.

Yan uwa musulmi hakika Riko da tauhidi yana kawo kariya tsakanin ka da mushrikai, Domin ALLAH madaukakin sarki yace "LALLAI ALLAH NA BADA KARIYA GA MASU IMANI" duk wani kokarin mushrikai nan cutar Allah bazai bari ba domin yayi alkawarin kariyar.

Yan uwa musulmi dole ne tunatar da muminai game da abunda ya shafi tauhidi domin kamar yadda muka fada shine ginshikin rayuwa,

Hakika tunatar da muminai game da imani yana da muhimmancin gaske domin zai zaburar da sabunta masu imanin su, Domin Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "IMANI KAMAR RIGA NE"

wato kenan yana tsufa idan har ba'a sabunta shi.

Yan musulmi akwai wasu musulmi dasu ke matukar adawa da maganar da shafi tauhidi, Domin wai su a ganin su tsanantawane yin maganar tauhidi, kawai abar kowa yayi yadda yake so...

To shi musulunci ba haka yake ba, Yana da tsari kuma da zarar anyi nisa cikin kaucewa tsarin sa to za'a iya halaka!!

Yazama wajibi kuma dole ga kowane musulmi yasan tauhidan nan guda 4 - Rububiya
-Qulihiya
-As-mau wassifat
-Risalah

Dole a sansu tare da sanin matsayin kowane daga cikin su.

Ta sanin su zai sa mu kaucewa duk abunda zai kange daga Allah, kamar shirka da Allah!!!

Domin kamr yadda muka sani shirka da Allah na warware ibadu sa imani baki daya.

Yin shirka ko duba ko bugun kasa da zuwa wurin bokaye na warware imani, Domin Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yaje wurin boka ko mai duba kuma ya gasgata abunda ya fada mashi to ya kafurta abunda aka saukar wa Annabi Muhammadu sallal lahu alaihi wassalam (Al'qurani mai tsarki)

Duk abunda kake nema ka tuna Allah ne ke badawa tun kafin a hallicce ka a rubuta duk abunda zai zama naka.,

Basai kaje wurin wani kazami ba mushriki, Ya raba ka da imanin ka ya raba ka da kudin ka.

Yan uwa musulmi mu kara tunawa fa lallai ALLAH ya hallicce mu ne dan kadai mu bauta mashi.

Idan har Zamu yi hakuri da talauci da rashi dole ne muyi hakuri da yawan yiwa Allah ibada domin akwai ranar sakamako.

Tun daga aure, sutura abinci gida mota abokan ta, Da duk wani abu na bukatar rayuwar mu basu kai muhimmancin tauhidi ba.

Yan uwa musulmi masu albarka idan muka diba yadda  rayuwa ba chan ba chan babu tauhidi wata rana sai mutuwa tazo ta riska shikenan!! 😨😵😷

Allah ya tabbatar da tauhidi a zukatan mu ya yafe mana yayi mana rahama, Ya ubangiji ka yafe mana kurakuren mu ya kare daga hassada da kyashi da jin zafi da gulma da annamimanci da karya da ciwo da kuturta da makanta da kurumta da sauran ciwuka.

Ya ubangiji ka zaunar damu lafiya ka biya bukatun mu na alkhairi ka gafarta wa mamatan mu, Allah kayi salati da tasleemi ga Shugaban mu Annabi Muhammadu da iyalinsa da sahabban sa da dukkan mataimakan sa da sahabban sa yardaddu baki daya har zuwa ranar sakamako.

Ameen ya rabb.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 24-Rabi'ul akheer {4}-1439
Friday 12-January - 2018 AB