Wednesday, 6 December 2017

HANI KAN TSAGA JIKI DAGA LITTAFAN SHI'AH

HANI KAN DUKAN JIKI KO TSAGA TUFA KO
IHOCE-IHOCE YAYIN WATA MUSIBA, BAFA CIKIN
LITATTAFAN SUNNAH KURUM YAZOBA, YA
TABBATA HATTA CIKIN LITATTAFAN
SHI'A.........

Daga: Malam Abdurrazak Uba Musa

Bari indan fitoda koda dozin dayane daga cikin
ruwayoyin :
ﺍﻟﻨﻴﺎﺣﺔ ﻣﻦ ﻋﻤﻞ ﺍﻟﺠﺎﻫﻠﻴﺔ . ‏( ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ١٢ /٩١٥
ﺑﺤﺎﺭ ﺍﻷﻧﻮﺍﺭ ٨٢ /١٠٣ )
Ihoce-ihoce na daga aikin jahiliyya.
ﻧﻬﻰ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺁﻟﻪ ﻋﻦ ﺍﻟﺮﻧﺔ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻤﺼﻴﺒﺔ ﻭﻧﻬﻰ ﻋﻦ
ﺍﻟﻨﻴﺎﺣﺔ ﻭﺍﻻﺳﺘﻤﺎﻉ ﺇﻟﻴﻬﺎ . ‏( ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٥ )
Annabi yayi hani ga daga sauti yayin kuka,da
ihoce-ihoce,da kuma jiyarda kukan yayin faruwar
musiba.
ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ‏( ﺻﻮﺗﺎﻥ
ﻣﻠﻌﻮﻧﺎﻥ ﻳﺒﻐﻀﻬﻤﺎ ﺍﻟﻠﻪ ،ﺃﻋﻮﺍﻝ ﻋﻨﺪ ﻣﺼﻴﺒﺔ ﻭﺻﻮﺕ ﻋﻨﺪ
ﻧﻌﻤﺔ، ﻳﻌﻨﻲ " ﺍﻟﻨﻮﺡ ﻭﺍﻟﻐﻨﺎﺀ ‏) ‏( ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ
ﻟﻠﻨﻮﺭﻱ . ١/١٤٤ ، ﺑﺤﺎﺭ ﺍﻷﻧﻮﺍﺭ ٨٢ /١٠١ )
Sautika 2 ababen tsinewane,Allah baya sansu,
daga murya da kuka yayin wata musiba,da daga
murya yayin farinciki.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ : ﻻ ﻳﺼﻠﺢ ﺍﻟﺼﻴﺎﺡ
ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻴﺖ ﻭﻻ ﻳﻨﺒﻐﻲ، ﻭﻟﻜﻦ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻻ ﻳﻌﺮﻓﻮﻥ .
‏(ﺍﻟﻜﺎﻓﻲ ٣/٢٢٦ ، ﺍﻟﻮﺍﻓﻲ ١٢ /٨٨ ، ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٦ )
Bai kyautuba kururuwa yayin mutuwa,bakuma ta
kamata ba,Amma kash 'yan Shi'a basu saniba.
}ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﻋﻠﻲ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﺇﻟﻰ ﺭﻓﺎﻋﺔ ﺑﻦ ﺷﺪﺍﺩ :{
ﻭﺇﻳﺎﻙ ﻭﺍﻟﻨﻮﺡ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻴﺖ ﺑﺒﻠﺪ ﻳﻜﻮﻥ ﺻﻮﺕ ﻟﻚ ﺑﻪ
ﺳﻠﻄﺎﻥ
‏( ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
Rubutun sayyidi Ali zuwa ga rifa'a, yace dashi:-
Kashedinka ga kuka yayin mutuwa.
ﻋﻦ ﺍﻟﺼﺎﺩﻕ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ :
ﻣﻦ ﺿﺮﺏ ﻳﺪﻩ ﻋﻞ ﻓﺨﺬﻩ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻤﺼﻴﺒﺔ ﺣﺒﻂ ﺃﺟﺮﻩ .
‏( ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٤ )
Duk Wanda ya doki cinyarsa da hannunsa yayin
musiba,to ya rushe ladansa.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ : ﻻ ﻳﻨﺒﻐﻲ ﺍﻟﺼﻴﺎﺡ
ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻴﺖ ﻭﻻ ﺗﺸﻖ ﺍﻟﺜﻴﺎﺏ .
‏( ﺍﻟﻜﺎﻓﻲ ٣ /٢٢٥ ، ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٦ )
Bai kamata ba kuka yayin mutuwa da kuma yaga
tufafi.
ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ : ﻟﻌﻦ
ﺍﻟﻨﺎﺋﺤﺔ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻤﻌﺔ . ‏(ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
An tsinewa mai koke-koke da kuma mai jiyar da
kukan.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺟﻌﻔﺮ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ : ﺃﺷـﺪ ﺍﻟﺠﺰﻉ ﺍﻟﺼﺮﺍﺥ
ﺑﺎﻟﻮﻳﻞ ﻭﺍﻟﻌﻮﻳﻞ ﻭﻟﻄﻢ ﺍﻟﻮﺟﻪ ﻭﺍﻟﺼﺪﺭ، ﻭﺟﺰ ﺍﻟﺸﻌﺮ ﻣﻦ
ﺍﻟﻨﻮﺍﺻﻲ، ﻭﻣﻦ ﺃﻗﺎﻡ ﺍﻟﻨﻮﺍﺣﺔ ﻓﻘﺪ ﺗﺮﻙ ﺍﻟﺼﺒﺮ، ﻭﺃﺧﺬ ﻓﻲ
ﻏﻴﺮ ﺍﻟﻄﺮﻳﻘﺔ . ‏( ﺍﻟﻜﺎﻓﻲ ٣/٢٢٣ ، ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٥ ،
ﺑﺤﺎﺭ ﺍﻷﻧﻮﺍﺭ ٨٢ /٧٦ ) .
Duk Wanda ya tsayu ga koke-koke Haqiqa yabar
haquri,kuma yayi ruqo da hanyar da ba ta gaskiya
ba.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺍﻟﻤﻘﺪﺍﻡ ﻗﺎﻝ : ﺳﻤﻌـﺖ ﺃﺑﺎ ﺍﻟﺤﺴﻦ ﻭﺃﺑﺎ ﺟﻌﻔﺮ
ﻋﻠﻴﻬﻤﺎ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻳﻘﻮﻝ ﻓﻲ ﻗﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ }: ﻭﻻ
ﻳﻌﺼﻴﻨﻚ ﻓﻲ ﻣﻌﺮﻭﻑ { ‏( ﻗﺎﻝ : ﺇﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺁﻟﻪ
ﻟﻔﺎﻃﻤﺔ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺍﻟﺴﻼﻡ : ﺇﺫﺍ ﺃﻧﺎ ﻣُـﺖ ﻓـﻼ ﺗﺨﻤﺸﻲ ﻋﻠﻲّ
ﻭﺟﻬﺎ ﻭﻻ ﺗﺮﺧﻲ ﻋﻠﻲّ ﺷﻌﺮﺍ ﻭﻻ ﺗﻨﺎﺩﻱ ﺑﺎﻟﻮﻳﻞ ﻭﻻ ﺗﻘﻴﻤﻦ
ﻋﻠﻲّ ﻧﺎﺋﺤﺔ، ﻗﺎﻝ : ﺛﻢ ﻗﺎﻝ : ﻫﺬﺍ ﻫﻮ ‏( ﺍﻟﻤﻌﺮﻭﻑ ‏) ﺍﻟﺬﻱ
ﻗﺎﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ (( ﻭﻻ ﻳﻌﺼﻴﻨﻚ ﻓﻲ ﻣﻌﺮﻭﻑ .
)) ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٥ -٩١٦ ، ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
Annabi yace da Nana Fadima : Idan nakoma ga
Allah kar kiyi kiran Na mutu na Lalace,kar kuma
kiyimin kururuwa.
ﻗﻮﻝ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻷﺧﺘﻪ ﺯﻳﻨﺐ : ‏( ﻳﺎ ﺃﺧﺘﺎﻩ
ﺃﻗﺴﻤﺖ ﻋﻠﻴﻚ ﻓﺄﺑﺮﻱ ﻗﺴﻤﻲ، ﻻ ﺗﺸﻘﻲ ﻋﻠﻲّ ﺟﻴﺒﺎ ﺟﻴﺒﺎ
ﻭﻻ ﺗﺨﻤﺸﻲ ﻋﻠﻲّ ﻭﺟﻬﺎ، ﻭﻻ ﺗﺪﻋﻲ ﻋﻠﻲّ ﺑﺎﻟﻮﻳﻞ ﻭﺍﻟﺜﺒﻮﺭ
ﺇﺫﺍ ﻫﻠﻜﺖ ‏) ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
Imam Husain ya fadawa 'yar uwarsa zainab
cewa: idan nakoma ga Allah to karki keta
tufarki,karkiyi kyruruwar jahiliyya.
ﺃﻥ ﻋﻠﻴﺎً ﻋﻠﻴﻪ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﻗﺎﻝ : ﻣﻦ ﺿﺮﺏ ﻳﺪﻩ ﻋﻨﺪ
ﻣﺼﻴﺒﺔ ﻋﻠﻰ ﻓﺨﺬﻩ ﻓﻘﺪ ﺣﺒﻂ ﻋﻤﻠﻪ . ‏(ﺍﻟﺨﺼﺎﻝ ﻟﻠﺼﺪﻭﻕ
ﺹ ٦١٢ , ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٣/٢٧٠ ) .
Sayyidi Ali yace: Duk Wanda wata musiba
tazomasa sai ya maka hannunsa kan cinyarsa,to
babu shakka ya rushe aikinsa.
BABBAN ABIN TAMBAYAR ANAN SHINE :-
WANNAN ABIN DA 'YAN SHI'A SUKEYI NA
AZABTAR DAKAI A INA SUKA SAMOSHI ??
ME YASA BASA AIKI DA WADANNAN
RUWAYOYIN DA DUKAI HANI KAN HAKA ??

MATSAYAR SALAFIYYA KAN KASHE JIKAN MANZON ALLAH S.A.W

MATSAYAR SALAFIYYA KAN KASHE JIKAN
MANZAN ALLAH ALHUSSAIN ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ .......

Daga:Malam Abdurrazak Uba Musa

Shehin musulunci ibn taimiya yake cewa:-
ﻓﻼ ﺭﻳﺐ ﺃﻥ ﻗﺘﻞ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﻣﻦ ﺃﻋﻈﻢ ﺍﻟﺬﻧﻮﺏ ﻭﺃﻥ ﻓﺎﻋﻞ
ﺫﻟﻚ ﻭﺍﻟﺮﺍﺿﻲ ﺑﻪ ﻭﺍﻟﻤﻌﻴﻦ ﻋﻠﻴﻪ ﻣﺴﺘﺤﻖ ﻟﻌﻘﺎﺏ ﺍﻟﻠﻪ . @
‏(ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﻨﺒﻮﻳﺔ ٤ /٥٦٠ )
Babu makawa/shakka tabbas kashe Alhussain na
daga mafi girman zunubai,kuma Haqiqa Wanda
yayi kisan,da Wanda ya yarda da kisan,da Wanda
ya taimaka da wani Abu wajan kisan, duk sun
can-can ci azabar Allah.
Anan Shehin ya bayyana cewa:- kisan yana cikin
ﺃﻋﻈﻢ ﺍﻟﺬﻧﻮﺏ mafiya girman zunubai.
Sannan ya bayyana cewa:- Wanda yayi da Wanda
ya taimaka da Wanda ya yarda,duk sun can-can
ci Allah ya azabtar dasu.
Shehin yakuma cewa :-
ﻭﺃﻣﺎ ﻣﻘﺘﻞ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﻓﻼ ﺭﻳﺐ ﺃﻧﻪ ﻗﺘﻞ
ﻣﻈﻠﻮﻣﺎ ﺷﻬﻴﺪﺍ ﻛﻤﺎ ﻗﺘﻞ ﺃﺷﺒﺎﻫﻪ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻈﻠﻮﻣﻴﻦ ﺍﻟﺸﻬﺪﺍﺀ
ﻭﻗﺘﻞ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﻣﻌﺼﻴﺔ ﻟﻠﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﻣﻤﻦ ﻗﺘﻠﻪ ﺃﻭ ﺃﻋﺎﻥ
ﻋﻠﻰ ﻗﺘﻠﻪ ﺃﻭ ﺭﺿﻰ ﺑﺬﻟﻚ @. ‏( ٤ /٥٥٠ )
Amma kisan Alhussain ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ babu
makawa tabbas An kashe Alhussain yana abin
zalunta kuma shaheedi,kamar yanda aka kashe
makamantansa suna ababan zalunta kuma
shahidai.
Kashe Alhussain Sabon Allah ne da manzo,ga
Wanda yai kisan ko ya taimaka kan kisan ko ya
yarda da kisan.
Anan kuma Shehin ya bayyana cewa :- Kashe
Alhussain zaluncine.
Sannan kuma ya bayyana cewa:- Alhussain
shahadace yayi.
Sannan Shehin ya bayyana cewa:- Mai kisan da
Wanda ya taimaka masa,da Wanda ya yarda,duk
sun sabawa Allah da manzan Allah.
Anyiwa shin musulunci tambaya hukuncin Wanda
ya kashe jikan manzan Allah Alhussain ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ
ﻋﻨﻪ, sai yace:-
ﻭﺃﻣﺎ ﻣﻦ ﻗﺘﻞ " ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ " ﺃﻭ ﺃﻋﺎﻥ ﻋﻠﻰ ﻗﺘﻠﻪ ﺃﻭ ﺭﺿﻲ
ﺑﺬﻟﻚ ﻓﻌﻠﻴﻪ ﻟﻌﻨﺔ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﻤﻼﺋﻜﺔ ﻭﺍﻟﻨﺎﺱ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ ؛ ﻻ
ﻳﻘﺒﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻨﻪ ﺻﺮﻓﺎ ﻭﻻ ﻋﺪﻻ . @. ‏( ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ
١/٣٩٢ )
Amma Wanda ya kashe Alhussain, ko yataimaka
kan kisan ko ya yarda da kisan,to tsinuwar Allah
data mala'iku,data baki dayan mutane ta tabbata
akansa,kuma Allah bazai karbi farillarsaba da
nafilarsa.
Anan kuma Shehin ya bayyana cewa:- Wanda
yayi kisan da Wanda ya taimaka kan kisan da
Wanda ya yarda da kisan, duk tsinannune.
ALLAH TA'ALA KA QARA TABBATAR DA
AZABARKA GA MAKASAN JIKAN MANZAN
ALLAH DA WADANDA SUKA TAIMAKA WAJAN
KISAN

AQEEDUN YAN TIJJANIYYA

AQEEDU GOMA DAGA AQEEDUN TIJJANIYYA!! ANYI WALQIYA.....!!;> AQEEDA TA FARKO ...................................... SHEIKH AHMADU TIJJANI ACIKIN CONSITUITION DIN TIJJANIYYA WATO JAWAHIRIL MA,ANIY YACE: ﺇﻥ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﻮﺭﺩ ﺍﺩﺧﺮﻩ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻟﻲ ﻭ ﻟﻢ ﻳﻌﻠﻤﻪﻷﺣﺪ ﻣﻦ ﺃﺻﺤﺎﺑﻪ ( – ﺇﻟﻰ ﺃﻥ ﻗﺎﻝ :- ) ﻟﻌﻠﻤﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺑﺘﺄﺧﻴﺮ ﻭﻗﺘﻪﻭﻋﺪﻡ ﻭﺟﻮﺩ ﻣﻦ ﻳﻈﻬﺮﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻳﺪﻳﻪ WANNAN WURIDIN ANNABINE YA ADANA MINI SHI BAI SANAR DA KOWA BA DAGA ­SAHABBANSA-----­
SABODA ANNABI YASAN LOKACINSA BAIZOBA SABODA BABU WANDA ZAI IYA BAIYANASHI AWANCAN LOKACIN!!!

DUBI YANDA YA JINGINAWA MANZON ALLAH BOYE ILIMI BAYAN ALLAH YANA CEWA: : ﻳﺎ ﺃﻳﻬﺎ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝﺑﻠﻎ ﻣﺎ ﺃﻧﺰﻝ ﺇﻟﻴﻚ ﻣﻦ ﺭﺑﻚ SURATL MA IDA: 67 DUBI YADDA YA FIFITA KANSA AKAN ABUBAKAR DA UMAR DA USMAN DA ALI DA AHLUL BAITI DA SAURAN SAHABBAI DUK ANNABI BAI KOYA MUSU WURIDIN TIJJANIYYA BA SABODA BAZASU IYA KOYAWA MUTANE BA SAI BAYAN ANNABI YABAR DUNIYA SAMA DA SHEKARA DUBU! AKA HAIFI TIJJANI SAI ANNABI YA DAWO DUNIYA YA BASHI WANNAN WURIDI!!!!!

YANZU YA KAMATA MAI LAFIYAYYEN  HANKALI YA YARDA DA WANNAN?

AQEEDA TA BIYU ------------------- AHAMADU TIJJANI YACE: ﺇﻥ ﺍﻟﻤﺮﺓ ﺍﻟﻮﺍﺣﺪﺓ ﻣﻦ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻔﺎﺗﺢ ﺗﻌﺪﻝ ﻛﻞ ﺗﺴﺒﻴﺢ ﻭﻗﻊ ﻓﻲ ﺍﻟﻜﻮﻥ ﻭﻛﻞ ﺫﻛﺮ ﻭﻛﻞ ﺩﻋﺎﺀ ﻛﺒﻴﺮ ﺃﻭ ﺻﻐﻴﺮ ﻭﺗﻌﺪﻝ ﺗﻼﻭﺓ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﺳﺘﺔ ﺁﻻﻑ ﻣﺮﺓ " SALATUL FATI DAI DAI YAKE DA KOWANE IRIN TASBIHI DA AKAI ABAYAN QASA, HAKA KOWACE ADDU,A BABBA DA QARAMAR TA KUMA YIN SALATIL FATI DAYA DAI DAI YAKE DA SAUKE ALQUR,ANI SAU DUBU SHIDA!!! duba jawahiril ma,ani: shafi:96 bugun attaqaddumul,ilmiyya. Bugu na farko. Dubi yanda wannan mutum ya fifita salatilfati akan qur,ani mai girma!!!!

ﺇﻥ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻳﻔﺘﺮﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﻜﺬﺏ ﻻﻳﻔﻠﺤﻮﻥ ﻣﺘﺎﻉ ﻗﻠﻴﻞ ﻭﻟﻬﻢ ﻋﺬﺍﺏ
ﺃﻟﻴﻢ{ ] ﺍﻟﻨﺤﻞ 116 117].

AQEEDA TA UKU ------------------- AHAMDU TIJJANI YACE: ﻗﺎﻝ ﻓﻲ ﺍﻹﻓﺎﺩﺓ : ) ﻣﻦ ﻟﻢ ﻳﻌﺘﻘﺪﺃﻧﻬﺎ – ﺃﻱ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻔﺎﺗﺢ – ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻟﻢ ﻳﺼﺐ ﺍﻟﺜﻮﺍﺏ ﻓﻴﻬﺎ ( " ﺹ 80 ".

DUK WANDA BAI YADDA SALATIL FATI ITAMA QUR,ANI BACE KO YAYI BASHI DA LADA!!! duba ifadatul ahmadiyya shafina:80
TO INA MASU SALATIL FATI? KODAI KU YADDA SALATIL FATI QUR,ANI CE WALLAHI IN KUKA FADI KUNYI RIDDA! KO KUMA BAKU YADDABA TO ANAN KUMA KUDA TIJJANI TUNDA GA ABINDA YA FADA: BAKU DA LADA!!! ZAKUJI SAURAN INSHA ALLAHU AKAN AQEEDA TA HUDU IN SHA ALLAH

ﻭﻻ ﺗﻘﻮﻟﻦ ﻟﺸﻲﺀ ﺇﻧﻲ ﻓﺎﻋﻞ ﺫﺍﻟﻚ ﻏﺪﺍ . ﺇﻻ ﺃﻥ ﻳﺸﺎﺀ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﺫﻛﺮ ﺭﺑﻚ ﺇﺫﺍ ﻧﺴﻴﺖ ﻭﻗﻞ ﻋﺴﻰ ﺃﻥ ﻳﻬﺪﻳﻨﻲ ﺭﺑﻲ ﻷﻗﺮﺏ ﻣﻦ ﻫﺬﺍ ﺭﺷﺪﺍ

ALLAH YA QARA KAREMU DAGA WADANNAN AQEEDUN NA SUFAYE!!!

MU'AWUYA BN ABU SUFYAN

*BABU MAI ZAGIN MU'AWUYYA SAI KAFIRI FASIQI MUNAFUKI!!!*

```GA KADAN DAGA CIKIN TARIHINSHI DA
NASABARSHI DA KHALIFANCISA!!!
.
.
.
Nasaba Da Sarakutar Mu’awiya binu Abi
Sufyan(RA).

Shi ne Mu’awiya dan Abu Sufyan (sunansa
Sakhar) dan Harb dan Umayya.

   Ya fito daga
gidan Banu Umayya, dangin Sarkin Musulmi
Usmanu(RA). Mahaifinsa Abu Sufyan ya jagoranci
mushirikan Makka a cikin adawarsu ga
Musulunci da yaqoqansu ga Annabi(SAW).

Ya
musulunta shi da mahaifinsa bayan bude Makka
kuma ya halarci yaqin Hunain tare da Annabi
(SAW).

Ya kasance daga cikin marubutan
Annabi(SAW) kuma Manzo(SAW) ya auri ‘yar
uwarsa Ummu Habiba Ramla diyar Abu
Sufyan, Allah ya yarda da ita.

    Mu’awiya(RA) mutum ne da ya laqanci qulle-
qullen siyaa.

Umar binul
Khaddab ya nada shi a kan wani bangare na
qasar Sham kuma Usmanu binu Affan ya game
masa mulkin Sham baki daya. Mu’awiya ya ja
da Sarkin Musulmi Ali(RA) a lokacin da ya qi
ya yi mubaya’a sai har Ali ya zaqulo wadanda
suka kashe Usmanu daga cikin rundunarsa ya
hukunta su. A sakamakon haka, yaqin Siffain
ya auku tsakanin Ali da Mu’awiya. Bayan da
aka samu qiqi-qaqa a qarshen wannan yaqin,
Mu’awiya ya yi amfani da iya janhurunsa na
siyasa ya yi qarfi, a yayin da Ali ya yi rauni,
kuma rundunarsa ta wargaje a sakamakon
ficewar Khawarijawa daga cikinta. Ali(RA) ya
shagala da yaqar Khawarijawa, abinda ya
qara masa rauni, a lokacin da shi kuma
Mu’awiya ya qara qarfi da kama qasa a cikin
lamarinsa. Ana cikin haka ne Khawarijawa
suka shirya maqarqashiyar kashe Ali da
Mu’awiya, Allah ya yarda da su, wai domin su
hade kan Musulmi kuma su yi maganin fitina.
Amma Mu’awiya ya tsallake wannan
maqarqashiya da qaddarar Allah; shi kuwa sayyidina Ali(R.A)
da aka qaddara masa qarar kwana ya yi
shahada. Bayan rasuwar Sarkin Musulmi Ali
(RA), magoya bayansa sun yi mubaya’a ga
dansa Hassan(RA) wanda ya zama khalifa na
tsawon wata shida.
Hassan binu Ali(RA) ya yi tunanin ya kai
qarshen jayayya da Mu’awiya wacce ya gada
daga mahaifinsa. Don haka ya dauki matakin yin
sulhu da Mu’awiya kuma ya sakar masa lamarin shugabancin al’umma
domin tsai da zubar da jinin Musulmi a
junansu. Da wannan ne Mu’awiya ya zama
Sarkin Musulmi kuma dukkan bangarori suka
shiga qarqashin da’arsa, in banda
Khawarijawa wadanda suka ci gaba da yaqar
sa. Kuma da wannan sulhu ne aka kai
qarshen zamanin Khulafa’ur Rashidun kuma
aka fara zamanin khalifofin Banu Umayya.
Wannan ya faru a shekara ta 40 bayan hijira,
shekarar da akewa laqabi da Amal Jama’a,
watau shekarar hadin kai, saboda haduwar
al’umma a kan Mu’awiya(RA).
Mu’awiya binu Abi Sufyan ya yi shekara
ishirin yana gwamnan Sham, kuma ya shekara
ishirin yana khalifa. Ya rasu a shekara ta 60
bayan hijira, yana da shekaru saba’in da
takwas a duniya.
Sarkin Musulmi Mu’awiya ya auri Fakhitatu
diyar Qurza, ta haifa masa Abdurrahman da
Abdullahi. Haka nan, ya auri Maisun diyar
Badajal wacce ta haifa masa dansa Yazid
wanda ya gaje shi a matsayin khalifa. Mun
gabatar da bayani cewa gidan su Mu’awiya,
Banu Umayya, surukan Annabi(SAW) ne. Ya
aurar da diyansa mata uku ga ‘ya’yan wannan
gida. Su ne Zainab ya aurar da ita ga Abul
Aas binu Rabi da kuma Ruqayya da Ummu
Kulthum ya aurar da su ga Usmanu binu
Affan. Kamar yadda shi kuma ya auri ‘yar
uwar Mu’awiya, watau Ramla wacce akewa
alkunya da Ummu Habiba, Allah ya yarda da
su baki xaya.```

Copyright©
*ABU-SINAN*

SAKO ZUWA GA YAN TIJJANIYYA 001

*GAREKU YAN TIJJANIYYA, KU KARE ZANTUKANKU IDAN KUN KASANCE MASU GASKIYA*

*HUJJOJI NA HANKALI DA ZASU KORE QARYAR DA SHEIKH AHMADU TIJJANI (R.A) YA KWANTARA NA CEWA YA HADU DA MANZON ALLAH IDO DA IDO.*

_Fitowa na daya (001)_

```Farkon sabanin da aka fara samu a Musulunci tsakanin sahabbai ya Faru ne bayan rasuwar Manzon Allah s.a.w, a lokacin ne mutanen madina sukace ma mutanen Makkah (muhajirai) mu zamu Nada namu jagora, kuma Ku Nada naku. Haka akayi har tsawon kwana uku kafin a rufe manzon Allah s.a.w.
Tambaya; ya akayi manzon Allah s.a.w bai tashi ya kai karshen wannan cece-kuce da sahabbai keyi ba(ma'ana: yace wane ne Khalifa a baya na)?

Ya akayi manzon Allah s.a.w ya bar wannan al'amari na khalifanci mai girma ba tare da ya tashi yayi bayani ba???

Da ace manzon Allah s.a.w zaiyi magana da wani a farke bayan ya mutu, da sahabbanshi zaiyi magana dasu domin magance musu waccan jayayyar akan ace ya bayyana ga shehu tijjani. Bayan shi Tijjani sai da Manzon Allah s.a.w ya bar duniya da shekara dubu da Dari daya da hamsin(1150AH) ko makamancin haka sannan aka haifeshi. Toh ya akayi hakan ta kasance???

Yan Tijjaniyya muna bukatar amsar wannan tambayar!!!

Allah ka shiryar damu akan hanya madaidaiciya.

Copyright©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU-SINAN)
08064734911```

HUDUBAR JUMA'AH002

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*HUBUDAR JUMA'AH DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABI-HURAIRAH AREA II TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

Taken hudubar: *wajabcin neman Shawara a addinin Musulunci kashi na biyu(002)*

Mai gabatarwa: *_Sheikh Sani Liman (ABU-HURAIRAH) Tsafe._*

Shiga links dake kasa domin saukewa.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://kiwi6.com/file/ij1jswtjn6

Masu matsalar browsing zasu iya bi ta wannan Link
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://k003.kiwi6.com/hotlink/ij1jswtjn6/02h

```wannan itace cigaban hudubar da Shehin Malamin ya gabatar a satin da ya gabata, idan son samu ne ka sauraresu gaba daya domin amfanuwa.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi, Mu kuma Allah ya bamu ikon amfani da wannan hudubah.```

Copyright©
*_MASJID ABI HURAIRAH SOCIAL MEDIA TSAFE_*

HUDUBAR JUMA'AH001

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*HUBUDAR JUMA'AH DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABI-HURAIRAH AREA II TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

Taken hudubar: *wajabcin neman Shawara a addinin Musulunci*

Mai gabatarwa: *_Sheikh Sani Liman (ABU-HURAIRAH) Tsafe._*

Shiga links dake kasa domin saukewa.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://kiwi6.com/file/p4cumpwxef

Masu matsalar browsing zasu iya bi ta wannan Link
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://k003.kiwi6.com/hotlink/p4cumpwxef/h

```Akwai cigaban wannan hudubah a sati mai zuwa insha Allahu.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi, Mu kuma Allah ya bamu ikon amfani da wannan hudubah.

Copyright©
_Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU-SINAN)_```
atstsamawy@gmail.com
08064734911

ZUMUNTA A MUSULUNCI

🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

*_TATTARAWA:_*

*MALAM SANI LIMAN (ABU HURAIRAH) TSAFE*

_Fitowa Na biyu(002)_

```Bisimillahir-rahmanir-raheem, Alhamdulillah, bayan bayanin da ya gabata na ABUBUWAN DA WANNAN RUBUTU ya kunsa, yanzu zamu fada cikin bayanin Abu na farko.

MECECE ZUMUNTA???

  Ibn athir yana cewa zumunta tana nufin taimakawa yan uwa na bangaren dangantaka da sarakuta da kula da halayen SU koda kuwa suna zaune a wurare masu nisa koda kuma suna munana maka. A daya bangaren kuma, yanke zumunta yana nufin kishiyar abubuwan da aka ambata a baya.

DA WANE ABU AKE SADAR DA ZUMUNTA???

Ana sadar da zumunta da al'amura masu yawa kamar; Ziyartarsu, bibiyar halayensu, tambaya game dasu, aika masu da kyaututtuka da kuma saukar da kowannensu a matsayin da ya dace dashi(wato su yan uwan da ya kamata a sadar da zumunta garesu), sannan kuma ana Sadar da zumunta da bada sadaka ga fakirai daga cikin su da tausasama mawadatan su da girmama manyansu da kuma tausayama kananan su da masu rauninsu da yawan tambayar halin da suke ciki, ziyartar su da kanka ko ka aika wasika ko kayi amfani da wayar salula.

    Mafi girman abunda ake sadar da zumunta dashi shine; mutum yayi kwadayin kiransu((yan uwansa) zuwa ga shiriya ya umurcesu da aiki mai kyau ya kuma hana su aikata miyagun ayyuka.

   Haka nan zumunta bata da wani kayyadadden lokaci da aka kayyade don sadar da ita. Duk abunda al'ada ingantatta ta tabbatar a matsayin Sada zumunta, ana daukarshi a matsayin haka. Haka kuma duk abunda al'ada ingantatta ta tabbatar a matsayin yanke zumunta to ana daukarshi a matsayin haka.

   Zumunta tana bambanta gwargwadon kusanci da matsayi na wadanda ake sadar da zumuntar zuwa garesu, zumuncin da yake tsakanin uba da dansa ya sha bam-ban da Dan uwa na nesa.

   Bugu da kari, zumunta tana banbanta gwargwadon halayen da su wadanda za'a sadarmawa suke ciki, kamar sadar da zumunta ga marar lafiya da mabukaci ta bambanta da sadarwa ga waninsu. Haka kuma sadarwa ga babba ta banbanta da ta karami

    Haka nan sadar da zumunta yana banbanta ta fuskar bagire, Wanda yake zaune a cikin gari ya banbanta da Wanda yake zaune a wani gari wajen ziyartar shi da tambayar halinda yake ciki, da yimasa sallama ko aika mashi da sakonni.

Zamu tsaya a nan, sai wani lokaci idan Allah ya kaimu insha Allahu.

Allah ya bamu ikon sadar da zumunta gwargwadon iko Amiin.

A gaba zamuyi bayani akan FALALAR SADAR DA ZUMUNTA insha Allahu.

Allah yayi mana jagoranci.

Copyright©
MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA```
+2348064734911

BIDI'AR SHAFAR FUSKA BAYAN KAMMALA ADDU'AH


BIDI'AR SHAFAR FUSKA BAYAN KAMMALA ADDU'A🙏
Ibn Rushud yace: an tambayi imamu malik akan mutumin da yake shafar fuska da tafukansa yayin kammala addu'a bayan ya shinfida tafukan kafin hakan?sai imamu Malik yayi inkarin haka,yace bansan wannan ba. nace (Ibn Rushud) Malik (R)yayi inkarin shafar fuska da tafukan hannu bayan addu'a domin yana ganin yin haka badi'a ne, domin babu wani asar daga manzon Allah yake nuna halaccin hakan kuma ra'yi baida mashiga a cikin
📚(albayan wattahsil 49/18)
Imam Abu Daud yace:naji an tambayi imamu Ahmad akan mutumin da ya ke shafar fuskar sa da hannunsa bayan ya kammala wuturi? Sai ya ce "bantaba jin wannan ba" a wani lokacin ma cewa yayi "bantaba jin wani Abu game da shiba". Abu Daud yace banga imamu Ahmad yana aikata hakan ba(ma'ana:babu wani Abu da ya tabbata daga manzaon Allah akan yin haka, kuma babu wani daya daga cikin magabata da ya aikata  haka.
📚(masa'ilah 102).

SIFFOFIN MACE TA GARI

📜📜📜
SIFFOFIN MACE TAGARI📜📜📜
Shaikhul Islam Ibn Taimiyya yace"mace ta gari tana kasancewa tare da miji nagari tsawon shekaru masu yawa.
Ita ce jindadin sa Wanda manzon Allah(saw) ya fada a cikin hadithi yace"ita duniya wani Dan jindadi/amfani ne kuma mafi alkhairin amafani/jindadin ta ita ce mace mumina wadda idan ka kalle ta sai ta  burgeka, idan kabata  umarni sai ta yi maka da'a, idan kafita kabarta zata  kiyaye ka ga kanta(ba zata ci amarnarka ba).

Itace wadda manzon Allah yayi umarni da ita a cikin  zancen sa lokacin da muhajiruna suka tambaye shi:wace dukiya ya kamata murika? Sai yace: "harshe mai yawan ambaton Allah, da zuciya mai yawan godiya, da MACE TAGARI mai taimakon dayanku bisa imani"
(📚Timidhi ya Ruwaito shi saga Salim ibn Abilja'ad daga  Sauban).

Ita ce wadda kauna/soyayya da tausayi yake tabbata da ita kamar yanda Allah (SWT) ya fada a cikin Alqr'an, radadin rabuwa da ita yafi tsanani sama da na mutuwa,wani lakacin ma yafi tsanani sama da kariyar arziki, yafi tsanani sama da barin wurin zama(gida) musamman idan akwai alaqa a tsakanin su (zumunta) ko kuma suna da  'ya 'ya a tsakanin su wadan da rabuwar zata jefasu cikin yanayi na kunci da  tozarta da kuma  gurbacewar dabi'un  su"
(📚majmu'ul fatawa 35/299)

🕌🕌COMMITTEE FOR SOCIAL MEDIA MASJID ABU HURAIRA TSAFE ZAMFARA STATE (07039140450)

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 007

*GORON SALLAH*1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na takwas(008)_

``` √ AKIDATUL BADA’A.

Akidatul Bada’a rukuni ce daga cikin rukunnan
addinin Shi’a, akidatul bada’a tana nufin Allah
yana yin kuskure a cikin ayyukansa da
maganganunsa. Sai daga baya ya gano kuskure
ne, sai ya canza. Sun sanya ta a cikin rukunnan
addinin su domin su watsar da nassosa na
shari’ar musulunci da nuna duk abunda musulmi
ya yarda da shi to Allah ya canzashi bayan ya
gano kuskurene. A takaice dai a wajen su Allah
yana jahiltar wasu ayyuka da magan-ganunsa,
wanna akidar tana daga cikin mafi munin akidar
su domin suna nuna tozarci da kasawa da jahilci
ga Allah wadanda duk sunkoru ga reshi (SWT).
Shi kuma Mahadin sunnah, ingantacciyar ruwaya
ta zo game da shi cewa yana daga cikin tsatson
Hassan bin Aliyu
(R.A).
Daga karshe yaku bayin Allah, wannan yar
takaitattar nasiha ce da tayi bayani akan micece
Shi’a da miyagun akidunta saboda haka ne
malamai sun yi hukunci cewa ‘Yan Shi’a kafirai
ne, kuma zindikai ne.
Imamu Malik yace “Wanda yake zagin sahabban
Manzon Allah ba shi da rabon muslunci” (Wato
ba musulmi bane)
Imamu Ahmad bin Hambal yana cewa “ba’a
auren mata ‘Yan Shi’a, kuma ba’a cin yankansu
domin sunyi ridda sun bar musulunci. Kaga anan
Imamu Ahmad yana nufin idan har baya halatta a
auri diyan su mata to min babi aula kenan mu
musulmai baya halatta mu basu aure, duk da
cewa addinin muslunci ya halatta auren
ahlulkitabi, wannan yana nuna munin Shi’a sama
da Yahudu da Nasara.
Manufar wannan bayanin bayana nuna karanta
darajar Aliyu ko ahlulbaiti bane, lallai
ahlussunnah suna son Aliyu da ahlulbaiti da
sauran sahabbai. Shi’a ita ce kungiya mafi hadari
ga addinin muslunci, domin suna kashe musulmai
suna kyale masu bautar gumaka, suna zagin
Sahabbai amma a hakika Annabi suke zagi
Imamu San’ani yana cewa “al-ummar musulmi ta
hadu akan kafircin Shi’a Imamiyya
Sheikh bin Baz yace “Shi’a Rafida da kumaini
suna kan shirka babba
Sheikh Albani yace “Lallai abun da kumaini yake
kira akan shi na cewa sahabbai sun juyar da
Qur’ani wannan kafirci ne babu shakka
Don haka babu wadanda sukafi ahlussunnah son
ahlulbaiti da sauran sahabbai da magabata gaba
daya
Kamar yadda Imamu Shafii ya kawo a cikin
diwaninsa
Ya ku ahlulbait Rasulullah, lallai Allah ya farlanta
sonku kamar yadda ya saukar a cikin Qur’anin sa
Ya isheku girman alfahari duk wanda yayi salati
ga Manzon Allah bai sanya kuba to bashi da
salati.

DA WANNAN NE MUKA KAWO KARSHEN
WANNAN RUBUTU, MUNA GODIYA GA MASU
BIBIYARMU A KODA YAUSHE, ALLAH YA
AMFANAR DAMU DA ABUNDA MUKA KARANTA,
YA KARA TSAREMU DAGA MIYAGUN AKEEDU.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 006

*GORON SALLAH* 1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na shida(006)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA IMAMA.

Imama a wajen ‘Yan Shi’a tana dai-dai da
Annabawa a wajen musulmi, don haka ma suka
ce imamansu (12) ma’asumaine (Basu yin laifi)
“Yan Shi’a sun kudurce cewa lallai Imama baza
ta kasan ce ga kowaba sai ga Aliyu da diyan sa
(12) kuma sun sanya wannan a cikin rukunnan
imani suka ce duk wanda yayi kudurin Imama ba
ga Aliyu ko diyansa ba to ya kafirta kafirci mai
girma.
Hakika malaman sunnah sun hadu akan cewa
wadanda suka can-canta da halifanci bayan
Manzon Allah gasu kamar yanda suke a jere: -
Abubakar, Umar, Usman, sannan Aliyu, kuma
haka suke a wajen falala.
Ma’ana: Abubakar shine mafifici, sannan Umar,
sannan Usman, sannan Aliyu. Malaman suka ce
duk wanda yace Aliyu yafi Abubakar da Umar
falala to shi dan bidi’a ne.

√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA ILIMIN FIQIHU.
‘Yan Shi’a sun sabama ahlussunah dangane da
ilimin Fiqihu saboda basu karbar hadisai
ingantattu da sunnoni da aka ruwaito a cikin
littafan sunnah.
‘Yan Shi’a mabukata ne ta bangaren fahimtar
sunnah.
Sun kir-kiri bidi’o’i a cikin kiran sallah kamar
haka:
Suna karawa da Ash-hadu anna Aliyu
Waliyuullah, Madadin Ash-hadu anna
Muhammadarrasulullah
Sun kir-kiri bidi’o’i ta bangaren sallah kamar
haka:
Suna hada sallah ba tare da wani uzuriba
Basu yarda da sallar juma’a ba ko da a zahiri
anga sunayi.
Sun haramta cin zomo
Sun halatta auren mutu’a
Duk wadannan haramunne ga Ijma’in malamai.
ALLAH YA KARA TABBATAR DAMU AKAN
HANYA MADAIDAICIYA.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 005

*GORON SALLAH*1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na biyar(005)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA TAUHIDI.

‘Yan Shi’a mushrikai ne ta bangaren tauhidi
domin suna rokon Aliyu, da Hussaini da Zainab
da Fatima, dare da rana, lokacin tsanani da
jindadi. A wurin ‘Yan Shi’a ziyartar kabarin
Hussaini yana daga cikin manya-manyan
sabubban samun waraka daga rashin lafiya, da
wadatar arziki da samun taimako da biyan
bukata.
Babban malamin Shi’ar nan Jafar Ibn Muhammad
Kaulawaihi ya kawo a cikin littafinsa mai suna
“Kamilizziyarat” wato kammalallar ziyara
Babin da ke Magana akan ziyarar Hussaini kamar
ya ziyarci Allah a alarshin sa
Babin da ke Magana akan wanda ya ziyarci
Hussaini tana kore dukkan bakin ciki
Babin da ke Magana akan ziyartar Hussaini tana
dai-dai da aikin Hajji da Umra
‘Yan Shi’a sun kudurce cewa lallai ziyartar
kabarin Hussaini yafi tsayiwur Arfa falala kuma
lallai Allah yana kallon wadanda suka ziyarci
Hussaini kafin ya kalli wadanda suka tsaya a
Arfa. Haka nan kuma ‘Yan Shi’a sun kudurce
lallai limaman su sha biyu (12) daga cikin diyan
Aliyu ma’asumai ne kuma sunfi Annabawa da
Mala’iku falala, kuma basu mutuwa, kuma sun
san gaibu kuma su ke kula da halittun Allah gaba
daya.
Yazo acikin littafin su “Alkafi”
babi da ke Magana akan lallai limamai (12)
hasken Allah ne
Babi da ke Magana akan lallai limamai (12) sun
san abun daya kasance da abun da zai kasance
nan gaba, babu wani abu da ke boyuwa a kan su
Babban mawakin nan na Shi’a Aliyu Sulaiman
Almazidi Allabanani (Libenon) ya fadi a cikin
wakar sa yayin da ya ke yabon Aliyu
Baban Hassan kaine ainihin abun bauta, kuma
kaine ikon Allah baki daya
Ilimin ka ya kewaye dukkan gaibi, ko akwai wani
abu da zai boye maka?
Baban Hassan kaine mijin Batula, kuma kaine
abun bauta kuma kaine ma Manzon Allah
Kaine cikakken wata, kuma kaine ranar hankulla
mamallakin ubangiji kaine mai mulki
Zuwa gareka makomar komai take, kuma kaine
masanin abunda ke cikin zukata
Kaine mai tayar da wadanda ke cikin kabari,
kuma nassi ya nuna kai ne mai hukunci a ranar
kiyama
Kai ne mai-ji kuma mai gani, kai ne mai iko akan
dukkan komai
Badon kai ba da tauraro baiyi tafiya ba badon kai
ba da falaki bai zagayaba
Kai ne masanin dukkan sarari, kai ne magana da
Ahlulrakim
Ba don kai ba da Musa bai zama kalimi ba, tsarki
ya tabbata gareka da kai ne yayi Magana
Badon kai ba da Annabawa basu zamoba
Badon kai ba da Manzanni basu zamoba
Badon kai ba da alkalami bai rubuta a alloba
Badon kai ba da talikai basu zamoba, dukkan su
bayinka ne kuma mallakar kane.
Tambaya ita ce miya rage ma Allah idan har
Aliyu ya zama haka? Allah ya nisanta Aliyu ya
ksanace yana da siffa ta rububiyya. Wannan ita
ce tsantsar akidar Kiristoci ga Annabi Isah da
suka ce masa Allah, kaga wannan yayi dai-dai da
akidar Shi’a ga Aliyu (R).
ALLAH YA TABBATAR DAMU AKAN SUNNAH.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 004

*GORON SALLAH*1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_* *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na Hudu(004)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA SUNNAH.
‘Yan Shi’a sune mafi jahiltar Hadisai da Sunnoni
da ruwayoyi daga Manzon Allah. Ba zaka samu a
cikin zancan su ba cewa daga Manzon Allah,
abun da zakaji kawai shine. Aliyu yace, ko Jafar
yace ko Hussaini yace mafi yawan ruwayoyin su
karya ce suka kirkira suka jingina ga Aliyu da
Ahlulbait musamman Ja’afarus-sadiq
‘Yan Shi’a basu yarda da littafin Bukhari, da
Muslim da sauran littafan Hadisan nan guda hudu
ba, suna cewa *kirkiren karya ne, kuma
tatsunniya ce a cikin su.
Suna da wani littafi wanda a wajen su yayi dai-
dai da bukhari da Muslim da sauran littafan
hadisi mai suna “Alkafi” wanda malamin su
Kulaini ya rubuta cike yake da karai-rayi da
tatsuniyoyi.

√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA SAHABBAI.
Sahabbai sune mafifitan halitta bayan Manzon
Allah (SAW). Allah (SWT) ya fada a cikin
littafinsa mai tsarki yana mai yabon su
“Muhammad Manzon Allah ne, kuma wadannan
da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai,
masu rahama ne a tsakanin su, kana ganin su
suna masu ruku’i masu sujada, suna neman
falala daga ubangijin su da yardarsa, alamarsu
tana a cikin fuskokin su daga kufar sujuda.
Wannan shine siffar su a cikin Attaura. Kuma
siffarsu a cikin Injila, itace kamar tsiron shuka
wanda ya fitar da reshen sa, sa’an nan ya
karfafa shi, yayi kauri, sa’annan ya dai-daita a
kan kafafunsa, yana bayar da sha’awa ga masu
shukar domin (Allah) ya fusatar da Kafirai game
da su, kuma Allah yayi alkawari ga wadanda
sukayi imani, kuma suka aikata ayyukan kwarai
daga cikin su da gafara da lada mai girma
(Suratul Fat’h – 29)
Duk wanda ya soki Sahabban Manzon Allah
hakika ya soki Manzon Allah domin zagin
Sahabbai gaba dayansu kafirci ne kuma ridda ne.
Kulaini ya fada a cikin littafin sa “Alkafi” cewa
“Lallai sahabbai gaba dayansu sunyi ridda bayan
rasuwar Manzon Allah in banda mutum ukku.
‘Yan Shi’a sunayin addu’a ta la’anci zuwaga
sahabban Manzon Allah a cikin salla, kamar
yanda Majiisi ya ambata a cikin littafinsa “Al-
anwar”. Suna cewa ‘Allah ka la’anci gumakan
Quraishawa guda biyu da makaryatansu guda
biyu da diyansu guda biyu’.
Gumakan sune Abubakar da Umar
Makaryatan sune Abubakar da Umar
Diyansu kuma sune Aisha da Hafsat
Kumaini (Batacce) ya fada a cikin littafinsa
“Hukumatil Islamiyya” cewa: Lallai Abubakar da
Umar fasikaine kuma wawaye ne.
Yan Shi’a suna da’awar cewa Usman munafukine,
Abubakar fasikine, Aisha mazinaciyace da dai
sauran miyagun maganganu da suka fada ga
sahabbai wanda da suna nan cike da littafan su.
ALLAH YA TABBATAR DAMU AKAN
INGANTACCIYAR AKEEDA.
ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 003

*GORON SALLAH*

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_* *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na uku(003)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA MUSULMI DA DAULAR MUSULUNCI.

      Yana daga cikin akidar Shi’a shine tsananin adawa ga musulunci da daulolin musulunci tun daga zamanin halifofi har zuwa wannan zamanin. Ga kadan daga cikin misalan da suka faru: -
Abu Lu’uluatal Majusi (Mai bautar wuta) shi ya kashe Umar dan Khattab
Wanda ya kashe Usman bin Affan daya ne daga cikin mabiyan Abdullahi bin Saba Alyahudi
Ashe ba Ibn Alkami da Dusii bane suka shigo da tattara a bagdad, suka kashe miliyoyin musulmai ba?
Ashe basu bane a (2003) suka shigo da mayakan America a Bagdad suka kashe dubban mutane ba?
Ashe ba ‘Yan Shi’a bane a (1885) suka hada kai da Yahudawa suka kashe daruruwan Falasdinawa?
Bugu da kari, ‘Yan Shi’a ne suka kai hari a Makka suka kashe Alhazai, suka sace Hajarul Aswad ya cigaba da zama a hannun su tsawon shekara (20). ‘Yan Shi’a Fadimiyya ne suka kafa daula sukayi mulkin Misra da Yammacin Africa suka kashe malaman Fiqihu wadanda suka hana zagin Abubakar da Umar
Wadannan sune kadan daga cikin misalai dake nuna irin yanda Shi’a ke kiyayya ga daulolin musulunci da musulmai.

√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA QUR’ANI.

       ‘Yan Shi’a sun qudurce cewa lallai Qur’ani karkatacce ne, suka ce Abubakar da Umar ne suka juyar da shi, suka shafe wasu surori da wasu ayoyi da ke nuna Aliyu shine Halifa bayan rasuwar manzon Allah. Suka ce Abubakar da Umar sun shafe Suratul Wilaya, ma’ana surar da ta nuna Aliyu ne Halifa bayan Manzon Allah, ga yan da surar take a wajen ‘Yan Shi’a
‘Yaku wadanda sukayi imani da Annabi da waliyyi (Aliyu) wadannan da muka aiko domin su shiryar da ku zuwa ga hanya madai-daiciya’
‘Yan Shi’a sun ce Abubakar da Umar sun juyar da Suratul Sharhi daga asalin ta wai asalinta shine:
‘Ashe bamu muka bude kirjin ka ba? Muka sanya Aliyu ya zama surukinka?
A shekara ta (1877) wani babban malamin Shi’a wanda ke zaune a garin Najib mai suna Alhaji Maimizan Hassan ibn Muhammad Takiyuddaini Addabaristi ya wallafa littafi mai suna:
“Rarrabe zance domin bayani akan juyar da littafin Ubangijin Halittu”. A cikin littafin yayi bayanin yanda Abubakar da Umar suka juyar da Qur’ani!
To mi ya rage ga musulmi? Idan har alqur’ani ya kasance anjuyar dashi a wajen wadan can bataccin? (Yan Shi’a) Ibn Hazm yayi jayayya da Kiristoci akan juyar da Bible sai suke ce shima Qur’ani ai anjuyar da shi kamar yadda Shi’a tace. Sai Ibn Hazm ya maida masu da raddi cewa lallai Shi’a ba musulunci bane a wurin mu ballantana har a kafa hujja da maganar su.

ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.

ALLAH YA SHIRYAR DAMU HANYA MADAIDAICIYA.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 002

*GORON SALLAH 1438/2017*

*_SHI’AH DA AKEEDOJINTA_*


_Wallafar:_  *_Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)_*

*Fitowa Na biyu(00)2*



“`√ ASALIN SHI’ANCI.

     Shi’anci ya bayyana ne a lokacin
halifancin Usman bin Affan ta hanyar
Abdullahi bn Saba’a alyahudi alyamani
mai tsananin kiyayya da musulunci.
Hakika ya watsa a tsakanin musulmai
cewa Aliyu shine yafi cancanta da
halifanci kuma Abubakar da Umar zalunci
sukayi domin Aliyu ne Manzon Allah yayi
ma wasiyya kamar yanda annabi Musa
yayi ga Yusha’u bin Nun. Wannan
mummunar Magana ta watsu a tsakanin
sashen wasu jahilai, har suka wuce wuri
game da Aliyu har suka qudurce cewa
Aliyu Allah ne.
Malaman tarihi sun ambata cewa Aliyu ya
dinga kona su da wuta
Aliyu ya fada a cikin diwanin sa na
wakoki yace”
“Yayin da naga al-amarin al-amarine mai
muni sai na hura wuta na kira yarana”
Ma’ana: ya hura wuta ya kira yaransa ya
umurcesu dasu dinga sanya yan Shi’a a
ciki sai suka ce ai babu mai kona mutane
da wuta sai ubangijin wuta. Malamai sun
fada cewa daga cikin sabubban bayyanar
shi’anci shine keta da kiyayya da
kabilanci da farisawa (Mutanen Iran)
masu bautar wuta sukayi akan Larabawa
da Abubakar da Umar saboda sun karya
daular Farisawa
Yana daga cikin abun daya kamata mu
sani cewa Abu lu’uluata Majusin nan duk
da cewa ba musulmi bane bautar wuta
ya keyi mutanen Iran sun samar da wata
hubbare a kasar Iran a garin Kashan suna
yi masa dawafi domin girmamawa zuwa
gareshi akan abun da yayi masu na
kashe Umar. Wannan yana nunawa karara
cewa shi’anci kabilanci ne tsantsa ba
musulunci ba.
Shi’anci ya cigaba da yaduwa a lokacin
halifancin Aliyu bayan kashe Hussaini (R)
shi’anci bai gusheba yana girmama har
ya zama wata mazhaba da miliyoyan
mutane suke bi a matsayin addini, wajibi
ne muyi hattara da yaduwar shi’anci a
cikin duniya.


√ AKIDOJIN SHI’A.

Shi’a tana da akidu masu yawa zamu fadi
kadan daga cikin su domin takaitawa

1. KAMANCECENIYAR SHI’A DA
YAHUDAWA DA KIRISTOCI.

Akidar shi’a tayi kama da ta yahudawa da
kiristoci domin duk musibar da take a
cikin Shi’anci itace musibar da take a
cikin Yahudanci.

* YAHUDAWA; sun ce baza’ayi jihadi
domin daukaka kalmar Allah ba har sai
Dujal ya bayyana.

* YAN SHI’AH; su ma ‘Yan Shi’a su na
cewa baza’ayi jihadi domin daukaka
kalmar Allah ba har sai mahadi ya fito Ma’ana: a wajen yan Shi’a duk jihadin da
Manzon Allah yayi da Sahabbansa har
zuwa Sheik Usman bin Fodiyo duk
wahalar banza ce kuma shirme ne.

* YAHUDAWA;  suna jinkirta sallah har
zuwa fitowar taurari.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a suna
jinkirta sallar Magariba har zuwa lokacin
sallar Isha’i.

* YAHUDAWA; suna karkacewa daga
alqibla suma.

* YAN SHI’AH; ‘Yan Shi’a suna karkata
kansu daga alqibla.

* YAHUDAWA; sun juyar da Attaura.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a sun juyar
da Alqur’ani.

* YAHUDAWA; sun haramtawa kansu cin
kifi.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a sun
haramtawa kansu cin zomo.

* YAHUDAWA; basu yin shafa akan huffi.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a basu yin
shafa akan huffi.

*YAHUDAWA; suna kiyayya da Mala’ika
Jibril.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a suna
kiyayya da Mala’ika Jibril suka ce yayi
kuskuren kawo wahayi maimakon ya kai
shi ga Aliyu sai ya kai shi ga Annabi
Muhammad kaga anan suna tuhumar
manzancin Manzon Allah (SAW).

*KIRISTOCI; suna halatta auren mata ba
tare da sadaki ba.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a sunayin
auren mutu’a.

Yahudawa da Kiristoci sunfi ‘Yan Shi’a da
dabi’o’i guda biyu.

* YAHUDAWA;  An tambayi yahudawa
suwa nene mafifita a cikin addinin ku?
Suka amsa da cewa sahabban Annabi
Musa.

* KIRISTOCI; suma kiristoci da aka
tambayesu suwaye mafifita a cikin
addinin ku? Sun amsa da cewa sahabban
Annabi Isah.

* YAN SHI’AH; Da aka tambayi ‘Yan Shi’a
suwa nene mafi sharri a cikin addinin ku?
sai suka amsa da cewa Sahabban Annabi
Muhammad(S.A.W).

An umurce su suyima sahabban Annabi
Istiqfari amma sai suka zage su.

Wannan yana nuna Yahudawa da kiristoci sunfi
‘Yan Shi’a girmama Annabawansu da
Sahabban su, kuma yana nuna irin yanda Shi’a ke nuna kiyayya ga Sahabban Annabi karara.

Wannan yana nuna cewa akidar Shi’a dai-
dai take da ta Yahudawa da Kiristoci.

ALLAH YA KARA SHIRYAR DAMU AKAN
HANYA MADAIDAICIYA, WADANDA KE
CIKIN WANCAN BATA KUMA ALLAH YA
SHIRYESU IDAN MASU SHIYUWA NE.

ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.“`

HAKKIN MALLAKA©
*_Hashim Sirajo Uba Tsamiya
(ABU~SINÃN)_*
+2348064734911

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 001


*SHI’AH DA AKEEDOJINTA*

WALLAFAR;  *_Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)_*

*GABATARWA*

“`Godiya ta tabbata ga Allah, muna
godemasa, muna neman taimakonsa,
muna neman gafararsa, muna neman
tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da
munanan ayyukan mu, wanda Allah ya
shiryar babu mai batar dashi, wanda
kuma Allah ya batar babu mai shiryar da
shi.
Na shaida babu abun bauta na gaskiya
sai Allah, shi kadai yake baya da abokin
tarayya, kuma na shaida Annabi
Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa
ne
Bayan haka, mafi gaskiyar zance shine
littafin Allah, fiyayyar shiriya ita ce
shiriyar Manzon Allah, mafi sharrin
alamurra sune wadan da aka kir-kiro a
cikin addini, dukkan abunda aka kirkiro a
cikin addini bidi’a ce dukkan bidi’a bata
ce, dukkan bata makomarta ita ce wuta.
Dalilin rubuta wannan ‘Yar takaitacciyar
nasiha shine na gabatar da huduba a
Masallacin Juma’a na Abu Huraira dake
Area 2 a Garin Tsafe mai taken Shi’a da
Hadarorinta, sakamakon haka ne wasu
‘yan uwa suka nemi da in fassara ta
zuwa harshen Hausa domin amfanin yan
uwa musulmi
Ina rokon Allah (SWT) ya azurta ni da
ikhlasi a cikin wannan aiki, kuma ya
amfanar dashi ga yan uwa musulmi.
√ MICECE SHI’A???
Shi’a daya ce daga cikin kungiyoyin bata,
da ake kira da sunaye daban-daban, ana
cemata Rafida, ko Ja’afariyya, ko Isna
Ashariyya.
√ SUWAYE ‘YAN SHI’A???
‘Yan Shi’a sune masu kokarin jingina
kansu zuwa ga Aliyu bin Abi Dalib, suna
kudurce cewa, Halifanci da Imama suna
tabbata ne kadai ga Aliyu bin Abu Dalib
bayan Manzon Allah, basu yarda da
Halifancin Abubakar da Umar da Usman
ba. Cibiyoyin su ta duniya a yanzu tana
kasar Iran da Lebenon, da Iraki da Syria
da Afganistan, tana da rassa a wasu
kasashen Africa musamman Nigeria inda
Alzakzaki ke jagorancin ta.


Zamu cigaba insha Allahu.


HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya
(ABU SINAN)“`
+2348064734911