Monday, 22 May 2017

AZUMIN WATAN RAMADHANA

🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉
*AZUMIN WATAN RAMADANA*
🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇

*بسم الله الرحمن الرحيم*

_Rubutawa;_ *HASHIM SURAJO UBA(ABU SINÃN)*

```ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU.

  Godiya ta tabbata ga Allah s.w.t shi kadai Wanda yayi mana umurni da azumtar ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada, Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da ibadar azumi da sauran ibadoji.

Bayan haka;

FALALAR WATAN RAMADANA DA AZUMI A CIKIN WATAN.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan ramadana ya shigo, ana bude kofofin sama, ana kulle kofofin jahannama, ana daure shaidanu.
A wani hadisin kuwa manzon Allah s.a.w cewa yayi" Dukkan wani aiki da dan Adam zaiyi, ana lunka aikin da lada goma irinsa, idan a ramadana ne, ana lunkashi zuwa lunki (700), sai Allah mai girma da daukaka yace ;  banda azumi, domin azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa Wanda yayi shi, yabar matarshi da abubuwan da yakeso, da abinci, da abin sha saboda ni, mai azumi Nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki (shan ruwa) da farin ciki lokacin haduwarshi da Allah, yamin/warin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

ABUBUWAN DA SUKA WAJABA GAREKA A RAMADANA

Ya dan uwa

Kasani cewa Allah ya wajabta mana azumi domin mu bauta masa dashi, sannan kuma ya kasance cewa azuminka ya zamto karbabbe mai amfani.
Dole ne ka kiyaye wadannan abubuwan da zasu zo domin samun cikakkar lada;

1- kiyaye sallah; Da yawa daga cikin masu azumi suna wasa da sallah, bayan kuwa cewa tana daga cikin gimshikan addini, barinta kuma yana kai mutum ga kafurci.

2- Dole ka kasance mai kyawawan dabi'u; Dole ne mu tsoraci kafurci da zagin addini, da aikata muna nan dabi'u a cikin mutane, kafirci yana fitar da musulmi daga addini.

3- Dole ne mu kiyaye halshenmu da sukar juna.
 
Manzon Allah s.a.w yana cewa; "idan dayanku yana azumi, to kada ya fadi maganganun da basu dace ba, idan wani ya zageka ko ya nemi yayi fada da kai, sai kace mashi ni azumi Nike, ni azumi Nike.

4- Ka nisanci zuwa wurin da ake aikata barna! Ko kallon fina-finai na banza, domin hakan zai kai ga bata azuminka.

5- Ka yawaita sadaka ga makusantanka da mabukata, da ziyartar yan uwanka.

6- Ka yawaita zikiri da karatun Qur'ani da saurararshi, da bibiyar ma'anoninsa, da aiki da karantar warshi, sannan da zuwa masallatai domin daukar darussa masu amfani, kamar sauraran tafsirai, yin i'itikafi a masallaci idan goman karshe na ramadana suka kama.

7- karanta takardu akan azumi, domin sanin hukunce- hukuncen da suka shafi azumi, ta yarda zakasan cewa cin abinci ko abin sha da mantuwa baya karya azumi, kasan cewa ita janaba wacce ta sameka da daddare bata hana ka daukar azumi da sauransu.

LADUBBAN DA SUKA SHAFI AZUMI.

1- kiyaye halshe; Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda bai bar zancen karya ba, da aiki da zancen karya, Allah baya da bukatar barin cinsa ko shansa.

2- BUDA BAKI DA SAHUR DA ADDU'AH.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan dayanku zaiyi buda baki, to ya fara da dabino domin akwai albarka a ciki, idan bai samu dabino ba toh sai yayi da ruwa, domin suna tsalkakewa.
Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi buda baki yana fadar;
ذهب الظمأ، وابتلت العروق، وثبت الأجر، إن شاء الله.

Ma'ana: "YUNWA TA TAFI, GABOBI SUN DAI DAI TA, LADA TA TABBATA DA YARDAR ALLAH".
Manzon Allah s.a.w yace; "mutane baza su gushe suna samun alkhairi ba matukar suna gaggauta buda baki.

Anan dole mu gujewa muna nan akeedun shi'ah wadanda basa shan ruwa sai duhu ya shigo sosai, suna kafa hujja da ayar Qur'ani dake cikin suratul bakara, inda Allah s.w.t yake cewa; "...sannan Ku cika azumi zuwa dare. Wanman magana malamai sunyi bayanin me ake nufi tun da dadewa, mai Neman Karin bayani ya duba tafsirin "Aisarat-tafaseer, na jabir jaza'iry."

Manzon Allah s.a.w yace"kuyi sahur, domin a cikin yin sahur akwai albarka."

Manzon Allah s.a.w yace"Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da an rage komai daga ciki ba.

3-  DAGA CIKIN FA'IDOJIN AZUMI

   Duk Wanda yayi azumin ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbansa.

Duk Wanda yayi tsayuwar ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.(ma'ana: tsayuwar tarawihi da kiyamul-laili.)

4- WADANDA AKA YIWA RANGWAMEN AZUMI.

   *Marar lafiya da matafiyi, zasu ranka saboda fadar Allah s.w.t cewa;"Wanda ya kasance a cikinku marar lafiya ko akan hanyar tafiya, zai ranka azumin a kwanakin sauran watanni."
Amma marar lafiya Wanda ba'asa ran warkewa a kusa, toh sai ya rinka ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mai haila, da jinin haihuwa zasu aje azumi, saboda fadar ummuna Aisha R.A; "mun kasance ana umurtanmu da ranka azumi, amma ba'a umurtanmu da ranka sallah.[Bukhari da Muslim].

* Dattijo da dattijiya, wadanda sun tsufa sosai basa iya daukar azumi toh zasu ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mace mai ciki da mai shayarwa idan sunji tsoron rayukansu, toh zasu aje azumi sannan su ranka kawai, amma idan suna jin tsoron yayansu ne kawai, toh zasu ranka kuma su ciyar.

5- ABUBUWAN DAKE BATA AZUMI.

Abubuwan dake bata azumi sun kasu gida biyu:
Na farko; Abunda ke bata azumi Wanda ke wajabta rankawa kawai;

* Cin abinci ko abinsha da gangan.

* Yin amai da gan gan, saboda fadar annabi Muhammad s.a.w cewa: " Duk Wanda yayi amai, toh zai ranka azumi.[Hakim ya ruwaito]

* Mace mai haila da mai haihuwa, koda sauran mintuna kadan ayi buda baki tazo musu, toh zasu ranka azumin.

* Istimna'i(masturbation) wasa da al'aura da hannunka har maniyyi ya fito shima yana bata azumi kuma sai ka ranka.

Abu na biyu dake bata azumi kuma yake wajabta ranko da kaffara shine JIMA'I, akan maganar malamai kaffarar shine yanta baiwa ko azumin kwana sittin(60) a Jere.

6- ABUBUWAN DA BASU BATA AZUMI

* Cin abinci ko abinsha da mantuwa, ko da kuskure ko da tilasci! Babu ranko kuma babu kaffara, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa"Wanda ya manta yana azumi ya ci ko ya sha toh ya cika azuminsa, Allah ne ya ciyar dashi kuma ya shayar dashi.[Bukhari da Muslim]

* Amai ba dagan gan ba.

* Yin aswaki a kowane lokaci ko brush da sauransu.

* Dandana abinci da sharadin kada ka bari ya wuce maka.

* Sumbantar matarka, da sharadin kada akai ga aikata jima'i. Saboda manzon Allah s.a.w ya kasance yana sumbantar Aisha alhali yana azumi[Bukhari da Muslim].

* Cirewar hakori, ko zubar jini daga baki ko hanci.

* idan Alfijir ya keto alhali abunsha na hannunka, kada ka aje har sai ka biya bukatarka.

*jinkirta wankan janaba ko haila ko na haihuwa daga dare zuwa hudowar alfijir. Abunda yafi shine ayi gaugawar yi kafin sallar asuba.

Muna rokon Allah ya amfanar damu da abunda muka rubuta, Allah yasa munyi domin Neman yardar shi, Allah ya sanya ibadojin da zamu gabatar a ramadana su zamo karbabbu, kuma su zamo sanadiyyar tsira garemu duniya da lahira. Inda mukayi kuskure Allah ya shefeshi daga idanun masu karatu ya fahimtar dasu tare damu gabaki daya. Allah ya doramu akan tafarki madaidaici.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.

COPYRIGHT©
Hashim Surajo Uba(ABU SINÃN)```

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.wordpress.com

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

+2348064734911
+2348064734911

AZUMIN WATAN RAMADHANA

🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉
*AZUMIN WATAN RAMADANA*
🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇

*بسم الله الرحمن الرحيم*

_Rubutawa;_ *HASHIM SURAJO UBA(ABU SINÃN)*

```ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU.

  Godiya ta tabbata ga Allah s.w.t shi kadai Wanda yayi mana umurni da azumtar ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada, Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da ibadar azumi da sauran ibadoji.

Bayan haka;

FALALAR WATAN RAMADANA DA AZUMI A CIKIN WATAN.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan ramadana ya shigo, ana bude kofofin sama, ana kulle kofofin jahannama, ana daure shaidanu.
A wani hadisin kuwa manzon Allah s.a.w cewa yayi" Dukkan wani aiki da dan Adam zaiyi, ana lunka aikin da lada goma irinsa, idan a ramadana ne, ana lunkashi zuwa lunki (700), sai Allah mai girma da daukaka yace ;  banda azumi, domin azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa Wanda yayi shi, yabar matarshi da abubuwan da yakeso, da abinci, da abin sha saboda ni, mai azumi Nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki (shan ruwa) da farin ciki lokacin haduwarshi da Allah, yamin/warin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

ABUBUWAN DA SUKA WAJABA GAREKA A RAMADANA

Ya dan uwa

Kasani cewa Allah ya wajabta mana azumi domin mu bauta masa dashi, sannan kuma ya kasance cewa azuminka ya zamto karbabbe mai amfani.
Dole ne ka kiyaye wadannan abubuwan da zasu zo domin samun cikakkar lada;

1- kiyaye sallah; Da yawa daga cikin masu azumi suna wasa da sallah, bayan kuwa cewa tana daga cikin gimshikan addini, barinta kuma yana kai mutum ga kafurci.

2- Dole ka kasance mai kyawawan dabi'u; Dole ne mu tsoraci kafurci da zagin addini, da aikata muna nan dabi'u a cikin mutane, kafirci yana fitar da musulmi daga addini.

3- Dole ne mu kiyaye halshenmu da sukar juna.
 
Manzon Allah s.a.w yana cewa; "idan dayanku yana azumi, to kada ya fadi maganganun da basu dace ba, idan wani ya zageka ko ya nemi yayi fada da kai, sai kace mashi ni azumi Nike, ni azumi Nike.

4- Ka nisanci zuwa wurin da ake aikata barna! Ko kallon fina-finai na banza, domin hakan zai kai ga bata azuminka.

5- Ka yawaita sadaka ga makusantanka da mabukata, da ziyartar yan uwanka.

6- Ka yawaita zikiri da karatun Qur'ani da saurararshi, da bibiyar ma'anoninsa, da aiki da abinda yake karantarwa, sannan da zuwa masallatai domin daukar darussa masu amfani, kamar sauraran tafsirai, yin ittikafi a masallaci idan goman karshe na ramadana suka kama.

7- karanta takardu akan azumi, domin sanin hukunce- hukuncen da suka shafi azumi, ta yarda zakasan cewa cin abinci ko abin sha da mantuwa baya karya azumi, kasan cewa ita janaba wacce ta sameka da daddare bata hana ka daukar azumi da sauransu.

LADUBBAN DA SUKA SHAFI AZUMI.

1- kiyaye halshe; Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda bai bar zancen karya ba, da aiki da zancen karya, Allah baya da bukatar barin cinsa ko shansa.

2- BUDA BAKI DA SAHUR DA ADDU'AH.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan dayanku zaiyi buda baki, to ya fara da dabino domin akwai albarka a ciki, idan bai samu dabino ba toh sai yayi da ruwa, domin suna tsalkakewa.
Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi buda baki yana fadar;
ذهب الظمأ، وابتلت العروق، وثبت الأجر، إن شاء الله.

Ma'ana: "YUNWA TA TAFI, GABOBI SUN DAI DAI TA, LADA TA TABBATA DA YARDAR ALLAH".
Manzon Allah s.a.w yace; "mutane baza su gushe suna samun alkhairi ba matukar suna gaggauta buda baki.

Anan dole mu gujewa muna nan akeedun shi'ah wadanda basa shan ruwa sai duhu ya shigo sosai, suna kafa hujja da ayar Qur'ani dake cikin suratul bakara, inda Allah s.w.t yake cewa; "...sannan Ku cika azumi zuwa dare. Wanman magana malamai sunyi bayanin me ake nufi tun da dadewa, mai Neman Karin bayani ya duba tafsirin "Aisarat-tafaseer, na jabir jaza'iry."

Manzon Allah s.a.w yace"kuyi sahur, domin a cikin yin sahur akwai albarka."

Manzon Allah s.a.w yace"Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da an rage komai daga ciki ba.

3-  DAGA CIKIN FA'IDOJIN AZUMI

   Duk Wanda yayi azumin ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbansa.

Duk Wanda yayi tsayuwar ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.(ma'ana: tsayuwar tarawihi da kiyamul-laili.)

4- WADANDA AKA YIWA RANGWAMEN AZUMI.

   *Marar lafiya da matafiyi, zasu ranka saboda fadar Allah s.w.t cewa;"Wanda ya kasance a cikinku marar lafiya ko akan hanyar tafiya, zai ranka azumin a kwanakin sauran watanni."
Amma marar lafiya Wanda ba'asa ran warkewa a kusa, toh sai ya rinka ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mai haila, da jinin haihuwa zasu aje azumi, saboda fadar ummuna Aisha R.A; "mun kasance ana umurtanmu da ranka azumi, amma ba'a umurtanmu da ranka sallah.[Bukhari da Muslim].

* Dattijo da dattijiya, wadanda sun tsufa sosai basa iya daukar azumi toh zasu ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mace mai ciki da mai shayarwa idan sunji tsoron rayukansu, toh zasu aje azumi sannan su ranka kawai, amma idan suna jin tsoron yayansu ne kawai, toh zasu ranka kuma su ciyar.

5- ABUBUWAN DAKE BATA AZUMI.

Abubuwan dake bata azumi sun kasu gida biyu:
Na farko; Abunda ke bata azumi Wanda ke wajabta rankawa kawai;

* Cin abinci ko abinsha da gangan.

* Yin amai da gan gan, saboda fadar annabi Muhammad s.a.w cewa: " Duk Wanda yayi amai, toh zai ranka azumi.[Hakim ya ruwaito]

* Mace mai haila da mai haihuwa, koda sauran mintuna kadan ayi buda baki tazo musu, toh zasu ranka azumin.

* Istimna'i(masturbation) wasa da al'aura da hannunka har maniyyi ya fito shima yana bata azumi kuma sai ka ranka.

Abu na biyu dake bata azumi kuma yake wajabta ranko da kaffara shine JIMA'I, akan maganar malamai kaffarar shine yanta baiwa ko azumin kwana sittin(60) a Jere.

6- ABUBUWAN DA BASU BATA AZUMI

* Cin abinci ko abinsha da mantuwa, ko da kuskure ko da tilasci! Babu ranko kuma babu kaffara, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa"Wanda ya manta yana azumi ya ci ko ya sha toh ya cika azuminsa, Allah ne ya ciyar dashi kuma ya shayar dashi.[Bukhari da Muslim]

* Amai ba dagan gan ba.

* Yin aswaki a kowane lokaci ko brush da sauransu.

* Dandana abinci da sharadin kada ka bari ya wuce maka.

* Sumbantar matarka, da sharadin kada akai ga aikata jima'i. Saboda manzon Allah s.a.w ya kasance yana sumbantar Aisha alhali yana azumi[Bukhari da Muslim].

* Cirewar hakori, ko zubar jini daga baki ko hanci.

* idan Alfijir ya keto alhali abunsha na hannunka, kada ka aje har sai ka biya bukatarka.

*jinkirta wankan janaba ko haila ko na haihuwa daga dare zuwa hudowar alfijir. Abunda yafi shine ayi gaugawar yi kafin sallar asuba.

Muna rokon Allah ya amfanar damu da abunda muka rubuta, Allah yasa munyi domin Neman yardar shi, Allah ya sanya ibadojin da zamu gabatar a ramadana su zamo karbabbu, kuma su zamo sanadiyyar tsira garemu duniya da lahira. Inda mukayi kuskure Allah ya shefeshi daga idanun masu karatu ya fahimtar dasu tare damu gabaki daya. Allah ya doramu akan tafarki madaidaici.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.

COPYRIGHT©
Hashim Surajo Uba(ABU SINÃN)```

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.wordpress.com

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

+2348064734911
+2348064734911

DABI'UN MAGABATA A CIKIN WATAN RAMADHANA

🍌🍌🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍌🍌
*DABI'UN MAGABATA A CIKIN WATAN RAMADANA*
🍇🍇🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍇🍇

_Rubutawa;_ *Hashim Ibn Surajo Ibn Uba(ABU SINÃN)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

```Assalamu Alaikum warahmatullahi wabarakatuhu.

Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda yayi umurni da azumtar watan ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w, Wanda ya koya mana yanda zamu gabatar da azumin.

Bayan haka;

Magabata suna da wasu dabi'u da ayuka da zantuka a cikin ramadana, watan ramadana shine watan da Allah s.w.t ke cewa; "watan ramadana Wanda q cikinshi ne aka saukar da Qurani, domin shiriya ga mutane, da kuma bayanai game da shiriyar....[bakara 185]

Magabata na kwarai suna da ayukan da suke aikatawa a ramadana  fiye da sauran watanni.  Daga cikin magabatan akwai;
*IMAMU MALIK IBN ANAS(imamu darul hijra) ya kasance baya dakatar da karatuka a masallacin Annabi Muhammad s.a.w sai a ramadana, domin yana shagaltuwa da karatun Qurani ne kawai.

*SUFYANUS-THAURY R.H; ya kasance idan Ramadana ya shigo, yana barin dukkan wasu ibadodi, yana shagaltuwa da tilawar Qur'ani.

* MUHAMMAD IBN ISMA'IL AL-BUKHARI(mai sahihul-bukhari): ya kasance a cikin duk yini daya yana sauke Qur'ani, yana tsayuwar tarawihi acikin kwana uku na tqrawihin yana sauke Quran.

*SA'ID IBN JUBAIR: ya kasance yana saukar Qur'an a duk kwana biyu.

* ABU AWANAH yace; naga IMAMU QATADA yana karantar da Qur'an a watan ramadana.

*IMAMU QATADA; ya kasance yana saukar Qur'ani a duk bayan kwana bakwai, idan ramadana ya shigo yana sauka duk kwana uku, idan kwanaki goma na karshe suka shigo yana saukewa a kowane dare.

*RABEEY IBN SULAIMAN(Dalibin imamush-shafi'i) R.H yana cewa; imamush-shafi'i ya kasance yana saukar Qur'ani a ramadana sau sittin (60)[kowace rana sau biyu] a kowane wata yana sauka sau talatin(30) bayan ramadana.

    Kiyamul-laili aikin Annabi Muhammad s.a.w da sahabbansa ne, Aisha R.A take cewa; "kada kubar tsayuwar dare, domin Manzon Allah s.a.w bai taba barinta ba, idan baya lafiya yana yi a zaune.

* Umar Ibn khaddab R.A ya kasance yana sallar dare dai dai gwargwado, idan dare ya raba, said ya tayar da iyalansa domin yin sallar, yana cewa SALLAH! SALLAH!! SALLAH!!! Sannan sai ya karanto aya ta 132 dake cikin suratu Daha, inda Allah madaukakin sarki yake cewa; "Ka umurci iyalanka da yin SALLAH ka kwadaitar dasu akanta, bamu tambayarka wani arziki mine masu azurtaka....

  Wannan shine dabi'un magabata na kwarai a watan ramadana, to mu ya halinmu yake a wannan wata mai albarka???

* Abdullahi Ibn umar(Allah ya kara masu yarda) ya kasance yana yin azumi ba ya buda baki(shan ruwa) sai tare da talakawa, ya kasance idan yana cin abinci sai wani mabukaci yazo ya tambaya sai ya tashi daga abincin ya mika masa, ya wuce da azumi ba tare da yayi sahur ba.

  Wadannan sune magabata na kwarai, kuzo Mani da irinsu a wannan zamanin yã Ku masu da'awar salafiyya da Sunnah!?

*YUNUS IBN YAZEED yake cewa; IBN SHIHAB AZ-ZUHURY ya kasance idan ramadana ya shigo yana cewa; "Wannan watan Qur'ani ne, da kuma ciyar da abinci".

* HAMMAD IBN ABI SULAIMAN ya kasance yana ciyar da mutum dari biyar(500) a watan ramadana. Ya kasance kuma yana ba kowane dayansu dirhami Dari(100).

  Yã yan uwa na masu daraja ya kamata mu kwatanta rabin abunda magabatanmu na kwarai suka aikata na ayukan alkhairi, kada mu shagaltu da abunda bazai amfanemu ba, daga baya mu koma da na sani! Allah madaukakin sarki yana cewa;"ومن أعرض عن ذكري فإن له معيشة ضنكا ونحشره يوم القيامة أعمى، قال رب لم حشرتني أعمى وقد كنت بصيرا، قال كذلك أتتك آياتنا فنسيتها وكذلك اليوم تنسى، وكذلك نجزي من أسرف ولم يؤمن بآيات ربه، ولعذاب الآخرة أشد وأبقى.

Allah yq karemu.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.



COPYRIGHT©
Hashim Ibn Surajo Ibn Uba(ABU SINÃN)```

atstsamawy@gmail.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.WordPress.com

http://shababusunnahtsafe.mywapblog.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

+2348064734911
+2349030201868

YA YA ZAMU FUSKANCI RAMADANA???

🍌🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍌
*YA YA ZAMU FUSKANCI RAMADANA???*
🍇🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍇

_Rubutawa:_ *Hashim Ibn Siraj Ibn Uba{ABU SINÃN}*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda ya wajabta mana yin azumin watan ramadana, Tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada  Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da azumin ramadana.

Bayan haka;

Allah s.w.t yana fada a cikin suratul bakara aya ta 185 cewa;" watan ramadana Wanda a cikinsa ne aka saukar da Qur'ani domin shiriya ga mutane da kuma bayyanar da shiriyar....."

Ya yan uwa

Allah s.w.t ya kebance watan ramadana da kebantattun abubuwa masu yawa akan waninsa. Daga cikin abubuwan akwai;

* Fadar manzon Allah s.a.w cewa: warin bakin mai azumi, yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.
* Mala'iku na nemawa mai azumi gafara har zuwa lokacin da zaiyi buda baki.
* Ana tsare shaidanu a cikin Ramadana.
* Ana bude kofofin aljanna, ana rufe kofofin wuta.
* A cikin Ramadana ne Daren lailatul kadri yake, wadda tafi wata dubu Alkhairi.
* Allah na gafartawa mai azumi a karshen daren ramadana.

Ya yan uwa
Da wane irin abu zamu tarbi ramadana? Da wasannin banza??? Ko da zuwa kallon kwallo??? Ko da kallon fina finai???
Muna neman Allah ya tsaremu da aikata daya daga cikinsu a wannan wata mai albarka.

Shi bawan Allah na kwarai yana fuskantar ramadana da tuba zuwa ga Allah, yana mika lokuttanshi gaba daya domin yin ayukan kwarai, bawan Allah na kwarai shine mai rokon Allah akan ya karba masa ibadojinsa da addu'oinsa.

1- AZUMI

Manzon Allah s.a.w yana cewa; "Dukkan wani aiki da mutum zai yi, yana da ladar goma irinsa, amma ga azumi ana lunka aikin zuwa lunki dari bakwai(700). Allah mai girma da daukaka yace; banda azumi! Azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa masu azumi,(ma'ana babu Wanda yasan adadin ladar mai azumi sai Allah) sun bar abubuwan da suke sha'awa da kauna, sun bar abinci da abin sha saboda ni, mai azumi nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki(shan ruwa), da kuma farin ciki lokacin haduwarsa da ubangijinshi. Warin/yamin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda ya azumci ramadana, yana mai imani, da kwadayin Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbanshi.[Bukhari da Muslim]
2- SALLAR TARAWIHI/KIYAMUL-LAILI.

Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda yayi tsayuwa a ramadana, yana mai kwadayin Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubanshi.[Bukhari da Muslim]

3- SADAKA
Manzon Allah s.a.w ya kasance yafi kowa sadaka a Ramadana da waninsa, manzon Allah kyautarsa tafi iskan dake kadawa yawa, domin tana game kowa da kowa. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana cewa; "Mafificiyar sadaka, itace wacce akayi a cikin Ramadana.

4- CIYAR DA ABINCI

Akwai alkhairai kwarai da gaske a cikin ciyar da abinci, a Ramadana ne ko waninsa. Kamar yadda Allah s.w.t ya ambata siffofin mutanen kirki a cikin suratul insãn aya ta 8-12 saboda suna ciyar da abinci tare da zukatansu na cikin jin dadi da walwala lokacin da suke ciyarwar.
Magabata na kwarai sun kasance suna ciyar da abinci a ramadana kwarai da gaske, manzon Allah s.a.w yana cewa; "yã Ku mutane Ku watsa sallama, Ku ciyar da abinci, Ku sadar da zumunta, kutashi lokacin da mutane ke barci domin kuyi sallah, zaku shiga aljanna da aminci.[imamu Ahmad ya ruwaito da tirmidhi, Albany ya ingantashi].
Manzon Allah s. a.w yace: "Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da anrage mashi komai ba.[imamu Ahmad ya fitar, da nasa'i, Albany ya ingantashi.

5- NEMAN LAILATUL-KADRI.
Allah madaukakin sarki yana cewa: "Lallai mu muka saukar dashi (Qur'ani) a daren daraja, wa ya sanar dakai me ake cewa daren daraja, daren daraja yafi Alkhairi fiye da wata dubu.
Manzon Allah s. a.w yace; "Duk Wanda yayi tsayuwar daren lailatul-kadri, yana mai imani da kwadayin Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.[Bukhari da Muslim]

Lailatul-kadari ana nemanta a daren 21,23,25,27 ko 29. Hadisi ya tabbata daga  ummuna Aisha R.A tacewa manzon Allah s.a.w idan na dace da daren lailatul-kadari me zan fada? Sai yace mata kice; اللهم إنك عفو،تحب العفو،فعف أني
Ma'ana; "yã Allah kai mai yafiya ne, kanason masu yafiya, ka yafe mani.[Ahmad ya ruwaito da tirmidhi, Albany ya ingantashi].

6- YAWAITA ZIKIRI DA ADDU'AH DA ISTIGFARI.

Ya yan uwa
  Kwanakin watan ramadana masu tsada ne, mu daure mu ribacesu da yawaita zikiri da addu'ah, musamman a kebantattun lokuta na amsar addu'ah. Daga cikin lokuttan akwai;
* Lokacin da mai azumi zaiyi buda baki, ba'a maida addu'ah a wannan lokacin.

*  Daya bisa ukun dare, lokacin da Allah s.w.t yake saukowa yana cewa: "ina mai rokona in amsa mashi, ina mai neman gafara in gafarta mashi.

Daga karshe ina kwadaitar damu akan mu tsaya mu ribaci wannan wata mai albarka kafin ya wuce! Idan ya wuce bamu da tabbacin zamu kara riskarshi.

Allah ya tabbatar damu akan aikata abubuwan da suka dace da sunnah a cikin wannan wata mai albarka.

        WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.



COPYRIGHT©
Hashim ibn Surajo ibn Uba(ABU SINÃN)
ATS~TSAMAWY```

atstsamawy@gmail.com

http://hashimtsamiya.mywapblog.com

http://abbansinaan.mywapblog.com

http://abbansinan.WordPress.com

http://shababusunnahtsafe.mywapblog.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

https://free.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

+2348064734911
+2349030201868