Friday, 8 December 2017

HUDUBAH MAI TAKEN LOKACIN SANYI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon limamin  Massallacin Jumu'a na Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na Liman'

Yayi Hudubar Sane Akan #LOKACHIN_HUNTURU

Bayan mukkaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka a yau Khudbar mu zatayi magana ne game da halin da muke ciki, Watau yanayi na hunturu da sanyi da kadawar iska.

Idan muka diba lokachin da muka fito na baya zamu ga cewa lallai yanayi yayi matukar chanzawa, Hakika yan uwa musulmi chanzawar lokachi wani sababi ne ga mai imani da zai kara masa imani, Da kara maida kai ga ALLAH Da jajircewa ga biyar sa!

ALLAH Madaukakin sarki cikin hikimar sa da yarda sa yana shata mana zuwan wannan lokachin duk shekara.

Ibn kaiyumul jauzi yana cewa 'Idan aka lura da yadda ALLAH juya lokutta zamu fahimci cewa akwai wata maslaha dake cikin yin hakan'

Idan da yaso sai ya barmu da lokachi daya ko zafi kawai ko sanyi kawai ko kuma ruwan sama kawai!

Yan uwa musulmi masu albarka ina maku wasiya dani da ku da muji tsoron ALLAH, Hakika da tsoron ALLAH Ne zukata ke kamuwa da natsuwa kuma ake fahimta ayoyi da manufofin ubangiji.

ALLAH Madaukakin sarki na cewa "SUNE (Masu imani) MASU DIBA YADDA MUKE JUYA AKAN LAMURA HAKIKA SUN SAMU IMANI KUMA SUNE MASU AMBATON ALLAH BA DARE BA RANA "

Hakama ALLAH S.W.T Na cewa "LALLAH JUYAWAR DARE DA YINI AYAH CE GA MASU IMANI"

Shi wannan lokachin na sanyi ALLAH Madaukakin sarki ne ya kaddaro shi da haka, Domin wuta ce keyin lumfashi!!

Ga hadisi daga Manzo s.a.w "Wata rana wuta takai kara ga ALLAH S.W.T Cewa wani sashen ta yana cin sashen ta sai ALLAH Yabata dama cewa ta rika numfashi wato taja iska (shine muke samun lokachin sanyi) sannan ta saki numfashi (shine lokachin zahi)"

Iman hasanul busariy na cewa 'ALLAH Ya tanadar da wannan lokutta ne dan tunatar damu game da kiyama, Domin idan nukaji sanyi yayi yawa sai mu tuna cewa sanyin azaba da kiyama yafi na duniya, Hakama zafi na duniya bai kai zahin kiyama ba"

Abdullahi dan Mas'ud r.a ya kasance idan sanyi yazo yana cewa 'Maraba da zuwan sanyi maraba da zuwan sanyi idan aka tambaye shi miye dalilin shi na fadar haka sai yace 'Lokachin sanyi lokachi ne da dare keda tsawo (Ana samun damar yin ibadah da kusantar ALLAH) Rana kuma batada tsawo ana yawaita azumi'

Yan uwa musulmi masu albarka lokachin hunturu yana da HUKUNCE HUKUNCEN sa..

*Yin alwala da kyau-Yazama wajibi mu kiyaye yadda muke alwala a lokachin sanyi, Domin muna sanya manya kaya kuma wajen alwala zakaga wasu saboda kaya masu nauyi basu yin alwala da kyau.

Manzo s.a.w "Yaga wasu na alwala amma basu shafawa yadda yakama sai Manzo s.a.w yace 'Boni ya tabbata ga masu alwala basu cikawa ' "

Babu laifi saboda sanyi ayi alwala da ruwan zafi wajen yin alwala.

*Ana son tuna saukin da shari'ah ta kawo mana, Ya halatta shafa sama safa ko takalma ko huffi, Idan har anyi alwala kafin a sanya safar ko takalman.

Mugira ya ruwaito hadisi kuma an ruwaito shi a sunnanin dauda cewa "Manzo s.a.w yana shafa saman khuffi amma idan yayi alwala,

Hakama wata rana Manzo s.a.w zai yi alwala sai Mugira yazo zai cire masa takalma sai Manzo s.a.w yace kabarshi domin nayi alwala kafin insa!

Larabawa na cewa lokachin sanyi namiji zahi kuma macce, Saboda yanayin karfin su ba daya ba.

A zamanin khalifan Manzo s.a.w na biyu wato Umar bn Khattab r.a yana kewa yawa cikin gari yana cewa 'Sanyi yazo sanyi makiyin mu ne dan haka mu tanadi kayan kariya kamar manya barguna da sauran kayan kariya daga sanyi'

Yaku yan uwa musulmi masu albarka, Hakika Umar r.a ya kasance yana taimakon marar sa galihu da kayan rufe jiki dan kariya daga sanyi.

Anan muna kira ga yan uwa musulmi da mu taimaki yan uwa marayu da makwabta da sauran mara sa galihu, Da kuma kula da iyali da kananan yara a tanadar masu kayan sanya kada mu barsu kamar  dabbobi domin zai iya yin illah garesu.

*Yawaita bautar ALLAH, Hunturu lokachi da dan Adam ke samun lafiya da walwala da kebantuwa daga mutane, Domin ko doguwar hirar da ake yi ragewa ake yi, Zaka fito karfe goma ka tarar babu kowa,

Dan haka sai muyi amfani da wanoan lokachin wajen bautar ALLAH ba yawan bacci ba.

*Mu rika cika alwala, Manzo s.a.w na cewa "Cika alwala ne mafi so a yanzu (Lokachin hunturu).

*Dumama jiki dan samun sauki, Sai dai yana da kyau musulmi ayi hattara sosai, Domin kada mu ajiye wuta ta rika kwana a dakunan mu.

Abul musa al'ashry ya ruwaito cewa "Wata rana ayi gobara a Madinah sai aka fadawa Manzo s.a.w sai yace 'Wannan wutar makiyar muce mu daina aje ta a dakunan mu'!!

Dan haka da zarar zamu kwanta sai mu kashe wuta a fito da ita waje,

Yan uwa musulmi mu taimaki yan uwa marar sa galihu, Mu taimaki marar kayan sanyawa.

Lallai ALLAH Na taimakon bawa, Matukar yana taimakon yan uwansa.

ALLAH Ka taimakemu da taimaka, Ka karemu da kariyar ka.

Ya ALLAH Ka biya mana bukatun mu na alkahri ka kiyaye mu kuma ka tsare mu.

Ya ubangiji kayi rahama garemu da iyayen mu.

Ya ubangiji ka zaunar damu lafiya, Ka albarka ci garin mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 19-Rabi'ul auwal-1439
Friday 18-December-2017 AB

HUDUBA MAI TAKEN TSORATARWA GAME DA RASHIN BADA ZAKKAH

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE



A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #TSORATARWA GA
MASU HANA # ZAKKAH
Bayan mukaddima.....
Yan uwa musulmi masu albarka, A wancan
makon daya gaba munyi bayani game da
#ZAKKAH da hukunce hukunce ta.
To a wannan makon da ikon Allah zamu yi
magana akan tsoratarwar ga halayyar ga masu
hana #ZAKKAH
Yan uwan musulmi muji tsoron Allah gaskiyar jin
tsoron sa musani yana kallo duk abubuwan da
muke aikata a kullum.
Muhimancin #ZAKKAH ba karami bane a
musulunce har Allah yahada ta tare da sallah
wurare 32 a cikin alqur'ani mai tsari,
Babban dalilin wajabta #ZAKKAH shine nuna
godiya ga Allah, Da kuma sadar da umarnin
Allah.
#ZAKKAH tana kankare talauci a tsakanin
mutane, Bada #ZAKKAH tsarkakewa ne wato
tsarkake dukiya da kuma rayuwa baki daya.
Saboda matsayin Allah ya umurci Manzon Allah
s.a.w akan ya karbo #ZAKKAH "KA ANSO
#ZAKKAH DAGA GARESU DAN ZAMA
TSARKAKEWA GARESU"
Yan uwa musulmi masu albarka, Hakika fidda
#ZAKKAH wajibi ne a musulunci kuma dole ne,
Rashin fidda #ZAKKAH yana kawo fitononi da
musibu a cikin al'ummah baki daya. Allah ya
umarce mu da fiddawa da yake cewa "KU FIDDA
DAGA ABUNDA MUKA AZURTA KU DASHI"
Rashin bada #ZAKKAH yana jawo masibu da
bala'oi kala kala!!
Nana Aisha r.a ta ruwaito daga Manzo s.a.w
cewa "Babu dukiyar da za'a tara ba'a fitar mata
da #ZAKKAH sai Allah tarwatsa ta"
Yan uwa musulmi masu albarka muna ganin
musibu da ake samu na gobara da masibu kala
kala, Hakika wannan duk daga hana #ZAKKAH
ne!
Rashin bada #ZAKKAH na kawo debe albarka ga
noma da kudi, Idan muka diba zamu ga yadda
anan garin aka noma shinkafa da farko tayi kyau
amma daga karshe wasu sun fadi warwas!
Duk fa wannan daga rashin bada #ZAKKAH da
muke yi, Manzo s.a.w na cewa "Mutane bazasu
hana #ZAKKAH ba face sai Allah ya debe
albarka ga abun su"
Hakika tsoratarwa mai karfi tazo akan masu qin
fidda #ZAKKAH har ma wani wuri a Qur'ani da
mushrikai.
Sau da yawa zakaga wami yasamu kudi da suka
kai nisabi, Ko kuma yayi noma yasamu albarka
amma sai ya rike #ZAKKAH ko kuma yabada ga
wanda yaga dama ko kuma badawa a lokachin da
yaso maimakon lokachin da yasamu.
Duk wanda yabada #ZAKKAH yadda yaga dama
malamai sunce kamar bai bada wato dashi da
wanda bai bada duk daya.
Rashin bada #ZAKKAH yana kawo musibu, Ita
kuma musiba munsan tana shafuwar har wanda
baiji ba bai gani ba, Wata qila ma tana iya wuce
wanda ya hana #ZAKKAHR Ta fada wani shi
kuma a kyale sa sai ranar kiyama!
Yan uwa musulmi masu albarka, Idan akwai
abokin ka ko dan uwanka ko wani makusancin ka
yake hana #ZAKKAH to kayi masa nasiha tare da
gargadi.
ALLAH Fa yayi mana babban gargadi (Serious
warning) game da hana #ZAKKAH
*BANI YA TABBATA MARAR BADA #ZAKKAH SU
(masu hana zakkah) MUSHRIKAI GA KIYAMA"
*MASU TARA DUKIYA #ZAKKAH DA SANMU
ZA'A JEFA SU A WUTAR JAHANNANAMA TANA
SUYA SU"
*"MASU TARA DUKIYA BASU BADA #ZAKKAH
KUMA BABU ABUNDA YASAMI DUKIYAR
WALLAHI YABAR MURNA DOMIN BALA'I CE
GARESA"
Manzo s.a.w ya fassara wannan ayar da cewa
"Allah zah maida dukiyar maciji mai baki biyu
yana saransa a wutar jahanama yana cewa 'Nine
dukiyar ka da ka hana #ZAKKAH' "
Yan uwa musulmi masu albarka Allah shirewa
duk dukiyar da aka hana #ZAKKAH albarka,
Idan muka diba matsalar tsaro da sauran
abubuwan da suka dame mu duk suna da alaqa
da kaucewa umarnin Allah.
Bayan wafatin Manzo s.a.w wasu sunce sunce
'Sun daina bada #ZAKKAH saboda Manzo s.a.w
ya rassu, Khalifan Manzo s.a.w ya yake su har
garuruwan su ya bisu ya karbo #ZAKKAH
Aliyu bn abi Thalib khalifan Manzo s.a.w ya hudu
yace 'ALLAH Baya dauke musiba sai an tuba!
Allah madaukakin sarki na cewa "DUK ABUNDA
YASAME KU TO DAGA ABUNDA KUKE
AIKATAWA NE"
Hakika ALLAH Yabamu labarin mutane da yawa
wadanda yayi wa ni'ima suka kafurce!
ALLAH Yana fada mana cikin suratul nahal cewa
"ALLAH YABUGA MISALI WATA ALKARYA DATA
KAFURCE"
Sai mu diba muga yanzu wace ni'imah ce Allah
baiyi mana ba??
Munsan labarin wani da ake kira Saba'a yadda
suka kafurce daga karshe ALLAH Kwace ni'imar
daga garesu.
Lallai ne kuma dole ne mu sadar da umarnin
ALLAH Dan samun falala da rahama wata bata
yankewa daga garesa.
Tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzo
s.a.w da iyalansa da sahabban sa dukkan
wadanda suka biyo bayan su da kyautatawa har
zuwa ranar sakamako.
Ya Allah ka biya mana bukatun mu kayi rahama
garemu ka gafarta mana yaye mana damuwa, Ya
Allah kara albarka ga dukiyar da ake bada
#ZAKKAH ya Allah ka tarwatsa duk dukiyar da
ake hana #ZAKKAH


©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 28-Safar-1439
Friday 17-November-2017

HUDUBAH MAI TAKEN BIDI'AH

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #BIDI 'AH DA
HUKUNCIN TA A MUSLUNCHI
Bayan mukaddimah...
Yan uwa musulmi a yau Khudbar tamu zata yi
magana ne game da #BIDI'AH da kuma hukuncin
ta a musulunce!!
Yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Gaskiyar jin
tsoron sa, Mu sani cewa da tsoron ALLAH
Rayuwa ke gudana .
Babbar ni'imah garemu ita ce musulunci domin
musulunci shine hanya daya rak dake sada dan
Adam da ubangiji ALLAH , ALLAH Yabamu
rayuwa (Musulunci) kamar yadda ya labarta
mana cewa "YANZU WANDA YA KASANCE
MATACCE (JAHILI) ZAI YI DAI DAI DA MAI RAI
(MAI ILMI)"
Hakika akwai abubuwa wadanda ke ruguza addini
da dama,Babba Daga ciki shine bidi'ah!
Ita bakwai ne kawo ita bidi'ar,
1-Son rai, Shi son rai shine babban jagora ga
qago bidi'ah a cikin addini, ALLAH Madaukakin
sarki kuma ya gargadi masu son da yake cewa
"BABU WANDA YAFI KOWA ZAMA BATACCE SAI
WANDA KE BIN SON RAI".
2-JAHILCI, Tabbas jahilci ya taka gagarumar
rawa a wajen qago bidi'ah a cikin musulunci,
ALLAH Madaukakin sarki na cewa "MAFI YAWAN
MUTANEN DUNIYA JAHILAI NE"
3-Kau da kai daga karbar gaskiya, Tabbas kauda
kai daga karbar gaskiya yana matukar kai dan
Adam ga kirkiro bidi'ah, Ita kau gaskiya duk
wanda ya karbe ta baya tabewa kamar yadda
madaukakin sarki ke cewa "DUK WANDA
SHARI'A TA BAYA TABEWA DUK WANDA YABI
SON RANSA ZA'A TABAR DASHI KUMA ZA'A
TADA SHI MAKAHO"
4-Nisantar masu ilmi, Tabbas nisantar masu ilmi
na fadin gaskiya da kuma takama da jahilci na
kawo kago bidi'ah a addini, Duk abunda mutun
bai sani yakamata yayi ya tambaya amma sai ya
kiya, ALLAH Kuma na cewa "KU TAMBAYI
MA'ABOTA ILMI IDAN BAKU SANI BA"
5- Jiji da kah da son ra'ayi, Hakika ji da kai yana
kawo mutun ya fadawa bidi'a ko kuma ya kirkiro
ta,
6-Son duniya, Tabbas masu mugun son duniya
suna kirkirar bidi'ah su kawo ta a musulunci,
ALLAH Kuma na cewa "SUN ZABI DUNIYA A
BISA LAHIRA " Wani wuri kuma yana cewa "SUN
ZABI RAYUWAR DUNIYA BISA GA TA LAHIRA"
Abubuwa biyu ne bidi'ah take...
1-Bidi'ah ta magana wadanda suke magana ta
izgili da sunan addini kamar mu'utazilawa da yan
Shi'ah.
2-Bidi'ah ta aiki, Kamar bautawa ALLAH Da
shari'ar da bai umarta ba, Ko kuma kari a cikin
ibadah, Misali wani yace maka 'Assalamu
Alaikum' to sai kaji wurin ansawa ance 'Ameen
'Wa alaikum salam anan cewa Ameen bidi'ah duk
da kalmar amin kalma ce mai kyau amma dai
sunnah bata karantar da haka ba, Akwai kara
wani abu wajen yin sallah da sauran su.
Manzo s.a.w ya koyar damu yadda ake yin Zikirai
kowane iri ya koyar damu na safe na rana na
yammah na dare dana komai,
Sannan akwai bidi'ar kebance wani lokachi
wanda shari'ah bata kebe ba dan yin ibadah,
Wannan baya cikin tsarin musulunci.
Hukuncin #BIDI'AH shine tana rushe aiki baki
daya.
Manzo s.a.w na cewa "Mafi sharrin ayyuka shine
kirkiro wani abu cikin addini"
Wata rana Umar bn Abdul'aziz r.a ya fito sai yaga
wani tsoho mai gudun duniya mai tsoron ALLAH
Ya yawaita ibadah amma kirista ne!!
Dan haka sai ya koma gida yayi ta kuka da aka
tambaye shi miye dalilin kukansa sai yace ganin
wannan ya tuna mashi da ayar nan dake cewa
"RANAR DA ZA'A
KIFE FUSKAM SU A CIKIN WUTA"
Ita #BIDI'AH tana kawo kasala ga aikata Sunnah!
Imam hasanul busary na cewa 'ALLAH Baya
karbar ibadun mai bidi'ah sai almajiransa suka ce
saboda mi? sai yace yana da hujja daga hadisin
dake cewa "ALLAH Ya tsinewa mai yin bidi'ah"
Muna rokon ALLAH Ya gafarta mana yayi mana
rahama, Ya karemu daga aikata bidi'ah yayi
rahama garemuda iyayen mu, Ya biya bukatun
mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 12-Rabi'ul auwal-1439
Friday 01-December-2017

HUDUBA MAI TAKEN HARAMCIN SATA A MUSULUNCI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #SATA
Godiya ta tabbata ga ALLAH S.W.T Wanda yayi
halitta ya kuma dai dai ta halittar kamar yadda
yake bukata!
Na shaida Annabi Muhammad s.a.w manzo
ALLAH, ALLAH Kayi salati da taslimi ka kara
aminci garesa, da iyalansa da sahabai da dukkan
wadanda suka biyo bayan shi da kyautatawa har
zuwa ranar sakamako.
Yan uwa musulmi masu albarka yau Khudbar
tamu zatayi magana ne kan wata dabi'a wadda
zamu iya cewa ta zama ruwan dare a rayuwar
mu, Wannan dabi'ar ita ce #SATA
Yan uwa musulmi ina maku wasiya na ni kaina da
muji tsoron ALLAH, Kamar yadda ALLAH Da
kansa ya umarce mu cewa "KUJI TSORON WANI
YINI DA ZA'A MAIDA KU GA ALLAH SANNAN
ZA'A SAKAWA KOWACE RAI DA ABUNDA TA
AIKATA KUMA BAZA'A ZALUNCE TA BA"
Su kudi ALLAH Madaukakin sarki ne ya saukar da
su daga sama dan amfanin mu, Dan mu gudanar
da rayuwar mu ta yau da kullum da kuma
gudanar da addini... ALLAH S.W.T Ya gargade
mu game da cin dukiya wadda ba tamu ba da
yake cewa "KADA KUCI KUDI KAN BARNA SAI
DA YARJEJENIYA (Cinikayya a tsakani)"
ALLAH S.W.T Cikin ikon sa ya hukunta cire
hannu ga duk wanda aka kama da laifin satar
dukiya, Kamar yadda yake cewa "BARAWO
NAMIJI DA BARAUNIYA KU YANKE HANNUWAN
SU"
Hatta wadanda ba musulmi basu aminta da
#SATA ba!!
Ko kudi ko wani abun amfani haramun ne satar
sa...
A farkon musulunci idan anzo yin mubayi'a ga
Manzo s.a.w daga cikin sharuddan yin mubayi'a
har da sai an barranta daga sata! kamar yadda
ALLAH Madaukakin sarki ke shaidawa cewa
"IDAN MUMINAI MATA SUKAZO WURINKA SUNA
SHAIDA MAKA CEWA SUNYI IMANI TO SAI SUN
BAR SHIRKA SUNBAR ZINA KUMA SUN BAR
KASHE YAYAN SU KUMA KADA SU SABA MAKA
GAME DA UMARNIN DAKA BASU"
Tun farko musulunci kenan, Ashe yana gwadama
mana illar #SATA kenan!!
A yanzu #SATA ta zama ba maza ba mata, Ba
yara ba tsoffin da matasa, An maida sata kamar
ibadah!!
A yanzu yan kasuwa na sata!
Ma'aikata na sata!
Kai lamarin ya kai har makabarta ma ba'a kyale
ba ana sata!
Ba makabarta ba kadai, Har massallaci sata, Inda
ake koyon imani, Kamar yadda aka sace mana
batir a nan massallacin!!
Har a asibiti ma ba'a tsira ba.
Ana sata ta hanyar bashi, Wato ka ranci kudin
mutun kuma kaki biya, A lokachi Manzo s.a.w ya
taba yanke hannun wata babbar mata saboda
idan taci bashi sai tace bata ci ba..
Idan muka diba hadisin Manzo s.a.w da yake
cewa "Karshen zamani mutun zai tara dukiya bai
damu da abunda ya tara ba na halal ko na
haram"
ABUBUWAN Dake kawo #SATA nada ta yawa
daga cikin akwai-
*Son dukiya da yawa yana kawo sata!
A yanzu #SATA har a sallar farilla ana sata,
Wata rana Manzo s.a.w ya fadawa sahabbai
cewa 'Barawon da yafi kowane barawo shine
barawo a sallah, Sai suka ce kamar yaya? Sai
Manzo s.a.w yace mai yin qotan kurciya'
*Ma'aikata suna sata, Idan ka saci kudin
Zamfara kamar ka saci kudin duk wani
bazamfare ne.
*Yan kasuwa suna sata, Masu tauye ma'auni
suna sata ne.
*Ma'aikatan lafiya, Gwamnati na biyam su amma
sai suna yan kauye suna karbar kudaden su.
*Wadanda ake ba bashi basu biya.
*Marar cika sallah, kamar yadda bayi ya gabata.
*Matar aure mai satar kudin mijinta ko bincikar
aljihu.
*Na tare da barayi, Wanda ake cewa kunci.
*Mai cin iyaka, Ta gona ko ta gida.
*Satar wutar lantarki.
*Direbobi masu cin amana.
*Satar ansar jarabawa.
Da sauran su...
Wallahi duk kudin da aka sata ALLAH Ya debe
masu albarka, Koda kuwa anyi aikin alkhairi da
kudin.
"SHI ALLAH MAI TSARKI NE BAYA KARBAR AIKI
SAI MAI TSARKI"
"ALLAH BAYA KARBAR SADAKA DA AKAYI DA
HARAM"
ALLAH SWT Ya haramta sata ne dan samar da
zama lafiya al'ummah,
Malamai sunce idan mutun ya saye kayam sata
kuma yasani to shima barawo ne!!
Yana da kyau iyaye su rika kwabawa yayan su
domin lura da tarbiyar su.
Saboda fargabar #SATA a yanzu ko massallaci
kazo kana shakka kada ayi maka sata, Duk da
nan ne fa wajen tsoron ALLAH.
KADAN Daga cikin illolin sata akwai-
>#SATA tana korar imani.
>#SATA tana sanya macewar zuciya.
#SATA aibi ce ga duniya da lahira, Domin tana
tasiri har ga yaya da jikoki.
>#SATA tana sa ALLAH Yabar karbar addu'a.
Yan uwa musulmi masu albarka mu tashi tsaye
mu tuba daga aikata #SATA
Duk abunda ka dauka ka maida shi zuwa ga
maishi, Idan bayanan ka kaiwa magadan sa, Idan
kuma babu su to ka sadakar da niyar ALLAH Ya
kai ladar garesa, Kuma ka yawaita istigfari!!
Yan uwa musulmi masu albarka mu yawaita yin
nafila domin ita nafila tana cika mana ayyuka
marar kyau da muke aikatawa.
Mu tuba tun kafin lokachin mu yakare, Domin
baya mantuwa kuma mai adalci ne ga bayi baki
daya.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 21-Safar-1439
Friday 10-November-2017

HUDUBAH MAI TAKEN ILLOLIN GIBA KASHI NA BIYU

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #ILLOLIN_GIBA_KA
SHI_NA_BIYU
Godiya ta tabbata ga ALLAH ubangijin halitu, Mai
rahama mai jinkai Mamallakin ranar sakamako,
Muna gode masa muna neman taimakon sa,
Tsira da aminci su kara tabbata ga Manzo tsira,
ALLAH Yayi salati ga manzon rahama da
alayensa da sahabbansa da dukkan wadanda
suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako.
Yan uwa musulmi a yau zamu chi gaba daga inda
muka tsaya a makwanin da suka gabata, La'akari
da wannan babin (Giba) yana bukatar fadaden
bayani sosai, To hakam tasa muka ci gaba daga
inda muka tsaya.
Hakika addinin musulunci ya wajabta kare harshe
da sauran abubuwan da musulunci ya shar'anta,
Musulunci ya haramta cutar da dan uwa musulmi
ta kowace fuska!
'Wata rana manzo s.a.w yana tare da sahabbai
R.a sai ya tambayesu shin mi kuka sani game da
giba? Sai sukace (Sahabbai) ALLAH Da manzon
sa ne suka sani, Sai Manzo s.a.w yace fadar
wani abu akan wani idan bayanan, Sai sukace
koda abun da kafada gaskiya ne? Sai manzo
s.a.w yace eh koda gaskiya ne, Idan kuwa ba
gaskiya bane to laifin biyu kenan (Laifin karya,
Da kuma na giba)!!
A yanzu Giba ta zama ruwan dare, Ta inda duk
wajen dakaje zakaji ana yinta ana fadar kalamai
kan wani ko wata.
ALLAH Madaukakin yana fada mana cewa "YAKU
MASU IMANI KU NISANCI ZATO DOMIN ZATO
YANKI NE NA ZUNUBI"
Hakama madaukakin sarki na cewa "SHIN
DAYANKU ZAICI NAMAN DAN UWANSA ALHALI
YANA RAYE"
Manzon rahama s.a.w ya fada mana dan
tsoratarwa game da # GIBA yana Cewa "Bani
(Bala'i) ya tabbata ga masu cin naman
dan'umansu"
A koda yaushe muna tare da masu sanya ido
akam mu domin rubuta duk abunda muke aikata
a fili ko a boye, Madaukakin sarki na cewa "KADA
KA FADI ABUNDA BAKA DA ILMI AKANSA
LALLAI DA SAURARE DA GANI DA ABUNDA
ZUCIYA TAYI DUKKAN SU ABUN TAMBAYA NE"
Hakama madaukakin sarki na cewa "DUK
ABUNDA ZAKU AIKATA KUNA TARE DA RAQIB-
ATID"
Tunda har ga masu daukar ayyukan mu tayaya
zamu yin sakaci, Mu rika fada abubuwa kan yan
uwan mu?
Wata rana sahabbai suna zaune da 'Manzo s.a.w
sai wasu sahabbai suka ce ai wane baya cin
abinci sai yaga mutane zasu ci, Kuma baya yin
tafiya sai yaga mutane zasuyi, Sai Manzo s.a.w
yace kunci namansa!!!'
Kudiba girma irin na sahabbai, Kuma abunda aka
fada halin sane, Amma manzo ya fada masu.
Jabir bn Abdullahi ya ruwaito cewa 'Wata rana
muna zaune a wajen Manzo s.a.w sai mukaji
wani wari mai marar dadi, Mai Manzo s.a.w yace
wannan warin wadanda ake konawa ne da juta
saboda sunci naman yan uwansu musulmi, Aka
turo'
Amru bn As wata rana ya tafiya tare da sahabbai
sai suka hadu da wani mushen Jaki a kan hanya,
Sai yace wa sahabbai shin kuna iya chin wannan
naman jakin? Sai suka ce a'a sai yace:Cin
naman sa yafi sauki bisa ga cin naman dan
uwanka musulmi'
Wata rana wani sahabi ya tambayi Manzo s.a.w
cewa 'Shin miye mafita daga Giba? Sai Manzo
s.a.w yace mafita itace ka kare kanka da
iyalanka daga aikata alfasha'
Bayan giba ta baki sai kuma Giba ta zuciya,
Minene giba ta zuciya??
Abunda ake cewa giba ta zuciya itace munana
zato ga musulmi..
Munana zato ga Musulmi ko kuma gibar zuciya,
Shima giba ce da ALLAH Baya yafewa! ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KU NISANCI ZATO
DOMIN YANKI NE NA ZUNUBI"
Hakama Manzo s.a.w yace "Kashedin ku da zato
domin yana daga cikin karyar magana"
Akwai wurare daya halatta kayi maganar mutu,
Wato an lissafa su a cikin Giba to babu laifi...
1-Zalunci-Idan an zalunce ya halatta kaje wajen
wani mai iko kamar sarki, Ko alqali ko iyaye ko
kotu dan a kwato maka hakkinka, Zakayi hakan
ne tare da maimaita duk abunda yafaru dai
dai,Aisha r.a ta ruwaito cewa 'Matar Abu sufyan
ta kawo karar mijinta ga Manzo s.a.w cewa
abincin da yake bata baya isa dan haka tana diba
ta kara dan ya ishesu, Sai Manzo s.a.w yace
mata ba komai dan haka"
Kunga anan akwai halacci mace ta kai kara irin
wannan ta mijinta,
2-Neman fatawa, Ya halarta ka baiyana halin
wani wajen neman fatawa, Misali babana ya
cuce ni, Ko yaya na ko mijina ko matata da niyar
neman fatarwar musulunci akan yadda zaka nemi
hakkin ka.
3-Neman taimako, Neman Taimako zuwa ga wani
shugaba kama ana aikata barna a wani wuri, Ana
shaye shaye ko zina, Zaka iya labartawa
shugaba cewa wane da wane na aikata, Kuma
kafadi hakan ne dan gusar da barnar da ake
aikatawa, To wannan ba'a kiranta Giba, Koda an
kirata to ba laifi akai.
4-Tsoratar da musulmi kan wani sharri, Kafadawa
wani game da wani sharri, Misali yazo neman
bincike game da aure halin wani ko wata, To
anan zaka fadi gaskiyar abunda kasani akai ko
minene babu laifi akan haka nan!
Sai dai idan anfada maka kada kuma ka koma
kafawa ita wada zaka aura ko iyayenta, Cewa
wane ai yace man kaza da kaza akanki, To
wannan kai kayi Gibar!!
Ko kuma kaga dalibin ilmi zaije wajen dan Shi'ah
neman fatawa, To kana iya neman sa kayi masa
bayani akan halinsa.
5-Mai baiyanar da barna qarara, Babu laifi kaga
kafadawa jama'a suyi hattara dashi, Musamman
idan kaga suna kokarin shige masa.
6- Shigiya, Babu laifin idan kaga ana cigiyar wani,
Ka ambaci kamar da dole sai da ita ake ganesa,
Kamar baki, Dogo, Mai qaton kai, Mai idanu da
sauransu, Amma fa da niyar kwatantawa bada
cin zarafi ba!
To a wadannan wuraren 6 kadai ne ake fadar
wani abu game da mutun!
Amma idan shugaba ya zaluncenka bai kamata
duk idan ka zauna kayita fadar saba, Kana
zaginsa alhali wanda kake fadawa baida wani iko
akan ya kwato maka hakkinka.
Hakama wasu sun dauka idan kawai kafadi
magana bayan mutun take giba! A'a Har a gaban
mutun idan kafadi magana wada bata dace kuma
ta bata masa rai to kayi gibar sa!!
Sannan kuma akwai masu gibar karamin yaro,
Suna cewa wancan yaron kaza da kaza suna
aiban tasa, Suna fadar miyagun kalamai kansa,
To duk wannan nau'i ne na giba!!
A wannan yanayin da muke ciki koda ka kare
kanka daga aikata giba, To wani na iya daukowa
yakawo yayi a gabanka, Dan haka sai a kiyaye a
san da suwa za'a zauna.....
Idan kayi gibar wani kuma baka nemi yafiyar sa,
To ranar kiyama za'a debo ladar ka a kara masa,
Idan kuma ta kare za'a debo zunubinka a zuba
masa!!!
Ya ALLAH Ya karemu daga aikata sharruka, Ka
kiyaye mu ka tsare mu, Ya ubangiji ka biya mana
bukatun mu, Kayi rahama garemu ka kyautata
karshe mu Ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 17-Zhul-Hijjah 1438 AH
Friday 8-September-2017

HUDUBA MAI TAKEN TASU'A DA ASHURA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #AZUMIN_TASU
'A_DA_ASHURA_DA_BIDI_OIN_DA_AK
A_QAGO_ACIKI
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki
muna gode masa muna neman taimakon muna
neman gafarar sa, Muna neman yakare mu daga
miyagun aiyuka!!
Wanda ALLAH Ya shiryar shine shiryayye babu
mai iya batar dashi, Wanda kuma ALLAH Yabatar
babu mai iya shiryar dashi!
Na shaida babu abun bautawa da gaskiya sai
ALLAH, Kuma na shaida annabi Muhammad
bawan sa ne kuma manzon sa.
Bayan haka, Yan uwa musulmi masu albarka
muna cikin sabuwar shekarar musulunci kuma
watan farko na shekarar, Wata mai albarka mai
falala..
Watan muharram wata ne da ALLAH Ya girmama
ya kuma karrama, kamar yadda yake fada cewa
"LALLAI ADADIN WATANIN 12 NE A WURIN KU
KARRAMA SU KADA KU ZALUNCI KAWUNAN KU
A CIKI"
Ashe kuwa duk abunda ALLAH Ya karrama to
wajibin mu muma mu karrama su,
An karbo daga Aisha r.a tace 'Mutanen jahiliya
sun kasance suna girmama watan Muharram har
suna kiransa da suna Muharram watan ALLAH
Kuma sun kasance suna kauracewa aikata sabo
a cikin '
Yana da kyau mu yawaita azumi a cikin watan
Muharram, Har ma an ruwaito daga Manzo s.a.w
cewa 'Mafificin azumin bayan na watan
ramadana shine azumin watan muharram'
Ibn Rajab yayi sharhi watan Muharram wata ne
falala da ake bukatar yawaita ibadu da
kauracewa zunubi,
Yan uwa musulmi bayan mun azumci kwana
goma a watan Zhul hijja (Watan karshe), Yanzu
kuma sai mu azumci kwana biyu a watan
muharram (Watan farko) za'a rubuta mana ladar
mun fara shekara da ibadah kuma mun kammala
ta da ibadah, Daga hakanan sai a sanyamu cikin
bayi na kirki.
Lallai an mustahabanta muna azumtar wannan
rana domin dinbin falalar dake ciki, An ruwaito
daga Manzo s.a.w cewa 'Azumin 10 ga watan
Muharram ina da yaqinin ALLAH Yagafarta
abunda yagabata'.
Jabir r.a ya ruwaito cewa 'Ban taba ganin manzo
s.a.w na kirdadar zuwan wani azumi ba kamar na
goma ga muharram'
Harma kuraishawa kafin zuwan Manzo s.a.w
suna azumtar wannan rana.
Hakama sadda Manzo yayi hijra zuwa Madina ya
tarar yahudawa nayin wannan azumin, Sai ya
tambaye su miyasa kuke azumtar wannan ranar?
Sai suka ce munayi dan murnar nasarar da
ALLAH Yabaiwa annabi Musa A.s akan fir'auna,
Sai Manzo s.a.w yace 'Ai mune muka fi
chanchanta muyi domin Musa dan uwan mu'
Amma tun yana Makkah yana wannan azumi ya
tambaye su dan yaji hujjar da suka dogara da ita.
Azumtar wannan lokachin nada falala da dama
ga wasu daga cikin.
*Manzo s.a.w yayi, Kenan yasamu falala daga
Manzo s.a.w
A yanzu munyi sa'a kasancewa gobe ne tara ga
wata sai mu tashi da tasu'a jibi muyi ashura.
ABUBUWAN DA AKA KIRKIRO A WANNAN
WATAN
Wasu na shafa kwalli, Wasu na lalle wasu na
dinki da dafe dafen abinci!
Wasu kuma baqin ciki a wannan rana, Har suna
koke koke da saran jikin juna da sauransu!
To a maganar gaskiya wannan baida asali daga
kowane magabaci na kwarai, Wasu kuwa na
cewa awadata gida da abinci wai saboda
shekarar zata kasance ma da kyau.
Wadanda sukeyi wannan kirkiren sune suka
kashe sayyidina Aliyu r.a suka kashe Hassan r.a
kuma suka kashe Hussaini R.a.
Su kuwa nawasib sune suke murna saboda sune
suka kashe ahlul baiti.
Yan shi'ah sune suka kashe sayyidina Hussani
r.a a Karbala kuma sun kashe mahaifinsa Aliyu
R.a, Dukkansu sunyi shahada.
Yan shi'ah sun tanadi ranar ashura a matsayin
ranar baqin ciki, Har suna yanka jikin su da
aikata rashin imani ga yara, Wannan yasabawa
musulunci da kuma lafiyayen hankali, Kuma
babbar alama ce dake nuna yadda addinin Shi'ah
yayi hannu riga da musulunci kuma yana nuna
cewa Shi'ah addini ne mai zaman kansa.
Annabi Zakariya A.s, Da Hassan r.a, Da Umar r.a
da Aliyu r.a duk kashe su akayi amma miyara
basu baqin cikin kashe su??
A musulunci babu wata rana da aka tanada dan
baqin ciki, Idan ma za'a sanya to ranar data fi
chanchanta itace ranar da Manzo s.a.w yabar
duniya. Domin Manzo s.a.w yace 'Duk wanda
wata musiba ta sama ko ta rashi to yayi hakuri
domin rashina shine babbar musiba'' !!!!
Shari'ah ta yarda idan akayi maka rassuwa kayi
jimami har da kuka tsawon kwana 3, Amma
abunda yafaru shekaru dubu daya da wani abu
da ya gabata.
Lallai muyi tsayin daka waje yakar shi'ah a
gidajen mu da yayan mu.
A ranar Ashura yan shi'ah nayi babbar bajakoli
da izgili da zagin sahabbai, Alhali Manzo s.a.w
yace "Kada ku zagi sahabbai na domin wallahi
koda dayanku yaciyar da kwatankwacin dutsen
uhudu na zinare bazai kai muddunsu daya ba, Kai
koda rabinsa!"
Wannan na nuna wallahi koda duk mutanen
duniya zamu bi ALLAH Da ibadah har tsawon
shekara bazamu kai nasu da kwana daya ba!! Ko
da rabi ma..
To mutane masu daraja irin haka kuma sune za'a
zaga??
Yan shi'ah na ziyartar makabartu har suna
ziyartar kabarin Hussaini r.a suna cewa' wai duk
wanda ziyarci kabarin sau daya yafi aiki hajji sau
ashirin' Kunj4 wani cin mutunci!!
A ranar ne suke aikata auren mutu'a!!
Lallai babban dalilin yin azumin shine ranar ne
ALLAH Ya halakar da fir'auna.
Yan uwa musulmi masu albarka an samu sabanin
lissafi inda wasu ke cewa yau tara ga wata, A'a
yau ne takwas ga wata kuma a kasar Saudiyya
yau tara ga wata, Sai dai zamuyi amfani da
abunda ke kasar mu!!
Muna rokon ALLAH Yabamu zaman lafiya, Yayi
jagora ga mai martaba Emir na Tsafe, Da kuma
gafarta margayin daya rassu, Ya ALLAH Yayi
salati ga Manzo rahama da iyalansa da
sahabbansa da wadanda suka biyo bayansu da
kyautata, Ka rahama mana ka biya mana bukatun
mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Yau Jumu'a 8-Al-Muharram 1439 AH
Friday 29-September-2017

HUDUBA MAI TAKEN HARAMCIN CAMFI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE


A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #CHAMFI
Godiya ta tabbata ga ALLAH Wanda ya halicci
duniya da abunda ke cikinta, Godiya ta tabbata
ga ubangiji daya ubangijin rana da wata, Godiya
ga wanda kagemu ya bamu ikon gudanar rayuwa.
Tsira da amincin ALLAH Su tabbata ga mafi
soyuwa wajen ubangiji, Annabi Muhammad s.a.w
da iyalansa da sahabban da duk wadanda suka
biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako muna rokon ya shiryar damu hanya
madaidai ciya ameen.
Yan uwa musulmi masu albarka a yau Khudbar
tamu zatayi magana ne game da #CHAMFI!!!
#CHAMFI wato ana nufin danganta faruwa ko
afkuwar wani abu na rayuwa ko mako bayan ta,
Ga lokachi ko zamani ko kwana ko wata ko
shekara ko dan Adam, Ko aure ko mutuwa da
sauransu!!
Bayan Manzo s.a.w yafa mana cewa "Duk wanda
ke #CHAMFI to ya tabbatar yayi shirka"
Shirkar kuwa zata iya kasancewa rakama ko
kuma babbah!!
Jingina faruwar wani abu ga aure ko shugaba
duk wani musulmi mai tauhidi yasan babban
kuskure ne.
Wasu kuma da danganta rashin lafiya da
#CHAMFI da kuma masu danganta duk wani
abunda yasame da #CHAMFI!!
Yan uwa musulmi masu albarka
Babu inda ya halatta ga musulmi yayi #CHAMFI
sai a wuri daya shine kayi #CHAMFI ga kanka
wato duk abunda yasameka a rayuwa ka dauka
cewa daga laifukan da kake aikatawa na rayuwa!
Shi #CHAMFI tsohon abu ne dake da tsohon
tarihi wato ba daga hausawa ne aka fara yin
#CHAMFI ba, Bari muji kadan daga wasu
al'ummah dake aikata #CHAMFI-
Yahudawa sun # CHAMFA Annabi Salihu (a.s)
domin yazo ya isko su cikin bata da shirka,
Yafara yi masu wa'azi ba dare ba rana, Da suka
qi yin imani sai ALLAH Ya jarabce su da musibu!
To sai suka fara yin #CHAMFI cewa Annabi
Salihu (A.S) yakawo masu!
Mushrikai na Makkah suma sun #CHAMFA
Manzo (s.a.w) domin ya isko su cikin kafurci da
bata, Yayi masu wa'azi da suka qi karba sai
ALLAH Ya jarabce su da talauci da rashi!
Suma sai suka #CHAMFA Manzo (s.a.w) cewa
kafin yazo suna cikin arziki, Amma da yazo sun
fara fadawa talauci!
Idan muka diba rayuwar mu ta Najeriya zamu ga
cewa kwatan kwacin rayuwar nan ta same mu, A
baya yan kasa na cikin wadata amma a yanzu
talauci wane hali muke ciki??
To nan yakamata yayi tauhidi yayi amfani,
Garemu.
Yan uwa musulmi masu albarka, Yakamata mu
kara sani talauci da arziki da komai da komai duk
suna hannu ubangiji, Amma sai mu dora laifi kan
shugabanin mu, Shin mu manta cewa akwai yan
Najeriya masu aikata Shirka wanda sune
kolulowar laifi ga ubangiji.
Mun manta fadar ALLAH s.w.t daya fada cewa
"DUK ABUNDA YASAME KU DAGA ALLAH DA
AYYUKAN DA AIKE AIKATAWA"
Hakama madaukakin sarki na cewa "DUK
ABUNDA YASAMU KU MAI KYAU DAGA ALLAH
MARAR KYAU KUMA DAGA ABUNDA KUKE
AIKATAWA NE"
Shi #CHAMFI inkari ne tauhidin rububiya.
Yan uwa musulmi masu albarka, Akwai abunda
jahilai keyi na #CHAMFA Watan safar wato
watan da muke ciki, Ma'ana wata na biyu a
musulunci, Jahilai sun kasance suna kauracewa
aikata ayyuka kamar aure da tafiya da sauransu!!
Sai Manzo s.a.w yace "Babu komai a watan
Safar, Wata ne kamar saura"
Akwai masu alaqanta cuta da #CHAMFI, a yanzu
turawan yamma na farfaganda ta cewa suna
cuta kamar ta sauro da sauransu, Wai sai suce
sun karar da ita, Hakika ita cuta tana samuwane
da iko da iznin ALLAH.
A cikin ayyukan turawa akwai tuka da warwara.
A cikin wannan watan akwai musulmi da suke
cewa wai ALLAH Na saukar da annoba dubu
ashirin da uku (23, 00.000) wai suna cewa ayi
nafila raka'a 4 da fatiha kafa 7 idan kagama za'a
rubuta 'Salamun ala nuhin' a rubuta a sha.
To wannan baida asali a musulunce kuma bidi'ah
ce!
Su duka al'amura da faruwa ne da ikon Allah.
Babban tabi'i imam alhambali yace "Kebance
wani lokachi dan a aiyana cuta garesa kuskure
ne"
Wani fasihin mawaki na cewa 'Muna ta dorawa
zamani laifi mun manta mune ke aikata laifin ba
zamani ba'
Yan uwa musulmi masu albarka, A kowane
lokachi mu zama masu imani domin bamu san
inda ajalin mu yake ba!
A takaice dukan wani abu da ake aikata wato
#CHAMFI shirka ne kuma bata ne!!
ALLAH Yabiya bukatun mu ya gafarta mana yayi
rahama garemu, Yabamu zaman lahiya mai
dorewa.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 13-Safar1439 AH
Saturday 03-November-2017

HUDUBA MAI TAKEN LAYYA DA HUKUNCE HUKUNCENTA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #LAYYA_DA_SALLAR
_IDI_DA_ABUBUWAN_BUKATA_A_WANN
AN_WATAN_DA_KYAWAWAN_HALAYE_A_
WAJEN_BIKIN_SALLAH
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin
sarki,Muna gode masa,Muna neman taimakon
sa,Muna neman ya kare da sharrin kawunan mu
da miyagun ayyukan mu, Tsira da amincin ALLAH
Su kara tabbata ga manzo tsira, Annabin rahama
sallallalahu alaihi wassalam, Da iyalansa da
sahabban sa da dukkan wadanda suka biyo
bayan su da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako.
Yan uwa musulmi yau Khudbar zata magana ke
wannan halin da ibadu dake gaban mu,
Yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Gaskiyar jin
tsoron sa, Kamar yadda umarce, Kuma mu kara
gode masa kamar yadda ya umarce mu, Sannan
abu ne mai kyau mu dage da ambaton ALLAH A
Wannan lokachin kamar ya umarce mu da cewa
"YAKU WADANDA KUKA YI IMANI KU AMBASHI
ALLAH AMBATO MAI WAYA KUYI KUMA TASBIHI
GARESHI"
Yan uwa masu albarka muyi tseararre a wannan
lokachin (Anan ana bukatar tsere) domin suna
cikin kwanakin da Allah ya kebance dan rahama
da tausayi ga bayin sa!
Yawaita ambaton ALLAH A cikin wannan lokachi
abu ne mai matukar muhimmanci, Hasalima an
ruwaito Abi Huraira R.a ya kasance yana shiga
ko ina yana yawaita yin kabbori, Har cikin
kasuwa yana shiga dan tunasar da yan kasuwa
da masu sayyayya, Yana daga murya yana cewa
'Allahu akbar Allahu akbbar, Allahu akbar wallahu
Akbar walil lahil hamdu'
>LAYYA
Daga cikin kwanakin goma akwai wata babbar
ibadah da ake aiwatar a wannan watan, Layya
nada sharudda
-Amfani da kudin halal wajen sayen dabbar
zakuyi amfani da ita,
Ita layya Sunnah ce daga sunnar annabawa,
Annabi Ibrahim A.s da kuma Annabi Muhammad
S.a.w , Inda tayo asali shine lokachin da annabi
Ibrahim yayi mafarkin ya yanka dansa wato
Annabi Isma'il A.s, Alqur"ani yabamu labarin
cewa Ya yanka dan nasa"SAI MUKA FANSHI
YARON DA ABUN YANKA MAI GIRMA (Rago)"
Layya abu ce dake kara kusanta bawa da
ubangijin sa, ALLAH Ya umarci Manzo s.a.w da
zuwa sallar idi, Da layya kamar yadda yake fada
cewa "KAYI SALLOLI KUMA KA YANKE LAYYA
KA DAN ALLAH DA KUMA TSARKAKA WAJEN
ALLAH"
Hadisi yazo daga sahabin manzo s.a.w cewa
"Mun kasance da ranar arfa da Manzo s.a.w
yace lallai yazama tillas ga kowane gida suyi
layya"
Ashe yazama wajibi ga kowane gida suyi layya,
Malamai sunce gida guda suna iya hadawa asayi
dabba dan ayi layya!
Hakama wani hadisi da yayo ya tsoratar da masu
tabi'ar matsolanci cewa "Manzo s.a.w yace 'Duk
wanda keda wadatar yin layya baiyi ba to kada
ma yaje massallachin idi' "
Sau da yawa zakaga magidan ci a ranar jajibiri
ya sawo wancan ya sawo wanchan, Dan adafa
abinci amma ya kasa yin layya, Ita wannan sallar
ba sallah bace ta dafe dafen abinci, Sallah ce
yanka layya!
Sheik Muhammad bn fodio yace: 'Idan bakayi
layya ba, Kuma ka dafa abinci ko wannan abincin
bidi'ah ce '!!
*Layya ta hau wajibi ga kowane musulmi, baligi,
Mai hankali, Mai wadata, Mazaunin gida, Amma
kananan yara sunnah ce, Yin layya koyi ne da
Manzon rahama s.a.w.
Ibn taimiyah yace 'A ibaduh na jiki babu kamar
sallah, A ibada ta kudi kuma babu kamar layya'
Layya ana yin tane daga dabbobin ni'imah wato
sune kamar haka-
~Rakumi rakuma
~Sa ko saniya
~Rago ko Tunkiya
~Bunsuru ko akuya.
Wadannan dasu ne kadai ake yin layya!
Sau da yawa zakaga wasu na sakaci wai da
sunam suna jin kunyar yanka bunsuru ko tinkiya
ko akuya, Dan basu da halin sayen Rago, Wannan
bai dace ba, Hausawa ma suna cewa dai dai kurji
dai dai ruwa!!
Yan uwa musulmi masu albarka, Sai dabbar layya
ta cika wadannan sharuddan sannan take layya,
~Rakumi ko rakuma sai sun kai shekara 5
~Sa ko saniya sai sunkai shekara 2 zuwa ta 3
~Bunsuru ko akuya sai sunkai shekara 1 zuwa
cikin ta 2
~Rago ko tunkiya sai sun kai shekara 1 !!
Duk da akwai basu dake cewa ana iya yanka mai
wata 6, Amma wannan bai inganta ba!
Dole ne dabba ta tsarkaka daga aibi, Wato wasu
kuma sharudda kamar haka,
~Ba'a layya da mai ido daya
~Rashin lafiyar da data baiyana
~Dabba mai gurgunta
~Tsohuwar dabba marar mai marar bargo
~Mai yankakke kunne, Ko bindi ko marar hauru
da sauran illoli baiya nan nu, DUK BA'A LAYYA
DA SU!!!
Ana son dabba wadda idan ka kalle ta zakaji
wadata.
Idan ka sawo dabba sai daya daga cikin matsalar
chan ta same ta, Malamai sunce ba ba komai
abunda dai ba'a so shine kaje saye kaganta da
wannan illar kuma ka sawo.
Hikmar dake cikin layya:
1-Kusanta bawa da ALLAH Domin ciki umarni ne
Na ubangiji kamar yadda madaukakin sarki ke
cewa "ALLAH BAYA BUKATAR NAMA KO JINI
YANA BUKATAR TSARKAKE NIYA"
2-Dan samarwa mabukata, Wato rabawa
wadanda basu yi ba, Saboda rashin hali
3-Kara soyyyaya tsakanin musulmi, Duk wanda
ya dauki nama ka bashi zaiji farin ciki da kara
sonka
4-Alamace ta daga addinin Allah, Domin yin layya
daga addini ne,
5-Koyi ce da jagorori wato annabi Ibrahim A.s da
Annabi Isma'il A.s, Mu diba fa annabi Ibrahim a.s
ce masa akayi yayi layya da dansa,Kuma ya
dauki azamar yi,
6-Yin layya ko ne da alhazai, Su suna yin hadaya,
mu kuma dake gida muna yin layya.
SALLAR IDI
Sai kuma bangare na biyu, Manzo s.a.w ya
wajabta mana sallar idi, akwai hadisi daga
manzo s.a.w da yake cewa "Manzo s.a.w yazo
garin yasrib (Madina) ya iske suna yi wassani
biyu a shekara, Sai manzo s.a.w yace ku aje
wadannan ga wasu nan wato ranakun sallah"
Manzo s.a.w yayi umarni a fita a ranar sallah
zuwa idi, Har wata mata tambaye sa to ni ina
son fita amma banda hijabi sai yace kije ki aro.
harda mata masu haila suna iya fita,
IDAN RANAR JUMU'A TA HADU DA RANAR EID
Manzo s.aw. idan ranar JUMU'AT Ta hadu da
ranar Eid to kana da zabi, Ba sai kayi jumu'a ba,
Amma Abu hurairah yace mu muna yi dan samun
lada mai yawa, Anyi haka dan falala garemu,
Saboda hidimar sallah wani na'iya mantawa da
sallar jumu'ar mah,
MIYAGUN DABI'U RANAR SALLAH
Ranar sallah rana ce ta farin ciki da murna,
Wadda musulunci ya ware muna a shekaru sai
biyu wato sallar azumi wato karamar sallar sai
kuma sallar layya ko kuma babbar sallah,
A lokachin sallah ana ado sosai kuma ana
ziyartar yan uwa da abokan arziki, Ko kiran waya
da dai sauran hanyoyin sada zumunta, Sai da
kash!
Ana samun masu amfani da wannan damar suna
wuce wuri har suna afkawa cikin haramun, Kusan
yazama al'adar wasu iyaye ta kyale yayan su
suyi abunda suka ga dama a ranar sallah ba tare
da taka masu burki ba,
A ranar sallah zakaga matasa musamman yan
mata sun chaba ado sun fito, Kirjin su a waje,
Bayan su a zahiri, Duk suna murnar sallah!
Wasu kuma a ranar suke fara iya shaye shaye
musamman samari, Wasu ma matasan a ranar
suke iya zina, Anan arewa cin Najeriya musan
yadda yayan mu suka tarbiyan tu da rufe jikin su
ta hanyar hijabi, Amma abun takaici zakaga wasu
ko gyale ma basu sawa,
Suwa keda laifi??
Manyan manyan masu laifi sune iyaye, Idan aka
ce iyaye ana nufin iyaye maza da iyaye mata,
Laifin uba anan shine shine ke sawo kayan to
dole kai zaka saka ido kan yadda za'a dunka
kayan dama yadda za'a sanya su, Zakaga uba
yasawo kaya kawai ya baiwa yayan, Haka bai
dace ba sam!
Ita kuma uwa ita ce ake kai dinkin agabanta,
Wajen sanya kayan ma agabanta, Amma bata iya
tsawatarwa akan abunda ke yi na kuskure, Iyaye
ku tuna Manzo Allah s.a.w yace mana "Dukkan
ku masu kiwo ne kuma za'a tambaye ku game da
abunda aka baku kiwo"
Masu laifi na biyu sune shuwagabani, Dole ne
shugabanin ku dauki matakan gyara tarbiyar
al"ummar su ta hanyar sanya idanu aka harkokin
su, mai makon haka sun bar al'umma kara zube
Na ukku sune malamai, Malamai sune suka san
hukuncin addini, Kuma sune masu wayar da kai
ta hanyar nasihohi da khudbobi da sauransu, Dole
ne malamai su zage damtse ka'in da na'in wajen
tabbatar da tarbiyar al'umma dan samun manya
gobe na kirki,
Manzo s.a.w yana cewa '"Mata ku zauna cikin
gida jen ku kada hali inyi na jahiliyah (fita
barkata)"
Sannan manzo s.a.w yakawo hadisi mai
tsoratarwa da yake cewa "Mata 2 yan wuta ne,
Ni ban gansu ba, Idan kun gansu ku tsine masu,
Sune masu sanya tufa amma basu sanya ba, Na
biyu sune masu fitar da gashi waje basu shiga
aljannah ko kan shinta bazasu ji ba, Duk da
akwai nisa daga kaza zuwa kaza"
Abun takaici wasu yan mata har dakunan samari
suke shiga da sunan yawon sallah,
Wasu kuma baso da murnar sallah basu yin
sallah suna ji ana kira amma basu zuwa, Dukka
dai muna fatar za'a gyara.
ALLAH Madaukakin sarki ya gafarta mana ya
rahama, Ya biya mana bukatun mu, Yayi rahama
ga mamatan mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'a 3-Zhul-Hijjah 1438 AH
Friday 25-August-2017

HUDUBAH MAI TAKEN RAMADANA DA ABUNDA YA KUNSA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #FALALAR WATAN
RAMADAN DA ABUNDA YA KUNSA
Godiya ta tabbata ga ALLAH Wanda ya sanyawa
bayin sa alamomi da zasu zama alama garesu da
yin bauta a lokachin,
Tsira da aminci su tabbata ga wanda ALLAH Ya
aiko da gaskiya da iyalansa da sahabbansa da
dukkan wadanda suka biyo bayansa da
kyautatawa sallallahu alaihi wassalam,
Yan uwa musulmi muna fuskantar wani yanayi
mai matukar alfanu, Wanda yana kyau muci ribar
wadannan kwanuka mu yawaita taimakon kanmu,
Mu yiwa kawunan mu hisabi, Yakamata muyi
amfani da wannan dama wajen neman gafara da
yafiya daga ubangiji ALLAH,
Watan ramadana wata ne mai alfarma wanda
ALLAH Yasanya shi daga cikin rukunan
musulunci, Ramadana wata ne na tausayi da
rahama da taimakon juna.
A cikin watan ramadan akwai wata rana wadda
tafi dare dubu,
Yan uwa musulmi mu karrama wannan watan da
abubuwa guda biyu (2), Na daya ALLAH Ya ara
mana rayuwa ta kawuwa wannan watan, Sai
kuma zuwan watan na ramadan mai albarka,
Yan uwa musulmi akwai abubuwan da yakamata
mu aikata a cikin wannan watan mai kamawa,
Daga cikin su akwai;
-Mu roki ALLAH Ya yarda damu, Ya karbi dukkan
ibadun da mukayi, Duk wanda aka karbi ibadun
su a cikin watan ramadan to yayi murna yayi
farin ciki,
Lallai kololowar murna ita ce kayi murna da
zuwansa, Da kuma ni'imar halartar sa, Akwai
wanda yafara jin kanshin sa Amma ALLAH Bai
nuna masa ba, Baya daga cikin addini yin murna
walau ta samun matsayi ko dukiya kamar yadda
aya take cewa "GASUNAN SUNA FARIN CIKIN
DAN SAMUN DUNIYA ALHALI BA KOMAI BACE
IDAN KA KWATANTA DA LAHIRA"
-Kiyaye salloli na farilla a cikin lokachi, Idan har
baka sallah cikin jam'i to yakamata kayi amfani
da watan ramadan dan koya da yin sallah cikin
jam'i
-Kaucewa yin sabo, Kaucewa aikata sabo kowane
irin, Ba kauracewa ci da sha ne kurum azumi ba,
A'a harda kiyaye gabobi baki daya daga aikata
zunubai,
-Mai hankali baligi ya sanya a ransa zaiyi azumi
dan ALLAH, Dan kwadayin lada, Da kuma
kaucewa fadawa azabar ALLAH.
Muddin aka samu mutun kawai zai yi azumi dan
yazama dole, Dan kada ace wane baiyi to akwai
matsala, Yakamata a gyara dan samun ladar da
ake nema.
Azumin watan ramadan yana farawa ne da zarar
wata sha'aban yakai ashirin da tara idan ba'a ga
wata ba kuma yakai talatin, kamar yadda hadisi
daga manzo rahama na cewa "KUYI AZUMI IDAN
KUNGA WATA KU AJE IDAN KUNGA WATA"
Idan har mai alfarma sarkin Musulmi yabada
umarnin daukar azumi, To kada ayi wata wata
wajen dauka,
Idan aka bada umarni to akwai abubuwan da
yakamata ayi kamar;
-Kulla niyyah a zuciya, Ba ambatawa da baki ba,
-Sallar tarawihi, Ko a daren yau za'a iya fara
tarawihi dama ana bukatar a tari wannan watan
da aiyuka na alheri dan su zame ma jiki, Idan
watan yazo zaka iya,
>Yan uwa musulmi abunda ake cewa azumi shine
barin chi da sha da kame gabobi, ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KUCI KUSHA HAR
SAI BAKIN ZARE YA FITO DAGA ALFIJIR"
=Hakama yakamata ladanai kuji tsoron ALLAH
kada ladanai su kuskura su kira sallah kafin
lokachi yayi ko bayan lokachi, A yanzu muna
cikin yanayi na damina wanda gari ke laulayewa,
Jiya anan Tsafe anyi ruwa, Wasu ladanai sunyi
kiran sallah tun karfe 6:30pm, Maimakon
6:55pm.
Anan fa mutane uku ne keda laifi na daya Ladani
shi da ya kira sallah kafin lokachi yayi,
Sai kuma limani wanda shine jagora yaje yabada
sallah,
Sai kuma mamu wanda yakamata ku lura da
jadawali, Kafin sallah!
Anan jahar, Gwamnati tana raba jadawali a duk
wani massallaci komai yadda yake cikin lungu,
Kada kuma sai ladani yaci yakoshi har lokachi ya
wuce sannan yace zai kira sallah,
Idan ladani ya kira sallah lokachi baiyi ba, To
Ladani ne keda alhaki na karewar azumin su,
Alfijir na fitowa ne 04:55/6, Magrib 06:55, duk
yanayi n chanzawa, A kula sosai idan ladanai
sunyi kuskure mafita kurum a dinga diba
jadawalin da gwamnati ke kawo, Kowane lokachi
basai radaman ba.
-Tarawihi babbar sunnah ce dake nuna alamar
tsayawar ramadan, Ana samun falala a ciki.
Limamai aji tsoron ALLAH
Limamai aji tsoron ALLAH
Limamai aji tsoron ALLAH
Sau da yawa zakaga limamai na wulakanta
sallah, Ta hanyar yin qoton kurciya da yin ta
yadda aka ga dama,
Manzo rahama na cewa "KUYI SALLAH KAMAR
YADDA KUKAGA INAYI"
To sai ayita gwargwadon hali,
Wani mutun yazo yana sallah yagama yazo
wajen manzo ALLAH Sai manzo s.a.w yace ka
koma kayi sallah dan bakayi sallah ba, Sai da
akayi sau 3, Daga nan manzo s.a.w ya gwada
masa yadda zaiyi da kyau ta hanyar jeranta
kira'a da yi anatse da cikin ruku'u da sujjada,
=Yana da kyau a rage sautin amsa kuwa (Loud
speaker), Domin kada karatu na chan dana chan
su hade sai kaji duk abu ya rikice.
Wata rana Manzo s.a.w ya shigo massallaci ya
tarar kowa na sallar sa anan yahada su kan
limami daya wato Ubaiy bn Ka'af R.A
Hakama wajen yin tahujjud akiyaye.
Yan uwa musulmi manzo s.a.w ya kai karshe
komai game da ganin wata, Idan an samu rikici
to ko kaine ko wani ne ya rikice, Manzo rahama
s.a.w na cewa "IDAN KUKA DAUKA BA'A GANI
BA KU CIKA TALATIN"
Idan sarki musulmi ya bada sanarwar angani ka
sallama kawai ka dauka,
Kasar Saudiyya Yau watan su talatin yake amma
mu 29, Idan mungani zamu dauka anan Najeriya,
Yan uwa musulmi a cikin watan ramadana ana
bukatar taimakon juna, A taimakawa talakawa da
abinci koda koko da kosai ne, Domin wani ko
abincin buda baki baida shi, "Manzo s.a.w ya
kasance idan watan ramadan yazo yakan yawaita
alheri kai kace iska ne ya taso".
Ka taimaki yan uwa musulmi anan za'a gane
kana taimako.
Kuma taimako bawai sai masu kudi ba kowa
yasan wanda yafi sai ka taimaka masa, ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KU TAIMAKA A KASA
NI DAKE SAMA ZAN TAIMAKA MAKU"
Muna rokon ALLAH Sunayen kyawawa, Tsarkaka
ya biya mana bukatun mu, Yayi mana gafara da
rahama, Ya karbi ibadun mu wadanda mukayi da
wadanda zamuyi,
Ya ALLAH Yabaiwa shugaban kasa da Mai
martab emir na Tsafe lafiya, Yayi jagora ga
shuwagabanni mu, Ya shiryamu hanya madaidai
ciya.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
29/Sha'aban/1438
26/05/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN SABUBBAN DAKE SA A SHIGA ALJANNA

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan SABUBBAN DAKE
KAIWA ZUWA GA ALJANNAH DA KUMA CIKAWA
MAI KYAU DA KUMA MASU KAIWA ZUWA WUTA
DA CIKAWAR MARAR KYAU
Godiya ta tabbata ga ALLAH Muna gode masa
muna neman taimakon sa, Mune neman yakare
daga sharrin kawu nan mu,
Duk wanda ALLAH Ya shiryar babu mai batar
dashi, Duk wanda ALLAH Yabatar babu mai iya
shiryar dashi,
Tsira da amincin ALLAH Su kara tabbata ga
mafifin halittun manzo tsira, Da iyalan da
sahabban sa, Da dukan wadanda suka biyo
bayansu da kyautatawa.
Yan uwa musulmi muyi gaggawar tuba zuwa ga
ALLAH Dan neman yagafarta mana daga laifukan
da muke aikatawa,
Ibadar da muke aikata duka bata kara ALLAH Da
komai, Hakama Fandare mai bai ragesa da
komai, Kamar yadda yake fada cikin hadisul kudsi
cewa ''YAKU BAYINA IDAN ZAKU KURE WAJEN
BAUTA MANI BAZAKU KARANI DA KOMAI BA
KUMA IDAN KUKA KAFURCE MANI BAZAKU
RAGE NI DA KOMAI BA''
YAN UWA MUSULMI Hakika aikata ayyukan alheri
suke kai mutun ga samun aljannah, Kolololuwar
sune ayyukan zukata,
Sannan aiyukan jiki sune ke taimaka ma zuciya
hadisin sahihi ya tabbata cewa ''DUKAN AYYUKA
TARE DA NIYA SUKE TAFIYA''
Aiyukan marar sa kyau kama daga Cuta, zalunci,
Yaudara munafucci E.t.c suke haddasa halin da
muke ciki kamar yadda ayar Qur'ani take cewa
''BANNA TA BAIYANA A SARARI DA KUMA CIKIN
TEKU SABODA AYYUKAN DA HANNAYE KE
AIKATAWA''
Ya yan uwa musulmi yin bauta dan ALLAH Dayin
wasiyya ta kwarai na jagoranta zuwa ga aljannah
hadisin ingantacce na cewa ''ANA CIKA AYYUKA
DA AIKI NA KWARAI DA KUMA CIKI MUNANA
MUMMUNAN KARSHE''
Yan uwa musulmi muyi dukan mai yiwuwa wajen
ganin mun cika da kyawawan ayyukan da samun
tsira gobe kiyama, ALLAH Yana gargadar mu
cewa a suratu ali imran cewa '' KUJI TSORON
ALLAH KADA KU MUTU FACE KUNA MUSULMI''
Kunga kenan wajibi mu nemi yin ayyukan kirki,
Da neman yafiya dan haduwa dashi da imani!
Yaku yan uwa musulmi shagaltuwa da ayyuka na
alheri sa samun cikawa ta kwarai, Hakama
Annabawa kamar su Ibrahim A.S Da Yunus A.S
Sunyi wasiya ga ''Kada ku bautawa kowa in
banda ALLAH'' Kunga wasiya ce mai kyau,
Ababen dake sanya Cikawa mai kyau nada yawa
ga wasu daga ciki
1-KYAKYAWAR NIYA Niya mai kyau wajen aikata
aiyuka.
2-IHLASI wato yi dan ALLAH Kai tsaye
3-KULA DA TSARE LOKACHIN SALLOLI CIKIN
JAM'I wato yin sallah a lokacinta kuma cikin
mutane.
4-GYARA Jawo al'umma zuwa ga hanyar gyara
da zata taimaka masu wajen kara kusanci da
ALLAH Kamar yadda ayar Qur'ani ke cewa ''DUK
WANDA YAYI AIKI NA KWARAI BAI DA TSORON
LOKACHIN MUTUWA''
5-TSORON ALLAH FILI DA BOYE
6-LIZIMTAR SUNNAH DA KOYI DA MAGABATA
NA KIRKI
7-KYAUTAMA AL'UMMA Yi masu fara'a, Da
yawan yi masu kyauta, Da Sadaqah da kuma
yawan yi masu sallama, Duk yana cikin
kyautawa. ALLAH Yana cewa ''WADANNAN
MASU TAIMAKO A FILI DA BOYE TO BABU
TSORON RANAR MUTUWAR SU''
8-KAMEWA CUTAR DA AL'UMMA
9-YIN ADDU'A Kamar yadda ALLAH Ke cewa ''KU
ROKE NI ZAN KARBA MAKU WADANNAN MASU
GIRMAN KAI DA ROKON ALLAH ZASU SHIGA
JAHANNAMA''
10-ADDU'A GA JAMA'A Wato yin jam'in addu'a
ga kamar cewa ALLAH Ka yafe mana, kayi mana
rahama ka gafarta mana, Hadisi ya tabbata cewa
''AKWAI MALA'IKA WANDA DUK KAYI ROKO SAI
YACE KAIMA HAKA'' kunga kenan idan muka roki
ALLAH Da roko mai kyau ko marar kyau duka
zata iya dawowa garemu.
Yaku yan uwa musulmi muyi hattara tare da
kiyaye aikata miyagun aiyuka, Da zarar ka mutu
babu imani to haqira kayi babbar hasara,
Suna da matukar yawa amma ga wasu daga
cikin su.
1-MUNAFURCI Wanda yanzu yazama ruwan dare,
A tsakanin al'umma wanda yake kaiwa ga
mummunar makoma
2-TOZARTAR DA SALLAR FARILLA Tozarta salla
ta farilla yana kaiwa zuwa ga zuwa wuta.
3-JAHILCI Wato rashin karatun addini, Da kin
gaskiya.
4-RASHIN SALLAR JUMU'A Tabbas rashin sallar
jumu'a yana kaiwa kai tsaye zuwa ga wuta.
5-RASHIN JAM'I Sai kaga kawai mutun yaki zuwa
massallaci, Yayi zaune yana sallah a gida.
6-SATA
7-CHIN MUTUNCI
8-KARYA wadda yanzu ta zama kamar ado a
tsakanin mutane musamman matasa.
9-KARKATUWA ZUWA GA DUNIYA DA KIN
LAHIRA.
10-GABATAR DA SON DUNIYA BISA GA TA
LAHIRA.
11-CUTAR ZUCIYA cutar zuciya tana da fadi da
kuma yawa ga misalan ta kamar haka
-GIRMAN KAI Wanda hausawa ke cewa rawanin
tsiya ''DUK MAI GIRMAN KAI DAI DAI DA
KWAYAR ZAIRA BAYA SHIGA ALJANNAH''
-HASSADA Wadda itama kanta yanzu ta zama
ruwan dare, Da zarar wani yaga kafara samun
wani abun hannu to shikenan kyashi da hassada,
Zasu fara biyo baya.
-JI DA KAI
-YAUDARA
-MAKIRCI
-ALGUSSU
-KIN ABUNDA ALLAH KESO
-SON ABUNDA ALLAH BAYASO
Ranar kiyama Kudi da yaya basu da tasiri kamar
yadda Qur'ani ke cewa.
12-SABAMA IYAYE A wannan lokachin
musamman matasa, Suna sabawa iyayen su
wanda iyaye sune suka rene su, Suka bada
kudaden su wajen samar wa yayan su da ilmi,
Amma da zarar sun girma sai su fara wulakanta
su, Har wata rana zakaji iyaye na bidar yayan
alhali suna cikin garin, Matasa yakamata muji
tsoron Hadisi daga manzo tsira na cewa
''ALJANNAR MU NA KARKASHIN KAFAFUN
MAHAIFAN MU''
13-YANKE ZUMUNTA A wannan zamanin yanke
zumunta yana da matuqar yawa a tsakanin
al'umma, Zakaga wa da qane uwa daya uba
daya, Ko kuma uba daya ko uwa daya, Ko kuma
wata dangantaka ta jini suna gaba da juna babu
magana a tsakani, Wanda haka na jagoranta
zuwa ga mummunar makoma, Da kuma zuwa
Jahannama, ALLAH Ya karemu ALLAH
Madaukakin sarki na cewa A cikin aya mai
matukar ban tsoro ''KUJI TSORON YININ DA ZA'A
MAIDA KU WAJEN ALLAH ZA'A CIKAWA WA
KOWA DA ABUNDA YA AIKATA BAZA'A ZALUNCI
KOWA BA''
Daga karshe muna rokon ALLAH Ya gafartamana,
Ya yafe mana, Yayi mana rahama, Ya ALLAH
Muna tuwasulli da wannan aiki daya biya mana
bukatun mu, Ya gafarta ma mamatan mu, Ya
rage mana zafin nan na sama da kasa dana
Aljihu, Ya ALLAH Ka yiwa jagororin linzami ka
daukaka musulunci da musulmai, Ka kara
kasqanta kafurci da kafurai, Ya ALLAH Ka kawo
ma musulman kasar Somalia mafita akan bala'in
yunwar dake damuwar su.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
25/Jimada Akhair/1438
24/03/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN WATAN SHA'ABAN

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #WATAN SHA'ABAN
Godiya ta tabbata ga ALLAH madaukakin sarki,
Muna gode masa, Muna neman taimakon sa,
Muna kara gode masa da baiwar bamu Haske
(Qur'ani) daga garesa,
Na shaida annabi Muhammadu bawan ALLAH Ne
kuma manzo sane, Da iyalan sa da sahabbansa
da dukan wadanda suka biyo bayansu da
kyautatawa,
Yan uwa musulmi yau Khudbar mu zatayi
magana ne akan Watan sha'aban falalar sa da
kuma ayyukan da'ake bukata a aikata, Da kuma
wadanda yakamata a kaura cewa,
Watan sha'aban daya ne daga cikin watanin
musulunci, Kuma wata ne mai daraja, Wata ne
wanda ALLAH Yahada ya kasance kusa da watan
Ramadana mai alfarma!
Manzo tsira S.A.W Yana cewa ''LALLAI ALLAH
MADAUKAKIN SARKI YANA ZUBA WATA BAIWA
WATA NI'IMA A KOWANE WATA DAN HAKA MU
TASHI MU NEMETA A WATAN''
Yaku yan uwa musulmi Wannan hadisin mai
daraja yana koyar damu abubuwa guda biyu
kamar haka
1-Muyi kokari mu dinga rokon ALLAH Da dagewa
wajen bauta masa, Domin dacewa da lokachin da
ALLAH Ke raba wannan ni'imar,
Manzo S.A.W Yana yawaita azumin nafila a cikin
wannan wata mai daraja na Sha'aban! Har ma
Aisha R.A Tana cewa ''"KAI KACE YANA
AZUMTAR WANNAN WATAN NE BAKI DAYA
"" (Saboda yadda yakasance yana azumtar
wannan watan)!
Yan uwa musulmi yawaita azumtar wannan
watan zai sa dan Adam yaji sauki wajen yin
azumin farilla (Ramadana)!
2-Kowane bawa ya lizimci rokon ALLAH Kowane
lokachi, Dan dacewa da wannan lokachin, Dan
samun ingantuwar rayuwa mai albarka, Muna
Ya ALLAH Ya amintar damu tare da ruhin mu, Ya
kuma yarda damu Ameen!
A wani hadisi wanda Usama ya ruwaito yana
nuna mana muhimmancin dake tattare da azumi
a cikin wannan watan na sha'aban! Hadisin na
cewa "USAMA YANA CEWA YA MANZO ALLAH
S.A.W NAGA KANA YAWAITA AZUMI A WANNAN
WATAN (SHA'ABAN) SAI MANZO S.A.W YACE
EH NAGA MUTANE NA QIN AYYUKA A CIKIN
WATAN GASHI KUMA ANA DAGA AYYUKAN BAYI
A WATAN DAN HAKA NIKEYI DAN A DAGA
AYYUKANA AKWAI AZUMI A CIKI"
Yan uwa musulmi muyi kokari mu gyara zukatan
mu, Mu gyara ayyukan mu, Mu gyara taraiyar mu
ta yau da kullun!
Yaku yan uwa musulmi akwai wasu abubuwa
dake bijirowa a cikin addinin marar sa asali,
Wadanda shedar ke kawo mana, Daga cikin
akwai, Yana sanya mutane azumi a watan daya
gabata (Rajab), Wanda babu wani nassi
ingantacce dake magana akan haka,
Yan uwa musulmi wannan watan sunansa
Sha'aban larabawa sun kasance suna yawaita
ayyuka a ciki kama daga noma, Fatauci da kuma
komawa cikin yaqi, Saboda basu yaki a cikin
watan daya gabata!
Koda addinin musulunci yazo sai ya maida watan
sha'aban watan aiki, Amma na azumi,
Magabata na kiran wannan watan da suna watan
Qira'a, Ko kuma watan karatu, Saboda tanadi da
shiryawa zuwa watan Ramadan
Idan kai mai Qira'a ne ko tafsis yakamata kaci
gaba da yin gwaji karatun ka dan zuwan
Ramadana,
Yan uwa musulmi mu gyara bitar mu, Da tafsir
idan kai mai tafsir ne!
Ya ALLAH Ya gwada mana zuwan sa lafiya,
Watan sha'aban wata ne mai daraja kamar
manzo s.a.w yake cewa "WATAN SHA'ABAN
IDAN YAYI ALLAH NA GAFATARWA MUTANE
DUKA IN BANDA MAI GABA DA MAI SHIRKA"
Yan uwa musulmi kunji fa illar take tattare da
Shirka da kuma gaba, Dam haka duk mai shirka
ko gaba yakamata yayi gaugwar tuba,
Kada mu bari wannan garaba sar mai tarin yawa,
Mu gyara ayyukan mu ta hanyar bin abunda
musulunci yazo daci sau da qafa, Mu kiyaye
bidi'a kada muyi wa shedan biyyaya,
Akwai wasu karyayyaki da wai akwai wasu
sallalo da zikirai, Da wai akeyi a cikin wannan ,
Wanda wannan baida asali a musulunci!
Hanyoyi qalilan da aka amince a aikata a wannan
watan sune
-Tsayuwa a tauhidi
-Azumin nafila
-Yawaita rokon ALLAH
Yaku yan uwa musulmi mu fadawa iyalan mu, Da
yayan mu su sani cewa su ranka dukan azumi na
ramadana wanda ake bin su,
Dukkan wadanda keda matsala kama daga
matafiya, Mai jego, Mai haila da kuma marar sa
lafiya, Dasu ranka wadannan azumin da ake biyar
su, Domin akwai hadari ALLAH Yasamu bawa ana
binsa bashin azumi ga kuma wani ya taho,
Yaku yan uwa musulmi mu kiyaye daukar azumi
kafin kowa yadauka, Domin akwai masu daukar
azumi kafin kwana daya ko biyu, Wai da gudun
idan an samu matsalar lissafi bata shafe su ba,
To yakamata su sani cewa manzo s.a.w yana
cewa "DUK WANDA YAYI AZUMI YANA SHAKKA
YA SA6AMA BABBAN QASEEM S.A.W" Kunga
dole ne a dauka tare kuma a aje tare,
Hakama wani hadisin na cewa "AZUMIN DA
ALLAH KE KARBA SHINE WANDA AKA DAUKA
TARE KUMA AKA AJE TARE"
Musulmi kada muyi rigima, Ko bijerewa umarnin
shuwagabanin mu, Koda an samu karin bai wuce
kwana daya, Kuma akwai hadisin dake bayani kan
haka manzo s.a.w yana cewa "IDAN KUNGA
WATA KU DAUKI AZUMI IDAN KUKA DIBA BAKU
GANSA BA TO ANRUFE MAKU SHI TO KU CIKA
TALATIN"
Kungani yan uwa musulmi akwai umarni daga
manzo s.a.w! dan haka muyi biyayya ga
shuwagabanin mu dan tsira gobe kiyama,
Ya ALLAH Kabamu lafiya da zama lafiya, Kayiwa
shuwagabanin mu jagoranci, Kayi mana maganin
zafi na sama da kasa dan aljihu, Ka biya mana
bukatun mu.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
08/Sha'aban/1438
05/05/2017.

HUDUBA MAI TAKEN WATAN RAJAB

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan WATAN RAJAB DA
HUKUNCIN SA.
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki,
Muna gode masa, Muna neman taimakon sa,
Muna neman ya kare daga sharrin kwunan mu,
Duk wanda ALLAH Ya shirya babu mai iya batar
dashi, Wanda kuma ALLAH Ya batar haqiqa babu
mai iya batar shi,
Na shaida ALLAH Shi kadai yake baida abokin
taraiya, Na shaida Annabi Muhammadu bawan
ALLAH Ne, Kuma manzon sa ne, Tsira da
amincin ALLAH Su kara tabbata gareshi da
alayen sa, Da sahabbansa da dukan wadanda
suka biyo bayan su da kyautatawa,
Yaku yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Kuma
mu sakankance cewa ALLAH Fa yana ganin mu a
duk abunda muke aikatawa,
ALLAH Madaukakin sarki ya zabi mala'iku a
matsayin yan aike, Hakama yafifita wasu
mutane, akan haka ya zabi wasu daga cikin
mutane a matsayin mazanni da Annabawa,
Hakama yana fifita gari kamar Makkah da
kowane gari, Hakama ya fifita wasu watanni
daga cikin sha biyu da muke dasu, Wadannan
watanni guda hudu ne sune-
Zhul hijja,
Rajab
Muharam,
Ramadan,
Wadannan watannin ALLAH Ya fifita su dan ana
ninki lada a ciki hakama ana ninka zunubi a ciki,
Ana bukatar kowane musulmi ya girmama
wadannan watanni,
Wadannan watanin ALLAH Ya karramasu kamar
yadda yake fada a cikin suratul taubah cewa
''LALLAI ADADIN WATANNIN SHA BIYU NE A
WURIN ALLAH KUMA AKWAI MAFIYA HUDU
DAGA CIKIN SU KADA SU ZALUNCI KAWUNAN
KU A CIKI''
Hakama manzon rahama yana cewa ''LALLAI
ZAMANI YANA YIN BAGA YANA TAFIYA''
Ya chanchanci kowane musulmi ya girmama su
ya kaucewa aikata duk wani sabawa ubangiji a
cikin su,
Masu hikima na cewa ALLAH Na lunka lada ga
zunubi a lokachi mai daraja (wato wadannan
watannin)
ALLAH Madaukakin sarki yana fada cewa ''SUNA
TAMBAYAR KA AKAN YIN YAQI CIKIN WATANNI
MASU DARAJA TO KAFADA MASU CEWA FADA
KISA KO FADA A CIKIN ABU NE MAI GIRMA''
Yan uwa musulmi mun shiga wata mai daraja
wato daya daga cikin wadancan watannin,
Yawaita azumi a cikin wannan watan a kullun
haramun ne,
Ibn asqalani ya rubuta littafi daya kawo karyakkin
da ake jingina hadisai wai daga annabi
Akwai hadisai na karya wadanda ake yadawa
kuma ga wasu daga cikin su.
-Annabi bai taba yin azumin watan biyu ba ajere
sune rajab da sha'aban, Wanda shima wannan
karya ne,
-Wai sunce yace falalar rajab da sauran watanni
kamas banbancin Qur'ani ne sauran littafan
annabawa wannan shima na karya ne
-Wai sunce Yace rajab watan ALLAH Shine
sha'aban, Rajab kuwa nawane, Ramadan kuwa na
al'ummata ne duk wanda yayi sallah raka'a biyu
a cikin daren farko da kuma sallar jumu'a ta
farko a cikin dare dan aljannah ne, Wannan shima
hadisin karya ne
-Hakama sunce wai manzo ALLAH Yace babu
wani da zaiyi azumi a ranar alhamis ta farko a
rajab, Sannao ya sallaci raka'a biyu za'a rubuta
mai ladar ibada ta shekara Dubu (1000), Wannan
shima na karya ne.
Ire iren su nada matukar yawa, Hakama ana
yada irin wadannan karyayyakin a shafukan sada
zumunta, Hakama dole ne a kiyaye saboda ba
kowane keda iya tsayawa ta tantance ba,
Yaku yan uwa musulmi aduk bakin dakaji
wadannan hadisan to dauka kaji bidi'a saboda
basu da asali ko kadan a cikin musulunci,
Musulmai na girmama magana wadda ta fito
daga bakin manzo ALLAH Saboda haka ne ake
fadar karya ake yadawa dan jahilai su dauka
ibadah ne su kama yi!
Idan kuka lura duk wadannan kalaman suna da
romo mai yawa wadanda ke kaiwa zuwa fadawa
bidi'ah!
Yaku yan uwa musulmi abunda akeso a sani
shine watan rajab daya ne daga cikin watanni
masu alfarma,
Mu kiyaye yada duk wadannan karyayyakin
musamman a shafukan sada zumunta,
Idan aka turo maka wadannan kalaman na karya
to kayi amfani da hadisin nan dake cewa ''DUK
WANDA YAGA ANA AIKATA WANI ABU MARAR
KYAU TO YA HAKA DA HANNUSA KO DA
HARSHEN KO KUMA YA NUNA KYAMA DA
ZUCIYAR SA, AMMA FA WANNAN SHINE
KARAMIN MATAKI NA IMANI''
Kada mu rudu da dukan abunda mukeji a daga
wajen malamai, Sannan yazama wajibi
shuwagabannin su tashi tsaye wajen hana
wandannan bidi'oin, Yakamata suyi koyi da
sayyidina Umar bn khaddab, Inda yake bi a ko'ina
dan hana masu azumtar wannan watan!
Dole ne gwamnatoci suyi koyi da hadisin nan
dake cewa ''DUKKANIN KU MAKIYAYA NE KUMA
ZA'A TAMBAYEKU KAN ABUNDA AKA BAKU
KIWO''
Yaku yan uwa musulmi shedan fa kamar
mahauniya yake ma'ana yana rikida, Ta kowace
fuska yana kokarin yaga dan adam ya mutu bai
tuba ba, Yana bullowa wa yan adam ta hanyoyi
da dama kamar su,
-Sallah Zakaga baligi yana takirus sallat idan yayi
wata ba yayin wata, ko kuma wani bayayi gaba
daya.
-Zakkah zakaga mai kudi ya tara su kamar suyi
magana amma baya fidda haqqi ALLAH, Ko kuma
yana badawa amma yana tafka kura kurai,
-Bidi'a, Ana shedan yana samun kafa dan ya
cusawa mutane wasu aiyuka wadanda a zahiri
zakaga kamar dai dai ne, Amma kuwa bidi'ah ce
subhannallah,
Yaku yan uwa musulmi shedan fa baya kyale dan
adam har sai yaga kabar duniya,
Ya ALLAH Ya azurtamu da kaucewa aikata
dukkan abunda musulunci ya haramta,
Amma babu laifi mai yin azumin litinin da
alhamis, ko kuma azumi ukku a wata yaci gaba a
wannan watan na rajab.
Daga Karshe muna rokon ALLAH Ya gafarta
mana yayi mana rahama, Ya ALLAH Ka karemu
daga aikata bidi'oi, Ya ALLAH Ka bamu lafiya da
zama lafiya, Ya ALLAH Ka karemu daga aikata
zunubai, Muna amfani da wannan damar muyi
addu'a ga mai martaba yandoton TSAFE Akan
ALLAH Ya bashi lafiya akan neman maganin da
yajeyi a kasar India, ALLAH Yasa asamu abunda
akaje nema, Muna rokon ALLAH Ya gafartawa
mamatan mu da wadanda suka samu hadarin
mota jiya da shekaran jiya da yau.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
2/Rajab/1438
31/03/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN JUMA'AH DA HUKUNCE HUKUNCENTA

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #RANAR_JUMU
'A_DA_HUKUKUNCE_HUKUNCETA
Muna godiya ga ALLAH Mai girman muna
godemasa a bisa ni'imar ta sanya mana ranar
Jumu'a a matsayin shugaban ranaku baki daya,
Sannam ya kebance mana ranar ta Jumu'a ga
al'ummar Manzo tsira a matsayio kyauta dan
muyi zikiri da ambaton ALLAH
Sallati da tsira su kasa tabbata ga mafificin
halitta Annabin mu Muhammad Sallallahu alaihi
wassalam.
YAKU YAN UWA MUSULMI Khudbar mu ta yau
tana magana ne akan Ranar JUMU'A
Yan uwa uwa musulmi ku sani ita ranar Jumu'a
rana ce ta musamman da ALLAH Ya bamu ita a
matsayin kyauta, Dan mu kara dagewa wajen
bauta masa, Saboda mune Al'umma datafi
kowace fifiko a wajen ALLAH
Hakika Hadisi ya tabbata daga Manzo tsira cewa
''MU WADANNAN AL'UMMAR MUNE NA KARSHE
KUMA MUNE NA FARKO A SHIGA AL'JANNAH''
Yahudawa Sun zabi ranar Assabar a matsayin
mafificiya, Su kuma Nasara sun zabi Lahadi A
matsayin mafifiyar rana!
Mu kuma Al'ummar Musulmi ALLAH Yazabar
mana Ranar Jumu'a a matsayin mafificiya.
Hakika ranar Jumu'a sama take ga kowace rana
daga cikin kwanaki bakwai.
Manzo tsira yana cewa a ''FIYAYYEN YINI DA
RANA KE FITOWA ITACE RANAR JUMU'A ''
YAN UWA MUSULMI Saboda girma da matsayi na
wannan ranar, A ranar ne aka halicci kakan mu
Annabi Adam (A.S),
Hakama A ranar ya shiga Aljannah, A kuma ranar
ya fita Aljannah,
YAN UWA MUSULMI Ranar Jumu'a ne za'ayi
tashin kiyama,
Idan ka cire mutun da Aljani to dukkanin halittu
suna cikin fargaba idan ranar Jumu'a tazo
saboda suna tsammanin a ranar kiyama zata
tsayu.
YAKU YAN UWA MUSULMI
Manzo tsira yana girmama wannan rana, Yana
yawaita salati ga kansa, Dan haka yazama Muma
wajibi garemu yawaita salati gareshi, Dan salati
Gareshi kamar Addu'a ce.
Daren Jumu'a nada matukar falala wato (Cikin
dare ranar Alhamis) Ana bukatar yawaita salati a
daren, Ana Bukatar kowane musulmi ya yawaita
neman lada a dare domin shirin zuwan ranar,
Kamar misali Daren Sallah ne da ake yin komai a
ranar Jajirbiri!
YAKU YAN UWA MUSULMI Akwai Wasu ayyuka
da Manzo tsira ya kasance yake aikata a cikin
dare da rana ta Jumu'a
1-Annabi na karanta surutul Sajada, Da kuma
Suratul kiyama, A cikin sallar asuba ta wannan
daren, Saboda wadannan surorin suna bayani
game da ranar kiyama,
Daren Jumu'a nada matukar falala, Kamar yadda
yazo a cikin hadisin sa ''MAFICIN SALLAH ITA
CE SAMUN SALLAR ASUBA A CIKIN JAM'I''
Yaku muminai kunji wannan falalar mai matukar
amfani wadda yakamata mukiyaye mu dinga
halarta sallar asuba cikin jam'i!
2-An so yawaita salati a ranar yana da kyau
takaita duk wata ibadah dan mukeyi a ranar dan
samun wannan garaba sar.
Domin salati kamar addu'a ce garesa,
Manzo Tsira da kansa yana fada cewa ''KUSANI
RANAR JUMU'A AKA HAIFI ADAM KUMA RANAR
ZA'A BUSA KAHO''
3-Anaso kowane musulmi yayi wanka, Yayi tsafta
yan sanya kaya mafi kyau, Ya sanya turare.
4-Aswaki
5-Zuwa massallaci da wuri
6-Inda hali kazo kasa.
Kamar yadda hadisi ya tabbata cewa ''BABU
WANI DA ZAIYI WANKA RANAR JUMU'A
SANNAN YAZO YA SALLACI SALLAR WAJIBI
FACE SAI AN GAFARTAMASA HAR ZUWA WANI
SATIN''
YAN UWA MUSULMI Ya chanchanta muzama
cikin masu zuwa da wuri saboda samun damar
zaunawa a massallaci dan yin salati, Sannan
kuma Mala'iku suna yiwa wanda ke zaune
massallaci addu'a.
To amma abun takaici wasu na kauracewa zuwa
da wuri, Zakaga wasu basu wuri sai anfara
khudbar, Wasu kuma sai anyi rabi wasu kuma sai
an gama, Wasu kuma sai Tada sallah, Kai wasu
ma sai an yi raka'a daya!
Shedan ya hana musulmi more ma wannan
romon!
Yaku yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH .
Hadisi daga manzo tsira na cewa ''DUK WANDA
YAYI WANKA IRIN NA JANABA (Dama wankan
tsarki iri daya ne a musulmi) ZA'A BASHI LADAR
WANDA YABADA KYAUTAR RAKUMI, WANDA
YAZO NA BIYU ZA'A BASHI LADAR WANDA
YABADA SADAKAR SA, NA UKU KUMA ZAI SAMU
LADAR WANDA YABADA KATON RAGO NA HUDU
KUWA ZAI SAMU LADAR WANDA YABADA KAZA/
ZAKARA NA BIYAR KUMA ZAI SAMU LADAR
WANDA YABADA KWAI''
Wanda kuma sai da limamin yazo ba'a sanyi shi
cikin lissahi.
Akwai abubuwa guda biyar da ake saran da adam
zai dace da Aljannah a ranar jumu'a akwai,
1-Gaida marar lafiya (ranar jumu'a)
2-Zuwa jana'iza (ranar jumu'a)
3-Azuni
4-Zuwa Massallaci da wuri
5-Inta bawa ko baiwa, (Taimakawa wajen biyan
bashi)
Tafiya Kasa zuwa massallaci ranar jumu'a nada
matukar falala kamar yadda yazo a cikin hadisi
cewa ''DUK WANDA YATASO DAGA GIDA DA
KAFAFUNSA SUKAYI KURA (DAUDA) TO
KAFAFUN SUN HARAMATA SHIGA''
JUMU'A Nada sharadi kamar haka
Yin shiru a lokachin huduba, Kamar yadda ALLAH
Madaukakin sarki yake cewa ''IDAN ANA
KARANTA QUR'ANI KU SAURARA WATA QILA SU
SAMU RAHAMA'' Kunga kuma huduba ana kawo
ayoyin Qur'ani. Kai wajibi ne yin shiru idan ana
huduba!
Banda wasa, ko gaishe gaishe,
Ba hallata kayi tafiya dab da lokachin Jumu'a sai
inda ta zama wajibi, Saboda karamawa da
girmama wannan ranar!
Yana da kyau karanta suratul kahfi a ranar
Jumu'a, Saboda Annabi na cewa ''DUK WANDA
YAKARANTA SURATUL KAHFI RANAR JUMU'A
ALLAH ZAI HASKAKA MASA HAR WANI SATIN''
Muna rokon ALLAH Tare da tuwassalin da
wannan khudbar ka biya mana bukatun mu, Ya
ALLAH Ka baiwa Mai martaba Emir na Tsafe
lafiya, Kasa asamo abunda akaje nema a kasar
india, Ya ALLAH Kasanya garin mu Albarka ka
yafemana kayi jagora ga shuwagabbani mu Baki
daya, Ka jikan mamatan mu Baki dayan su.
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
18/Jimada Akhair/1438
17/03/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN KALMAR SHAHADA KASHI NA BIYU

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #KALMAR_SHAHADA
KASHI NA BIYU
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki,
Muna gode masa muna neman yakare mu daga
sharrin kawunan mu, Tsira da aminci su kara
tabbata ga Manzon rahama Muhammad S.A.W
da alayen sa da sahabban sa, Da dukkan
Wadanda suka biyo bayansu da kyautatawa, Har
zuwa ranar sakamako.
A makon daya gabata malan yafara khudba akan
kalmar shahada, Inda yakawo mana sharudda
hudu da cikin takwas na kalmar shahada,
To a wannan makon ma Insha Allahu zamuji
cikon hudun tare da jin karin bayani, Dan amfana
da kuma kara fahimta ga yan uwa musulmi,
YAKU YAN UWA MUSULMI
Ita fa wannan kalmar ta LA'ILA HA ILALLAH A
Halicci duniya ne dan baki daya ne dan ita,
Hakama An halicci mutane da aljannu kaf dan
wannan kalmar haka Sama da kasa baki daya
duk an haliccesu ne dan wannan kalmar!
Wannan kalmar da ita ake banbanta kafuri da
muminin musulmi,
Wannan kalmar tana da rukuni guda biyu.
1-Korewa
2-Tabbatarwa
Ma'anar Korewa shine LA'ILAHA Babu wanda ya
chanchanta da bauta kowanene
IL'LALLAH (Tabbatarwa) Sai Allah madaukakin
sarki.
Yakamata Ko kuma wajibi kowane musulmi ya
dinga hakaito wannan ma'anar a lokacin da yake
furta wannan kalmar,
Ma'anar kalmar gaba daya shine BABU ABUN
BAUTAWA NA GASKIYA SAI ALLAH
ALLAH S.W.T Yafada cikin Suratul hajj cewa
''LALLAI SHI ALLAH SHINE WANDA YA
CHANCHANCI A BAUTAW AL-ALIYU AL-KABIRU''
Dukkan wani abun bautawa a duniya gaba daya
bai cika Al-aliyu ba, kuma bai cika Al-kabiru ba,
Shi kuwa duk wanda bai cika da wadannan
matakan ba to bai chanchanci bauta ba,
Tauhidi baya taba cika har sai an san wannan
kalmar, Kuma an dabbaka ta.
Dukkan Annabawan da Allah ya aiko har da
Manzo S.A.W Sunzo ne dan jaddadda wannan
kalmar.
Ba'a bautawa kowa sai Allah, koda Annabi ne, ko
mala'ika, Ko malamai ko waliyai ko kabarin su
Domin suma Allah sukabi har suka zama waliyai!
YAKU YAN UWA MUSULMI
Ga chi gaban sharudda
5-Idan ka fadeta yakasance kanason ALLAH Har
a zuciya ba'a baka kawai ba,
Ana fadan tane kawai dan zikiri bawai dan sanyi
jin haushi ga wani ba, Idan ka fadeta da wata
niya to tabba baka da lada.
A cikin sahihul bukhari ya ruwaito daga Manzo
S.A.W Cewa duk wanda ya kammala wasu
abubuwa guda ukku zai samu dandano na imani,
Akwai son ALLAH Dakuma son Manzo S.A.W
Muddin kanason cikawa da imani kaso ALLAH
Fiye da komai Ka kuma son Manzo ALLAH S.A.W
Fiye da kowa.
ALLAH Madaukakin sarki na cewa ''IDAN KUN
KASANCE KUNA SON ALLAH TO KUBINI ALLAH
ZAI SOKU''
YAKU YAN UWA MUSULMI
Dole ne a matsayin mu na musulmi mu kasance
muna son Alqur'ani da Hadisai na Manzo ALLAH
A koda yaushe ka kasance kana karatun Qur'ani
Kana karatun Hadisi.
6-Dole ka mika wuya ga Kalmar
Dole a mika wuya ga Kalmar Ma'ana Bin duk
abunda ke halal, Da kuma kauracewa haram,
Biyayya ga duk abunda kalmar ta kunsa.
A cikin suratul Lukman ALLAH Na cewa ''DUK
WANDA YA MIKA WUYA HAKIKA YAYI RIKO DA
IGIYA MAI KARFI''
7-Ka karbi duk Abunda kalmar tazo dashi
Ma'ana yarda da ita, Da dukkan abunda ta kunsa
baki daya,
ALLAH Na cewa ''KAFURAI SUNA GIRMAN KAI
DA ITA(KALMAR SHAHADA) SUNA CEWA YANZU
ZAMUBAR ABUNDA MUKA GADA MU BAUTAWA
ABU DAYA TAK''
Wannan kuwa shine yasanya kafurai wuta ma'ana
kin yadda da ita.
8-Dolene kafurcema dagutu
Ma'ana duk wani abu da wasu ke bautawa ka
kaurace masa,
Allah na cewa ''DUK WANDA YA KAFURCEWA
DAGUTU YAYI IMANI DA ALLAH YAYI RIKO DA
WATA IGIYA MAI KARFI''
YAKU YAN UWA MUSULMI
Akwai hadisai da yawa daga Manzo rahama
S.A.W Wadanda ke koyar damu falalar wannan
kalmar
Manzo S.A.W Yana cewa ''DUK WANDA YAFADI
KALMAR LA'ILAHA ILLALLAH WAHADAHU LA
SHARI KALA LAHUL MULKU WA HUWA ALA
KULLI SHAI'IN QADEER'' Hakika za'a kankare
masa zunubansa koda sunyi girman dutsen uhud.
A wani hadisin kuma yana cewa ''FIYAYYEN
ABUNDA NAKE FADA SHINE ''DUK WANDA
YAFADI KALMAR LA'ILAHA ILLALLAH
WAHADAHU LA SHARI KALA LAHUL MULKU WA
HUWA ALA KULLI SHAI'IN QADEER''
Duk wanda yafadi wannan a rana sau dari za'a
yafemai zunuban sa duka koda sunyi yawan
kunfar teku.
Duk wanda yafadi ''''DUK WANDA YAFADI
KALMAR LA'ILAHA ILLALLAH WAHADAHU LA
SHARI KALA LAHUL MULKU WA HUWA ALA
KULLI SHAI'IN QADEER'''' za'a kankare masa
zunubai dubu, kuma za'a basa lada dubu.
Hadisan nada yawa sosai wadannan misalai ne.
Daga karshe muna rokon Allah yasa kalmar mu
ta karshe ta kasance wannan kalmar, Ya gafarta
mana, Yajikanmu yayiwa jagororin ja gaba.
Ameen
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
04/Jimada Akhair/1438
03/03/2017.

HUDUBAH AKAN KALMAR SHAHADA

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #KALMAR_SHAHADA
Godiya ta tabbata ga ALLAH Muna gode masa
muna neman taimakom wanda ALLAH Yashiryar
Shine shiryayye, Wanda ALLAH Yabatar Babu mai
iya shiryar dashi,
Hudubar Yau tayi magana ne akan Wata
tsaddadiyar kalma wato KALMATUSH SHAHADA !
Ita wanman Kalmar mai girman ita ce mabudi na
shiga musulunci, Da kuma banbatawa tsakanin
kafurci da imani,
Wannan Aya ALLAH Madaukakin sarki ya shaida
kanta kamar yadda Yafada a cikin Suratul Ali
imran ALLAH YA SHAIDAR CEWA BABU WANDA
YA CHANCHANTA DA BAUTAWA SAI SHI
ANNABAWA SUN SHAIDA MALA'IKU SUN
SHAIDA MALAMAI MA SUN SHAIDA
Yaku yan uwa musulmi musulunci mutun baya
ingantuwa har sai ya yarda da kalmar,
Ita ce kalmar shahada ana ce mata KALMAR
YAKINI
Wannan kalmar ita ke banbamta kafurci da
musulunci
Hadisi yazo daga manzo tsira cewa DUK WANDA
YAFADI KALMAR SHAHADA YANA
SAKANKANCEWA DA ITA HAR YA MUTU ZAI
SHIGA ALJANNAH.
Annabawan da ALLAH Madaukakin sarki ya tura
zuwa ga jama'a dukansu dan jaddadda KALMAR
SHAHADA
Kamar yadda Aya tazo cewa HAKIKA MUN AIKA
DA KOWANE ANNABI ZUWA GA AL'UMMAR SA
DAN SU BAUTAWA ALLAH SU KAFURCEWA
DAGUTU''
Misalin ALLAH Madaukakin sarki ya aikawa
kafuran Al'umma da manzanni
Samudawa ALLAH Ya aika masu da Annabin
Salihu dan yayi kira akan tsaida kalmar Shahada
Hakama Annabin Shu'aib an aikasa ga mutanen
madiya Dan yayi kira akan kalmar shahada.
Annabawa da manzanni dukkansu an aiko su dan
isar da wannan Kalmar ta LA'ILAHA ILLALLAH.
Hatta mafificin halitta Manzo sallallahu alaihi
wassalam Yazo ne dan isar da KALMAR
SHAHADA
Yaku yan uwa musulmi Kusani wajibi ne ga
musulmi yasan fassarar ta, bawai fadin ta ba
kadai,
Kuskurene Fassar da hausawa kewa KALMAR
SHAHADA Cewa
-Babu sarki sai ALLAH
Ko kuma masu cewa
-Babu iko sai na ALLAH, Wanda duk wannan
Fassarar kuskure ne.
Yaku yan uwa musulmi KALMAR SHAHADA Tana
da sharudda guda Takwai 8
1-Dole ne kasan Ma'anar ta
Sanin Ma'anar ta na nufin Haddaceta da sanin
hakikan nin fassarar ta da abunda ta kunsa.
2-SAKANKANCEWA
Ma'ana yarda da duk abunda ta kunsa banda
shakku ko ko kwanto, Sau daya a wannan
zamanin wasu na walwale KALMAR SHAHADAR
Su ta hanyar kalaman su da ayyukansu, kamar
fadar wata kalmar shirka, ko kuma aikata shirka
kamar sihiri da tsafe-tsafe Da zuwa wajen yan
duba ko malaman tsibbo ko bokaye.
3-Dole ne kayi Zikiri da ita
Ma'ana fadar ta a matsayin zikiri wato ambaton
Dan yin zikiri Bawai fadar ta dan nishadi ba, ko
dan baiwa wani haushi ko kuma ana fadar ta ana
rawa, dukkan wannan kuskure ne, Hakama
hadata da wata daudar duniya Misali kaga wata
mota mai kyau sai kaji an fadi LA'ILAHA
ILLALLAH
Kunga wannan kuskure a hada daudar duniya da
wannan babbar kalmar ita fa duniya ALLAH YA
TSINE MATA DUK ABUNDA KE CIKINTA IN
BANDA AMBATTON ALLAH DA ZIKIRIN SA
4-Fadar ta da gaske
Ma'ana fadar ta gaske bada niyar wasa ba ko
kuma ganganci ko kuma karya kamar yadda
munafukai sukeyi a lokachin Annabi Kamar yadda
ALLAH Yafada a cikin Suratul munafikun ''IDAN
MUNAFUKAI SUNZO WAJENKA SUNA CEWA SUN
SHAIDA KAI MANZO ALLAH NE TABBAS ALLAH
YA SHAIDA KAI MANZO NE AMMA SU
MUNAFUKAI MAKARYATA NE''
5-Dole kaso kalmar
Ma'ana kaso kalmar har a zuciya ta hanyar son
tane zaka ki tare da kauracewa wanda baya
sonta.
8-Ka yarda da ita
Ma'anar yarda da ita da duk abunda ta kunsa
dan hakika duk wanda yafadeta amma bai yarda
da ita to hakika shima munafuki ne kuma za'a
hada shi da munafukai na lokachin magabata
ALLAH Madaukakin sarki yana cewa ''WANDA YA
KAFURCEWA DAGUTU YAYI IMANI DA ALLAH
HAKIKA YAYI RIKON DA WATA IGIYA MAI KARFI
WADA BATA YANKEWA''
Igiyar da mai karfi ita ce KALMAR SHAHADA
Yaku yan uwa musulmi duk wanda ya furta ta to
dole ne yasan ma'anar ta
ALLAH Madaukakin sarki yana cewa ''BABU
MASU SHIGA ALJANNAH SAI WANDA YA
SHAIDA DA KALMAR SHAHADA.
Ba makawa saika san ma'anar ta
Akwai kura kurai da wasu keyi na furta ta
bagatatan wasu zaka gansu suna furta ba kan
gado wanda duk abunda ke duniyar nan ta fishi
daraja a wurin ALLAH Idan da duniya nada daraja
wajen ALLAH Da kafuri ko ruwan sha bai samu,
Wani hadisi yana cewa ''DUKAN WANDA YA
MUTU YASAN MA'ANAR KALMAR SHAHADA ZAI
SHIGA ALJANNAN
Wata rana wani yazo ya tambayi manzo tsira
cewa Wanene zai samu cetonka sai manzo tsira
yayi shiru (dan yaji ta sahabbai) sai abi huraira
ya tambayi ANNABI Yaya,
Sai manzo tsira yace dama nasan kai zaka fara
magana ''NA SHAIDA CEWA NI MANZO ALLAH
NE KUMA NA YARDA DA ALLAH HAKIKA DUK
WANDA YA MUTU YA SHAIDA WANNAN KALMAR
ZAI SAMU CETONA''
Imam bukhari yayi babi na musamman daya
sanyawa suna babi Dan ya nuna muhimmancin
sani abu,
Mai ahadari na cewa ''Baya halatta kai aikata
wani aiki har sai kasan hukuncin ALLAH Akansa''
Ya ALLAH Kasamu daga cikin muminai, masu
imani, masana KALMAR SHAHADA, Ka shiryamu
tare da iyalanmu,
Ya ALLAH Ka taimaki musulunci da musulmai, ka
kasqanta kafurci da kafurai, ka yiwa
shuwagabbani jagoranci kabar mu mutu muna
musulmi masu imani.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
26 /05/1438
24/02/2017.