Thursday, 25 March 2021

02 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

DARASI NA BIYU (002)

📒ABU NA BIYU: YIWA IYALAN MAMACI TA'AZIYYA DA KUMA LAFUZZAN DA AKE AMFANI DASU📒

Ana yiwa iyalan mamaci ta'aziyya da duk wadansu kalamai da ake sa ran zasu lallashe su, su rage masu radadi da damuwar wannan rashi tare da sanya su yarda da hukuncin Allah da kuma hakuri, musamman ma lafuzzan da Annabi Muhammad SALAL LAHU ALAIHI WA SALLAM yayi amfani da su, idan mutum ya san su, idan kuwa mutum bai san su ba, to, sai yayi amfani da kyakkyawar kalma domin cimma wannan manufa, kuma kada su sabawa Shari'ah. Dangane da wannan akwai hadithai kamar haka:

📌1. Hadithin Usama bin Zayd (R.A) yace:..... Wata diyar Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ta aika masa cewa danta na dab da mutuwa sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare sa ya aika mata cewa: Yana yi mata sallama kuma yace: "DUK ABINDA ALLAH YA KARBA NASA NE KUMA ABINDA YA BAYAR NASA NE, KO WANE ABU A WURIN SA YANA DA IYAKANTACCEN LOKACI, TAYI HAKURI TA NEMI LADA (a wurin Allah)."  [Bukhariy da Muslim suka ruwaito sa] .

📌2. Hadithin Buraidah bin Husaib (R.A) inda ya nuna cewa:....... Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ya je yiwa wata mata daga cikin matan Madina ta'aziyya sai ya ce mata:" BABU WANI MUTUM KO MACE MUSULMA DAKE DA 'YA' YA UKU (da suka rassu) FACE ALLAH YA SHIGAR DA SU ALJANNA SANADIYAR 'YA' YAN" Sayyidina Umar (R.A) yana gafen dama da Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WA SALLAM, sai yace koda 'ya' ya biyu?, sai Annabi yace: "KODA BIYU" [Bazzar da Hakim suka ruwaito sa, kuma Hadithi ne ingantcce] 

📌3. Ta'aziyyar da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare sa ya yiwa Ummu Salamah a lokacin da mijin ta abu-Salamah ya rassu, sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WA SALLAM ya ce: "YA ALLAH KA GAFARTAWA ABU SALAMAH KA DAUKAKA DARAJAR SA A CIKIN SHIRYAYYU, KA MAYE BAYAN SA, KA GAFARTA MUNA TARE DA SHI, YA UBANGIJIN HALITTU, KA YILWATA MASA KABARIN SA KA HASKAKA MASA". [Muslim ne ya ruwaito sa] 

📌4. Ta'aziyyar da Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM yayiwa Abdullahi bin Ja'afar sai Manzon Allah ya ce:.... "YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA, KA SANYA ALBARKA GA DANSA ABDULLAHI (dansa) KUMA KA (Sanya Albarka ga) KASUWANCI" ya fadi haka sau uku. [Ahmad ya ruwaito sa, kuma hadithi ne ingantcce] 

💡Wasu kenan daga cikin lafuzzan da Annabi Muhammad SALAL LAHU ALAIHI WA SALLAM yayi amfani dasu wurin yiwa Sahabban sa ta'aziyya. 

Wallahu a'alamu bissawab. 

Mu hadu a darasi na uku (003)

✍️Nasiru Bala Bungudu. 
(Chief Imam Salih bin Abdul Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

001 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA FARKO (001)

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai jinkai, Tsira da Amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah. 

Bisa ga la'akari da muhimmancin ta'aziyya da kuma bukatuwar musulmi ga sanin yadda take a Sunnar Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM, domin kaucewa bidi'o'i naga ya dace in tunatar da kaina game da takaitaccen bayani akan ta'aziyya wanda ya kunshi abubuwa guda shidda (6) kamar haka:
👉1. Shar'antuwar Ta'aziyya a Musulunci
👉2. Yiwa iyalan mamaci ta'aziyya da kuma lafuzzan da ake amfani dasu.
👉3. Ba'a iyakance ta'aziyya da kwana uku ba kamar yadda wasu suke riyawa.
👉4. Abubuwa biyu (2) da ya kamata a nisanta a lokacin mutuwa.
👉5. Sunnah ne dangin mamaci da makwabtan sa suyi abincin da zai kosar da iyalan mamacin su aika masu.
👉6. Mustahabbancin shafa kan maraya da tausaya masa.

📒NA FARKO: SHAR'ANTUWAR TA'AZIYYA A MUSULUNCI:📒

An Shar'anta yin ta'aziyya ga iyalai da dangin mamaci, saboda hadithai da suka yi bayanin haka:

📌 1. Hadithin Qurra Al-Muzanniy (R.A), cewa: a lokacin da Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ya samu labarin rassuwar dandan wani daga cikin Sahabban sa, ya je yayi masa ta'aziyya har ma yace masa "MINENE YAFI SOYUWA A GAREKA? SHIN KAJI DADIN RAYUWAR KA TARE DA WANNAN YARO? KO (kafi son) KA ISKO SHI BAKIN KOFAR ALJANNA YANA JIRAN KA, YA BUDE MAKA (don ka shiga)?" sai yace: ya Annabin Allah!, nafi son ya riga ni ya bude mani. Wannan Hadithi [[Nasa'iy ya ruwaito shi da wannan siyaqi, haka kuma ibn Hibban da Hakim da Ahmad duka sun ruwaito sa. Kuma hadithin Sahihi ne.]]

📌 2. Hadithin Anas dan Malik (R.A), yace: Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM yace: "DUK WANDA YAYIWA DAN UWAN SA MUMINI TA'AZIYYA AKAN WATA MUSIBA, (da ta same sa) ALLAH ZAI TUFATAR DA SHI CIKAKKUN TUFAFI A RANAR ALKIYAMA WADANDA MUTANE ZASU YI FATAR SAMUN IRINSU" [Khadeeb Al-Baghdadiy ya fitar da shi da bin Asakir da kuma bin Adiy. Hadithi ne ingantcce] 

Wallahu a'alamu bissawab. 

Mu hadu a darasi na biyu (002) insha'allah. 

✍️ Nasiru Bala Bungudu. 
(Chief Imam Salih bin Abdul Aziz Juma'at Mosque Bungudu)