Friday, 10 January 2020

021 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_021_

RASHIN LAFIYA (CIWO)

Ciwo daga Allah ya ke babu wanda ya fi qarfin Allah ya jarrabe shi da ciwo ko wane iri ne, in muka bibiyi tarihi za mu ga bayin Allah da dama sun yi fama da rashin lafiya ba don kome ba sai dai don Allah ya daukaka darajarsu da kuma kankare ma su zunubansu. Gwargwadon imanin mutum gwargwadon yadda Allah zai jarraba shi. Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya gaya mana cewa girman lada na tare da girman jarrabawar da Allah ya jarrabe ka da ita, haqiqa idan Allah ya so wasu mutane sai ya jarraba su (da wata cuta), wanda ya yarda da hukuncin Allah to yana da yarda, wanda ya yi hushi to yana da sakamakon fushinsa.
[Tirmidhi ya ruwaito]

Don haka ciwo ba abin zargi ba ne domin akwai wani sakamako wanda Allah ya ke bai wa wanda ya yi ciwo,
haka ma’aiki sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya fada mana a wani hadisi da aka samo daga Anas Allah ya qara masa yarda ya ce, “Manzon Allah sallal Lahu Alayhi wa alihi wa sallam ya ce, ‘Idan Allah ya so bawansa da alheri sai ya sa masa wata cuta (uquba) a nan duniya, amma idan Allah ya nufi bawansa da sharri sai ya qyale shi da zunubinsa har ya cika masa da shi ranar qiyama.’”
[Tirmidhi ya ruwaito]

Wannan magana ta manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ta nuna mana ashe duk wanda ciwo ya same shi ya yi haquri ba kansa ne farau ba, manyan mutane su ma sun yi ciwo na tsawon lokaci mai tsawo, misali kamar Annabi Ayyub da Allah ya gaya mana ya yi ciwo na tsawon lokaci wanda har ya kai na shekara 18 ba ya fita saboda ciwo, wanda har ya kai ga gaba dayan dukiyarsa ta qare ‘ya’yansa duk suka mutu baki dayansu saboda tsananin ciwo, sai da ta kai gaba dayan jikinsa ba ya amfani sai zuciyarsa kawai, wasu malaman tafsirin ma cewa suka yi sai da ya kai jikinsa ya kasance yana yankewa yana faduwa qasa. Wata rana matarsa ta ce masa ya roqi Allah ya ba shi lafiya mana, sai ya ce shekarata saba’in lafiyata lau amma in kasa haquri da rashin lafiya ta shekara sha bakwai? [IBN KATHER]

ﺍﻟﻠﻪ ﺃَﻛْﺒَﺮُ
Bayin Allah ke nan shekara da shekaru suna fama da rashin lafiya amma suka yi haquri, haka aka san bayin Allah cikin haquri ko da yaushe.

Kusan idan muka bibiyi tarihi zamu ga yadda Allah Ya ke jarraba bayinsa da cututtuka ba don komai ba sai don Ya qara masu daraja da daukaka. Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa salam ya yi ciwo, haka shi ma babban sahabinsa Abubakar shi ma haka, haka shi ma Imam Malik ya yi rashin lafiya har ya kai ba ya zuwa masallaci sai a gidansa yake yin sallah,haka ya mutu cikin wannan rashin lafiya. Allah Ya rahamshe shi amin. Shi ma dalibinsa Imamu Shafi’i ya yi rashin lafiyar da ta kai in ya hau doki jini na zuba a duburarsa, har ya cika masa huffinsa (takalminsa). A qarshe dai ina mai cewa ciwo ko rashin lafiya daga Allah ne kuma ba abin zargi ba (ba aibu ba ne) ne domin jarrabawa ce daga Allah, kuma akwai sakamako mai yawa ga wanda ya yi haquri kuma ya miqa al’amarinsa ga Allah. Imam Ahmad shi ma ya yi ciwo mai tsanani har ta kai ga yana nishi da qyar, kuma a cikin wannan ciwon ya rasu Allah Ya rahamshe shi amin.
Ana so mara lafiya ya yi haquri da cutar da ta same shi ya miqa lamarinsa ga Allah kuma ya yi haquri, babu abu mafi tsada fiye da Allah Ya ba ka haquri, kuma Allah Ya yabi masu haquri a cikin littafinsa kuma Ya yi ma su bushara da lada mai yawa kuma Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya fadi irin falalar haquri, shi mumini duk abin da ya same shi lada ne.
Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya ce, “Abin sha’awa ga al’amarin mumini komai nashi lada ne. Idan abin farin ciki ya same shi ya gode wa Allah alkhairi ne a gare shi, in kuma abin baqin ciki ko damuwa ya same shi ko ciwo ne ya yi haquri alkhairi ne a gare shi.” [Muslim]
Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce wanda Allah ya nufe shi da alkhairi sai ya sanya ma shi wata cuta. [Bukhari da Muslim]
Babu wata damuwa ko baqin ciki ko ciwo ko wani abu mai cuta da zai sami mumini face lada ne a gare shi. Har qaya idan ya taka face Allah Ya kankare masa kurakuransa. [Bukhari da Muslim]
Ibn Mas’ud ya shiga wajen Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya taras da shi yana zazzabi, sai ya ce ma shi, “ Ashe kai ma kana zazzabi zazzabi mai tsanani haka?” Sai Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce, “Haka ne abin yake, ni ciwon mutane biyu nake yi.” Sai Ibn Mas’ud ya ce, “Kana nufin kana da lada biyu ke nan?” Sai Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce, “Na’am.” Sannan
sai ya ce, “Babu wani ciwo ko qaya da zai sami musulmi face Allah ya kankare masa munanan ayyukansa kamar yadda itaciya take kakkabe ganyayen ta. [Bukhari da Muslim]

Zamu dakata anan, idan Allah ya kaimu wani sati zamu cigaba Insha Allahu.

Wannan duka yana zuwa muku ne a cikin littafin: *HUKUNCE HUKUNCEN JANAZA A MUSULUNCI* Wallafar: _Malam Haruna Abubakar Shika._

MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA* SAI SU TURA CIKAKKEN SUNA DA GARI ZUWA GA
+2349030201868 A WHATSAPP

Https://fb.me/abbansinan

022 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_022_

*LADDUBAN ZIYARAR MARA LAFIYA DA ABIN DA KE KAN MAI JINYA DA LIKITA DA AN GUWAR ZOMA.*

Kamar yadda muka gani a baya cewa ciwo daga Allah yake kuma ciwo kaffara ne na zunubai, kuma mun ga cewa hatta
manya-manya daga cikin bayin Allah
sun yi ciwo. Musulunci ya koyar da komai domin hatta yadda a ke zuwa ziyarar/gaida mara lafiya manzon sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya koyar da mu ladubban zuwa ziyarar/gaida da mara lafiya. Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa aihi wa sallam ya kasance yakan je gaida mara lafiya kuma hadisi ya tabbata daga manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam da ya ke nuna mana idan mutun ba shi da lafiya yana da haqqi a kanka na ka je ka gaishe shi, muddin ba ka je ba ka tauye masa haqqinsa. *[Muslim]* Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya ce, “Ku gaishe da mara lafiya Musulmi, ku ciyar da abinci,ku ‘yanta wuyaye.” *[Bukhari]*
Hakqin Musulmi ga Musulmi guda shida ne: Idan ya haxu da shi ya yi masa Sallama, idan ya kira ka ka amsa ma shi, in ya nemi ka yi masa nasiha ka yi ma shi, in ya yi atishawa ya kuma ce Alhamdu lil Lah, ka gasshe shi, in ya yi rashin lafiya ka je ka gasshe shi. Ya ce mai gaida Mara lafiya yana tafiya a gavar
Aljanna ne har ya je ya dawo. *[Bukhari]*

Ga ladubban kamar haka;

*NIYYA  KYAKKYAWA:*

Domin dukkan ayukka ba sa ingantuwa sai da niyya. Ana so niyyar ta zamanto kyakkyawa koda yaushe, mai zuwa ziyarar mara lafiya ana so ya yi niyyar zuwa gasshe da mara lafiya domin Allah ba wai don wani abu ba, a’a ya je ne domin samun lada wajen Allah, haka Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ambaci lada mai yawa ga wanda ya je gasshe da mara lafiya domin Allah. *[Muslim 268 da Abu Daud 3569]*

*NEMAN IZINI:*
Ana so ka nemi izinin mara lafiyan kafin ka shiga wajensa kamar yadda ya zo cikin Sahihul Bukhari Ibn Abbas ya nemi izinin shiga wajen Nana A’isha Allah ya qara mata yarda lokacin da ba ta da lafiya kafin ya shiga.  *_(Yana da kyau ‘yan‘uwa su kiyaye shiga gidajen jama’a, wannan bala’i ne kuma laifi ne shiga gidajen jama’a ba tare da izini ba, ko da ka yi sallama sai ka jira an ba ka izini kafin ka shiga, haka Annabi sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya koyar da mu. Haka nan ma haramun ne qanin miji ya shiga xakin matar wansa sai da izinin yayan nasa, idan kuma baya nan to haramun ne kai qaninsa ka shiga xakin matar. Allah ya ba mu ikon gyarawa amin)._*
Kai ma ana so ka nemi izinin mara lafiya kafin ka shiga wajensa ko da kuwa a asibiti, yayin da Ibn Abbas ya je gaishe da Nana A’ishatu Allah ya qara mata yarda, da ya je ya nemi izinin shiga sai ta ce kada ya shigo, sai aka gaya mata Ibn Abbas ne fa dan baffan Annabi sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam, sai ta ce kada dai ya shigo, da aka matsa mata sai ta ce, “Ina tsoron in ya shigo zai yabe ni, amma ya shigo. Da ya shigo sai ya ce mata, “yaya jiki?” kamar dai yadda a ka koyar da su, sai ta amsa da cewa, “Muna fatar rahamar Allah kuma muna tsoron azabarsa.” Sai Ibn Abbas ya ce, Haba ke da kike matar Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam! Ke ce fa wadda Annabi ya fi so, kuma ke ce wadda aka saukar da aya kaza da kaza saboda ita.” Ya yi ta gaya mata kyawawan ayyukanta. sai ta ce, “Da ma abin da na ke tsoro ke nan na ce kada ka shigo, da ma na san sai ka yabe ni sai ka yi ma ni Kirari.” *[Bukhari]*
Shi Ibn Abbas ya yi abin da Annabi
sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya yi umurni ne da a yi wa mara lafiya, ita kuma ta yi tawali’u ne kuma da ma tawali’u hali ne na mutanen kirki, don haka babu kyau a rinqa tuna wa mara lafiya munanan ayyukansa, haramun ne a je ziyarar mara lafiya kana a riqa tuna masa munanan ayyukansa.
Abdullahi ibn Umar lokacin da ya ke ciwon ajali Hajjaj ibn Yusuf As Saqafi ya nemi izinin ya shiga ya gaishe shi, sai
Abdullahi ibn Umar ya ce a ce masa ba ya so, ya taqura sai ya shiga, da ya shiga ya yi sallama Abdullahi bn Umar ya yi banza da shi. *_(Hajjaj bn Yusuf saqafi shi ne ya sa aka soki Sahabi mai daraja Abdullahi bn Umar Allah ya qara masa yarda da wani masoki mai dafi, ba don komai ba sai don zalunci da mugunta, Abdullahi bn Umar ya yi wa Hajjaj magana ne ranar juma’a a kan ya tsananta wa jama'a wajen huduba har la’asar, sai ya sa aka soke shi. Wannan sukar ce ta zama sanadiyyar Rasuwar sa. Bayan an soke shi ne daga baya ya zo gaishe shi don yaudara, sai shi kuma Abdullahi bn Umar ya ce ba ya so, shi ya sanya Shamsudden Zahabi a cikin littafinsa Siyar ya fadi miyagun maganganu a kansa ba don komai ba sai don ya kashe sahabai da bayin Allah nagari har a qarshe yake cewa, “Muna qin sa ne saboda Allah ya ce ’’ mugu dan ta’adda azzalumi dan kama karya jabberi’’ ya dai sossoke shi. Mai karatu yana da kyau ya karanta tarihinsa a cikin SIYAR A’ALAMUN NUBALA shafi 343/4)._*
Bukhari ma ya kawo magana mai kama da wannan da ke nuna ladabin zuwa
ziyarar mara lafiya.
Dattijon arziqi mafifici mai daraja a bayan qasa bayan manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam
Abubakar Siddiq, shi ma ya nemi izinin shiga ya gaishe da Nana Fatimatu Allah ya qara ma ta yarda lokacin da ba ta da lafiya, ya yi sallama Sayyina Ali dan Abi Dalib Allah ya qara ma sa yarda ya fito sai ya ce masa ya nema ma sa izinin shiga ya gaishe da Nana Fatimah, sai Ali ya shiga ya gaya ma ta Abubakar yana neman izinin ya shigo ya gaishe ta, sai ta ce ya shigo, shi kuma ya shiga ya gasshe ta.
Ana so mai zuwa ziyarar mara lafiya ya nemi izinin shiga kafin ya shiga wajen mara lafiya.

ANAN ZAMU DAKATA, A GABA ZAMU CIGABA DA BAYANI AKAN LADDUBAN ZIYARAR MARA LAFIYA INSHA ALLAHU.

Wannan duka yana zuwa maku ne a cikin littafin: *HUKUNCE HUKUNCEN JANAZA A MUSULUNCI* Wallafar: _Malam Haruna Abubakar Shika_

MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA* SAI SU TURA CIKAKKEN SUNA DA GARI ZUWA GA +23430201868 A WHATSAPP

https://fb.me/abbansinan

022 MU KOYI IBADA A SAUKAKE