Friday, 15 February 2019

WAZAN ZABA? 2015/2019

🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶
*وليتذكرأولولألباب !!!*
*Domin masu hankali suyi tunani!!!*
🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷

_Rubutawa;_ *MURYAR SHABABU AHLIS-SUNNAH WALJAMA'AH TSAFE*

_Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu._

Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki wanda ya fifita Addinin Musulunci akan duk sauran addinai a bayan kasa, Ya kuma fifita Musulmai akan wanda ba Musulmi ba, ya kuma bayyana shine addinin da zai karba a ranar alkiyama.
Tsira da aminci Allah su tabbata ga shugaban mu da yafi duk wani shugaba a doron kasa, wanda yafi kowa cikin halittun Allah (S.W.T) baki daya; Annabi Muhammad (S.A.W) da iyalansa da sahabbansa da wadanda suka taimaki addinin  Allah da dukiyarsu da kawunansu, da wadanda suka bisu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

1⃣ *SHIN KO SIYASA ADDINI CE???*
          Siyasa na iya zama  addini ta lura da fadar Allah (S.W.T) *“Kace lallai sallah ta da yanka na da rayuwata da mutuwa ta na Allah ne Ubangijin halittu, babu abokin tarayya a gareshi, Kuma da wannan ne aka umarce ni kuma nine farkon masu mika wuya”*
{Al-An’am; 162-163}.

Tunda an umarci Manzon Allah (S.A.W) da cewa dukkan rayuwarshi yayi ta ga Allah (S.W.T), haka ma kai/ke aka umurce ku da dukkan rayuwar ka/ki yita ga Allah (S.W.T). Duk wanda zai jagorance ku zai jibinci Al’amurranku ne da addinin ku, to wajibine ya zama musulmi na kwarai.
Hakanan malamai sunce za’a saka addini a cikin siyasa ta lura da wasu abubuwa masu zuwa, ga kadan daga cikinsu:

✅ *_Ya kasance ga musulmi ga kafiri:_*
wajibine a zabi Musulmi.

✅ *_Ya kasance ga musulmi na kwarai ga kuma na banza (Fasiki):_*
Wajibine a zabi Musulmi na kwarai.

✅ *_Ya kasance ga Musulmai duka na kwarai amma daya yafi daya Imani, tausayi, taimako da son addini:_*
wajibi ne a zabi mai imani da tausayi da taimakon al’umma da son addini.

Duk wannan wajibi ne a saka addini a cikin siyasa domin duba ga abunda zai kawo ci gaba ga addini da al’umma, sannan wace amsa za ka/ki ba ma Allah (S.W.T) a ranar alkiyama idan ya tambayeka/ki dalilinka/ki na zabar kafiri ko fasiki alhali ga Musulmi ko mumini.

2. *Shin ko ya halatta in zabi kafiri alhali ga Musulmi?*

A’a baya halasta a zabi kafiri alhali ga musulmi, dalili kuwa Allah (S.W.T) yana cewa: *_“Ya ku wadanda sukayi imani kada ku riki kafirai a matsayin masoya koma bayan muminai shin kuna nufin sanya ma Allah dalili bayyananne ne a kanku”._*
{Al-Nisa’; 144}.

Allah ya kara cewa: *_“Ya ku wadanda sukayi imani kada ku riki abokan sirri daga waninku (wadanda ba Musulmai ba), basu takaita maku barna kuma suna gurin abunda zai cutar da ku, hakika kiyayya ta bayyana daga bakunansu amma abunda zukatansu ke boyewa ne mafi girma, kuma lallai mun bayyana ayoyi ne a gareku domin ku hankalta. Ku dinnan kune kuke sonsu (alhali) su basu son ku…”_*
{Ali-Imran; 118-119}.

Allah ya kara cewa: *_“Ya ku wadanda sukayi imani kada ku riki makiyana da makiyanku (a matsayin) masoya kuna jefa soyayya zuwa garesu alhali kuwa sun kafirta da abunda yazo maku na gaskiya…”_*
{Al-mumtahina; 1}.

3. *Wa ya kamata in zaba a matsayin shugaba (wanda zai jibinci al-amurrana)?*

Zabar shugaba nuni ne ga so da kauna da kuma yarda da cewa wanda ka zaba ka yarda ya jibinci al-amurran rayuwar ka da addininka, to dole ne ka zabi wanda yasan kima da mutuncin rayuwar taka da addininka.
Allah (S.W.T) yana cewa *_“Abun sani majibincin al-amurranku (shine) Allah da ManzonSa da wadanda suke tsayar da sallah suke bada zakkah...._*

Duk wanda ya jibinci Allah da ManzonSa, kace rundunar Allah itace mai rinjaye” {Al-Ma’idah; 55-56}.

Muna rokon Allah yasa ayi wannan zabe lafiya, ya zaba muna shuwagabanni na kwarai masu kaunar addininmu na musulunci ba masu fada dashi ba.

*SANARWA!!!*

Mun rubuta wannan takarda ba don goyon bayan wata jam’iyya ko wani mutum ba, a’a munyi ta ne domin isar da sakon Allah (S.W.T) zuwa ga bayinsa da nufin kawo gyara ga al’ummarmu da rayuwarmu.

Wassalamu Alaikum.

*SHABABU AHLIS SUNNAH WAL JAMA’AH TSAFE ZAMFARA STATE*
08064607294, 08139348898

shababuahlissunnahwjtsf@gmail.com

No comments: