*NASIHAR BARKA DA ASUBA*
Idan wani yazo wurin ka domin ka taimake shi akan bukatarsa, toh fa kaine mai amfanuwa da hakan, domin Allah SWT shine yayi maka ni'ima, ya buɗe maka ƙofar Alkhairi.
A wannan lokacin kyautatawar da za kayi mashi kanka ne zaka kyautata ma; Allah Madaukakin Sarki yana cewa: (Idan kun kyautata, toh kanku kuka kyautatamawa) a wani wuri kuma yace: (Ka kyautata kamar yadda Allah ya kyautata maka)
Allah ya bamu abinda zamu taimaki wanda yazo nema a wurin mu🤲
©Dr. Hussein Al-feefy
Fassarar:
*AbbanSinan Tsamiya*
30 Rabi'u Awwal 1444AH
26th October, 2022
No comments:
Post a Comment