Sunday, 25 November 2018

(A) DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

*وليتذكر ألوا الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*

_Gabatarwa:_ *MUKYAUTATA NIYYA GROUPS*

PART *A*

📌 *WANNAN ITACE HUJJAR MU AKAN CEWA MAULIDI BIDI'AH NE...!!!*

*==============*

▫ Abubakar siddiq(RA) yayi khalifanci tsawon shekara biyu amma baiyi maulidi ba, tare da cewa shi mai gaskiyar wannan al'ummar ne, kuma abokin manzon Allah s.a.w a cikin kogo lokacin hijira..!!
*▪▪▪▪▪▪▪*

🔸 Umar bn khaddab(RA) yayi khalifanci shekaru goma(10), amma ba'a ruwaito cewa yayi maulidi ba, tare da cewa shine FARUQ na wannan al'umma..!

*▪▪▪▪▪▪▪*

🔹Usman bn affan(RA) yayi khalifanci shekaru 13, amma baiyi maulidi ba, kuma baice ayi ba, tare da cewa ya auri yayan annabi guda biyu, kuma yayi hijira guda biyu, Wanda yafi kowa kunya a cikin wannan al'umma..!
*▪▪▪▪▪▪▪*

🔸 Aliyu bn Abi dalib(RA) yayi khalifanci shekaru 4 amma bai aikata maulidi ba, baiyi umurni da ayi ba, kuma shi Dan baffan manzon Allah s.a.w ne, kuma shine ya auri shugabar matan yan aljanna...!
▪▪▪▪▪▪▪

▫Hassan bn Aliyu bn Abi dalib yayi khalifanci wata shida(6) amma baiyi maulidi ba, gashi jikan Manzon Allah s.a.w, kuma shine shugaban samarin aljanna...!
▪▪▪▪▪▪▪

◼ Mu'awiya bn Abu sufyan yayi mulki na adalci a cikin kabilun larabawa, amma baiyi maulidi ba, bai kuma ce ayi ba
▪▪▪▪▪▪▪
◻Daular umawiyya tazo, a cikinta akwai irinsu Umar bn Abdulaziz, daular Abbasiyya tazo, a cikinta akwai misalin Harun Ar-rasheed, amma dukansu basuyi maulidi ba, basu kuma yi umurni da ayi ba..!
▪▪▪▪▪▪▪

🔹 Yanzu ma malaman gaskiya, masoya manzon Allah s.a.w gaskiyar so, basuyi maulidi ba tun daga karnukan nan guda uku, tare da tsananin sanin su akan abunda Allah ya saukar, da kuma girman fahimtarsu ga Qur'ani, ya akayi basuyi ba? Tare da cewa sune suka iso da Qur'ani da hadissai zuwa garemu..?

▪▪▪▪▪▪▪
  Mu dai yanzu zamu ce;  Da maulidi alkhairi ne da sun rigamu aikatashi..!
▪▪▪▪▪▪▪
Zamu fadi Abunda Imamu Malik(RH) ya Fada; ```Duk abunda bai zama addini a lokacin manzon Allah s.a.w da sahabbai ba, ba zai taba zama addini ba har tashin Al-kiyama..!```
▪▪▪▪▪▪▪
➡ Abu sananne kawai shine; Manzon Allah s.a.w bai bar duniya ba sai da ya kammala Isar da sakon da Allah ya aikoshi dashi..!
▪▪▪▪▪▪▪
   ▪ ya tsoratar da sahabbanshi akan kirkirar wani abu a cikin addini, da aikata abunda bai aikata ba..!
▪▪▪▪▪▪▪

▫ Ya kamata kusan cewa; wadancan karnukan masu girma basu San wani biki mai suna Maulidi ba! Shifa Maulidi wata bidi'ah ce da yan shi'ah *(FADIMIYYUNA)* suka kirkira, a karkashin wani shugabansu da suke kira Mai daukaka addinin Allah, sai dai karya suke, shi mai cutar da addini ne..!
▪▪▪▪▪▪▪
🔸 yayi mulki a bisa kafirci, da fasikanci, ta inda ya halasta shangiya, ya halasta kowane  farji na mace, ya tsinewa sahabbai kuma yayi umurni da hakan a saman mimbarorin juma'ah, wannan Dan ta'addan shine ya kirkiri maulidi fa! Ya kasa maulidin gida shida, Na farko; Maulidin Manzon Allah s.a.w, sai na Fadima, Aliyu, Hassan, Hussaini(ALLAH YA YARDA DASU) sai Maulidin kanshi..!
▪▪▪▪▪▪▪

Daga nan sai yan fadimiyyuna suka jahiltar da musulmai akan wannan bidi'ar, ya kamata kusan cewa babu wani dalili a wurin yan tamaulide akan halascin maulidi, kawai hujjarsu wasu nassosi ne suke yim a gurguwar fahimta, ko kuma hadissai na karya koda sun inganta sai ka samu basu nuni akan maulidi amma sai su juyar da ma'anarsu.
▪▪▪▪▪▪▪

◼ *YANZU GA WASU YAN TAMBAYOYI GUDA UKU DA MUKESON MU JEFAWA YAN TAMAULIDE, MUNA NEMAN AMSARSU:*
▪▪▪▪▪▪▪

1⃣ Shin bikin maulidi biyayya ne ga Allah da Manzon Allah s.a.w ko sabon Allah ne??

Idan sunce biyayya ne! Ko kuma sunce Sabo ne, duka akwai tuhuma garesu..!

2⃣ Yawwa, idan sukace biyayya ne ga Allah kuma zasu samu lada akai!
Sai muce Ko Manzon Allah s.a.w yasan da wannan biyayyar?
Ko bai sani ba?

➡ Da zasu ce bai sani ba, da sai muce kaiconku! Yanzu kuna tuhumar Babban malami(Manzon Allah s.a.w) da jahilci, wannan kafurci ne, kuma zindikanci ne..!
▪▪▪▪▪▪▪

🔸 Da zasu ce ya sani, toh sai muje a tambaya ta uku.

3⃣ Kunce biyayya ne, kuma Manzon Allah s. a.w ya sani, shin ya bayyanar dashi ga mutane ko kuwa ya boye???

Idan sunce bai Isar ba, wannan tozarci ne ga Manzon Allah s.a.w, da kuma tuhumar Manzon Allah s.a.w da boye wani Abu na manzanci, bayan a Qur'ani Allah s.w.t ya Fada cewa; ```Yaa kai Manzon Allah ka Isar da abunda ya sauka gareka daga ubangijinka, idan bakayi haka ba, baka Isar da Manzancin ba.```

Idan kuma sunce ya Isar, sai muce; Toh kuzo mana da dalili, ina aikin magabata akai?
Yanzu muna bukatar amsoshi daga gareku.

ALLAH YA NUNA MANA GASKIYA YA BAMU IKON BINTA, YA NUNA MANA BIDI'AH YA BAMU IKON KAUCE MATA

KU WATSA WANNAN A TSAKANIN MUTANE DOMIN AL'UMMA SU GANE GASKIYAR BIDI'AR MAULIDI...

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN;
✍ *Hashim Siraj Uba Tsamiya ( _ABBAN-SINAN_ )*
+2348064734911

No comments: