Wednesday, 26 December 2018

HUKUNCIN HADE SALLOLI A LOKACIN TAFIYA

🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸
*HUKUNCIN HADE SALLOLIN AZUHR DA LA'ASAR KO MAGRIB DA ISHAA A LOKACIN TAFIYA*
🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah s.w.t, Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w da iyalan gidansa da sahabbansa da duk Wanda ya biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

_Bayan haka:_

Maganganu sun yawaita akan wannan matsalar ta inda zaka samu daliban ilimi kullum cikin rigima muke da junanmu akan wannan matsalar, wannan yace GA abunda malaminshi yace shima dayan sai ya kawo maganar shugaban islamiyyarsu, wannan duka yana faruwa ne imma a haduwar mota ce ko a campuses na manyan makarantu, wannan shine dalilin da yasa nabi malamai domin nayi rubutu akan wannan matsalar, nima kuma zan kawo maganganun mai gidana *Manzon Allah s.a.w,* sai dai tunda ance matsala ce da ta shafi daliban ilimi inaga ba dole sai an bude komai ba, za'a Dan haska fitila ne kadan sai mutum yayi dogon hange kafin hasken ya dauke.

Allah yayi mana jagora.

Hadisi ya tabbata daga Manzon Allah s.a.w, hadisin da Abdullahi Dan Abbas R.A ya ruwaito cewa:
كَان
َ رَسُولُ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم يَجْمَعُ بَيْنَ صَلاةِ الظُّهْرِ وَالْعَصْرِ , إذَا كَانَ عَلَى ظَهْرِ سَيْرٍ , وَيَجْمَعُ بَيْنَ الْمَغْرِبِ وَالْعِشَاءِ .
Wannan hadisi ne sahihi da karara yake nuna mana cewa Manzon Allah s.a.w yana hade salloli.

Idan baka fahimci wannan hadisin ba, toh ga wani Wanda Anas Dan maliku R.A ya ruwaito yace:

كان رسول الله صلى الله عليه وسلم إذا ارتحل قبل أن تَزيغ الشمس أخّر الظهر إلى وقت العصر ثم نزل فجمع بينهما ، وإذا زاغت قبل أن يَرْتَحِل صَلَّى الظهر ثم ركب . رواه البخاري ومسلم .
Tirkashi kaji hadisi daga littafan da malamai kecewa sune mafi girman littafai bayan Qur'ani wato(SAHIHUL bukhari da Muslim), kunji fa Manzon Allah s.a.w idan ya daura aniyar tafiya kafin rana ta kawo(wato kafin lokacin sallar azuhr) yana jinkirta azuhr zuwa lokacin sallar La'asar, sannan sai ya sauka ya hade sallolin, idan kuma lokacin sallar azuhr yayi kafin ya fara tafiya yana yin azuhr kawai sai ya fara tafiya.

Ga hadisin mu'az bin jabal R.A a gazwati tabuka yake cewa:

أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ كَانَ فِي غَزْوَةِ تَبُوكَ إِذَا زَاغَتْ الشَّمْسُ قَبْلَ أَنْ يَرْتَحِلَ جَمَعَ بَيْنَ الظُّهْرِ وَالْعَصْرِ ، وَإِنْ يَرْتَحِلْ قَبْلَ أَنْ تَزِيغَ الشَّمْسُ أَخَّرَ الظُّهْرَ حَتَّى يَنْزِلَ لِلْعَصْرِ ، وَفِي الْمَغْرِبِ مِثْلُ ذَلِكَ ؛ إِنْ غَابَتْ الشَّمْسُ قَبْلَ أَنْ يَرْتَحِلَ جَمَعَ بَيْنَ الْمَغْرِبِ وَالْعِشَاءِ ، وَإِنْ يَرْتَحِلْ قَبْلَ أَنْ تَغِيبَ الشَّمْسُ أَخَّرَ الْمَغْرِبَ حَتَّى يَنْزِلَ لِلْعِشَاءِ ثُمَّ جَمَعَ بَيْنَهُمَا . رواه الإمام أحمد وأبو داود والترمذي .

Kunga shima wannan hadisin yana tabbatar muna da halascin hade salloli biyu a lokacin tafiya.

A wannan hadisin sai imamut tirmidhi yake cewa;

وبهذا الحديث يقول الشافعي ، وأحمد وإسحاق يقولان : لا بأس أن يَجمع بين الصلاتين في السفر في وقت إحداهما .
Kundai ji, a wurin su imamush shafi'i da imamu Ahmad da ISHAQ bin rahwiyya dukkansu sunce babu laifi a hade salloli biyu a lokacin daya, idan ana cikin tafiya.

Wancan hadisin da ya gabata na tabuka, imamu Muslim ya ruwaitoshi da wani lafazi kamar haka;

خَرَجْنَا مَعَ رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَامَ غَزْوَةِ تَبُوكَ ، فَكَانَ يَجْمَعُ الصَّلاةَ ، فَصَلَّى الظُّهْرَ وَالْعَصْرَ جَمِيعًا ، وَالْمَغْرِبَ وَالْعِشَاءَ جَمِيعًا .
A riwayar Muslim hade sallolin sai ya bayyanar mana da riwayar Imamu Ahmad da tirmidhi da Abi daud da ta gabata.

Abu na gaba shine addinin Allah sauki gareshi, tunda Allah yayiwa matafiyi rangwame akan ya ajiye *azumi* saboda kada ya wahala, ai banga abun rikici ba akan hade salloli, ana zaune gida ma akwai wasu dalilai da suna iya sa a hade salloli.
Hade salloli ga matafiyi ya kasu gida biyu;
1. تقديم
2. أو تأخير

Wato yin sallar azuhr da la'asar a lokacin azuhr ko yin sallar azuhr da la'asar a lokacin la'asar, sai dai dole idan zakayi taqdeem ko ta'akheer sai kayi niyya, ma'ana idan zakayi ta'akheer, dole sai kayi niyya kafin fitar lokacin sallar farko(azuhr)

Abu na gaba shine;

*DAGA KILOMETERS NAWA NE KASARU KE KAMAWA???*

TIRQASHI!!!

Wannan itace matsalar da nafi cin karo da ita a tsakaninmu dalibai yan islamiyya, Wanda kowa na ganin shi malamin kanshi ne, tare da ta'assubanci ga wani malami ko mazhaba, a karkashin wannan zan kawo wata gamsassar magana da Sheikhul Islam ibn Taimiyya ya kawo akan wannan matsalar Wanda ina kyautata zaton zata gamsar da duk wani mai Neman gaskiya akan wannan matsalar, Sheikhul Islam ibn taimiyya yake cewa;
فالفرق بين السفر الطويل والقصير لا أصل له في كتاب الله ولا في سنة رسوله بل الأحكام التي علقها الله بالسفر علقها به مطلقا .

Allahu Akbar, wannan magana ta ibn Taimiyya ta wadatar akan muce sai munyi dogon bayani, abune Wanda yake bude Allah bai kayyade ba kai waye da zaka kayyade?

Toh, rubutun idan akace za'ayi tayi baya karewa, don akwai hujjoji barkatai dake nuna halascin hade salloli a lokacin tafiya, a hakika yanzu nayi rauni a wurin rubutu, amma mu dauka cewa wannan kamar mukaddima ce, idan bukatuwar hakan ta kama zamu kara cewa wani Abu insha Allahu.

ALLAH YA KARA MANA IKHLASI DA KARFIN GWUIWA A WURIN AIKI DA DAI DAI DA FADAR GASKIYA.


✍ *Hashim Siraj Uba Tsamiya ( _ABU~SINAN_ )*

+2348064734911
+2349030201868

atstsamawy@gmail.com

atstsamawy@yahoo.com

No comments: