🍉🍉🥭🍑🍎🍊🍋🍌🍉🍉
*_BARKA DA SHAN RUWA_*
🍉🍉🥭🍑🍎🍊🍋🍌🍉🍉
_001_
1⃣ *MI KE TABBATAR DA SHIGAR WATAN RAMADAN???*
*_AMSA_*
Yana tabbatuwa da abubuwa guda biyu;
*_Na farko:_* cikar watan sha'aban kwana talatin
*_Na biyu:_* Ganin jinjirin watan Ramadan
2⃣ *MENENE HUKUNCIN WANDA YAGA JINJIRIN WATAN RAMADAN SHI KADAI 👌 AMMA BA'A KARBI SHAIDARSHI BA???*
*_AMSA_*
Ba zaiyi azumi ba sai tare da mutane, saboda hadisin da yazo a jaami'ut-thirmidhi da waninsa, Manzon Allah s.a.w yace: "azuminku ranar da kuke azumi(ranar da kowa ya fara)"
3⃣ *MUTUM NAWA NE ZA'A IYA KARBAR SHAIDARSU TA GANIN JINJIRIN WATAN RAMADAN???*
*_AMSA:_*
Za'a Karbi shaidar mutum daya zuwa sama, saboda hadisin da imamu Abu daud da waninsa suka ruwaito, Abdullahi Dan Umar (RA) yace; "Mutane sunga wata, sai naje na fadawa Manzon Allah s.a.w cewa ni naga wata, sai Annabi s.a.w yayi azumi, kuma ya umurci mutane da suyi azumi, imamut tirmidhi yace: ma'abota ilimi suna aiki da wannan karantarwa.
*FADAKARWA*
_Amma a wurin fitar watan Ramadan sai da shaidar mutane biyu ake ajiye azumi, kuma malamai basuyi sabani akan wannan ba._
#ABU_SINAN
+2348064734911
No comments:
Post a Comment