Monday, 5 December 2016

ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBU BA...!!! 001

*ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAI SAN GAIBU BA...!!!*

*_Fitowa ta daya(01)_*

*_DAGA; Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*
*بسم الله الرحمن الرحيم*

  ```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda baya da Abokin tarayya. Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga farin jekada   Wanda babu wani Annabi bayansa,Annabi Muhammad s.a.w tare da jama'ar gidansa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan takaitaccen rubutu saboda ganin yadda wasu yan bidi'ah ke cusa ma kananan yara Akeedar cewa Annabi yasan gaibu a makarantunsu Na Zawuyya da sauran Majami'oinsu.
Zan takaitu insha Allahu akan Qur'ani da hadisai ingantattu, saboda kada in kawo maganar wani malami na sunnah wani kuma ya kawo man ta Inyass ko wani shehi!
Ga wasu daga cikin Ayoyin Qur'ani dake nuna cewa Annabi baisan gaibu ba.```

*وعنده مفاتح الغيب لايعلمها إلا هو...*
_Ma'ana;_ *_kuma A wajenshi(Allah) makullan gaibu suke babu Wanda ya sansu sai shi(Allah)_*

*A wani wurin kuma Allah S.W.T cewa yayi;*
*_قل لايعلم من في السماوات والأرض الغيب إلا الله، وما يشعرون أيان يبعثون_*

_Ma'ana;_ ```Kace(yã kai Annabi Muhammad s.a.w) babu Wanda yasan gaibu a sama ko a kasa sai Allah, kuma basu San yaushe ne za'a tashesu ba(bayan mutuwa).```

*Idan kuma muka leka a suratu lukman aya ta karshe Allah S.W.T cewa yayi;*
*_إن الله عنده علم الساعة وينزل الغيث ويعلم ما فى الأرحم، وما تدرى نفس ماذ تكسب غدا، وما تدرى نفس بأي أرض تموت، إن الله عليم خبير_*
_Ma'ana;_ *_Lallai a wurin Allah ne Ilimin sa'a yake(Tashin kiyama) kuma shine ke saukar da girgije, kuma yasan Abunda ke cikin mahaifa, kuma babu Wata Rai da tasan Abunda zata Aikata a gobe ko Anjima, babu Wanda yasan a wace kasa ko a wane gari zai  mutu. Lallai Allah masani ne kuma mai bada labari ne._*

```Wadanan Ayoyi da na kawo dukkansu idan ka duba Tafsiran manyan Malamai wadan da ba son Rai a zuciyarsu, zaka samu sunyi cikakken bayani karara, babu boye boye ko shaci fadi, zaka samu babu Wanda ya kawo cewa Annabi yasan Gaibu.
Idan muka dawo a cikin hadissai kuwa, ga hadisi na biyu dake cikin AR'BA'UNA HADITH, Wanda tun bamu da wayo ake karantar damu shi, Hadisin Sayyidina Umar R.A Wanda imamu Muslim ya ruwaito, Lokacin da Mala'ika jibril lokacin da yake yima Annabi Muhammad s.a.w Tambayoyi, daga karshe yake tambayar shi;``` 
*فأخبرني عن الساعة: قال: ما المسئول عنها بأعلم من السائل....*
_Ma'ana;_ *_ka bani Labarin sa'a(Tashin kiyama)? Sai Annabi Muhammad s.a.w yace; Ai Wanda aka tambaya baifi Wanda yayi Tambayar sani ba._*
``` Shin idan  manzon Allah s.a.w yasan gaibu meyasa bai fada masa Ranar da za'ayi tashin kiyama ba???
Daga karshe inason in fadawa yan uwa cewa; Maganar gaskiya Annabi Muhammad s.a.w bai San gaibi ba sai Allah ya sanar dashi ta fuskar wahayi, amma kafin Allah yayi masa wahayi bai sani ba.

  Allah s.w.t Nike Roko da ya karemu da bin son zukatanmu, ya bamu ikon yin koyi da farin jekada Annabi Muhammad s.a.w a dukkanin Rayuwarmu.

Sai mun hadu a fitowa Na biyu insha Allahu```

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*

Shiga link dake kasa mu hadu a Facebook
https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

IYAYENMU NE

*_ALLAH S.W.T YACE; MATAN ANNABI IYAYENMU NE!*_

      *_Amma shi Dan shi'ah yace ba uwayenshi bane yana zaginsu, sai mukace duk Wanda yace ba iyayenshi bane toh mu munsan uwarshi, uwarshi itace hãwuyah, (wuta)_*

```ABU SINAAN```

ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBI BA...!!!

🎙🎙🎙🎙🎙🎙🎙
*ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBU BA...!!!*🎤🎤🎤🎤🎤🎤

*_Fitowa ta biyu(02)_*

*Daga; Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*Godiya ta tabbata ga Allah Wanda ya sanar da Dan Adam Abunda bai sani ba, tsira da Amincin Allah su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w tare da iyalan gidansa da sahabbansa da duk Wanda yabi hanyarsu da kyautatawa har zuwa ranar da kudi da yaya basu da amfani sai Wanda yaje ma Allah da zuciya mai tsoronshi da mika wuya gareshi.*

*_Bayan haka_*

```Nayi rubutu Mai irin wannan taken a sama sai wasu yan bidi'ah da wadanda basu fahimci addini ba suka yo Mani chaa, sai naga dacewar na kara haskaka ma Al'umma domin kowa ya kara gane inda aka nufa.

Da farko dai Menene Ma'anar gaibu???

     Ita dai Kalmar gaibu kalma ce ta larabci, wadda take hawa akan duk abunda ya boyewa sanin mutum, duk abinda tunanin mai tunani ko hankalin mai hankali bazai iya riskarsa ba to shi ake cewa gaibu. Misali; Sanin yaushe zaka mutu, sanin Abinda zai sami rayuwarka a nan gaba, da sanin ranar tashin Kiyama duk suna daga cikin Misalan gaibu. (Nemi rubutun Abokin da'awa a fagen Media Malam Awaisu Al'araby fagge Wanda yayi a 28/04/2015 domin Karin bayani.)
Idan ka fahimci ma'anar gaibu, toh sai mu leka Qur'ani domin mu warware matsalar.
A cikin Qur'ani Allah S.W.T yake cewa;```
*يسئلك الناس عن الساعة، قل إنما علمها عند الله، وما يدريك لعل الساعة تكون قريبا.*
_Ma'ana;_ *_suna tambayarka(Annabi Muhammad s.a.w) akan lokaci(Tashin kiyama), sai Allah yace, kace saninta(Tashin kiyama) yana wurin Allah kadai. Kuma meya sanar dakai watakila ta kasance kusa._*

   ```Wannan ayar koda ace ita kadai aka saukar akan ilimin gaibu to tabbas ta isa hujja akan wadancan yan bidi'ar, abunda mutane basu fahimta ba akan wannan lamarin shine, su yan bidi'ah suna son fakewa da guzuma domin Harbin karsana, idan su ka yarda Almajiransu suka gane cewa Annabi Muhammad s.a.w baisan gaibu ba, sai Wanda Allah ya sanar dashi,idan kuma Allah ya sanar dashi ya tashi daga gaibu zuwa wahayi, toh idan suka fahimci wannan toh zasu gane cewa Ashe wadancan waliyyan na bugi yaudararsu sukeyi, domin sunce Sunsan gaibu, hujjarsu ta cewa haka saboda saboda tijjani da inyass duk jikokin Annabi ne, toh tunda Annabi yasan gaibu toh toh toh ai ai ai shi kuma jikane, saboda haka dole mu haska ma Al'umma domin su fahimci ina gaskiyar take.
  Wata ayar kuma Allah S.W.T cewa yayi;```
*ولا أقول لكم عندى خزائن الله ولا أعلم الغيب...*

_Ma'ana:_ *_(Allah ne da kanshi ya cewa Annabi Muhammad s.a.w ya fadawa mutane cewa) Ban ce muku Taskokin Allah a hannuna suke ba, sannan kuma bansan gaibu ba._*

   ```To anan Abunda zance shine duk Wanda ya fahimci ma'anar gaibu wacce muka ambata a farkon rubutu, to zai fahimci cewa Manzon Allah s.a.w baisan gaibu ba,sai Wanda Allah ya sanar dashi, idan kuma Allah ya sanar dashi ya tashi daga gaibu zuwa wahayi, Allah ya kara fahimtar damu gaskiya ya bamu ikon binta.
Toh yanzu bari mu leka cikin hadisi.```
 
*Hadisi ya tabbata daga ummuna Aisha R.A akan cewa Annabi baisan gaibu ba.*
*عن عائشة رضي الله عنها قالت؛ من حدثك أن محمدا صلى الله عليه وسلم رأى ربه فقد كذب وهو يقول(لاتدركه ألابصار)، ومن حدثك أنه يعلم الغيب فقد كذب وهو يقول لايعلم الغيب إلا الله*

_Ma'ana:_ *_Nana Aisha tace "duk Wanda yace maka Annabi Muhammad s.a.w yaga Allah toh karya yakeyi, sannan duk Wanda yace maka Annabi yasan gaibu to karya yakeyi, domin shi din yana cewa babu Wanda yasan gaibu sai Allah._*[Bukhari 7380,6945, Muslim 457,287]

   ```Toh yan uwa kunji zancen Nana Aisha matar Manzon Allah s.a.w wacce take kusa dashi a koda yaushe, Masu karyata Ahlis sunnah akan wannan zancen to me zakuce akan zancen Nana Aisha??? Nasan indai ka yarda Nana Aisha uwar muminai ce to baza ka karyata taba, domin indai kai mumini ne to uwarka ce, idan kace ba uwarka bace sai muce toh ai munsan wacece uwarka, eh itace hãwuya, Allah ya kyauta. Bari na dakata a nan idan bukatuwar fitowa na uku ta taso, toh a matsayinmu na dalibai zamu kara cewa wani Abu.
Allah ka jikan sheikhul Islam Muhammad ibn Abdulwahab, a cikin Littafinsa kashfus shubuhãt yake cewa;```
*والعامي من الموحدين يغلب ألفا من علماء هؤلاء المشركين، كما قال تعال؛(وإن جندنا لهم الغلبون) [الصافات ١٧٣]*

_Ma'ana;_ *_Mai karamin sani(ilimi) cikin masu kadaita Allah yana rinjayar mutum dubu cikin mushirikan Malaman bidi'ah, kamar yadda Allah yace; Rundunar Allah sune Masu yin nasara. Rundunar Allah sune masu yin nasara da hujja Qur'ani da hadisi, haka kuma suke yin nasara da harshensu._*

```Allah ya tabbatar damu akan sunnar Annabi Muhammad s.a.w ya dawwamar damu a cikin aiki da ita Amiin.```

https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

Copyright©
*Hashim Surajo Uba Tsamiya*
📞08064734911📞

MA'ANAR SAHABI

🎙🎙🎙🎙🎙🎙🎙
*MU WASA KWAKWALWA*
🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤

*_MA'ANAR SAHABI'_* _Wanda ya hadu da Manzon Allah s.a.w yayi imani dashi, ya mutu akan imani! Ka'ida uku kenan._

*_TAMBAYA ANAN ITACE;_* _Wanda ya hadu da Manzon Allah s.a.w baiyi imani dashi ba, sai bayan Annabi ya rasu, sannan yayi imani dashi, kuma ya mutu akan imani, shi kuma meye sunanshi???_

*Amsa nikeso tare da cikakkar hujja, mu hadu a private chat a _08064734711_ ko a Facebook message, ta https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya domin tattaunawa idan ka kawo amsa tare da hujja mai karfi.

*ABU SINÃN* *_Hashim surajo uba Tsamiya_*

العقيدة

♨ﻋﻠﻤﻮﺍ ﺃبناءكم و اخوانكم ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ﺑﺘﻜﺮﺍﺭ ﻫﺬﻩ ﺍﻷﺳﺌﻠﺔ ﻋﻠﻴﻬﻢ♨
🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺
🔴ﺱ /1 ﻣﻦ ﺃﻳﻦ ﻧﺄﺧﺬ ﻋﻘﻴﺪﺗﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ .
🔴ﺱ /2 ﺃﻳﻦ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻓﻲ ﺍﻟﺴﻤﺎﺀ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻌﺮﺵ .
🔴ﺱ /3 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻌﺮﺵ ؟
🔹ﺝ : ( ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻌﺮﺵ ﺍﺳﺘﻮﻯ ) .
🔴ﺱ /4 ﻣﺎ ﻣﻌﻨﻰ ( ﺍﺳﺘﻮﻯ ) ؟
🔹ﺝ : ﻋﻼ ﻭﺍﺭﺗﻔﻊ .
🔴ﺱ /5 ﻟﻤﺎﺫﺍ ﺧﻠﻖ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺠﻦ ﻭﺍﻹﻧﺲ ؟
🔹ﺝ : ﻟﻌﺒﺎﺩﺗﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ .
🔴ﺱ /6 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﺧﻠﻖ ﺍﻟﺠﻦ ﻭﺍﻹﻧﺲ ﻟﻌﺒﺎﺩﺗﻪ ؟
🔹ﺝ : ( ﻭﻣﺎ ﺧﻠﻘﺖ ﺍﻟﺠﻦ ﻭﺍﻹﻧﺲ ﺇﻻ ﻟﻴﻌﺒﺪﻭﻥ ) .
🔴ﺱ /7 ﻣﺎ ﻣﻌﻨﻰ ( ﻳﻌﺒﺪﻭﻥ ) ؟
🔹ﺝ : ﻳﻮﺣﺪﻭﻥ .
🔴ﺱ /8 ﻣﺎ ﻣﻌﻨﻰ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻻ ﻣﻌﺒﻮﺩ ﺑﺤﻖ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ .
🔴ﺱ /9 ﻣﺎ ﺃﻋﻈﻢ ﻋﺒﺎﺩﺓ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ .
🔴ﺱ /10 ﻣﺎ ﺃﻋﻈﻢ ﻣﻌﺼﻴﺔ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻟﺸﺮﻙ .
🔴ﺱ /11 ﻣﺎﻫﻮ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ؟
🔹ﺝ : ﺇﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﺎﻟﻌﺒﺎﺩﺓ .
🔴ﺱ /12 ﻣﺎﻫﻮ ﺍﻟﺸﺮﻙ ؟
🔹ﺝ : ﻋﺒﺎﺩﺓ ﻏﻴﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻊ ﺍﻟﻠﻪ .
🔴ﺱ /13 ﻛﻢ ﺃﻗﺴﺎﻡ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ؟
🔹ﺝ : ﺛﻼﺛﺔ .
🔴ﺱ /14 ﻣﺎﻫﻲ ﺃﻗﺴﺎﻡ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ؟
🔹ﺝ :ﺍﻟﺮﺑﻮﺑﻴﺔ ﻭﺍﻷﻟﻮﻫﻴﺔ ﻭﺍﻷﺳﻤﺎﺀ ﻭﺍﻟﺼﻔﺎﺕ .
🔴ﺱ /15 ﻣﺎ ﺗﻌﺮﻳﻒ ﺗﻮﺣﻴﺪ ﺍﻟﺮﺑﻮﺑﻴﺔ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ ﺃﻓﻌﺎﻟﻪ ﻣﺜﻞ ﺍﻟﺨﻠﻖ ﻭﺍﻟﺮﺯﻕ .
🔴ﺱ /16 ﻣﺎ ﺗﻌﺮﻳﻒ ﺗﻮﺣﻴﺪ ﺍﻷﻟﻮﻫﻴﺔ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﺄﻓﻌﺎﻝ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩ ﻣﺜﻞ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻭﺍﻟﺬﺑﺢ ﻭﺍﻟﺴﺠﻮﺩ .
🔴ﺱ /17 ﻫﻞ ﻟﻠﻪ ﺃﺳﻤﺎﺀ ﻭﺻﻔﺎﺕ ؟
🔹ﺝ : ﻧﻌﻢ .
🔴ﺱ /18 ﻣﻦ ﺃﻳﻦ ﻧﺄﺧﺬ ﺃﺳﻤﺎﺀ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺻﻔﺎﺗﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ .
🔴ﺱ /19 ﻫﻞ ﺗﺸﺒﻪ ﺻﻔﺎﺕ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻔﺎﺗﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ﻻ .
🔴ﺱ /20 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺻﻔﺎﺕ ﺍﻟﻠﻪ ﻻ ﺗﺸﺒﻪ ﺻﻔﺎﺗﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ( ﻟﻴﺲ ﻛﻤﺜﻠﻪ ﺷﻲﺀ ﻭﻫﻮ ﺍﻟﺴﻤﻴﻊ ﺍﻟﺒﺼﻴﺮ ) .
🔴ﺱ /21 ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻛﻼﻡ ﻣﻦ ؟
🔹ﺝ : ﻛﻼ‌ﻡ ﺍﻟﻠﻪ .
🔴ﺱ /22 ﻣﻨﺰﻝ ﺃﻡ ﻣﺨﻠﻮﻕ ؟
🔹ﺝ : ﻣﻨﺰﻝ ﻭ ﻫﻮ ﻛﻼﻣﻪ ﺣﻘﻴﻘﺔ ﺑﺤﺮﻑ ﻭ ﺻﻮﺕ .
🔴ﺱ /23 ﻣﺎ ﻫﻮ ﺍﻟﺒﻌﺚ ؟
🔹ﺝ : ﺇﺣﻴﺎﺀ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺑﻌﺪ ﻣﻮﺗﻬﻢ .
🔴ﺱ /24 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﻛﻔﺮ ﻣﻦ ﺃﻧﻜﺮ ﺍﻟﺒﻌﺚ ؟
🔹ﺝ : ( ﺯﻋﻢ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻛﻔﺮﻭﺍ ﺃﻥ ﻟﻦ ﻳﺒﻌﺜﻮﺍ ) .
🔴ﺱ /25 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﺳﻴﺒﻌﺜﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ( ﻗﻞ ﺑﻠﻰ ﻭﺭﺑﻲ ﻟﺘﺒﻌﺜﻦ ) .
🔴ﺱ /26 ﻛﻢ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻹﺳﻼﻡ ؟
🔹ﺝ : ﺧﻤﺴﺔ .
🔴ﺱ /27ﻛﻢ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻹﻳﻤﺎﻥ ؟
🔹ﺝ : ﺳﺘﺔ .
🔴ﺱ /28ﻛﻢ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻺﺣﺴﺎﻥ ؟
🔹ﺝ : ﻭﺍﺣﺪ .
🔴ﺱ /29 ﻣﺎﺗﻌﺮﻳﻒ ﺍﻺﺳﻼﻡ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻻﺳﺘﺴﻼﻡ ﻟﻠﻪ ﺑﺎﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ﻭﺍﻻﻧﻘﻴﺎﺩ ﻟﻪ ﺑﺎﻟﻄﺎﻋﺔ ﻭﺍﻟﺒﺮﺍﺀﺓ ﻣﻦ ﺍﻟﺸﺮﻙ ﻭﺃﻫﻠﻪ .
🔴ﺱ /30 ﻣﺎ ﺗﻌﺮﻳﻒ ﺍﻹﻳﻤﭑﻥ ؟
🔹ﺝ : ﺃﻥ ﺗﺆﻣﻦ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻭﻣﻼﺋﻜﺘﻪ ﻭﻛﺘﺒﻪ ﻭﺭﺳﻠﻪ ﻭﺍﻟﻴﻮﻡ ٱﻵخر ﻭﺍﻟﻘﺪﺭ ﺧﻴﺮﻩ ﻭﺷﺮﻩ،
ﻭﺍﻹﻳﻤﭑﻥ ﺇﻋﺘﻘﺎﺩ ﺑﺎﻟﻘﻠﺐ ﻭﻗﻮﻝ ﺑﺎﻟﻠﺴﺎﻥ ﻭﻋﻤﻞ ﺑﺎﻟﺠﻮﺍﺭﺡ ﻳﺰﻳﺪ ﺑﺎﻟﻄﺎﻋﺔ ﻭﻳﻨﻘﺺ ﺑﺎﻟﻤﻌﺼﻴﺔ
.
🔴ﺱ /31 ﻟﻤﻦ ﻧﺬﺑﺢ ﻭﻧﺴﺠﺪ ؟
🔹ﺝ : ﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ .
🔴ﺱ /32 ﻫﻞ ﻳﺠﻮﺯ ﺍﻟﺬﺑﺢ ﻭﺍﻟﺴﺠﻮﺩ ﻟﻐﻴﺮ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻻ .
🔴ﺱ /33 ﻣﺎﺣﻜﻢ ﺍﻟﺬﺑﺢ ﻭﺍﻟﺴﺠﻮﺩ ﻟﻐﻴﺮ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﺷﺮﻙ ﺃﻛﺒﺮ .
📚 انشرها قدر استطاعتك

ALLAH YA KYAUTA

*_YANXU IDAN AKA CIRE WASU  JAHOHIN DAKE NORTHEAST (BORNO, ADAMAWA, GOMBE, YOBE), BABU JAHAR DA TAFI RASHIN ZAMAN LAFIYA KAMAR ZAMFARA!_* 

```KO MEYA KAWO HAKAN???

A NAWA TUNANIN SHINE HARDA WASA DA SHARI'AH DA MUKEYI ZAI IYA KAWO HAKA!  ANCE ANA SHARI'AR MUSULUNCI, TOH AMMA GA WANI YA SACI HANDSET (WAYA) AN DAURESHI SHEKARU A GIDAN KASO, SHI KUMA WANCAN YA SACI DUKIYAR GWAMNATI(BAITUL MALI) KUSAN BILIYOYAN KUDI, AMMA AN KYALESHI, KUMA MUTANE BÃSUYI MASHI KALLON BARAWO!

ANYA! ANYA!! ANYA!!!

ALLAH YA KYAUTA```

Sunday, 4 December 2016

KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???

🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤
*_KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???_*
🔊🔈🔊🔈🔉🔉🔊

_Fitowa ta daya 001_

_Rubutawa:_ *Hashim Surajo Uba Tsamiya*  *(ABU SINÃN)*

    *_Godiya ta tabbata ga Allah, Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga Manzon Allah s.a.w da mutanen gidansa da  Sahabbansa da wadanda suka bi tafarkinsa._*

_Bayan haka;_

```Naga da cewar nayi wannan rubutun ne saboda yadda naga watan da yan bidi'ah ke sheke ayarsu ya kama, sannan kuma a wannan watane suke rudar jahillai suna batar dasu.
Amsar taken wannan rubutu itace; Bai halasta ayi bikin Maulidin Annabi ko maulidin waninsa daga cikin magabata, saboda yin haka yana daga cikin bidi'o'in da aka kirkiro a cikin addini, domin kuwa Manzon Allah s.a.w bai yiba, haka ma khalifofinshi guda Hudu shiryayyu da sauran sahabbai da wadanda suka bisu da kyautatawa duk basu yi maulidi ba, tare da cewa sunfi kowa sanin Sunnah da kuma aiki da ita, sunfi kowa So da kyaunar Annabi Muhammad s.a.w da kuma biyayya ga shari"'arsa, bisa wadanda suka zo bayansu.
Hadisi ya tabbata daga Annabi Muhammad s.a.w cewa;```
(من أحدث في أمرنا هذا ما ليس منه فهو رد).

_Ma'ana;_ *_Wanda ya kirkiro wani Abu a cikin wannan Al'amari namu(Addininmu) Wanda baya cikinsa, toh wannan Abu an mayar masa dashi.(Baza'a karba ba)_*

_Manzon Allah s.a.w a wani hadisin kuma sai yace;_
عليكم بسنتي وسنة الخلفاء الراشدين المهديين من بعدي، تمسكوا بها وعضوا عليها بالنواجد وإياكم ومحدثات الأمور، فإن كل محدثة بدعة وكل بدعة ضلالة.

_Ma'ana;_ *_Kuyi Riko da sunnah ta da sunnar khalifofi shiryayyu masu shiryarwa a bayana, kuyi riko da ita, kuma Ku cije a kanta da ha'koranku na can ciki, kuma Ku kiyayi kirkirarrun al'amurra, domin dukkan 'kir'kirarren Abu (a cikin Addini) bidi'ah ne, kuma dukkan bidi'ah bata CE._*

  ```A cikin wadannan hadisai biyu, akwai kashedi mai tsanani a kan kirkirar bidi'ah da kuma aiki da ita!
Allah madaukakin sarki ya fada a cikin littafinsa mai tsarki cewa;```
((وما ءاتكم الرسول فخذوه وما نهاكم عنه فانتهوا)).

_Ma'ana;_ *_Abin da Manzon Allah yazo muku dashi to Ku rikeshi, abin da kuma ya haneku ga barinsa, toh Ku hanu. [Al-hashr, aya ta 7]_*
A nan Allah yayi mana umurni da bin manzon Allah ba da yin maulidi ba

A wani wurin kuma sai Allah yace;
((فليحذر الذين يخالفون عن أمره أن تصيبهم فتنة أو يصيبكم عذاب أليم))
_Ma'ana;_ *_Wadanda suke saba wa umurninsa, baza suyi tunanin wata fitina ta samesu ba, ko wata azaba mai radadi ta samesu[An-Nur, aya ta 63]_*
A Wata ayar sai Allah yace;
اليوم أكملت لكم دينكم وأتممت عليكم نعمتي ورضيت لكم الإسلام دينا.

_Ma'ana;_ *_A yau na kammala maku addininku, kuma na cika ni'imata a kanku, kuma na yarda da musulunci ya zama Addini a gareku._*
          [Al-ma'ida aya ya 3]
 
Da kuwa ace maulidi addinine da yazo kafin saukar wannan ayar.

```Ayoyi da suke da irin wannan ma'ana suna da yawa, kuma kirkiro irin wadannan tarurruka na Maulidi yana nuna cewa Allah s.w.t bai cika Addini ba! Kuma Manzon Allah s.a.w bai Isarwa Al'umma da abunda ya kamata suyi aiki dashi ba! (Wanda duk ya fadi haka kuwa to tabbas ya zama ARNE)
Domin kuwa manzon Allah s.a.w a cikin hadisi ingantace yake cewa;
((ما بعث الله من نبي إلا كان حقا عليه أن يدل أمته على خير ما يعلمه لهم، وينذرهم شر ما يعلمه لهم)).

Ma'ana; Allah bai aiko wani Annabi ba, face ya kasance hakki ne akan wannan Annabin ya nuna wa Al'ummarsa Alherin da ya sani garesu, kuma yayi musu gargadi daga sharrin da ya sani garesu. [Muslim]

Wadannan ayoyi da hadissai kawai sun isa su tabbatar mana da cewa Maulidi ba Addinin Annabi Muhammadu bane, ba ya daga cikin hanyoyin shiriya na Addini, Hasali ma BIDI'AH CE abar kyama.

BIDI'AH SAMM

        TAUHIDI SAKKKKK

          MAULIDI SAM SAM SAM SAM SAM```

Sai mun hadu a fitowa na gaba.

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*
📞08064734911
Https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya
Http://hashimtsamiya.blogspot.com