*ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAI SAN GAIBU BA...!!!*
*_Fitowa ta daya(01)_*
*_DAGA; Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda baya da Abokin tarayya. Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga farin jekada Wanda babu wani Annabi bayansa,Annabi Muhammad s.a.w tare da jama'ar gidansa da sahabbansa baki daya.
Bayan haka; Nayi nufin yin wannan takaitaccen rubutu saboda ganin yadda wasu yan bidi'ah ke cusa ma kananan yara Akeedar cewa Annabi yasan gaibu a makarantunsu Na Zawuyya da sauran Majami'oinsu.
Zan takaitu insha Allahu akan Qur'ani da hadisai ingantattu, saboda kada in kawo maganar wani malami na sunnah wani kuma ya kawo man ta Inyass ko wani shehi!
Ga wasu daga cikin Ayoyin Qur'ani dake nuna cewa Annabi baisan gaibu ba.```
*وعنده مفاتح الغيب لايعلمها إلا هو...*
_Ma'ana;_ *_kuma A wajenshi(Allah) makullan gaibu suke babu Wanda ya sansu sai shi(Allah)_*
*A wani wurin kuma Allah S.W.T cewa yayi;*
*_قل لايعلم من في السماوات والأرض الغيب إلا الله، وما يشعرون أيان يبعثون_*
_Ma'ana;_ ```Kace(yã kai Annabi Muhammad s.a.w) babu Wanda yasan gaibu a sama ko a kasa sai Allah, kuma basu San yaushe ne za'a tashesu ba(bayan mutuwa).```
*Idan kuma muka leka a suratu lukman aya ta karshe Allah S.W.T cewa yayi;*
*_إن الله عنده علم الساعة وينزل الغيث ويعلم ما فى الأرحم، وما تدرى نفس ماذ تكسب غدا، وما تدرى نفس بأي أرض تموت، إن الله عليم خبير_*
_Ma'ana;_ *_Lallai a wurin Allah ne Ilimin sa'a yake(Tashin kiyama) kuma shine ke saukar da girgije, kuma yasan Abunda ke cikin mahaifa, kuma babu Wata Rai da tasan Abunda zata Aikata a gobe ko Anjima, babu Wanda yasan a wace kasa ko a wane gari zai mutu. Lallai Allah masani ne kuma mai bada labari ne._*
```Wadanan Ayoyi da na kawo dukkansu idan ka duba Tafsiran manyan Malamai wadan da ba son Rai a zuciyarsu, zaka samu sunyi cikakken bayani karara, babu boye boye ko shaci fadi, zaka samu babu Wanda ya kawo cewa Annabi yasan Gaibu.
Idan muka dawo a cikin hadissai kuwa, ga hadisi na biyu dake cikin AR'BA'UNA HADITH, Wanda tun bamu da wayo ake karantar damu shi, Hadisin Sayyidina Umar R.A Wanda imamu Muslim ya ruwaito, Lokacin da Mala'ika jibril lokacin da yake yima Annabi Muhammad s.a.w Tambayoyi, daga karshe yake tambayar shi;```
*فأخبرني عن الساعة: قال: ما المسئول عنها بأعلم من السائل....*
_Ma'ana;_ *_ka bani Labarin sa'a(Tashin kiyama)? Sai Annabi Muhammad s.a.w yace; Ai Wanda aka tambaya baifi Wanda yayi Tambayar sani ba._*
``` Shin idan manzon Allah s.a.w yasan gaibu meyasa bai fada masa Ranar da za'ayi tashin kiyama ba???
Daga karshe inason in fadawa yan uwa cewa; Maganar gaskiya Annabi Muhammad s.a.w bai San gaibi ba sai Allah ya sanar dashi ta fuskar wahayi, amma kafin Allah yayi masa wahayi bai sani ba.
Allah s.w.t Nike Roko da ya karemu da bin son zukatanmu, ya bamu ikon yin koyi da farin jekada Annabi Muhammad s.a.w a dukkanin Rayuwarmu.
Sai mun hadu a fitowa Na biyu insha Allahu```
Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*
Shiga link dake kasa mu hadu a Facebook
https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya