Saturday, 2 November 2019

04 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD

🖋 *BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD S.A.W*

● MALAMAN LAJNATUD DA'IMAH(Allah ya gafarta musu) SUKA CE:

*《Bukukuwan da akeyi saboda munasaba ta ranar da aka haifi Annabi bidi'ah ce haramtacciya, saboda babu dalili a cikin qur'ani ko hadisi da yake nuna halascin yin hakan, Kuma ba'a samu wani daya daga cikin khalifofin Annabi ba Wanda ya aikata, haka a cikin Qarnukan Nan masu falala ba'a samu wani Wanda ya aikata ba》.*

📓📔|[ فتاوى اللجنة الدائمة (٢٤٤/٢) ]|

https://fb.me/abbansinan

#ABBAN_SINAN
+2349030201868

03. BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD

*🖋 BIDI'AR MAULIDIN ANNABI.A.W*

● ALLAMA AT-TUWAIJARY(RH) YANA CEWA:

*《Wadannan da suka riki maulidi ya zama idi, basu daga cikin wadanda ake yima fatar Allah ya basu lada akan wannan bidi'ar, abunda ma muke jiye musu tsoro shine azabar Allah, saboda saba umurnin abunda Manzon Allah S.A.W da Sahabbai suke akanshi.*
📓📔 |[ الرد القوي على الرفاعي والمجهول ابن علوي (ص ٢٢٣) ]|

https://fb.me/abbansinan

WANENE MAI GIRMAN KAI?

*WANENE MAI GIRMAN KAI GA ALLAH*❓

🍂IBN BA'D'DA AL-UKBARY(RH) YANA CEWA:

*Duk Wanda yaji gaskiya yayi inkarinta bayan yasan gaskiya ce, wannan Yana daga cikin masu girman Kai ga Allah, duk Wanda ya taimaka wurin yin sabo/zunubi/laifi Yana daga cikin tawagar shaidan.*

*📚 الإبانة في شرح أصول الديانة (٦٨٨)*

https://fb.me/abbansinan

02 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD

*🖋 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI S.A.W*

● AL-ALLAMA NASIRUDDEEN AL-ALBANY(RH) YANA CEWA:

*Mu AHLISSUNNAH dasu(yan bidi'ah) mun hadu akan cewa wannan bikin na maulidi abune kirkirarre, bai kasance ba a zamanin Manzon Allah S.A.W, Kai ba zamanin Manzon Allah S.A.W kadai ba, har karni uku(300+ years) suka wuce ba'a San dashi ba, Manzon Allah S.A.W bai taba yin biki ba saboda murnar haihuwar wani mutum a rayuwarsa, bikin maulidi hanyace ta kiristoci nasraniyya, masihiyya, musulunci bai San da maulidi ba Sam a wadancan karni masu daraja da muka ambata.*

📓📔 |[ من شريط بدعة المولد ]|

https://fb.me/abbansinan

01 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI

*🖋 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI S.A.W*

AL-ALLAMA ABDULLAHI BN HUMAID(RH) YANA CEWA:

*《Masu tsayuwa akan wadancan bukukuwan(maulidi) idan suna nufin sunyi hakan ne saboda girmama Manzon Allah S.A.W, toh su sani su masu sabawa shiriyarshi ne, masu kuskure ne akan hakan, baya daga cikin girmama Manzon Allah S.A.W kirkiro bidi'ah a cikin addinin daya zo dashi, ta hanyar ragi ko Kari, ko chanjawa ko karkatarwa, kyakyawar niyya da manufa Mai kyau basu halasta kirkiro bidi'ah a cikin addini 》.*

📓📔 |[ الرسائل الحسان في نصائح الإخوان للشيخ ابن حميد (ص ٣٩) ]|

https://fb.me/abbansinan

KIRKIRAR BIDI'AH

*KIRKIRAR BIDI'AH A CIKIN ADDINI IZGILI NE DA ALLAH; DOMIN KANA KUSANTAR MASHI ABUNDA BAI SHAR'ANTA BA.*

القول المفيد على كتاب التوحيد لابن عثيمين (١/٦٧)

https://fb.me/abbansinan

KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA

🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤
*_KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???_*
🔊🔈🔊🔈🔉🔉🔊

_Fitowa ta daya 001_

_Rubutawa:_ *Hashim Surajo Uba Tsamiya*  *(ABU SINÃN)*

    *_Godiya ta tabbata ga Allah, Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga Manzon Allah s.a.w da mutanen gidansa da  Sahabbansa da wadanda suka bi tafarkinsa._*

_Bayan haka;_

```Naga da cewar nayi wannan rubutun ne saboda yadda naga watan da yan bidi'ah ke sheke ayarsu ya kama, sannan kuma a wannan watane suke rudar jahillai suna batar dasu.
Amsar taken wannan rubutu itace; Bai halasta ayi bikin Maulidin Annabi ko maulidin waninsa daga cikin magabata, saboda yin haka yana daga cikin bidi'o'in da aka kirkiro a cikin addini, domin kuwa Manzon Allah s.a.w bai yiba, haka ma khalifofinshi guda Hudu shiryayyu da sauran sahabbai da wadanda suka bisu da kyautatawa duk basu yi maulidi ba, tare da cewa sunfi kowa sanin Sunnah da kuma aiki da ita, sunfi kowa So da kyaunar Annabi Muhammad s.a.w da kuma biyayya ga shari"'arsa, bisa wadanda suka zo bayansu.
Hadisi ya tabbata daga Annabi Muhammad s.a.w cewa;```
(من أحدث في أمرنا هذا ما ليس منه فهو رد).

_Ma'ana;_ *_Wanda ya kirkiro wani Abu a cikin wannan Al'amari namu(Addininmu) Wanda baya cikinsa, toh wannan Abu an mayar masa dashi.(Baza'a karba ba)_*

_Manzon Allah s.a.w a wani hadisin kuma sai yace;_
عليكم بسنتي وسنة الخلفاء الراشدين المهديين من بعدي، تمسكوا بها وعضوا عليها بالنواجد وإياكم ومحدثات الأمور، فإن كل محدثة بدعة وكل بدعة ضلالة.

_Ma'ana;_ *_Kuyi Riko da sunnah ta da sunnar khalifofi shiryayyu masu shiryarwa a bayana, kuyi riko da ita, kuma Ku cije a kanta da ha'koranku na can ciki, kuma Ku kiyayi kirkirarrun al'amurra, domin dukkan 'kir'kirarren Abu (a cikin Addini) bidi'ah ne, kuma dukkan bidi'ah bata CE._*

  ```A cikin wadannan hadisai biyu, akwai kashedi mai tsanani a kan kirkirar bidi'ah da kuma aiki da ita!
Allah madaukakin sarki ya fada a cikin littafinsa mai tsarki cewa;```
((وما ءاتكم الرسول فخذوه وما نهاكم عنه فانتهوا)).

_Ma'ana;_ *_Abin da Manzon Allah yazo muku dashi to Ku rikeshi, abin da kuma ya haneku ga barinsa, toh Ku hanu. [Al-hashr, aya ta 7]_*
A nan Allah yayi mana umurni da bin manzon Allah ba da yin maulidi ba

A wani wurin kuma sai Allah yace;
((فليحذر الذين يخالفون عن أمره أن تصيبهم فتنة أو يصيبكم عذاب أليم))
_Ma'ana;_ *_Wadanda suke saba wa umurninsa, baza suyi tunanin wata fitina ta samesu ba, ko wata azaba mai radadi ta samesu[An-Nur, aya ta 63]_*
A Wata ayar sai Allah yace;
اليوم أكملت لكم دينكم وأتممت عليكم نعمتي ورضيت لكم الإسلام دينا.

_Ma'ana;_ *_A yau na kammala maku addininku, kuma na cika ni'imata a kanku, kuma na yarda da musulunci ya zama Addini a gareku._*
          [Al-ma'ida aya ya 3]
 
Da kuwa ace maulidi addinine da yazo kafin saukar wannan ayar.

```Ayoyi da suke da irin wannan ma'ana suna da yawa, kuma kirkiro irin wadannan tarurruka na Maulidi yana nuna cewa Allah s.w.t bai cika Addini ba! Kuma Manzon Allah s.a.w bai Isarwa Al'umma da abunda ya kamata suyi aiki dashi ba! (Wanda duk ya fadi haka kuwa to tabbas ya zama ARNE)
Domin kuwa manzon Allah s.a.w a cikin hadisi ingantace yake cewa;
((ما بعث الله من نبي إلا كان حقا عليه أن يدل أمته على خير ما يعلمه لهم، وينذرهم شر ما يعلمه لهم)).

Ma'ana; Allah bai aiko wani Annabi ba, face ya kasance hakki ne akan wannan Annabin ya nuna wa Al'ummarsa Alherin da ya sani garesu, kuma yayi musu gargadi daga sharrin da ya sani garesu. [Muslim]

Wadannan ayoyi da hadissai kawai sun isa su tabbatar mana da cewa Maulidi ba Addinin Annabi Muhammadu bane, ba ya daga cikin hanyoyin shiriya na Addini, Hasali ma BIDI'AH CE abar kyama.

Sai mun hadu a fitowa na gaba.

*ABU SINÃN*
📞08064734911

Https://fb.me/abbansinan