Saturday, 15 July 2017

MEYASA BA'A AMSA ADDU'OINMU???


*MEYASA MUKE ADDU'AH, AMMA SAI MUGA KAMAR BA'A KARBA MANA???*

```An tambayi Ibrahim bn Adham(RH) akan cewa meya samemu ne, muna Addu'ah amma ba'a karba mana??

Sai yace: Zukatanku sun mutu da Abubuwa takwas(8).

NA FARKO; Munsan Allah, amma ba muyi mashi biyayya(ma'ana; munsan hakkin Allah, amma bamu gabatar mashi da hakkinshi).

NA BIYU; Muna karanta Alkur'ani, amma bamu aiki dashi(ma'ana: Bamu aiki da iyakokin da Allah ya gindaya a cikin Qur'anin).

NA UKU: Munce munason Manzon Allah (Salallahu alaihi wasallam), amma sai muka yi mashi tawaye, muka kiyin amfani da sunnar shi.

NA HUDU: Munsan cewa Shaidan makiyinmu ne, amma sai muka sakar mashi akala muna binshi.(Muna yi mashi biyayya wajen sabon Allah).

NA BIYAR: Munsan cewa Aljanna gaskiya ce, amma bamu aiki domin mu shigeta.

NA SHIDA: Munsan cewa wuta gaskiya ce, amma bamu guje mata.

NA BAKWAI: Mun wayi gari mun shagaltu da aiboban(harkokin) mutane, mu kuma mun bar namu aiboban(harkokin).

NA TAKWAS: Kun binne mataccinku, amma Baku lura da kuma wataran za'a binneku.

NA TARA: Mun ce, muna tsoron mutuwa, amma ba muyi mata tanadi ba.

NA GOMA: Muna cinye ni'imomin Allah, Amma bamu gode mashi(muna cinye abincin Allah, abin shan Allah, da sauran ni'imomi amma mun kasa gode mashi).

Wadannan da wasunsu sune dalillan dake sa muke rokon Allah sai Allah ya kyalemu da dabararmu.

Yaa Allah ka bamu ikon gode maka.
Yaa Allah ka karo mana ni'imominka ta hanyar da muka sani da wacce bamu sani ba.```

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
+2348064734911
+2349030201868

SHAFUKAN SADA ZUMUNTA DOMIN BIBIYARMU.

atstsamawy@gmail.com

hashimusurajo5@gmail.com

I G @ abbansinan

http://hashimtsamiya.blogspot.com/

http://abbansinaan.blogspot.com/

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com/

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com/

https://mobile.facebook/hashimusurajo.tsamiya/

Saturday, 1 July 2017

MUHADARA MAI TAKEN; AMFANI DA KUMA ILLOLIN SOCIAL MEDIA

*MUHADARA MAI TAKEN; AMFANI DA KUMA ILLOLIN SOCIAL MEDIA*

   Muhadara mai taken amfani da kuma illolin social media a cikin al'umma wacce kwamitin matasa na *SHABABU AHLISSUNNAH WALJAMA'AH SUKA SHIRYA DOMIN GORON SALLAH,* muhadarar wacce *USTAZ MUSA S LAWAL(Abu salih Ibn salih)* ya gabatar a masallacin *UTHMAN BIN AFFAN TSAFE,*

Wallahi akwai abubuwan da ya kamata mu amfana dasu kwarai da gaske a cikin wannan muhadara.
Kai dai kawai shiga link dake kasa domin saukewa a wayanka.
👇👇👇👇👇👇👇👇
*Amfani da illolin social media by Ustaz musa s lawal Tsafe*

http://darulfikr.com/s/24715

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi akan wannan lecture da yayi mana.

darulfikr.com takuce domin yada Sunnah a koda yaushe.

Copyright©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya
+2348064734911
+2349030201868

Monday, 26 June 2017

2017 RAMADAN TAFSEER

*2017 COMPLETE  RAMADAN  TAFSEER*

   COMPLETE  2017 RAMADAN  TAFSEER DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABU HURAIRA AREA  II TSAFE.

  wanda Malam Sani Liman Tsafe (ABI HURAIRA)   yake gabatarwa a Area II Tsafe, jahar Zamfara  Nigeria.

Shiga  links dake kasa  Domin saukewa Cikin sauki ka saurara  Cikin kyakykyawan Sauti.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

01 Ramadan Tafseer 1438Ah Suratul Nisa i By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24378

02 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24379

03 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24380

04 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24381

05 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Sani LimanTsafe
http://darulfikr.com/s/24382

08 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24383

09 Ramadan Tafseer Akan Hukunce Hukunce Mata Na Dare By Mal San Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24384

10 Ramadan Tafseer Na Dare By Abu-Hurairah Tsafe
http://darulfikr.com/s/24385

11 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24386

12 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24387

14 Ramadan Tafseer 1438 Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24388

15 Ramadan Tafseer Na Dare Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24389

16 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal SaniLiman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24390

17 Ramadan Tafseer Na Dare 1438 By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24391

19 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24392

20 Ramadan Tafseer 1438 Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24393

21 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24394

Kasance do darulfikr.com a koda yaushe domin  samun karatuttukan maluman  sunnah.

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

2017 RAMADAN TAFSEER

*2017 COMPLETE  RAMADAN  TAFSEER*

   COMPLETE  2017 RAMADAN  TAFSEER DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABU HURAIRA AREA  II TSAFE.

  wanda Malam Sani Liman Tsafe (ABI HURAIRA)   yake gabatarwa a Area II Tsafe, haha Zamfara  Nigeria.

Shiga  links dake kasa  Domin saukewa Cikin saki LA saurara  Cikin kyakykyawan Saudi.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

01 Ramadan Tafseer 1438Ah Suratul Nisa i By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24378

02 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24379

03 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24380

04 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24381

05 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Sani LimanTsafe
http://darulfikr.com/s/24382

08 Ramadan Tafseer Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24383

09 Ramadan Tafseer Akan Hukunce Hukunce Mata Na Dare By Mal San Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24384

10 Ramadan Tafseer Na Dare By Abu-Hurairah Tsafe
http://darulfikr.com/s/24385

11 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24386

12 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24387

14 Ramadan Tafseer 1438 Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24388

15 Ramadan Tafseer Na Dare Suratul Ma ida By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24389

16 Ramadan Tafseer 1438 Na Dare By Mal SaniLiman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24390

17 Ramadan Tafseer Na Dare 1438 By Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/24391

19 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24392

20 Ramadan Tafseer 1438 Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24393

21 Ramadan Tafseer 1438Ah Na Dare By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/24394

Kasance do darulfikr.com a koda yaushe domin  samun karatuttukan maluman  sunnah.

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

IN ANSHA RUWA...

*IN ANSHA RUWA A KOMA AIKI!!!*
NASIHA KAFIN ZUWAN LIMAN DAGA MASALLACIN IDI NA DAYA DAKE GARIN TSAFE, WACCE USTAZ MUSA S LAWAL YA GABATAR MAI TAKEN: _MUHIMMANCIN LOKACI, BAYAN RAMADANA SAI ME?_   DAN UWA YA KAMATA KA SAUKE DOMIN AKWAI ABUBUWAN DA YA KAMATA KASANI KWARAI DA GASKE, MALAM YA BADA ILIMI.
Muhimmancin lokaci meya kamata in aikata bayan ramadan?
DAGA BAKIN *_USTAZ MUSA S LAWAL TSAFE(ABU SALIH IBN SALIH)_*
http://darulfikr.com/s/24540
Kasance da darulfikr.com a koda yaushe domin samun karatukan maluman Sunnah a saukake.
Darulfikr.com takuce domin yada Sunnah.
Copyright©
*_Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)_*
+2348064734911
+2349030201868

IN ANSHA RUWA A KOMA AIKI

*IN ANSHA RUWA A KOMA AIKI!!!*

Karatun littafin NIHA YATIL ÃLAM wallafar Dr.Muhammad Abdulrahman Al-arify, karatun da *USTAZ MUSA S LAWAL TSAFE* ya fara gabatar mana a jiya SALLAH 01/10/1438AH
25/06/2017AC
Malam ya fara mana da mukaddimar littafin, kuma littafin yana magana akan alamomin tashin kiyama Manya da kanana.

Daure ka sauke wannan karatun yana da amfani matuka
👇👇👇👇👇👇👇👇
نهاية العالم د. العرفي
DAGA BAKIN; *USTAZ MUSA S LAWAL TSAFE(ABU SALIH IBN SALIH)*

http://darulfikr.com/s/24541

darulfikr.com takuce domin yada sunnah.

Copyright©
*_Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)_*

+2348064734911
+2349030201868

Monday, 22 May 2017

AZUMIN WATAN RAMADHANA

🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉
*AZUMIN WATAN RAMADANA*
🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇

*بسم الله الرحمن الرحيم*

_Rubutawa;_ *HASHIM SURAJO UBA(ABU SINÃN)*

```ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU.

  Godiya ta tabbata ga Allah s.w.t shi kadai Wanda yayi mana umurni da azumtar ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada, Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da ibadar azumi da sauran ibadoji.

Bayan haka;

FALALAR WATAN RAMADANA DA AZUMI A CIKIN WATAN.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan ramadana ya shigo, ana bude kofofin sama, ana kulle kofofin jahannama, ana daure shaidanu.
A wani hadisin kuwa manzon Allah s.a.w cewa yayi" Dukkan wani aiki da dan Adam zaiyi, ana lunka aikin da lada goma irinsa, idan a ramadana ne, ana lunkashi zuwa lunki (700), sai Allah mai girma da daukaka yace ;  banda azumi, domin azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa Wanda yayi shi, yabar matarshi da abubuwan da yakeso, da abinci, da abin sha saboda ni, mai azumi Nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki (shan ruwa) da farin ciki lokacin haduwarshi da Allah, yamin/warin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

ABUBUWAN DA SUKA WAJABA GAREKA A RAMADANA

Ya dan uwa

Kasani cewa Allah ya wajabta mana azumi domin mu bauta masa dashi, sannan kuma ya kasance cewa azuminka ya zamto karbabbe mai amfani.
Dole ne ka kiyaye wadannan abubuwan da zasu zo domin samun cikakkar lada;

1- kiyaye sallah; Da yawa daga cikin masu azumi suna wasa da sallah, bayan kuwa cewa tana daga cikin gimshikan addini, barinta kuma yana kai mutum ga kafurci.

2- Dole ka kasance mai kyawawan dabi'u; Dole ne mu tsoraci kafurci da zagin addini, da aikata muna nan dabi'u a cikin mutane, kafirci yana fitar da musulmi daga addini.

3- Dole ne mu kiyaye halshenmu da sukar juna.
 
Manzon Allah s.a.w yana cewa; "idan dayanku yana azumi, to kada ya fadi maganganun da basu dace ba, idan wani ya zageka ko ya nemi yayi fada da kai, sai kace mashi ni azumi Nike, ni azumi Nike.

4- Ka nisanci zuwa wurin da ake aikata barna! Ko kallon fina-finai na banza, domin hakan zai kai ga bata azuminka.

5- Ka yawaita sadaka ga makusantanka da mabukata, da ziyartar yan uwanka.

6- Ka yawaita zikiri da karatun Qur'ani da saurararshi, da bibiyar ma'anoninsa, da aiki da karantar warshi, sannan da zuwa masallatai domin daukar darussa masu amfani, kamar sauraran tafsirai, yin i'itikafi a masallaci idan goman karshe na ramadana suka kama.

7- karanta takardu akan azumi, domin sanin hukunce- hukuncen da suka shafi azumi, ta yarda zakasan cewa cin abinci ko abin sha da mantuwa baya karya azumi, kasan cewa ita janaba wacce ta sameka da daddare bata hana ka daukar azumi da sauransu.

LADUBBAN DA SUKA SHAFI AZUMI.

1- kiyaye halshe; Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda bai bar zancen karya ba, da aiki da zancen karya, Allah baya da bukatar barin cinsa ko shansa.

2- BUDA BAKI DA SAHUR DA ADDU'AH.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan dayanku zaiyi buda baki, to ya fara da dabino domin akwai albarka a ciki, idan bai samu dabino ba toh sai yayi da ruwa, domin suna tsalkakewa.
Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi buda baki yana fadar;
ذهب الظمأ، وابتلت العروق، وثبت الأجر، إن شاء الله.

Ma'ana: "YUNWA TA TAFI, GABOBI SUN DAI DAI TA, LADA TA TABBATA DA YARDAR ALLAH".
Manzon Allah s.a.w yace; "mutane baza su gushe suna samun alkhairi ba matukar suna gaggauta buda baki.

Anan dole mu gujewa muna nan akeedun shi'ah wadanda basa shan ruwa sai duhu ya shigo sosai, suna kafa hujja da ayar Qur'ani dake cikin suratul bakara, inda Allah s.w.t yake cewa; "...sannan Ku cika azumi zuwa dare. Wanman magana malamai sunyi bayanin me ake nufi tun da dadewa, mai Neman Karin bayani ya duba tafsirin "Aisarat-tafaseer, na jabir jaza'iry."

Manzon Allah s.a.w yace"kuyi sahur, domin a cikin yin sahur akwai albarka."

Manzon Allah s.a.w yace"Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da an rage komai daga ciki ba.

3-  DAGA CIKIN FA'IDOJIN AZUMI

   Duk Wanda yayi azumin ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbansa.

Duk Wanda yayi tsayuwar ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.(ma'ana: tsayuwar tarawihi da kiyamul-laili.)

4- WADANDA AKA YIWA RANGWAMEN AZUMI.

   *Marar lafiya da matafiyi, zasu ranka saboda fadar Allah s.w.t cewa;"Wanda ya kasance a cikinku marar lafiya ko akan hanyar tafiya, zai ranka azumin a kwanakin sauran watanni."
Amma marar lafiya Wanda ba'asa ran warkewa a kusa, toh sai ya rinka ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mai haila, da jinin haihuwa zasu aje azumi, saboda fadar ummuna Aisha R.A; "mun kasance ana umurtanmu da ranka azumi, amma ba'a umurtanmu da ranka sallah.[Bukhari da Muslim].

* Dattijo da dattijiya, wadanda sun tsufa sosai basa iya daukar azumi toh zasu ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mace mai ciki da mai shayarwa idan sunji tsoron rayukansu, toh zasu aje azumi sannan su ranka kawai, amma idan suna jin tsoron yayansu ne kawai, toh zasu ranka kuma su ciyar.

5- ABUBUWAN DAKE BATA AZUMI.

Abubuwan dake bata azumi sun kasu gida biyu:
Na farko; Abunda ke bata azumi Wanda ke wajabta rankawa kawai;

* Cin abinci ko abinsha da gangan.

* Yin amai da gan gan, saboda fadar annabi Muhammad s.a.w cewa: " Duk Wanda yayi amai, toh zai ranka azumi.[Hakim ya ruwaito]

* Mace mai haila da mai haihuwa, koda sauran mintuna kadan ayi buda baki tazo musu, toh zasu ranka azumin.

* Istimna'i(masturbation) wasa da al'aura da hannunka har maniyyi ya fito shima yana bata azumi kuma sai ka ranka.

Abu na biyu dake bata azumi kuma yake wajabta ranko da kaffara shine JIMA'I, akan maganar malamai kaffarar shine yanta baiwa ko azumin kwana sittin(60) a Jere.

6- ABUBUWAN DA BASU BATA AZUMI

* Cin abinci ko abinsha da mantuwa, ko da kuskure ko da tilasci! Babu ranko kuma babu kaffara, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa"Wanda ya manta yana azumi ya ci ko ya sha toh ya cika azuminsa, Allah ne ya ciyar dashi kuma ya shayar dashi.[Bukhari da Muslim]

* Amai ba dagan gan ba.

* Yin aswaki a kowane lokaci ko brush da sauransu.

* Dandana abinci da sharadin kada ka bari ya wuce maka.

* Sumbantar matarka, da sharadin kada akai ga aikata jima'i. Saboda manzon Allah s.a.w ya kasance yana sumbantar Aisha alhali yana azumi[Bukhari da Muslim].

* Cirewar hakori, ko zubar jini daga baki ko hanci.

* idan Alfijir ya keto alhali abunsha na hannunka, kada ka aje har sai ka biya bukatarka.

*jinkirta wankan janaba ko haila ko na haihuwa daga dare zuwa hudowar alfijir. Abunda yafi shine ayi gaugawar yi kafin sallar asuba.

Muna rokon Allah ya amfanar damu da abunda muka rubuta, Allah yasa munyi domin Neman yardar shi, Allah ya sanya ibadojin da zamu gabatar a ramadana su zamo karbabbu, kuma su zamo sanadiyyar tsira garemu duniya da lahira. Inda mukayi kuskure Allah ya shefeshi daga idanun masu karatu ya fahimtar dasu tare damu gabaki daya. Allah ya doramu akan tafarki madaidaici.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.

COPYRIGHT©
Hashim Surajo Uba(ABU SINÃN)```

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.wordpress.com

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

+2348064734911
+2348064734911