📚📚📚📚📚📚📚📚📚📚
*KO YANA HALASTA MAMU YAYI TASBIHI A LOKACIN DA LIMAN YA KARANTA SURATUL A'ALA A CIKIN SALLAH???*
📚📚📚📚📚📚📚📚📚📚
Rubutawa: *Abu Hussain, Abdulhameed As-safrawy*
Fassarawa: *ABU-SINAN ATS~TSAMAWY*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, tsira da aminci su kara tabbata ga farin jekada, Annabi Muhammad S.AW, da iyalan gidansa da sahabbansa baki daya.
Bayan haka:
Bayan tambaya da mutane suka yawaita akan wannan matsalar naga ya dace in fassara wannan amsa da babban Malami ABU HUSSAIN ya ba wani Wanda yayi mashi irin wannan tambayar amsa a 04/09/2011 kusan shekaru tara kenan da suka gabata.
Kai tsaye ga hujjojin da malam ya kawo akan halascin hakan Daga bakin magabata
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇
*IMAMUS SUYUDY (RH) A CIKIN*
الدر المنثور
Ya kawo hadisi Wanda imamu Ahmad da Abu daud da ibn Murdawaihy da imamul Baihaqy a cikin سنن nashi, Daga ibn Abbas(R.A): Manzon Allah s.a.w ya kasance idan ya karanta سبح اسم ربك الأعلى yana cewa: سبحان ربي الأعلى
Haka Abdurrazak ya fitar a Musnad nashi, da ibn Abi Shaibah, da Abd bn Humaid, da ibn jarir, Daga ibn Abbas: ya kasance idan ya karanta: سبح اسم ربك الأعلى yana cewa: سبحان ربي الأعلى
Haka ibn Abi Shaibah da Abd bn Humaid sun fitar Daga Aliyu bn Abi Dalib (R.A) ya kasance idan ya karanta سبح اسم ربك الأعلى sai yace: سبحان ربي الأعلى Alhali yana cikin Sallah, sai aka tambayeshi: shin anyi kari ne a cikin Qur'ani? Sai yace: A'a, mun kasance ana umurtarmu da fadar hakan, sai muke fada.
Haka Sa'eed bn Mansur da Abi Shaibah da Abd bn Humaid da Imamul Munzary sun fitar Daga Abi Musa Al-Ash'ary(R.A) cewa Abi Musa Al-Ash'ary ya karanta سبح اسم ربك الأعلى a sallar Juma'ah sai yace: سبحان ربي الأعلى
Haka Nan Sa'eed bn Mansur da Abd bn Humaid da ibn Jarir da ibnul Munzary da imamul Hakim(kuma ya inganta) Daga Sa'eed bn Jubair yace: Naji Ibn Umar yana karanta: سبح اسم ربك الأعلى sai yace: سبحان ربي الأعلى sai yace: wannan itace Qira'ar Ubayyu ibn Ka'ab
Haka ibn Abi Shaibah da Abd bn Humaid Daga Abdullahi bn Zubair, cewa: Abdullahi bn Zubair ya karanta سبح اسم ربك الأعلى sai yace سبحان ربي الأعلى Alhali yana cikin Sallah.
Haka Nan Abd bn Humaid ya fitar da wani hadisin Daga Dhahhak cewa: yana karanta SURATUL A'ALA, Sannan yana cewa duk Wanda ya karanta ta ya fadi: سبحان ربي الأعلى
Haka Nan Abd bn Humaid ya fitar Daga Qatada, yace: Manzon Allah S.A.W ya kasance idan ya karanta SURATUL A'ALA yana cewa: سبحان ربي الأعلى
Haka Nan Ibn Abi Shaibah ya fitar daga Umar, ya kasance idan ya karanta: سبح اسم ربك الأعلى yana cewa سبحان ربي الأعلى
Ibn Katheer a cikin Tafsirinsa yake cewa:
Imamu Ahmad yace, Waqee' ya bashi labari, Isra'il ya bashi labari, Daga Abi Ishaq, Daga Muslim Al-bad'een, Daga Sa'eed bn Jubair, Daga ibn Abbas: Manzon Allah S.A.W ya kasance idan ya karanta سبح اسم ربك الأعلى yana cewa: سبحان ربي الأعلى
Ibn jarir Ad-dabary(R.H) yace: ibn Humaid ya bani labari, Hakam ya bani labari, Daga Anbasah, Daga Abi Ishaq Al-hamdany: Ibn Abbas ya kasance idan ya karanta: سبح اسم ربك الأعلى yana cewa: سبحان ربي الأعلى
Haka idan ya karanta: لا أقسم بيوم القيامة idan ya Kai karshen ta أليس ذلك بقادر على أن يحيي الموتى
Sai yace: سبحانك وبلى
Bayan wadannan akwai wasu manyan malaman musulunci da dama da suka kasance suna aikata wannan Sunnah
Sheikh Muhammad Nasiruddeen Albany(R.H) a cikin Sahih Abi daud(4/39)
Daga ibn Abbas: Manzon Allah S.A.W ya kasance idan ya karanta سبح اسم ربك الأعلى yana cewa: سبحان ربي الأعلى
Albany yace: Hadisi ne ingantacce, imamul Hakim ma ya inganta shi akan sharadin Buhari da Muslim.
Da wannan zamu fahimci kenan ba laifi bane don liman ya karanta SURATUL A'ALA mamu suyi Tasbihin da ya tabbata, kamar yadda hadisi ya tabbata akan hakan Daga bakin Manzon Allah S.A.W , kuma sahabbai suka kasance suna aikata wannan Sunnah.
Allah ya kara fahimtar damu sunnar Annabi Muhammad S.A.W, ya bamu ikon aiki da ita.
*Hashim Siraj Uba Ats~tsamawy (ABU-SINAN)*
+2349030201868
15/04/1441H
12/12/2019
https://fb.me/abbansinan