Monday, 5 December 2016

SUNNAH NE YIN SALLAH DA TAKALMI

🔈🔉🔊🔈🔉🔊🔈
*SUNNAH NE YIN SALLAH DA TAKALMI, DAGA GROUPS DIN MUKYAUTATA NIYYA!!!*
📣📣📣📣📣📣📣

*Rubutawa:* *_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)_*

*Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa, muna Neman gafararSa, muna Neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, Wanda Allah ya shiryar babu mai iya batar dashi Wanda kuma ya batar babu mai iya shiryar dashi, kuma ina shaidawa babu abin bauta bisa cancanta sai Allah kuma ina shaidawa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne, yabo da godiya sun tabbata ga fiyayyen halitta Wanda  yace Wanda yayi mashi da'a Dan Aljanna ne, Wanda ya saba mashi Dan wuta ne!*
_Bayan haka:_

*وعن أبى سعيد رضى الله عنه قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: "إذا جاء أحدكم المسجد، فلينظر، فإن رأى فى نعليه أذى أو قذرا فليمسحه، وليصل فيهما.*
(أخرجه أبو داود، وصححه ابن خزيمة).

```Hadisi ya tabbata daga Abi sa'id(R.A) yace, Annabi Muhammad s.a.w yace: idan dayanku yayi Nufin zuwa Masallaci to ya duba idan yaga datti ko Wata 'kazanta a takalminshi, to ya goge sannan yayi SALLAH a cikinsu.```

Yan uwa mu lura, Manzon Allah s.a.w cewa yayi: *MU DUBA IDAN MUKA GA WANI DATTI KO KAZANTA MU GOGE MUYI SALLAH A CIKINSU!*  kuma hadisi ingantacce Wanda Abu daud ya fitar a cikin littafinshi kuma ibn khuzaima ya ingantashi. Imamu Nasirudden bn Albany ya ingantashi.
*Imamu Ahmad(imamu Ahlis sunnah waljama'ah) yake cewa: " من رد حديث رسول الله صلى الله عليه وسلم فهو شفا هلكة*
```Ma'ana: Duk Wanda za'ace ga Hadisi ingantacce amma ya tsaya jayayya yana son raddi ga Hadisin, imamu Ahmad yace yana gefen Halaka!

Ma'abota cewa ba'a SALLAH da takalmi ko zaku bamu hujjarku???``` 

*ABU SINAN* ```na jiran yaji rubabbun hujjojinku. Domin yasan inda kuka dogara.```

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*

Http://Hashim141473.mywapblog.com

No comments: