HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.
DARASI NA BIYAR (005) DA NA SHIDDA (006)
📒ABU NA BIYAR: SUNNAH NE DANGIN MAMACI DA MAKWABTAN SA SUYI ABINCIN DA KOSAR DA IYALAN MAMACI SU AIKA MASU📒
📌1.Yana daga cikin karantarwar Annabi Muhammad SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM domin tausaya ga iyalan mamaci, dangin sa da makwabtan sa su aika masu abincin da zai Kosar da su. Saboda Hadithin Abdullahi bin Ja'afar da yake cewa: lokacin da labarin mutuwar mahaifin mu (Ja'afar) ya zo, sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM yace: "KUYI ABINCI DON IYALAN GIDAN JA'AFAR (ku aika masu) HAKIKA ABIN DAKE SHAGALTAR DA SU YA ZO MASU". [Abu Dawud da Tirmiziy da bin Majah suka ruwaito sa kuma Hadithi ne ingantacce].
🖋️Haka kuma Imam As-Shafi'iy a cikin littafin sa AL-UMM yana cewa: "INA SO GA DANGI DA MAKWABTAN MAMACI SUYIWA IYALAN MAMACI ABINCI DA ZAI KOSAR DASU A YINI DA DAREN DA YA RASSU, DOMIN SUNNAH NE KUMA YANA DAGA CIKIN AYUKKAN MUTANEN KIRKI A GABANIN MU (Sahabbai da Tabi'ai) DA MA NA BAYAN MU (sauran mabiyan Sunnar Annabi). A karshe sai ya kawo Hadithin Abdullahi bin ja'afar da ya gabata.
📒ABU NA SHIDDA:MUSTAHABBANCIN SHAFA KAN MARAYA DA TAUSAYA MASA📒
📌1. Mustahabbi ne shafa kan maraya da girmama sa, saboda Hadithin Abdullahi bin Ja'afar da yake cewa:.....Manzon Allah ya wuce mu yana kan dabba ni da Qathm da Ubaidullah bin Abbas, sai yace ku miko man shi (wannan yaro) sai aka mika ni ya dora ni a gabansa, sai yacewa Qathm ku miko man shi, sai aka mika masa shi, sai ya dora sa a bayan sa...... a duk lokacin da ya shafi kaina sai yace: "YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA". [Ahmad da Baihaqiy suka ruwaito sa kuma Hadithi ne ingantacce].
Wannan shine abinda Sunnar Annabi Muhammad SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM ta tabbatar dangane da ta'aziyya.
Wallahu a'alamu bissawab.
✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz Juma'at Mosque Bungudu)
No comments:
Post a Comment