HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.
DARASI NA UKU (003)
📒ABU NA UKU: BA'A IYAKANCE TA'AZIYYA DA KWANA UKU BA KAMAR YADDA WASU SUKE RIYAWA 📒
Ita Ta'aziyya ba'a iyakance lokacin yin ta da kwana uku ba, a'a, ana yin ta duk lokacin da aka ga fa'idar yin ta ko kuma lokacin da aka samu haduwa da wanda aka yiwa rassuwa, saboda Hadithin Abdullahi bin ja'afar da ya gabata a darasi na biyu kamar yadda yake cewa: bayan shi ja'afar yayi shahada sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM yayi jinkiri na kwana uku bai je gidan Ja'afar ba, sannan yazo yace: "KADA KU SAKE KUKA GA DAN UWANA DAGA YAU".
Abdullahi yace: sai Annabi yasa aka zo damu, sai muka zama kamar 'ya'yan tsuntsaye (saboda maraici) kuma yasa aka aske muna kawunan mu sannan ya mike hannu na a sama yace: YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA, KA SANYA ALBARKA GA ABDULLAHI (dansa) KUMA KA SANYA ALBARKA GA KASUWANCIN SA". ya fadi haka har dau uku. Daga nan dai mahaifiyar mu ta zo tana ambata masa maraicin mu kuma tana cike da damuwa, sai Annabi ya ce mata: "KINA JI MASU TSORON TALAUCI NE? ALHALI NINE MAJIBINCIN SU DUNIYA DA LAHIRA?".
Wallahu a'alamu bissawab.
Mu hadu a darasi na hudu(004) insha'allah.
✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz juma'at Mosque, Bungudu)
No comments:
Post a Comment