Saturday, 27 January 2018

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN SHIRKA DA NAU'OINTA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#SHIRKA_DA_NAU'O'INTA

BAYAN mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka hakika banban abunda ALLAH yafi kauna shine riko da tauhidi, Kuma babban abunda ALLAH yafi kin shine shirka!!

ALLAH madaukakin na cewa "KU BAUTA MA ALLAH KADA KU HADA SHI DA KOWA"

lallai yan uwa musulmi mafi girman zunubi shine yin shirka da Allah....

ALLAH madaukakin na cewa yayi "DUK WANDA YAYI SHIRKA DA ALLAH MAKOMAR SHI WUTA (idan ya mutu bai tuba ba)"

Sannan kuma Allah na cewa "LALLAI ALLAH BAYA GAFARTAWA IDAN AKAYI SHIRKA DASHI AMMA YANA GAFARTA WANI LAIFIN WANDA BA SHIRKA BA GA WANDA YASO"

Yan uwa musulmi hakika Allah ya tsoratar da dukkan annabawan da ya aiko game da Shirka,  ALLAH yana cewa "MUNYI WAHAYI GAREKA DA WADANDA SUKA GABACE KA IDAN KAYI SHIRKA LALLAI DUK AYYUKAN KA SUN LALACE"

Yan uwa musulmi mu duba girman Annabawa amma Allah yace masu idan suka yi shirka ayyukan su sun lalace balle mu, Wannan kiran fa ba Allah yana nufin Annabawa ba!!

A'a ana nufin mu, Domin annabawa basu yin shirka...

Yan uwa musulmi idan muka diba musulmi fa yawa sun fadawa shirka da sanin su wasu kuma bada sanin su ba!!

ALLAH madaukakin sarki na cewa "DA YAWAN SUNYI IMANI AMMA SUN HADA ALLAH DA WANI"

Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya gargade mu gargadi mai tsauri yana cewa "lallai abunda nafi tsoratar maku a rayuwar Ku shine shirka karama"

Wata rana Abubakar assidiq radiyyallahu anhu yaje wajen Manzon Allah sai Manzo Allah yace mashi lallai shirka tana nan cikin musulmi, Lallai shirka tafi boyuwa a cikin Ku Sama da tururuwa a saman bakin dutse cikin dare "

Amma ga wata addua da zaka rika karanta wa domin neman kariya kace" YA ALLAH INA ROKONKA KA GAFARTA MANI KA KARENI DAGA SHIRKA "

NAU'OIN SHIRKA

*Rokon kabari, Sau da yawa zaka ga wasu masu karancin islamiyya suna zuwa rokon kabari, Ko aljanu ko waliyai ko annbawa Alaihis salam

Alhalin Allah madaukakin sarki ya haramta hakan har ma ya fada cikin suratul ahkaf cewa" BABU BATACCE IRIN MAI KIRAN WANIN WANIN ALLAH "

Kuma duk musulmi mai imani ya amince cewa kiran WANIN Allah shirka ne, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Roko ibada ne " Dan haka duk wanda ya roki WANIN Allah dan neman biyan wata bukata ko neman kariya hakika yayi shirka!!

* Kudurta cewa wani  na cutar wa...

Sau da yawa idan wani abu yafaru da dan Adam sai ya dora laifin bisa wani abu, Ko dora shi ga wani dalili ko kuma cewa ai wane ne dalili da sauran su...

ALLAH madaukakin sarki yace "IDAN ALLAH YA KAWO MAKA CUTA BABU MAI IYA DEBE MAKA ITA SAI SHI"

*SHIRKA TA HANYAR YIN MAGANA...

sau da dama wasu na fadar wasu maganganu alhalin shirka ce, Kamar cewa 'Taya Allah kiwo yafi Allah na nan'!

Kamar cewa Idan Allah ya yarda tare da wane, Ba' a cewa hakan nan cewa ake yi idan Allah ya yarda sannan wane ya yarda, Kaga dole sai ka fara sanya Allah farko.

Sannan masu cewa mun dogara ga Allah mun dogara gareka,  Huzaifa ya ruwaito cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada Kuce abunda ALLAH yaso da abunda wane yaso"

* JINGINA NI'IMAH GA WANI ABU....

jjngina samuwar Ni'ima ga wani abu kamar aiki, Ko sana'a ko, Alhali yin haka sanya wa Allah kishiya ne, Allah kuma yace "KADA KU SANYA MA ALLAH KISHIYA"

* SIHIRI...

Yanzu yawan yin sihiri ya yawaita cikin musulmi, A yanzu yadda sihiri yazama ruwan dare ya koma wa wasu kamar jini, Saboda yawan yin sihiri har sanya wasu anan Zamfara na Jefa Alqur'ani Mai tsarki cikin makewayi (Toilet) subhannallah...

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yaje wurin boka ko dan sihiri ya karyata abunda aka saukar wa Manzo Allah (Alqur'ani)" 

* YIN RANTSUWA DA WANIN ALLAH...

wasu nada tabi'ar yin rantsuwa da, kaddara ko lokachi ko iyaye da sauran su, Har munzo zamanin da akafi yarda da rantsuwar da akayi ba Allah a ciki...

* IZGILI DA WANI ABUN ADDINI....

wasu kuma nada tabi'ar yin izgili da Abubuwan addini kamar, Gemu hijabi, aswaki, Yawaita sallama da sauran su.

* RATAYA LAYA KO KARHU

Daga cikin musulmi akwai masu tabi'ar daura laya ko karhu ko guru ko qaho da sauran su, Da sunan samun kariya ko wani abu, Wannan duk shirka ne.

*JIBINTAR KAFURAI
wasu nada tabi'ar jibintar kafurai fiye da musulmai, Alhali basu son Allah kuma basu son Manzon Allah.

Tabbas duk wanda ya fada shirka tabbas ya halaka, Duniya da Lahira.

ABUBUWAN DAKE SAMUWAR MAI YIN SHIRKA

- Rayuwar mai shirka tana lala cewa.

- Kullum cikin tashin hankali mai shirka ke kasancewa.

-Cirewar natsuwa daga rayuwa.

- shiga cikin batattu domin Allah yace "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA BACE"

-Rosa ayyukan bawa, Duk wanda yayi shirka ya roza ayyukan shi.  ALLAH madaukakin sarki ya cewa Manzo Allah cewa "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA LALATA AYYUKAN SHI"

-DUSHE HASKE.

duk mai yin shirka Allah zai sanya wa rayuwar shi duhu, Baya taba ganin hasken alkahri.!!

Yan uwa musulmi hakika shirka tana tauye imani, Lallai yazama wajibi garemu muyi watsi da duk abunda zai kowa mana tangarda a cikin imanin mu, Domin samun tsira gobe Kiyama mu da iyalan mu da yan uwan mu baki daya.
. Allah ka albarkaci rayuwar mu baki daya.

Allah kayi mana kariya daga shirka, Ka biya mana bukatun mu na alkhairi, Ya Allah Muna tawasuli da sunayen ka ka biya mana bukatun mu na alkhairi baki daya, Ya Allah kara albarka ga garuruwan mu kabamu lafiya da cikakken zama lahiya ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 01-5-1439
Friday 19-January - 2018 AB

HUDUBAH MAI TAKEN MATSAYIN TAUHIDI GA RAYUWAR MUSULMI

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#MATSAYIN_TAUHIDI_GA_RAYUWAR_MUSULMI

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

BAYAN mukaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka kamar yadda kuka gani kan abunda khudbar mu zata yi magana, Yan uwa hakika shi tauhidi shine rayuwar bawan Allah kacokan..

Yan uwa musulmi hakika hakika Allah madaukakin sarki ya halicce mu baki daya dan mu bauta mashi, Babban dalilin halittar mu baki daya shine dan yin bauta ga Allah ga Allah mahallici.

Allah madaukakin sarki ya halicce mu kuma yabamu umarnin bauta mashi, A cikin suratul zariyat Allah madaukakin sarki na cewa "BAN HALICCI MUTUN DA ALJANI BA SAI DAN SU BAUTA MANI"

Bautar Allah ga kowane mutun da aljani dole ne kuma wajibi ne, Mafi girman abun bukata ga bawan Allah shine kadaita Allah ba tare da sanya mashi kishiya ba a ko ina..

Hakika cikin imaninka da tauhidinka dole ne sai kazama mai furtawa da kaskantar da kai da kwadayin rahamar sa da tsoron azabar sa, Da kuma kasancewa mai sujjada gareshi da cikakken tsoron sa!!

Yan uwa musulmi masu albarka hakika domin kara tabbatar da tauhidi Allah ya wajabta mana karanta suratul fatiha a cikin kowace sallah da zamu yi, A ciki muke cewa "IYAKA NA ABUDU WA'IKA NAS TA'IM"

IDAN HAR BAWA YAKI YIN BAUTA GA ALLAH HAKIKA YAYI ASARAR DUNIYA DA LAHIRA!!! 😨😨😨

Yan uwa musulmi hakika Allah ya aiko mazannin shi baki daya domin su tabbatar da tauhidi da musulunci a kasa, Kuma Allah ya aiko littafan baki daya dan tabbatar dan tauhidi a kasa '

ALLAH madaukakin sarki ya fada cikin suratul nahli cewa "WALLAHI MUN AIKOWA KOWACE AL' UMMAH DA MANZO DOMIN SU BAUTA MA ALLAH KUMA SU KAFURCEWA DAGUTU"

Yan uwa musulmi hakika wannan ayar kadan ce daga cikin ayoyin dake tabbatar da dole ne yin bauta ga Allah da kuma kare yin tauhidi.

Yan uwa musulmi masu albarka lallai da tauhidi ne rayuwa ke natsuwa kuma ta samu kwanciyar hankali, Hakika idan rayuwa ta kasance babu tauhidi a cikin ta tabbas dabba ta fishi,

Duk wanda keda tauhidi to hakika shi rayayyene, Idan kuma baida tauhidi komai mulkin sa da duk wani gata nashi to matacce ne.

Allah madaukakin sarki yana cewa cikin suratul an'am cewa "WANDA YA KASANCE MATACCE MUKE RAYASHI MU SANYA MASHI HASKE"

hakama Allah madaukakin sarki na cewa "KU KARBA KIRAN ALLAH DA MANZO IDAN AN KIRAKU GA RAYUWA (TAUHIDI)

Yan uwa musulmi wallahi duk wanda baisan Allah ba baida banbanci da dabbah, Har ma dabba tafi shi domin kuwa ita dabba babu wani hisabi da za'a yi masu.

Idan har muka yi imani lallai ALLAH zai samar mana da jindadi, Allah yana fada cikin suratul nur cewa "ALLAH YAYI ALKAWARI IDAN KUKAYI IMANI DA AIKI NA KWARAI ZAMU KHALIFANTAR DAKU DA SHARADIN KUN KADAITA ALLAH"

kafurcewa Allah lallai shine babban jigon samun zaman lafiya mai dorewa.

Riko da tauhidi shine jigo na samuwar arziki, Allah madaukakin sarki na cewa "DUK WANDA YAYI IMANI DA ALLAH YA AIKATA AIKIN KWARAI ZAMU AZURTASHI"

Arziki na nufin wadatar zuci, Koda kaga kafuri da kudi da dukiya zaka same shi babu kwanciyar hankali da natsuwa.

Amma idan kana da cikakken imani da Allah zaka ji natsuwa da wadata koda baka da kudi 😀

Yan uwa musulmi masu albarka hakika Riko da tauhidi na kawo natsuwa daga shaidanu,Bai yiwuwa shaidani ya tsaya idan ake gudanar da tauhidi.

Duk inda ake kiran sallah shaidan yakan tsere da gudu, Har sai an gama sannan idan za'ayi ikama haka, Saboda a cikin kiran sallah da ikama akwai tauhidi a cikin su.

Hakama ayatul kursiyu aya ce mai girman gaske, Wanda duk ya karanta ta kafin ya kwanta Allah zai turo mala'iku su rika gadin shi wannan duk dalilin tauhidin dake ciki ne.

Yan uwa musulmi hakika Riko da tauhidi yana kawo kariya tsakanin ka da mushrikai, Domin ALLAH madaukakin sarki yace "LALLAI ALLAH NA BADA KARIYA GA MASU IMANI" duk wani kokarin mushrikai nan cutar Allah bazai bari ba domin yayi alkawarin kariyar.

Yan uwa musulmi dole ne tunatar da muminai game da abunda ya shafi tauhidi domin kamar yadda muka fada shine ginshikin rayuwa,

Hakika tunatar da muminai game da imani yana da muhimmancin gaske domin zai zaburar da sabunta masu imanin su, Domin Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "IMANI KAMAR RIGA NE"

wato kenan yana tsufa idan har ba'a sabunta shi.

Yan musulmi akwai wasu musulmi dasu ke matukar adawa da maganar da shafi tauhidi, Domin wai su a ganin su tsanantawane yin maganar tauhidi, kawai abar kowa yayi yadda yake so...

To shi musulunci ba haka yake ba, Yana da tsari kuma da zarar anyi nisa cikin kaucewa tsarin sa to za'a iya halaka!!

Yazama wajibi kuma dole ga kowane musulmi yasan tauhidan nan guda 4 - Rububiya
-Qulihiya
-As-mau wassifat
-Risalah

Dole a sansu tare da sanin matsayin kowane daga cikin su.

Ta sanin su zai sa mu kaucewa duk abunda zai kange daga Allah, kamar shirka da Allah!!!

Domin kamr yadda muka sani shirka da Allah na warware ibadu sa imani baki daya.

Yin shirka ko duba ko bugun kasa da zuwa wurin bokaye na warware imani, Domin Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yaje wurin boka ko mai duba kuma ya gasgata abunda ya fada mashi to ya kafurta abunda aka saukar wa Annabi Muhammadu sallal lahu alaihi wassalam (Al'qurani mai tsarki)

Duk abunda kake nema ka tuna Allah ne ke badawa tun kafin a hallicce ka a rubuta duk abunda zai zama naka.,

Basai kaje wurin wani kazami ba mushriki, Ya raba ka da imanin ka ya raba ka da kudin ka.

Yan uwa musulmi mu kara tunawa fa lallai ALLAH ya hallicce mu ne dan kadai mu bauta mashi.

Idan har Zamu yi hakuri da talauci da rashi dole ne muyi hakuri da yawan yiwa Allah ibada domin akwai ranar sakamako.

Tun daga aure, sutura abinci gida mota abokan ta, Da duk wani abu na bukatar rayuwar mu basu kai muhimmancin tauhidi ba.

Yan uwa musulmi masu albarka idan muka diba yadda  rayuwa ba chan ba chan babu tauhidi wata rana sai mutuwa tazo ta riska shikenan!! 😨😵😷

Allah ya tabbatar da tauhidi a zukatan mu ya yafe mana yayi mana rahama, Ya ubangiji ka yafe mana kurakuren mu ya kare daga hassada da kyashi da jin zafi da gulma da annamimanci da karya da ciwo da kuturta da makanta da kurumta da sauran ciwuka.

Ya ubangiji ka zaunar damu lafiya ka biya bukatun mu na alkhairi ka gafarta wa mamatan mu, Allah kayi salati da tasleemi ga Shugaban mu Annabi Muhammadu da iyalinsa da sahabban sa da dukkan mataimakan sa da sahabban sa yardaddu baki daya har zuwa ranar sakamako.

Ameen ya rabb.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 24-Rabi'ul akheer {4}-1439
Friday 12-January - 2018 AB

Saturday, 30 December 2017

YAR UWA KINASON SHIGA ALJANNA???

*YAR UWA KINASON SHIGA ALJANNA???!!!*

*KI KIYAYE DOKOKIN ALLAH!*

```Hadisi ya tabbata daga Abi Hurairah R.A yace; Manzon Allah s.a.w yace: "Mutane guda biyu yan wutane, ban taba ganinsu ba!(babu irin wadannan mutanen a lokacin manzon Allah s.a.w).
Na farko: Wasu mutane ne wadanda a hannunsu akwai bulala, kamar bindin shanuwa, suna bugun mutane da wannan bulalar,(malamai sunyi fassara biyu, na farko sukace ana nufin azzaluman shuwagabanni, na biyu sukace yan fashi da makami da duk wani mai zalunci). Annabi yace suna daga cikin yan wuta.

Na biyu: sune yan mata wadanda suna sanye da tufafi amma a hakikanin gaskiya tsirara suke! Saboda tufafin bai rufe abunda akeson ya rufe ba(wato suna sanya tufafi Wanda ke bayyanar da tsiraicinsu) kamar hijaba dai gyale na zamani irinsu; show me your back, show me your breast, show me your chest, ustazu baida rabo, baba na balaga da sauransu, wannan duk haramun ne a musulunci!

Annabi ya cigaba da cewa karkatattu ne, kuma suna karkatar da wasu( wato masu ketare abunda shari'ah ta gindaya musu, suna ketare iyakokin Allah, kuma suna koyar da wasu matan irin wadannan dabi'u nasu.
Kawunansu kamar tozon rakumi ne Wanda yake karkatacce(ma'ana suna tara gashi sosai, sai su kulleshi wuri daya, a turashi gefe guda! A yanzu ka iya cewa a cuci maza da sukeyi).
Ba nan matsalar take ba, irin wadancan mutane Annabi Muhammad s.a.w yace ba zasu shiga Aljanna ba sannan baza suji kamshin aljannar ba,  shi kuwa kamshin aljanna ana jinsa daga Nisan wuri kaza zuwa kaza, a wata ruwayar Nisan tafiyar shekara dari biyar.
[Muslim ya ruwaito]

Yar uwa kinason shiga aljanna???

Na roke ki don girman Allah ki ajiye wayewar turawa ki rungumi addininki na musulunci.
Wallahi ina jin zafi a duk lokacin da naga mata suna wata shiga ta fitsara, hankali na na tashi kwarai.

Yar uwa Allah ya gafarta miki, kada ki yarda shaidan ya rinjayeki har ya kaiki ga halaka!
Soyayya da kauna da son mu gudu tare mu tsira tare shine yasa na rubuta wannan takaitacciyar nasiha.

ALLAH YA KARA SHIRYA MANA YAN UWANMU MATA A DUK INDA SUKE A FADIN DUNIYA.


DAN UWANKU A MUSULUNCI.

BABAN_SINAN```
+2348064734911

أقوال العلماء في الرفضة.

أقوال العلماء في الرافضة.

◀ قال ابن تيمية - رحمه الله -:
قال القاضي : ومن قذف عائشة رضي الله عنها بما برأها الله منه كفر بلا خلاف .

【الصارم المسلول【١٠٦٦/٣】
____________________________
◀ قال شيخ الإسلام ابن تيمية - رحمه الله -:
"الرافضة حمير اليهود يركبون عليهم في كل فتنة".

【منهاج السنة【20/ 21-1】
____________________________
◀ قال ابن تيمية - رحمه الله - :
وقال أبو حاتم : حدثنا حرملة قال :
سمعت الشافعي يقول : لم أرَ أحداً أشهد بالزور من الرافضة.

【منهـاج السنـة【٦٠/١】
____________________________
قال ابن تيمية - رحمه الله -:
النصارى الذين قاتلهم المسلمون بالشام كانت الرافضة من أعظم أعوانهم .
【المنهـاج【٣٧٨/٣】
____________________________
◀ قال شيخ الإسلام ابن تيمية - رحمه الله -:
" الرافضة من أجهل الناس وأضلهم كما أن النصارى من أجهل الناس. والرافضة من أخبث الناس كما أن اليهود من أخبث الناس ففيهم نوع من ضلال النصارى ونوع من خبث اليهود ".

【منهـاج السنـة【2/65】
____________________________
◀ قال شيخ الإسلام ابن تيمية - رحمه الله -:
" الرافضة ...أعظم عباداتهم عندهم: لعن المسلمين من أولياء الله مستقدمهم ومستأخرهم ".

【مجموع الفتاوى【٢٨/ ٤٨٨】
____________________________
◀ قال ابن القيم - رحمه الله -:
"ولقد أصبح هؤلاء الشيعة عاراً على بني آدم يسخر منهم كل عاقل".

【المنار المنيف【صـ152】
____________________________
◀ قال الإمام أحمد بن حنبل -رحمه الله -:
ليست الرافضة من الإسلام في شيء.

【طبقات الحنابلة【جـ١صـ٣٢】
____________________________
◀ قال الإمام أحمد بن حنبل - رحمه الله -:
من شتم أصحاب النبي ﷺ لا نأمن أن يكون قد مرق عن الدين.

【السنـة للخـلال【٧٧٩】
____________________________
◀ قال الامام مالك - رحمه الله -:
" الذي يشتم أصحاب رسول الله ليس له سهم -أو قال نصيب - في الإسلام ".

【الإبانـة الصغـرى【ص123】
____________________________
◀ قال أشهب - رحمه الله -:
سئل مالك عن الرافضة فقال : ﻻ تكلمهم ولا ترو عنهم فإنهم يكذبون.

【منهـاج السنـة【60/1】
____________________________
سئل شيخ الإسلام - رحمه الله -:
هل الشيعة من الضالين؟

فأجاب:
"وهل يوجد أضلّ من قوم يعادون السابقين الأولين من المهاجرين والأنصار، ويوالون الكفار والمنافقين".

وقال - رحمه الله -:
(الرافضة ليس لهم سعي إلا في هدم الإسلام ونقض عراه وإفساد قواعده)"

وقال عن الرافضة:
"دائماً يوالون الكفار من المشركين واليهود والنصارى ويعاونونهم على قتال المسلمين ومعاداتهم"
المنهاج 3/378.
____________________________
قال شيخ الإسلام ابن تيميّة - رحمه الله -:
"الرافضة هم أصل كل فتنةٍ وبليَّه، وكثير من السيوف التي سُلَّت على المسلمين إنما كانت من جهتهم".
المنهاج6/370.

وقال:
"الذي ابتدع دين الرافضة[ابن سبأ] كان زنديقاً ملحداً عدواً للإسلامِ وأهله".
منهاج السنّة4/362.
_______

🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘
للاشتراك في مجموعة _*على منهاج النبوة*_ واتساب إرسال الإسم الى
+249966945085

للاشتراك بقناة على منهاج النبوة على التلغرام

https://telegram.me/minhaj7

Friday, 29 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN; MUHIMMANCIN SALLAR DARE

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

Bayan mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka yau khudbar mu zata yi magana ne game da #MUHIMMANCIN_SALLAR_DARE (kiyamul laili)

Yan uwa musulmi a makon da ya gabata munyi khuduba ne game da sallar nafila..

To yau in sha Allah Zamu yi magana ne game da Sallar Dare wato kiyamul laili.

Hakika Allah ya yabi masu yin sallar dare a cikin suratul sajadah, "ALLAH ya kan rokon sa kuma suna ciyar da abunda muka basu,  Suna tashi sallar dare,  suna da makoma ta kwarai"

Hakika saboda kaunar mu da Allah yake yi  ya bamu damar aikata ibadu kala kala har ma yakan bamu lada idan mun aikata.

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Mafificiyar sallah itace sallar nafila bayan ta sai sallar dare"

Hakama Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana cewa "Sallar da Allah yafi so itace sallar dare"

Yan uwa musulmi masu albarka lallai wannan sallar wato sallar dare tana karawa ihlasi.

Hakika tsayuwa cikin dare yana karawa bawa tsoron Allah da natsuwa, Hakama duk ranar da dan Adam yayi sallah to zaiji natsuwa da kwanciyar hankali.

Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace ma sahabin sa "In fada maka wata hanyar alkhairi??
Sai sahabin yace eh, Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace 'Ka yawaita azumin nafila, Da sadaqah domin sadaqah tana cinye zunubai kamar yadda ruwa suke kashe wuta sai kuma ka lizimci sallar dare"

Yan uwa musulmi masu albarka muhimmancin sallar dare baya misaltuwa, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "ALLAH yayi rahama ga wanda ya tashi yayi sallar dare"

Hakika yan uwa musulmi sallar dare tana cikin salloli masu karawa dan Adam ihklas.

Manzo sallal lahu alaihi wassalam shine baban abun koyi garemu baki daya, Hakika Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya kasance yana tsayuwar dare har kafasun sa su fara tsagewa har Aisha radiyyallahu anha tace masa miyasa kana Manzo Allah kake Ibadah kamar haka??

Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace Shin bazan zamo bawa mai godiya ba??

Yan uwa musulmi masu albarka hakika yawan yin sallar dare yana kauda bala'oi da musibuh.

Sallar Dare tana gyara halaye kuma tana gyara halaye.

Ibn hajr asqalani yace 'Ita sallar dare tana wanke zukata'

Saboda muhimmancin sallar dare Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya hore mu da yin sallar dare inda yake cewa "NA hore Ku da sallar dare domin tana share zukata"

Hakika sallar dare tana kara lafiya da kwarin jiki,

Ina wadanda basu da lafiya likita yace sai sun rika motsa jiki duk safiya???

To ga exercise daga likitan likitoci Manzo sallal lahu alaihi wassalam idan har ka tsarkake niya to hakika Allah zai baka lafiya da yardar sa.

Ibn Salam ya ruwaito daga cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Ku yada sallama a tsakanin ku Ku raba Sadakar abinci Ku sada zumunta kuyi sallar dare"

Duk mai kokarin sallar dare Allah zai haska zuciyar sa....

Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana baiwa sahabbai labari cewa "A cikin aljannah akwai wasu benaye masu tsawo ana ganin abunda ke ciki saboda tsabar hasken su a wata ruwayar har matan da suke ciki ya kwatanta, Sai wani mutanen karkara yace ya Manzo Allah wake da wadannan benayen??
Sai Manzo Allah yace na wadanda suka iya magana ne (Magana mai kyau Sadaka ce) da wanda ya sada zumunci da wanda ya yawaita azumi da wanda ya lizimci sallar dare "

ALLAH Ya umarci Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya tashi yayi sallar dare" KA TASHI KAYI SALLAR DARE KA ROKI UBANGIJIN KA "

Manzo sallal lahu lahu alaihi yayi addu'a ga wanda ya tada iyalinsa suka yi sallar dare.

Idan mata ta tashi zatayi to tana iya tada mijinta Shima idan bai tashi ba tana iya yayyafa masa ruwa amma idan babu matsala 😁

Yan uwa musulmi masu albarka saboda muhimmancin sallar dare Umar bn Khaddab ya kasance yana tada iyalinsa suyi sallah a karshen dare.

Hakika ALLAH yana sauka a sulisin dare a saman duniyar nan yana cewa "INA MASU NEMAN GAFARA INYI MASU INA MASU NEMAN BIYAN BUKATA IN BIYA MASHI??"

Yan uwa musulmi a yanzu mun bar sallar dare sai a lokachin azumin ramadana.

Idan baka iya tashi da dare to kana iya yin sallar ka bayan isha'i.

Yan uwa musulmi lokachin da yakamata muyi sallar shine misalin karfe 2,3,4 domin shine sulisin dare.

A yanzu muna ganin yadda a duniyance kowa yana neman hanyar rayuwa, Kama daga bidar kudi da sauran su.

Ita lahira babu batun kudi ko wani abu hakika yakamata mu maida hankali dan lahirar mu.

Lallai kada mu kuskura shaidan yayi tasiri garemu.

Mai hankali ne wanda keyi lahirar sa tanadi kafin yaje.

ALLAH Ka taimakemu da taimakon ka ya ubangiji ka yafe mana kurakuren mu.
Ya Allah ka biya mana bukatun mu kayi rahama ga mamatan mu ya amintar damu daga abunda muke tsoro.

(Dan Adam ajizi ne Allah ka gafarta mana abunda muka yi kuskure)

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 10-Rabi'ul akheer-1439
29 Friday -December-2017 AB

Sunday, 24 December 2017

AN GABATAR DA DAURA KASHI NA FARKO MAI TAKEN; BAYYANA KIRKIRARRUN KARYA DA AKE JINGINAWA IBN TAIMIYYA AKAN HALASCIN MAULUDI.

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*MASJID ABU-HURAIRAH YAR YARA TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

```AN GABATAR DA DAURA KASHI NA FARKO MAI TAKEN; BAYYANA KIRKIRARRUN KARAI-RAYI DA AKA JINGINA GA SHEIKHUL ISLAM IBN TAIMIYYA AKAN HALASCIN MAULUDI...

   Daurar wadda Sheikh Sani Liman (ABU HURAIRAH) Tsafe ya gabatar,  bayan Malam yayi khudubatul haaja, yayi sallama ga Yan uwa musulmai da suka taru a wajen.

  Sheikh sani Liman ya cigaba da cewa; abunda ya hada mu a wannan waje shine domin mu tattauna abunda ya shafi bukukuwan maulidi, muna yima Yan uwa musulmi maraba da karba wannan kira da sukayi, suka nuna cewa su lallai su mazajen sunnah ne, masu jira ace Sunnah tayi kira domin su amsa kiran.

  Sheikh Sani ya cigaba da cewa; Yan uwa kafin mu shiga cikin wannan littafin akwai wata shimfida da nikeson in gabatar, domin ta zamo mana haske a tafiyarmu ta Sunnah...

   Yan uwa musulmi ahlus-sunnah da muka taru a wannan masallaci bisa wannan muna saba ya kamata mu San cewa shi Ahlus-sunnah duk inda ya samu kansa to wajibi ne gareshi yayi fada da Bidi'ah!

Sheikh yace, shi fada da Bidi'ah ana yinsa ne ta hanyoyi guda biyu.

*HANYA TA FARKO:*
Fadakar da al'umma akan Bidi'ah a kowane lokaci, a kowane zamani, yadda dan Bidi'ah baiji kunyar jajircewa wajen dabbaka bidi'ashi ba, toh ai mu yafi cancanta ace mun jajirce wajen tabbatar da Sunnah, kada mu dauka cewa bidi'ar mauludi ita kadai ce zamu tsaya akanta! A'a Na daga cikin bidi'oin da ya kamata muyi fada dasu; Fadar ''SADAKHALLAHUL-AZEEM" bayan kammala karatun Qur'ani! Wannan Bidi'ah ne!!!   Na gaba shine; Fadar "AMIIN WA'ALAIKUMUS-SALAM" a wajen maida sallama, kara AMIIN Bidi'ah ne!!! da wasu daga cikin bidi'oin da basu da bambanci da bidi'ar mauludi.

Sheikh Liman yace ya kamata mu zauna mu zakulo wadannan bidi'oin domin a bayyanawa al'umma, kamar yadda babban Malami Sheikh Usman bin fodiyo ya rubuta littafi akan irin wadannan bidi'oin.

Sheikh Sani Liman ya cigaba da cewa; ba wai dole sai a irin wannan zaman bane zamu rika yakar Bidi'ah! Muna da masallatai, da makarantun islamiyyu da sauran wurare, idan ya zamana cewa ana yima bidi'ah tsirara a irin wadannan wurare a koda yaushe, babu shakka ma'abota Bidi'ah zasu ji tsoron  bayyana bidi'arsu, kuma zasu rikice.

*HANYA TA BIYU:*
hanya ta biyu da ake yakar bidi'ah shine riko da Sunnah, da dabbaka Sunnah, saboda idan Ahlus-sunnah mukayi rauni wurin riko da Sunnar Manzon Allah s.a.w, bamu koyi dashi a wajen maganganunmu da mu'amalarmu da wajen sutura da kasuwanci da sauransu, toh an samu matsala!  Ashe kenan yana daya daga cikin hanyoyin fada da bidi'ah raya Sunnah, saboda Annabi ya kira raya Sunnah a matsayin raya addini ne, saboda haka ya zama wajibi akan Ahlus-sunnah ya raya Sunnah! Abar jin kunyar aje gemu ko dage wando da sauransu.

Sheikh Liman yace, wannan ita ce wasiyya ta gareku...


   Sai Malam ya shilla akan maganar abunda ya taramu a wajen, Malam ya sukwane akan maganar bidi'ah, har ya kawo hadissai dake nuna cewa wajibi ne mu kyamaci bidi'ah, sannan ya kawo mana ayoyi dake nuna wajabcin biyayya ga manzon Allah s.a.w, ya kuma kawo mana manyan malaman musulunci da sukayi suka akan mauludi suka ce ba addini bane.

Bayan Malam ya gama wannan jawabin sai yace kai tsaye sunan littafin da zamu karanta;
تبيين كذب المفتري بما نسب إلى شيخ الإسلام ابن تيمية من استحسان الاحتفال بالمولد النبوي صلى الله عليه وسلم.
Wanda babban malaminmu na jahar zamfara Sheikh Muhammad kabir ibn umar Al-marwy(ABU SUMAYYA) ya rubuta.

Daga nan sai sheikh Sani Liman yayi mana bayanin irin kokarin da marubucin littafin yakeyi wajen baiwa sunnar Annabi kariya, da wasu ayyukan da yake yima Sunnah, malam yayi mana bayanin marubucin littafin sosai, inda har ya fada mana wasu daga cikin littafan da ya rubuta.  Na daga cikin littafan da malamin ya rubuta wanda sheikh sani ya ambata akwai;

√ TUHUFATUL AKHYAAR, BIMA'ARIFATI MALA ASLA LAHU MINAL-AKHBAR.

√ MASHAYIKHIS-SUFIYYA YAKULUNA ALLAHU FISSAMÃ(malaman sufaye sun tabbatar da cewa Allah yana sama)

√ ITTIHAFIL MU'UMININA BIT-TAKHRIJI AHADISI BUGYATUL MUSLIMEENA.

√ AHSANUL-AQAWEEL FI ISBATIS- SUNNIYATI LUBSIS-SARAWEEL, WAR-RADDU ALA MAN ZA'AMA ANNAHU BIDI'AH(wannan raddi ne ga katon dan Bidi'ah Abduljabbar akan littafin da ya rubuta ya nuna cewa sa wando Bidi'ah ne).

√ KASHFUZ-ZUNUN FI TAFSIRI QAULIHI TA'ALA;  ﻗُﻞْ ﺑِﻔَﻀْﻞِ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﻭَﺑِﺮَﺣْﻤَﺘِﻪِ ﻓَﺒِﺬَٰﻟِﻚَ ﻓَﻠْﻴَﻔْﺮَﺣُﻮﺍ ﻫُﻮَ ﺧَﻴْﺮٌ
ﻣِّﻤَّﺎ ﻳَﺠْﻤَﻌُﻮﻥ

Da wasu littafai kusan sha uku da Malam ya ambata kuma ya ba daliban ilimi shawarar su nemesu domin amfanuwa.
Daga nan ne Sheikh yaja burki saboda lokaci da yayi halinsa, malam yace a kashi na biyu zamu shiga cikin littafin ne kai tsaye.```

Ga masu bukatar audio Na wannan Daura suna iya garzayawa a dandalin sunnah Na darulfikr.com a folder Malam zasu sameshi a cikin muhadara insha Allahu.

Allah ya sakawa marubucin wannan littafi da Alkhairi dashi da Sheikh Sani Liman da ya zakulo littafin domin fadakar da al'umma.

Sai mun hadu a fitowa Na gaba insha Allahu.



*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA COMMITTEE*
+2348064734911

05-04-1439AH
24-12-2017AC

Friday, 22 December 2017

HUDUBAR JUMU'AH MAI TAKEN, HUKUNCIN BIKIN KIRSIMETI DA SABUWAR SHEKARA A MUSULUNCI.

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

Bayan mukaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka a yau khudbar mu zata yi magana ne game da hukuncin #BIKIN_KIRISMETI_DA_SABUWAR_SHEKARA_GA_MUSULMI

Yan uwa musulmi masu albarka mu girmama ubangiji Allah kuma mu gode masa game da ni'imar shi garemu ta musulunci, Kuma mu gode masa bisa ga alkawarin sa na kare addinin musulunci daga duk wani sharri!

Yan uwa musulmi masu albarka hakika riko da addini dole kuma wajibi haka ma dole rokon ALLAH mutun ya zama musulunci shine addinin shi har zuwa karshen rayuwar shi.

Hakika Allah madaukakin sarki ya zaba mana musulunci ya zama addinin mu kamar yadda yake fada cewa "NA ZABA MASU MUSULUNCI YA ZAMA ADDININ KU"

Hakika shi addinin musulunci ya cika kuma ya kammalo kuma ta tanadi dokoki da ka'idodi, Babu wani bangaren rayuwar mu da musulunci ya kyale, Kama daga

- mu'amula 'Musulunci ya tsara yadda za' a yi mu'amula.

-Siyasa hatta ita ma musulunci ya tsara yadda za'a yi ta a cikin tsafta.

-Ibadah tabbas musulunci ya tsara yadda za'a Ibadah baki daya.

Da sauransu.

Shi musulunci addini ne wayyaye wamda yake dai dai da kowane irin zamani, Kamar yadda Allah madaukakin sarki ke cewa "MUN SAUKAR MAKA DA LITTAFI NE DAN BAYANI GAME DA KOMAI"

Yan uwa musulmi masu albarka kada mu yadda muyi wani abu da zai kaskantar da addinin mu, Ko yaya abun yake komai yadda muke kallo shi karami!!

Yan uwa musulmi a yanzu wani abun takaici da ban tsoro dake faruwa tsakanin musulmi shine yadda zaka ga wai musulmi na bikin kirismeti, Har yana zuwa wuraren su yana taya su murna yana nishadi da annashuwa.

Har takai ga wasu jahilai daga cikin musulmi na cewa 'Ai babu banbanci tsakanin musulmi da kirista !!!

Har suna cewa ai duniya yanzu ta waye, Kai har masu cewa wai ai duk Allah ne ya saukar da musulunci da kiristanci  Subhannallah!!!

To fadin wannan maganar fa kafirci ne, Allah ne yace "ALLAH YA KAFIRTA MASU CEWA ALLAH UKU NE"

A wani Wuri kuma yace "WALLAHI ALLAH YA KAFIRTA MASU CEWA ISAH (ALAIHIS SALAM) DAN ALLAH NE!!"

ALLAH madaukakin sarki ya gargade mu da so da kaunar kafurai tun daga yahudawa na nasarawa wato kirista...

Yana cewa "YAKU WADANDA SUKAYI IMANI KADA KU RIKI  YAHUDU DA NASARA A MATSAYIN MAJIBINTA DUK WANDA YA RIKE SU (MAJIBINTA)  TO YANA TARE DASU LALLAI ALLAH BAYA SHIRYAR DA AZZALUMAI"

Hakama Allah madaukakin sarki yana kara cewa "KAI MUSULMI YAHUDU KO NASARA BASU TABA YARDA DA DA KAI HAR SAI KA ZAMO DAGA CIKIN SU (wato ka koyi dabi'unsu)"

Yan uwa musulmi ana samun wasu musulmi na zuwa wajen kafurai har suna cewa murnar haihuwar Annabi Isah Alaihis salam, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yayi kama da kiristoci to yana cikin su"

Zama da kiristoci a lalura babu laifi sai dai dole ne a kiyaye duk wata alaka wadda data danganci addinin ka.

Yan uwa musulmi Ibn taimiyah yana cewa 'Abunda kiristoci keyi a addinin Annabi Isah Alaihis salam haramun ne!!!

Yan uwa musulmi masu albarka ma' abota ilmi sunyi gargadi game da taya kafurai murna.

Umar bn Khaddab khalifan Manzo sallal lahu alaihi wassalam na biyu yana cewa 'Kada musulmi su kuskura yaje wajen da kiristoci ke bukukuwan su domin Allah yana saukar da fushin sa a nan to idan musulmi yaje wurin abun na iya faruwa dashi "

Kada ka kuskura wani ya jaka ko ya rude ka cewa wai ai duk ana tare ko kuma kasa daya jama'a daya wallahi kada ko sau daya kaje wajen da kafurai ke yin bukukuwan su!

Su kafurai basu son Allah basu son Manzo sallal lahu alaihi wassalam duk abunda zasu fada maka karya ne kuma adawar ka tana cikin jinin su da rayuwar su

SABUWAR SHEKARA  (NEW YEAR)

Bayan kwana ki kuma kiristoci na bikin sabuwar shekara, Kuma abun takaici kaga musulmi na murna da annashuwa cewa sabuwar shekara ta kama!!

Har zakaga musulmi na turawa a yanar gizo cewa happy new year

Wannan abun takaici ne matuka!!

Shin musulmi sun manta da ainihin shekarar su??

Wai har ana samun musulmi wanda zaka tambaya yau naga ga watan musulunci ya kasa fada??

Wannan abun takaici ne!!!

Lallai wajibi mu fifita amfani da kwanan watan musulunci fiye da nasu, Watanni musulunci a bayyane suke kuma akwai dalilin saukar dasu Allah madaukakin sarki yana cewa "SUNA TAMBAYAR KA GAME DA JINJIRIN WATA MUN SANYA WANNAN NE DAN SANIN LOKACHIN IBADAH DA AIKIN HAJJI"

hakama madaukakin sarki na cewa "ADADIN WATANNI A WURIN ALLAH SUNE GUDA GOMA SHA BIYU AKWAI HUDU MAFI FALALA A CIKIN SU"

kenan ga manu Zamu dauki na wasu??

Amfani da watan ni kafurai sai lalura da kuma dole!!

Kada mu dauka cewa amfani da watan musulunci al'ada ne...... A'a addini ne.

Muna tawasuli da sunayen Allah dari ba daya ya shiryar damu hanya madaidaiciya ya biya bukatun mu na alkhairi.

Allah ka taimaki yan uwa musulmi dake zirin gaza ka kaskantar da yahudawa da masu goya masu Baya.

Allah ka amintar damu Kabamu lafiya d zama lafiya ya ubangiji kayi rahama ga mamatan mu.

Ya ubangiji kayi albarka da bunkasa kasashen mu da jahar mu da garin mu baki daya.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 2-Rabi'ul thani-1439
Friday 22-December - 2017 AB