Saturday, 2 November 2019

WANENE MAI GIRMAN KAI?

*WANENE MAI GIRMAN KAI GA ALLAH*❓

🍂IBN BA'D'DA AL-UKBARY(RH) YANA CEWA:

*Duk Wanda yaji gaskiya yayi inkarinta bayan yasan gaskiya ce, wannan Yana daga cikin masu girman Kai ga Allah, duk Wanda ya taimaka wurin yin sabo/zunubi/laifi Yana daga cikin tawagar shaidan.*

*📚 الإبانة في شرح أصول الديانة (٦٨٨)*

https://fb.me/abbansinan

02 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD

*🖋 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI S.A.W*

● AL-ALLAMA NASIRUDDEEN AL-ALBANY(RH) YANA CEWA:

*Mu AHLISSUNNAH dasu(yan bidi'ah) mun hadu akan cewa wannan bikin na maulidi abune kirkirarre, bai kasance ba a zamanin Manzon Allah S.A.W, Kai ba zamanin Manzon Allah S.A.W kadai ba, har karni uku(300+ years) suka wuce ba'a San dashi ba, Manzon Allah S.A.W bai taba yin biki ba saboda murnar haihuwar wani mutum a rayuwarsa, bikin maulidi hanyace ta kiristoci nasraniyya, masihiyya, musulunci bai San da maulidi ba Sam a wadancan karni masu daraja da muka ambata.*

📓📔 |[ من شريط بدعة المولد ]|

https://fb.me/abbansinan

01 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI

*🖋 BIDI'AR BIKIN MAULIDIN ANNABI S.A.W*

AL-ALLAMA ABDULLAHI BN HUMAID(RH) YANA CEWA:

*《Masu tsayuwa akan wadancan bukukuwan(maulidi) idan suna nufin sunyi hakan ne saboda girmama Manzon Allah S.A.W, toh su sani su masu sabawa shiriyarshi ne, masu kuskure ne akan hakan, baya daga cikin girmama Manzon Allah S.A.W kirkiro bidi'ah a cikin addinin daya zo dashi, ta hanyar ragi ko Kari, ko chanjawa ko karkatarwa, kyakyawar niyya da manufa Mai kyau basu halasta kirkiro bidi'ah a cikin addini 》.*

📓📔 |[ الرسائل الحسان في نصائح الإخوان للشيخ ابن حميد (ص ٣٩) ]|

https://fb.me/abbansinan

KIRKIRAR BIDI'AH

*KIRKIRAR BIDI'AH A CIKIN ADDINI IZGILI NE DA ALLAH; DOMIN KANA KUSANTAR MASHI ABUNDA BAI SHAR'ANTA BA.*

القول المفيد على كتاب التوحيد لابن عثيمين (١/٦٧)

https://fb.me/abbansinan

KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA

🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤
*_KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???_*
🔊🔈🔊🔈🔉🔉🔊

_Fitowa ta daya 001_

_Rubutawa:_ *Hashim Surajo Uba Tsamiya*  *(ABU SINÃN)*

    *_Godiya ta tabbata ga Allah, Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga Manzon Allah s.a.w da mutanen gidansa da  Sahabbansa da wadanda suka bi tafarkinsa._*

_Bayan haka;_

```Naga da cewar nayi wannan rubutun ne saboda yadda naga watan da yan bidi'ah ke sheke ayarsu ya kama, sannan kuma a wannan watane suke rudar jahillai suna batar dasu.
Amsar taken wannan rubutu itace; Bai halasta ayi bikin Maulidin Annabi ko maulidin waninsa daga cikin magabata, saboda yin haka yana daga cikin bidi'o'in da aka kirkiro a cikin addini, domin kuwa Manzon Allah s.a.w bai yiba, haka ma khalifofinshi guda Hudu shiryayyu da sauran sahabbai da wadanda suka bisu da kyautatawa duk basu yi maulidi ba, tare da cewa sunfi kowa sanin Sunnah da kuma aiki da ita, sunfi kowa So da kyaunar Annabi Muhammad s.a.w da kuma biyayya ga shari"'arsa, bisa wadanda suka zo bayansu.
Hadisi ya tabbata daga Annabi Muhammad s.a.w cewa;```
(من أحدث في أمرنا هذا ما ليس منه فهو رد).

_Ma'ana;_ *_Wanda ya kirkiro wani Abu a cikin wannan Al'amari namu(Addininmu) Wanda baya cikinsa, toh wannan Abu an mayar masa dashi.(Baza'a karba ba)_*

_Manzon Allah s.a.w a wani hadisin kuma sai yace;_
عليكم بسنتي وسنة الخلفاء الراشدين المهديين من بعدي، تمسكوا بها وعضوا عليها بالنواجد وإياكم ومحدثات الأمور، فإن كل محدثة بدعة وكل بدعة ضلالة.

_Ma'ana;_ *_Kuyi Riko da sunnah ta da sunnar khalifofi shiryayyu masu shiryarwa a bayana, kuyi riko da ita, kuma Ku cije a kanta da ha'koranku na can ciki, kuma Ku kiyayi kirkirarrun al'amurra, domin dukkan 'kir'kirarren Abu (a cikin Addini) bidi'ah ne, kuma dukkan bidi'ah bata CE._*

  ```A cikin wadannan hadisai biyu, akwai kashedi mai tsanani a kan kirkirar bidi'ah da kuma aiki da ita!
Allah madaukakin sarki ya fada a cikin littafinsa mai tsarki cewa;```
((وما ءاتكم الرسول فخذوه وما نهاكم عنه فانتهوا)).

_Ma'ana;_ *_Abin da Manzon Allah yazo muku dashi to Ku rikeshi, abin da kuma ya haneku ga barinsa, toh Ku hanu. [Al-hashr, aya ta 7]_*
A nan Allah yayi mana umurni da bin manzon Allah ba da yin maulidi ba

A wani wurin kuma sai Allah yace;
((فليحذر الذين يخالفون عن أمره أن تصيبهم فتنة أو يصيبكم عذاب أليم))
_Ma'ana;_ *_Wadanda suke saba wa umurninsa, baza suyi tunanin wata fitina ta samesu ba, ko wata azaba mai radadi ta samesu[An-Nur, aya ta 63]_*
A Wata ayar sai Allah yace;
اليوم أكملت لكم دينكم وأتممت عليكم نعمتي ورضيت لكم الإسلام دينا.

_Ma'ana;_ *_A yau na kammala maku addininku, kuma na cika ni'imata a kanku, kuma na yarda da musulunci ya zama Addini a gareku._*
          [Al-ma'ida aya ya 3]
 
Da kuwa ace maulidi addinine da yazo kafin saukar wannan ayar.

```Ayoyi da suke da irin wannan ma'ana suna da yawa, kuma kirkiro irin wadannan tarurruka na Maulidi yana nuna cewa Allah s.w.t bai cika Addini ba! Kuma Manzon Allah s.a.w bai Isarwa Al'umma da abunda ya kamata suyi aiki dashi ba! (Wanda duk ya fadi haka kuwa to tabbas ya zama ARNE)
Domin kuwa manzon Allah s.a.w a cikin hadisi ingantace yake cewa;
((ما بعث الله من نبي إلا كان حقا عليه أن يدل أمته على خير ما يعلمه لهم، وينذرهم شر ما يعلمه لهم)).

Ma'ana; Allah bai aiko wani Annabi ba, face ya kasance hakki ne akan wannan Annabin ya nuna wa Al'ummarsa Alherin da ya sani garesu, kuma yayi musu gargadi daga sharrin da ya sani garesu. [Muslim]

Wadannan ayoyi da hadissai kawai sun isa su tabbatar mana da cewa Maulidi ba Addinin Annabi Muhammadu bane, ba ya daga cikin hanyoyin shiriya na Addini, Hasali ma BIDI'AH CE abar kyama.

Sai mun hadu a fitowa na gaba.

*ABU SINÃN*
📞08064734911

Https://fb.me/abbansinan

Tuesday, 22 October 2019

BAKIN RIJIYA BA WURIN WASAN MAKAHO BANE...

🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
*BAKIN RIJIYA BA WURIN WASAN MAKAHO BANE....*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki Wanda ya hada yi mashi biyayya da yima malamai biyayya a aya daya a cikin Qur'ani, tsira da aminci su kara tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w Wanda yace: MALAMAI MAGADA ANNABAWA NE...

Bayan haka:

*NAMAN MALAMAI GUBA NE...*

  Abu ne sananne cewa malamai magada annabawa ne, kuma sune sukafi kowa falala bayan manzanni, sune fitilar dake haskawa jahilan dake cikin duhu domin su gane gaskiya, sune ke riko da hannun mutane zuwa ga hanyar shiriya, kuma sune sukafi kowa tsoron Allah, Allah s.w.t yana cewa: "ABUN SANI KADAI SHINE WADANDA SUKAFI KOWA TSORON ALLAH DAGA CIKIN BAYINSHI SUNE MALAMAI[Fadir:28], A wani wurin kuma Allah s.w.t yace: " SHIN KO MASU ILIMI ZASUYI DAI DAI DA JAHILAI? [Zumar:9]
Sai dai duk da wannan daraja tasu sai kaga an samu wasu daga cikin mutane wadanda aka jarabta da raunin imani, da rashin yiwa harshe linzami, da rashin sanin mutuncin na gaba dasu, sai ka gansu suna wulaqanta malaman wannan al'umma, wadanda sune suka takura rayukansu domin hidimtawa addini, da nuna wa musulmai hanyar shiriya. Amma a tare da hakan sai kaga an samu wasu masu gurbataccen tunani suna zagi da cin mutuncinsu.

*MAGANGANUN MANYAN MALAMAN MUSULUNCI AKAN MASU ZAGIN MALAMAI.*

_Saboda mu kubutar da yan uwanmu dalibban ilimi da irin wannan rudani ya kwasa..._

🔷Imamud-dahawy(RH) a cikin littafinshi(Dahawiyya) [2/740] yana cewa: "Malaman salaf wadanda suka gabata da kuma wadanda suka biyo bayansu sune ma'abota alkhairi da Sanin hadisi, sune ma'abota fiqhu da bincike, kada ka ambacesu sai da magana mai kyau, duk Wanda ya ambacesu da mummuna to baya kan shiriya(batacce ne).

🔶Haka imamu Ahmad(RH) yana cewa: " Naman malamai guba ne, duk Wanda ya taba zaiyi rashin lafiya, wanda yaci zai mutu murus.[Almu'eed fy adabul mufeed wal mustafeed, shafi na 71]

🔹Haka malik bn dinaar(RH) yana cewa: "Ya ishi mutum sharri, ka kasance kai ba mutumin kwarai bane amma kuma sai ka koma zagin mutanen kwarai." [Sha'abul iman, na imamul baihaqy;5/316]

🔸Haka ibnul Mubarak (RH) yana cewa; "Duk Wanda ke wulaqanta malamai, toh ya sani cewa lahirarshi ce yake wulaqantawa...[siyaru A'alamun nubala' 4/408]

🔹Alhafiz ibn Asakir ya fadi kwatankwacin wannan magana, haka ABU SINAN AL-ASDY(R) a cikin [Tarteebul madarik, 2/14]

*KARSHEN/SAKAMAKON MAI ZAGI DA CIN MUTUNCIN MALAMAI*

1. *Ya chanchanci a kirashi da sunan fasiqi bayan da yana da imani:*
  Kamar yadda aya ta [11] a cikin suratu hujraat ta tabbatar da hakan

2. *Ya sunnanta wata sunnah mummuna:*
       Duk Wanda ya sunnanta mugun aiki yana da zunubin aikin da zunubin duk Wanda yayi koyi dashi.

3. *Yana daga cikin mafi sharrin halitta:*
        Imamu Ahmad ya fitar da hadisi daga Abdurrahman bn ganam(R.A) daga manzon Allah s.a.w yace: " Mafi alkhairin mutane sune wadanda idan ka gansu za kaga suna ambaton Allah, mafi sharrin mutane sune masu yada Annamimanci, masu rabawa tsakanin masoya...

4. *Ya daura damarar yaki da Allah:*
         A hadisin bukhari(Hadisin qudusy) Allah s.w.t yana cewa: "Duk Wanda yayi adawa ko fada da masoyina, toh yazo ina shelanta mashi fada dani.

5. *Zai hadu da addu'ar malamin da ya zalunta/ya daga:*
        Addu'ar Wanda aka zalunta ba tada shamaki tsakaninta da Allah, toh ina ga addu'ar waliyyin Allah? Wanda Allah ke fada dangane dasu yana cewa: " idan suka rokeni zan Karba musu, idan suka nemi tsarina zan tsaresu...[Bukhary]

6. *Allah zai hukuntashi da abunda yayi:*
         Rama cuta ga macuci ibada inji malam bahaushe, kai dake zagin malamai ka tsoraci ramuwar da Allah s.w.t zaiyi musu a kanka!

7. *Za'a jarabceshi da mutuwar zuciya:*
         Babban malami IBN ASAKIR(R) yana cewa: "Duk Wanda ya saki harshenshi akan zagin malamai, Allah zai jarabceshi da mutuwar zuciya tun kafin ya bar duniya.

8. *Duk mai zagin malamai yana cikin hadari babba:*
           Wanda ke zagin malamai saboda addininsu, da maganganunsu akan hukunce-hukuncen shari'ah, ko don sun fadi wata magana ta gaskiya wacce ba yayi maka dadi ba, lallai kana cikin hadari babba, karanta aya ta [65-66] dake cikin suratu tauba.

9. *Allah zai jarabceshi da mummunar cikawa(iyyazan Billah):*
            Wannan itace sunnar Allah ga duk wani dan banzan da ya cutar da annabawan Allah tun daga fir'auna har zuwa wannan lokacin da muke cikin.

ALLAH YA NUNA MANA GASKIYA YA BAMU IKON BINTA, YA NUNA MANA QARYA YA BAMU IKON KAUCE MATA, ALLAH YA KARE HARSUNAN MU DAGA ZAGIN MALAMAI, MASU YI KUMA ALLAH YA SHIRYESU IDAN MASU SHIRYUWA NE, IDAN BA MASU SHIRYUWA BANE KAYI MANA MAGANINSU.

✍ *ABBAN_SINAN*
+2348064734911🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
*BAKIN RIJIYA BA WURIN WASAN MAKAHO BANE....*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki Wanda ya hada yi mashi biyayya da yima malamai biyayya a aya daya a cikin Qur'ani, tsira da aminci su kara tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w Wanda yace: MALAMAI MAGADA ANNABAWA NE...

Bayan haka:

*NAMAN MALAMAI GUBA NE...*

  Abu ne sananne cewa malamai magada annabawa ne, kuma sune sukafi kowa falala bayan manzanni, sune fitilar dake haskawa jahilan dake cikin duhu domin su gane gaskiya, sune ke riko da hannun mutane zuwa ga hanyar shiriya, kuma sune sukafi kowa tsoron Allah, Allah s.w.t yana cewa: "ABUN SANI KADAI SHINE WADANDA SUKAFI KOWA TSORON ALLAH DAGA CIKIN BAYINSHI SUNE MALAMAI[Fadir:28], A wani wurin kuma Allah s.w.t yace: " SHIN KO MASU ILIMI ZASUYI DAI DAI DA JAHILAI? [Zumar:9]
Sai dai duk da wannan daraja tasu sai kaga an samu wasu daga cikin mutane wadanda aka jarabta da raunin imani, da rashin yiwa harshe linzami, da rashin sanin mutuncin na gaba dasu, sai ka gansu suna wulaqanta malaman wannan al'umma, wadanda sune suka takura rayukansu domin hidimtawa addini, da nuna wa musulmai hanyar shiriya. Amma a tare da hakan sai kaga an samu wasu masu gurbataccen tunani suna zagi da cin mutuncinsu.

*MAGANGANUN MANYAN MALAMAN MUSULUNCI AKAN MASU ZAGIN MALAMAI.*

_Saboda mu kubutar da yan uwanmu dalibban ilimi da irin wannan rudani ya kwasa..._

🔷Imamud-dahawy(RH) a cikin littafinshi(Dahawiyya) [2/740] yana cewa: "Malaman salaf wadanda suka gabata da kuma wadanda suka biyo bayansu sune ma'abota alkhairi da Sanin hadisi, sune ma'abota fiqhu da bincike, kada ka ambacesu sai da magana mai kyau, duk Wanda ya ambacesu da mummuna to baya kan shiriya(batacce ne).

🔶Haka imamu Ahmad(RH) yana cewa: " Naman malamai guba ne, duk Wanda ya taba zaiyi rashin lafiya, wanda yaci zai mutu murus.[Almu'eed fy adabul mufeed wal mustafeed, shafi na 71]

🔹Haka malik bn dinaar(RH) yana cewa: "Ya ishi mutum sharri, ka kasance kai ba mutumin kwarai bane amma kuma sai ka koma zagin mutanen kwarai." [Sha'abul iman, na imamul baihaqy;5/316]

🔸Haka ibnul Mubarak (RH) yana cewa; "Duk Wanda ke wulaqanta malamai, toh ya sani cewa lahirarshi ce yake wulaqantawa...[siyaru A'alamun nubala' 4/408]

🔹Alhafiz ibn Asakir ya fadi kwatankwacin wannan magana, haka ABU SINAN AL-ASDY(R) a cikin [Tarteebul madarik, 2/14]

*KARSHEN/SAKAMAKON MAI ZAGI DA CIN MUTUNCIN MALAMAI*

1. *Ya chanchanci a kirashi da sunan fasiqi bayan da yana da imani:*
  Kamar yadda aya ta [11] a cikin suratu hujraat ta tabbatar da hakan

2. *Ya sunnanta wata sunnah mummuna:*
       Duk Wanda ya sunnanta mugun aiki yana da zunubin aikin da zunubin duk Wanda yayi koyi dashi.

3. *Yana daga cikin mafi sharrin halitta:*
        Imamu Ahmad ya fitar da hadisi daga Abdurrahman bn ganam(R.A) daga manzon Allah s.a.w yace: " Mafi alkhairin mutane sune wadanda idan ka gansu za kaga suna ambaton Allah, mafi sharrin mutane sune masu yada Annamimanci, masu rabawa tsakanin masoya...

4. *Ya daura damarar yaki da Allah:*
         A hadisin bukhari(Hadisin qudusy) Allah s.w.t yana cewa: "Duk Wanda yayi adawa ko fada da masoyina, toh yazo ina shelanta mashi fada dani.

5. *Zai hadu da addu'ar malamin da ya zalunta/ya daga:*
        Addu'ar Wanda aka zalunta ba tada shamaki tsakaninta da Allah, toh ina ga addu'ar waliyyin Allah? Wanda Allah ke fada dangane dasu yana cewa: " idan suka rokeni zan Karba musu, idan suka nemi tsarina zan tsaresu...[Bukhary]

6. *Allah zai hukuntashi da abunda yayi:*
         Rama cuta ga macuci ibada inji malam bahaushe, kai dake zagin malamai ka tsoraci ramuwar da Allah s.w.t zaiyi musu a kanka!

7. *Za'a jarabceshi da mutuwar zuciya:*
         Babban malami IBN ASAKIR(R) yana cewa: "Duk Wanda ya saki harshenshi akan zagin malamai, Allah zai jarabceshi da mutuwar zuciya tun kafin ya bar duniya.

8. *Duk mai zagin malamai yana cikin hadari babba:*
           Wanda ke zagin malamai saboda addininsu, da maganganunsu akan hukunce-hukuncen shari'ah, ko don sun fadi wata magana ta gaskiya wacce ba yayi maka dadi ba, lallai kana cikin hadari babba, karanta aya ta [65-66] dake cikin suratu tauba.

9. *Allah zai jarabceshi da mummunar cikawa(iyyazan Billah):*
            Wannan itace sunnar Allah ga duk wani dan banzan da ya cutar da annabawan Allah tun daga fir'auna har zuwa wannan lokacin da muke cikin.

ALLAH YA NUNA MANA GASKIYA YA BAMU IKON BINTA, YA NUNA MANA QARYA YA BAMU IKON KAUCE MATA, ALLAH YA KARE HARSUNAN MU DAGA ZAGIN MALAMAI, MASU YI KUMA ALLAH YA SHIRYESU IDAN MASU SHIRYUWA NE, IDAN BA MASU SHIRYUWA BANE KAYI MANA MAGANINSU.

✍ *ABBAN_SINAN*
+2348064734911

Tuesday, 7 May 2019

03 BARKA DA SHAN RUWA

🍉🍉🥭🍑🍎🍊🍋🍌🍉🍉
*BARKA DA SHAN RUWA*
🍉🍉🥭🍑🍎🍊🍋🍌🍉🍉

_003_

8⃣ *KO YANA HALASTA IN DOGARA GA KIRAN SALLAH DA AKE YADAWA A GIDAJEN RADIO A WURIN YIN BUDA BAKI KO SHIGAR ALFIJIR?*

_AMSA_

Yana halasta, musamman idan an tabbatar kafafen masu inganci ne a wurin ayyukansu, ko kuma  musulmi ke jagorantarsu, wannan itace fatawar *SHEIKH MUHAMMAD BN UTHAIMIN RAHIMAHULLAH*

9⃣ *MINENE HUKUNCIN SAHUR GA WANDA YAYI NUFIN YIN AZUMI?*

_AMSA_

Yin sahur mustahabbi ne kamar yadda *sheikh muhammad bn salih al-uthaimin RAHIMAHULLAH* ya tabbatar da hakan, kamar yadda yake sunnah ne yin sahur din a daya bisa ukun karshen dare, saboda fadar *ZAID BN THABIT (RA)* _"MUNYI SAHUR TARE DA MANZON ALLAH S.A.W, SAI MUKA TASHI DOMIN MUYI SALLAH, SAI AKA TAMBAYI ZAID, NA WANE TAZARA TSAKANIN KIRAN SALLAH DA SAHUR? SAI YACE: KAMAR KWATANKWACIN KA KARANTA AYA HAMSIN(50)."_ [Bukhari da muslim]

Da kuma fadar manzon Allah s.a.w cewa: _"AL'UMMATA BA ZASU GUSHE SUNA SAMUN ALKHAIRI BA MATUKAR SUNA GAGGAUTA BUDA BAKI, SUNA JINKIRTA SAHUR"_ [Imamu Ahmad ya ruwaito]

🔟 *DAME AKE SON MAI AZUMI YAYI BUDA BAKI?*

_AMSA_

Anason fara buda baki da *DABINO,* idan bai samu ba sai ya fara da *RUWA* Dalili akan haka shine hadisin da yazo daga salman bn Aamir (RA) yace, Manzon Allah s.a.w yace: _"idan dayanku ya kasance yana azumi yayi buda baki da *DABINO,* Idan bai samu ba sai yayi da *RUWA,* Saboda su ruwa tsarkakakku ne"._ [Maruwaita biyar suka ruwaito shi ] thirmidhi yace hadisi ne HASAN SAHIH



*ALLAHUMMA TAQABBAL SIYAMANA* 👏👏👏👏

#ABU_SINAN
+2348064734911