📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
*LADUBBAN MUSULMI A LOKACIN SANYI*
_001_
*ﺑﺴﻢ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ*
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Wanda yake jujjuya yanayi yanda yaso, Wanda cikin hakan akwai ayoyi da izina, yabo da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad da iyalansa da sahabbansa da wadanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
Lokacin sanyi lokaci ne mai falala da mumini ke iya ribatarsa wajen neman yardar Allah, hakika magabata sun kasance suna bushara da murna da zuwansa
ﻗﺎﻝ ﻋﻤﺮ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ:
) ﺍﻟﺸﺘﺎﺀ ﻏﻨﻴﻤﺔ ﺍﻟﻌﺎﺑﺪﻳﻦ )
ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﻣﺴﻌﻮﺩ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ : )ﻣﺮﺣﺒﺎً ﺑﺎﻟﺸﺘﺎﺀ ﺗﺘﻨﺰﻝ ﻓﻴﻪ ﺍﻟﺒﺮﻛﺔ ﻭﻳﻄﻮﻝ ﻓﻴﻪ ﺍﻟﻠﻴﻞ ﻟﻠﻘﻴﺎﻡ ، ﻭﻳﻘﺼﺮ ﻓﻴﻪ ﺍﻟﻨﻬﺎﺭ ﻟﻠﺼﻴﺎﻡ).
ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺤﺴﻦ ﺍﻟﺒﺼﺮﻱ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ : ) ﻧﻌﻢ ﺯﻣﺎﻥ ﺍﻟﻤﺆﻣﻦ ﺍﻟﺸﺘﺎﺀ ﻟﻴﻠﻪ ﻃﻮﻳﻞ ﻳﻘﻮﻣﻪ ، ﻭﻧﻬﺎﺭﻩ ﻗﺼﻴﺮ ﻳﺼﻮﻣﻪ ).
Akwai ladduba da *HUKUNCE-HUKUNCE* daya kamata mu kiyaye daga cikinsu akwai:
1: *RIBATARSA DA IBADU MUSAMMAN AZUMI,*
yazo a hadisi Wanda malamai sukayi sabani kan ingancinsa, sai dai ya tabbata daga Abu huraira, '' ﺍﻟﻐﻨﻴﻤﺔ ﺍﻟﺒﺎﺭﺩﺓ ﺍﻟﺼﻮﻡ ﻓﻲ ﺍﻟﺸﺘﺎﺀ''
*Ganima mai sauki azumi lokacin sanyi*.
babu shaka yin azumi a lokacin sanyi garabasa ne saboda abubuwa kamar haka:
A: Gajartar yini da raguwarsa.
B: Rashin zafin rana.
C: Saukin qishirwa.
2: *KIYAYE SHAN RUWA:*
Wannan abin nema ne a likitance, Saboda yin sakaci da shan ruwa yana janyo Rashin lafiya, Bincike na lafiya, ya nuna cewa sakaci da shan ruwa a lokacin sanyi yana janyo mutuwa lokaci daya, saboda idan mutum yabar shan ruwa zuciyarsa zata tsaya daga aiki.
Don haka masu Kula da lafiya suna bada shawarar shan ruwa kafin bacci da bayan tashi daga bacci, da lokacin cin abinci.
3: *AMFANI DA RUWAN ZAFI WAJEN WANKA DA TSAFTACE JIKI*
Domin ba jarumta bane yin Amfani da ruwa me tsananin sanyi lokacin sanyi domin yana iya janyo ma mutum Rashin lafiya, Addini yazo da kare lafiya da rayuwar mutum.
Allah yace:
[ ﻭﻻ ﺗﻠﻘﻮﺍ ﺑﺄﻳﺪﻳﻜﻢ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﺘﻬﻠﻜﺔ]☆
Kuma yace
[ ﻭﻻ ﺗﻘﺘﻠﻮﺍ ﺃﻧﻔﺴﻜﻢ ﺍﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻛﺎﻥ ﺑﻜﻢ ﺭﺣﻴﻤﺎ]☆
Yazo a hadisi cewa wasu sahabbai sunyi fatawa ga wani dan-uwansu da janaba ta sameshi, lokacin sanyi.
Kuma suna matafiya, kuma bashida lafiya.
Dayayi wanka da ruwan sanyi sai ya mutu, da suka dawo suka fadawa Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam sai yace:
*[ﻗﺘﻠﻮﻩ ﻗﺘﻠﻬﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺃﻻ ﺳﺄﻟﻮﺍ ﺣﻴﻦ ﺟﻬﻠﻮﺍ ﻓﺎﻧﻤﺎ ﺷﻔﺎﺀ ﺍﻟﻌﻲ ﺍﻟﺴﺆﺍﻝ ]*
4: *KYAUTATA ALWALA DA CIKATA, KOMAI TSANANIN SANYI,*
Saboda hadisin da Muslim ya rawaito:
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ'' ﺃﻻ ﺃﺩﻟﻜﻢ ﻋﻠﻰ ﻣﺎ ﻳﻤﺤﻮ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻪ ﺍﻟﺨﻄﺎﻳﺎ ﻭﻳﺮﻓﻊ ﺑﻪ ﺍﻟﺪﺭﺟﺎﺕ: ﻗﺎﻟﻮﺍ: ﺑﻠﻰ ﻳﺎ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻗﺎﻝ: ﺇﺳﺒﺎﻍ ﺍﻟﻮﺿﻮﺀ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻜﺎﺭﻩ، ﻭﻛﺜﺮﺓ ﺍﻟﺨﻄﺎ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻤﺴﺎﺟﺪ ﻭﺍﻧﺘﻈﺎﺭ ﺍﻟﺼﻼﺓ ﺑﻌﺪ ﺍﻟﺼﻼﺓ، ﻓﺬﻟﻜﻢ ﺍﻟﺮﺑﺎﻁ ﻓﺬﻟﻜﻢ ﺍﻟﺮﺑﺎﻁ '' ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ.
Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam yace: *" Shin bazan fada muku abinda Allah yake shafe kurakurai dashi ba, kuma yake daga darajoji dashi.*
*Suke eh ya Manzon Allah.*
*Sai yace:*
*CIKA ALWALA TARE DA SAMUN ABABEN DA ZASU SA KIN HAKAN.........................*
ﻗﺎﻝ ﺍﻟﻨﻮﻭﻱ ﻓﻲ ﺷﺮﺡ ﻣﺴﻠﻢ:
ﻭﺇﺳﺒﺎﻍ ﺍﻟﻮﺿﻮﺀ ﺇﺗﻤﺎﻣﻪ ، ﻭﺍﻟﻤﻜﺎﺭﻩ ﺗﻜﻮﻥ ﺑﺸﺪﺓ ﺍﻟﺒﺮﺩ ﻭﺃﻟﻢ ﺍﻟﺠﺴﻢ ﻭﻧﺤﻮ ﺫﻟﻚ. ﺍﻧﺘﻬﻰ .
5: *KIYAYE SALLAR ASUBA CIKIN JAM'I*
Hadisai dayawa sunzo suna tsoratarwa kan Rashin halartar asuba da isha a jam'i, Har manzon allah yace sune sukafi nauyi ga munafukai, kayi kokari ya kai bawan allah ka ceci kanka daga fadawa gungun munafukai da barin sallar asuba lokacin sanyi domin bakasan sanda mutuwa zatazo maka ba, Hakanan hadisai sunzo suna bushara ga masu kiyeye sallar asuba a lokacinta cikin jam'i, malamai sukace wadannan hadisai sun kunshi kusan busharori goma ga masu kiyayeta.
ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU
DOMIN SHIGA GROUP DIN:
*MU KYAUTATA NIYYA*
+2349030201868
https://fb.me/abbansinan