🎙🎙🎙🎙🎙🎙🎙
*ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBU BA...!!!*🎤🎤🎤🎤🎤🎤
*_Fitowa ta biyu(02)_*
*Daga; Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*Godiya ta tabbata ga Allah Wanda ya sanar da Dan Adam Abunda bai sani ba, tsira da Amincin Allah su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w tare da iyalan gidansa da sahabbansa da duk Wanda yabi hanyarsu da kyautatawa har zuwa ranar da kudi da yaya basu da amfani sai Wanda yaje ma Allah da zuciya mai tsoronshi da mika wuya gareshi.*
*_Bayan haka_*
```Nayi rubutu Mai irin wannan taken a sama sai wasu yan bidi'ah da wadanda basu fahimci addini ba suka yo Mani chaa, sai naga dacewar na kara haskaka ma Al'umma domin kowa ya kara gane inda aka nufa.
Da farko dai Menene Ma'anar gaibu???
Ita dai Kalmar gaibu kalma ce ta larabci, wadda take hawa akan duk abunda ya boyewa sanin mutum, duk abinda tunanin mai tunani ko hankalin mai hankali bazai iya riskarsa ba to shi ake cewa gaibu. Misali; Sanin yaushe zaka mutu, sanin Abinda zai sami rayuwarka a nan gaba, da sanin ranar tashin Kiyama duk suna daga cikin Misalan gaibu. (Nemi rubutun Abokin da'awa a fagen Media Malam Awaisu Al'araby fagge Wanda yayi a 28/04/2015 domin Karin bayani.)
Idan ka fahimci ma'anar gaibu, toh sai mu leka Qur'ani domin mu warware matsalar.
A cikin Qur'ani Allah S.W.T yake cewa;```
*يسئلك الناس عن الساعة، قل إنما علمها عند الله، وما يدريك لعل الساعة تكون قريبا.*
_Ma'ana;_ *_suna tambayarka(Annabi Muhammad s.a.w) akan lokaci(Tashin kiyama), sai Allah yace, kace saninta(Tashin kiyama) yana wurin Allah kadai. Kuma meya sanar dakai watakila ta kasance kusa._*
```Wannan ayar koda ace ita kadai aka saukar akan ilimin gaibu to tabbas ta isa hujja akan wadancan yan bidi'ar, abunda mutane basu fahimta ba akan wannan lamarin shine, su yan bidi'ah suna son fakewa da guzuma domin Harbin karsana, idan su ka yarda Almajiransu suka gane cewa Annabi Muhammad s.a.w baisan gaibu ba, sai Wanda Allah ya sanar dashi,idan kuma Allah ya sanar dashi ya tashi daga gaibu zuwa wahayi, toh idan suka fahimci wannan toh zasu gane cewa Ashe wadancan waliyyan na bugi yaudararsu sukeyi, domin sunce Sunsan gaibu, hujjarsu ta cewa haka saboda saboda tijjani da inyass duk jikokin Annabi ne, toh tunda Annabi yasan gaibu toh toh toh ai ai ai shi kuma jikane, saboda haka dole mu haska ma Al'umma domin su fahimci ina gaskiyar take.
Wata ayar kuma Allah S.W.T cewa yayi;```
*ولا أقول لكم عندى خزائن الله ولا أعلم الغيب...*
_Ma'ana:_ *_(Allah ne da kanshi ya cewa Annabi Muhammad s.a.w ya fadawa mutane cewa) Ban ce muku Taskokin Allah a hannuna suke ba, sannan kuma bansan gaibu ba._*
```To anan Abunda zance shine duk Wanda ya fahimci ma'anar gaibu wacce muka ambata a farkon rubutu, to zai fahimci cewa Manzon Allah s.a.w baisan gaibu ba,sai Wanda Allah ya sanar dashi, idan kuma Allah ya sanar dashi ya tashi daga gaibu zuwa wahayi, Allah ya kara fahimtar damu gaskiya ya bamu ikon binta.
Toh yanzu bari mu leka cikin hadisi.```
*Hadisi ya tabbata daga ummuna Aisha R.A akan cewa Annabi baisan gaibu ba.*
*عن عائشة رضي الله عنها قالت؛ من حدثك أن محمدا صلى الله عليه وسلم رأى ربه فقد كذب وهو يقول(لاتدركه ألابصار)، ومن حدثك أنه يعلم الغيب فقد كذب وهو يقول لايعلم الغيب إلا الله*
_Ma'ana:_ *_Nana Aisha tace "duk Wanda yace maka Annabi Muhammad s.a.w yaga Allah toh karya yakeyi, sannan duk Wanda yace maka Annabi yasan gaibu to karya yakeyi, domin shi din yana cewa babu Wanda yasan gaibu sai Allah._*[Bukhari 7380,6945, Muslim 457,287]
```Toh yan uwa kunji zancen Nana Aisha matar Manzon Allah s.a.w wacce take kusa dashi a koda yaushe, Masu karyata Ahlis sunnah akan wannan zancen to me zakuce akan zancen Nana Aisha??? Nasan indai ka yarda Nana Aisha uwar muminai ce to baza ka karyata taba, domin indai kai mumini ne to uwarka ce, idan kace ba uwarka bace sai muce toh ai munsan wacece uwarka, eh itace hãwuya, Allah ya kyauta. Bari na dakata a nan idan bukatuwar fitowa na uku ta taso, toh a matsayinmu na dalibai zamu kara cewa wani Abu.
Allah ka jikan sheikhul Islam Muhammad ibn Abdulwahab, a cikin Littafinsa kashfus shubuhãt yake cewa;```
*والعامي من الموحدين يغلب ألفا من علماء هؤلاء المشركين، كما قال تعال؛(وإن جندنا لهم الغلبون) [الصافات ١٧٣]*
_Ma'ana;_ *_Mai karamin sani(ilimi) cikin masu kadaita Allah yana rinjayar mutum dubu cikin mushirikan Malaman bidi'ah, kamar yadda Allah yace; Rundunar Allah sune Masu yin nasara. Rundunar Allah sune masu yin nasara da hujja Qur'ani da hadisi, haka kuma suke yin nasara da harshensu._*
```Allah ya tabbatar damu akan sunnar Annabi Muhammad s.a.w ya dawwamar damu a cikin aiki da ita Amiin.```
https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya
Copyright©
*Hashim Surajo Uba Tsamiya*
📞08064734911📞