Sunday, 1 January 2017

HUKUNCIN JININ HAIHUWA(JININ BIKI)

HUKUNCIN JININ
HAIHUWA ( JININ BIKI)

Gabatarwa: Da sunan Allah Mai yawan rahama
mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su
tabbata ga fiyayyan halittar Allah Annabin tsira
Annabi Muhammad, da Iyalan shi da Sahabban
shi baki daya. Bayan haka a yanzu kuma muna
daukene da abinda ya shafi jerin hukunce
hukuncen jinin biki wanda ake kira jinin haihua
wanda yake da izinin Allah bayanshi za mu
kawo a wannan karon bayan da abayanan da
suka gabata muka kawo bayanai akan jinin
al'ada.
Menene Jinni Biki: Jinine da yake fitowa daga
mahaiffa ta sanadiyyar haihuwa. Kenan shi jinin
biki jinine da yake da alaka da haihuwa, idan
mace taga jini kwana daya ko biyu kafin
haihuwa to shima malamai suna lissafashi cikin
jinin haihuwa.
Mafiyawan Kwanakinsa: Mafi yawan kwanakin
da macan data haihu zata ga jinin haihuwa
malamai sun karawa juna sani, wadansu sukace
kwanaki ar'bainne (40), wadansu kuma sukace
kwanaki sittinne (60) kamar yadda mai Akhdari
ya bayyana. Sabanin na al'ada shi kwanaki
goma sha-biyarne.
Idan mace ta haihu sai jinin bai dauke ba to
zata jira kwanaki arba'in, ko sittin, idan ya
dauke a kwanakin shikenan sai ta yi wankan
tsarki na daukewar jinin haihuwa ta ci gaba da
sallah da kuma sauran ayyuka na ibada, idan
kuma bai daukeba to sai a nemi magani ya
zama jinin ciwo sai ta yi wankan tsarki ta ci
gaba da ibada, idan kuma jinin ya dauke kafin
kwanakin kamar ya dauke ranar da aka yi
haihuwar to annan ma zata yi wankana ta ci
gaba da sallah, laifine maigirman gaske mace
jinin haihuwarta ya dauke amma taki yin sallah
wai sai ta yi arba'in wannan ba tsari bane na
addinin musulunci, domin tsarin musulunci
dazarar jinin yananan kafin kwanaki arba'in to
dazarar ba za'a yi sallah ba, amma dazarar jini
ya dauke ko kafin sunane to dazarar za'a ci
gaba da sallah, sai a kiyaye.
Imam Tirmizi yake cewa: Malamai sun yi
ijima'i tun daga Sahabbai da Tabi'ai da wadanda
suka zo bayansu (Sun yi ijima'i) akan cewa lalle
mace mai haihuwa zata bar salla tsawon
kwanaki arba'in sai dai idan ta ga tsarki kafin
hakan (kafin kwanaki arba'in din) sai ta yi
wanka ta kuma yi sallah.
Idan mace ta yi bari sai ya zamana halittar
mutum ta bayyana a barin kamar ace ga tsarin
halittar ba wai gudan jini bane ya zamana kuma
akwai jini day a zuba to anan tana da hukuncin
jinin biki jinin haihuwa, gwar gwadon kwanakin
da asune ahalittar take bayyana a ciki sune
watanni ukune galibi ammadai mafi karanci
sune kwanaki tamanin (80).
Idan ta yi barin gudan jini ko gudan tsoka ta
yadda halittar mutum bata bayyanaba to ba'a
la'akari da wannan jinin da ya zubo, saboda
haka ba zatabar sallah ba kuma ba zatabar
azumiba saboda jinin domin bata da hukuncin
jinin biki.
Idan jinin haihuwa ya dauke kafin wadancan
kwanakin da aka yi bayaninsu to zata yi
wankane ta kuma yi sallah ko da jinin ya
daukene a ranar da aka yi haihuwar, to idan
jinin ya dauke kafin wadancan kwanakin sai
kuma ya dawo to sai mu tsaya mu gani idan
tsakani daukewar da dawowar ya kai kwanaki
goma sha-biyar zuwa abinda ya yi sama to
wanda ya dawodin jinin al'adane bana biki bane,
amma idan tazarar batakai kwanaki goma
shabiyarba to jinin da ya dawo cikon jinin
haihuwane.
Abubuwan Da Basu Halatta Ga Mai Jinin
Bikiba: Mu sani dukkan abuwan da jinin al'ada
yake hanawa ayiwa mai al'ada to jinin
haihuwama yana hanawa a yi wa mai biki, haka
namma abinda jinin al'ada yake hanawa mai
al'adar ta yi to jinin haihuwama yana hanawa ta
yi, kamar: Saki, saduwa, taba Alkur'ani, zama a
masallaci dadai sauransu kamar yadda bayani
ya gabata a jinin al'ada.
Haka namma kamar yadda ya halatta mai
al'ada ta yi kunzugu megidanta ya shasshafata
ya taba ko ina a jikinta in banda daga cikibiya
zuwa gwiwa to haka namma ya halatta ga mai
jinin haihuwa.
Kammalawa: Daga wadannan takaitattun
bayanai da suka gabata ya bayyana a fili cewa
al'amarin jinin haihuwa ba abune da za'a yi
wasa akansaba, watakila hankali ya tafi kan
bukukuwa suna maijego kuma bata sallah kuma
ga shi jinni ya dauke, kuma mun fahimci munin
tsohuwar al'adar nan na cewa maijego sai ta yi
arba'in kafin ta fara sallah ashe al'amari da
bashi da alaka da addinin.

Aliyu Muhammad Sadisu,
Minna Jahar Neja, Nijeriya.

HUKUNCIN JININ ISTIHALA(JININ CIWO)

HUKUNCIN JININ
ISTIHALA ( JININ CIWO)


Gabatarwa: Da sunan Allah Mai yawan rahama
mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su
tabbata ga fiyayyan halittar Allah Annabin tsira
Annabi Muhammad, da Iyalan shi da Sahabban
shi baki daya. Bayan haka a yanzu kuma muna
daukene da abinda ya shafi jinin istihala wato
jinin ciwo, saboda baya amsa jinin al'ada wato
jinin haila haka kuma ba amsa sunan jinin biki
wato jinin haihuwa kenan, wato kenen shi
wannan jinin ba jinin al'ada bane ba kuma jinin
haihuwa bane saboda haka baya dauke da
hukunce-hukuncensu, baya hana sallah da
azumi da saduwa kamar yadda wadancan suke
hanawa.
Matashiya: Domin yin kandagarki yana da
matukar kyau da tsari mace ta lura da abubuwa
kamar haka:
(1) Launin Jininta: Ta yi kokari ta gane launin
jininta na al'ada wanne kala yake zuwa mata
'Baki ne ko Ja'.
(2) Lokacin Zuwa: Shin al'adarta tana zuwa
mata ne a farkon wata ko tsakiyarsa ko karshe.
(3) Kwanakinsa: Kuma ta kiyaye kwanaki nawa
yake zuwa mata a duk lokacin da take al'ada.
(4) Shinshina: Wato yanayinsa yana da karnine
ko wari.
Dukkanin wadannan abubuwa ana bukatar ta
gane su kuma ta fahimcesu tun lokaci da take
lafiya, -Allah ya sawwake – domin idan jini ya ci
gaba da zuwa saboda ciwo da wadannancan
bayanai za'a yi aiki domin a gano mata
kwanakin jininta na al'ada da kuma kwanakin da
suke na rashin lafiya.
Jinin Istihala : Shine ballewar jini ba'a
lokacinsaba, ta wata jijiya da ake kira 'Azil' .
Al'amari mai jinin Istihala al'amarine mai
rikitarwa domin yadda jinin al'ada yake kama da
jinin istihala, to idan jinin ya kasance yana zuba
a koda yaushe ko mafi yawancin lokaci to a irin
wannan lokaci me zata yi la'akari da shi a
matsayin al'ada me kuma zata yi la'akari da shi
a matsayin jinin istihala ta yadda ba zatabar
azumi da sallah ba saboda shi? Domin mai jinin
istihala ana mata hukunci mata masu tsarkine,
kada a manta ya kandauki mace tsawan
shekaru ko watanni ba al'amarine da za'a yi
wasa da shi ba. La'akari da wannan bayani lalle
mace mai jinin istihala tanada yanayi guda uku:
Yanayi Na Farko: Ya kasance dama tanada
lissafin tsarin al'adarta kafin wannan ciwo na
zubar jini ya sameta, kamar ace dama ta
kasance kafin jinin istihala tana al'adane tsawan
kwanaki biyar ko takwas missali a farkon wata
ko a tsakiya kuma ta san adadin lokacin, to
wannan zata zauna ne a matsayin mai al'ada
gwargwadon yadda ta saba, sai ta bar sallah da
azumi domin a wannan lokacin ana mata
hukuncin mace mai jinin al'ada, idan al'adar ta
dauke (Kwanakin da ta kaddarasu cewa sune na
al'adar) sai ta yi wanka ta kuma yi sallah, sai
ya zama jinin da ya ci gaba da zuwa jinin
istihalane ba jinin al'adaba, kamar yadda
Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su
tabbata a gareshi) yace ma Ummu Habiba '' Ki
zauna gwargwadon da al'adarki take zuwa,
sannan sai ki yi wanka ki kuma yi sallah'' , Muslim
334, hakanan kuma Ma'aikin Allah (Tsira da
amincin Allah su tabbata a gareshi) ya fadawa
Fatima diyar Abu Hubaish cewa : ''Ai wannan
wata jijiyace, ba al'ada bace idan lokacin al'adarki
ya iso sai ki bar sallah'' Bukhari 228 , Muslim
333 .
Yanayi Na Biyu: Idan ya zama bata da wani
yanayi sananne saidai jinin nata ana
banbanceshi yana dauke da siffar jinin al'ada,
kamar ya kasance baki ko mai kauri ko ya
kasance yana da wata shinshina amma sauran
baya kama da siffar jinin al'ada, kamar ya
kasance jaa amma bashi da shisshina kuma
bashi da kauri, to a irin wannan yanayi za ta yi
la'akari da jinin da yake dauke da siffar jinin
al'ada a matsayin jinin al'ada sai ta bar sallah
da azumi…' sai kuma ta yi la'akari da wanda ba
shiba jinin ciwone bana al'adaba, sannan sai ta
yi wanka idan wannan jinin da yake dauke da
siffar jinin al'adar ya dauke, daga nan kuma sai
ayi mata hukuncin mace mai tsarki, kenan sai
ta ci gaba da sallah da azumi…' ko dako jinni na
zuba, kamar yadda Ma'aikin Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gareshi ya fadawa
Fatima diyar Abi Hubaish:
'' Idan ya kasance jinin al'ada, shifa jinine baki
akasanshi, to sai ki dakatar da sallah, idan kuma
dayanne sai ki yi alwala ki yi sallah'' . Abu Daud
286, Nasa'I,220, Ibnu Hibban 1348.
Yanayi Na Uku: Idan ya kasance bata da wani
abu da take gane jinin al'ada da shi, kuma babu
wata siffa da take banbance jinin al'ada da
wanda ba na al'adaba, to anan zata yi la'akarine
da mafi yawan kwanakin al'ada a kowanne wata
wato kwanaki shida ko bakwai, domin wadannan
kwanakin sune mafi yawan kwanakin da mata
suke al'ada, wannan ko saboda hadisin
Hamnatu diyar Jahash Ma'aikin Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gareshi:
'' Abin sani kawai wannan (Jinin ciwon)
wani zungurine daga shaidan, saboda haka sai ki
yi al'adarki kwana shida ko kwanaki bakwai,
sannan sai ki yi wanka, idan kika tsarkaka sai ki
yi sallah kwanaki ashirin da hudu ko ashirin da
uku, kuma ki yi azumi ki yi sallah, yin haka ya
isarmiki, haka za ki dinga yi kamar yadda mata
suke al'ada'' . Tirmizi: 128, Abu Daud: 287, Ibnu
Majah: 627.
Atakaice: Idan aka yi la'akari da bayan da
suka gabata za mu fahimci cewa; mai yanayi
tabbatacce zata yi anfani da wannan yanayin
ne, wacce take abinda take banbance al'ada da
jinin da ba na al'adaba za ta yi anfanine da
wannan, amma wacce bata da wata alama to
za ta yi al'ada kwanaki shida ko bakwai.
Abinda kan mai jinin istihala (jiwo): Dudda
cewa a hukumce mace mai jinin istihala wato
jinin ciwo macece mai tsarki dudda cewa jinni
na tare da ita alokaci, saboda haka za ta yi lura
da abubuwa kamar haka:
1. Ya zama wajibi ta yi wankan daukewar jinin
al'ada bayan wucewar kwanakin da aka yi
la'akari da su a matsayin jinin al'ada.
2. Za ta wanke gabanta domin gusar da abinda
ya fita alokacin kowacce sallah.
3. Za ta sanya auduga ko makamancinta a
gabanta domin hana shi diga kasa, wato zata yi
kunzugu kenan.
4. Za ta dinga yin al'awala a kowacce sallah,
kenan ba zata yi salloli biyu da al'awala dayaba,
saidai idan ramuwace, Allah kadai shine masani.
Kammalawa: Daga wadannan bayanan da suka
gabata ya bayyana a fili yadda musulunci ya
kula sosai kan abinda ya shafi hukunce-hukunce
jinin dake samun mata, kama daga jinin al'ada
jinin biki har zuwa wannan jinni na istihala wato
jinin ciwo, kuma wannan yana nuna
muhimmancin al'ummar muslmi su tashi tsaye
domin sanin wannan al'amari musammanma
mata, kuma daga nana za mu dasa aya akan
abinda ya shafi tsarki za kuma mu shiga abinda
ya sahafi Sallah da izinin Allah.

Aliyu Muhammad Sadisu,
Minna Jahar Neja, Nijeriya.

HUKUNCE HUKUNCEN ALWALA

HUKUNCE-HUKUNCEN
ALWALA

Gabatarwa: Alwala ibadace mai zaman kanta
wacce Allah madaukakin sarki ya sahar'antata
kafin gabatar da wadansu ibadu musammamma
sallah, mutum yana samun cikakken ladan
alwala idan ya yi ta cikakkiya, Allah madaukakin
sarki ya saukar da hukunce-hukuncen alwala a
cikin littafinsa mai girma alkur'ani:
'' Ya ku dukkanin wadanda suka yi imani, idan
kuka ta shi za ku yi sallah to ku wanke
fuskokinku da hannayanku zuwa gwiwar hannu
ku kuma shafa kawunanku da kafafanku zuwa
idan sawu (idan kafa)…'' Suratu Ma'ida, aya ta: 6.
Tabbas wannan aya ta ti bayanin wajibcin
alwala lokacin da za'a yi sallah, kuma ta
bayyana gabban da ya zama wajibi anwanke ko
kuma anshafa, sannan kuma ayar ta iya kance
ko wanne mahalli, sannan kuma Ma'aikin Allah
–Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi-
ya bayyana siffar yadda alwalar take da
maganarsa da kuma aikinsa bayanin da yake
gamsasshan bayani.
Ka sani lalle ita wannan alwala tanada falala da
kuma sharudda da kuma farillai sannan tana da
sunnoni da kuma mustahabbai, sharuddannan
da farillai tabbas a tabbata ansame alokacin
gabatar da alwala iya gwargwado domin da
sune alwala zata zama karbabbiya, amma su
sunnoni da mustahabbai suna cika alwalarne ta
inda matsayinsu bai kai matsayin sharuddai da
farillaiba.
Falalar Alwala: Dudda cewa alwala wajibice
wannan kadai ya isheta samun matsayi a
musulunci domin dukkan abinda akace farillane
to wannan matsayi ne me zaman kansa, bayan
hadisi na 62 a cikin Muwadda'u Malik yana
cewa: '' An karbo daga Abdullahi As-Sunaabihi,
lalle ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su
tabbata agareshi yace:
''Idan bawa mumini ya yi alwala sai ya yi
kuskurar baki dukkanin laifukan dake bakin sun
fice, idan kuma ya face laifukan (Day a shaka)
sun fice, to idan kuma ya wanke fuskarsa
laifukan da ke fuskar ta sa sun fice, har wadanda
ke karkashi girar shi, idan ya wanke hannayansa
laifukan dake hannayansa sun fice, har wadanda
ke karkashi faratansa (jam'in farce), to idan
kuma ya shafi kanshi laifukan dake kan nashi sun
fice har wadandake kunnuwansa, to idan kuma
ya wanke kafafuwansa duk laifukan dake
kafafuwan nasa sun fice, har wadanda ke
karkashi farcen kafafun nashi. Sannan kuma
tafiyar da ya yi zuwa masallaci ya zama wani
karine da yake da shi''.
Lalle wannan bakamar falala bace da alwala
take da shi, domin mai alwala zai kasance yana
kammala alwala zunubanshi suna digewa a
kasa, amma gudu ba hanzariba wannan ladan
zai tabbata ne ga wanda ya yi alwala da
shara'a ta tabbatar da ita ba wacce ya tsinta a
kan titi ba.
Sharuddan Alwala: Sharuddan alwala sune
abubuwan da ake so mai alwala ya cika su
kafin ya fara alwalar, sune kamar haka:
(1) Musulunci , kenan idan wanda ba musulmiba
ya yi alwala bata yi ba.
(2) Hankali , idan mahaukaci ya yi alwala itama
bata yi ba.
(3) Wayau , idan dan karamin yaro mara dabara
ya yi bata yi ba.
(4) Ruwan ya zama mai tsarki, idan ya zama
ruwane mara tsarki to alwalar bata yi, bayanai
sun gabata akan hukunce-hukuncen ruwa.
(5) Ruwan ya zama na halas, idan ruwane da
mutum ya sata ko ya same shi bata shar'an
tacciyar hanyaba to alwalar bata yi ba.
(6) Ya kasance mai tsarki , idan mai alwala ya
kasance ya yi fitsari ko bayan gida misali wato
ya kasance mara tsarki kafin alwala to ko ya yi
alwalar bata yi ba.
(7) Gusar da duk abinda zai hana ruwa shiga,
kenan idan mutum ya kasance yaba sanye da
wani abunda zai hana ruwa ya kai ga fatar jiki
to dolene ya cire shi, kamar tabo (laka)…'.
Farillan Alwala :
(1) Niyyah: Domin a banbance wanda ya sa
ruwa donin sanyaya jiki, ko domin gusar da
datti, duk wannan ba niyyace ta alwalaba.
(2) Wanke Fuska: ita kuma fuska ta bangaren
tsawo tana farawane daga matsirar gashin kai
(banda sanko) zuwa karshen mukamiki, amma
ta fuskar fadi tana farawane daga kunnan dama
zuwa kunnan hagu, wannan shine abinda yake
amsa fuska, kenan dole mai alwala ya tabbatar
ko ina ya sami ruwa kamar kasan haba, gefan
ido da gefan kunne da matsa-matsin karan
hanci, ayi hattara sosai domin wasu alwalarsu
kamar alwalar yarace.
(3) Wanke Hannaye Zuwa Gwiwar Hannu. Mai
alwala mace ko namiji ya tabbata ya wanke
hannayansa tun daga saman yatsunsa (farce-
akaifa) harzuwa gwiwar hannu ya tabbata
gwiwar ta shiga inda ya wanke, anamma akwai
manya masu alwalar yara.
(4) Shafar Kai: Ka tabbata ka hada yatsunka
sannan kuma ka fara shafar daga goshi (daidai
matsirar gashi) sannan ka shafa zuwa keya.
(5) Wanke Kafa: Hakanan mai alwala ya
tabbata ya wanke kafarsa harzuwa idon sawu,
wato wadannan kasusuwan guba biyu dake
gefan kafafuwa sun shiga cikin inda aka wanke.
(6) Cudanyawa: Mai alwala ya tabbata ya
cudanya duk inda ya wanke ya dirza ruwa ya
shiga ko ina.
(7) Yinsu Baidaya: Abinda ake nufi shine
alokacin da ka fara alwala to ka dakatar da
komai sai ka kammala, amma kana alwala kana
kuma wata sabga daban wannan bai yi ba.
Mai alwala ya tabbata ya gabatar da
wadannan ayyuka a lokacin da yake alwala ta
yadda idan aka rasa daya daga cikin su to
alwalarsa ta shiga hadari.
Sinnonin Alwala:
(1) Wanke Hannaye Kafin A Tsoma Su A Ruwa.
Ta yadda mai alwala zai karkato butar alwala
domin ya wanke hannayansa zuwa Ku'u wato
wuyan hannu.
(2) Kuskurar Baki: mai alwala ya tabbata ya
sanya ruwa a bakinsa sannan kuma ya kada
ruwan a baki, wannan shi ake kira da kuskurar
baki.
(3) Shaka Ruwa: Shine mai alwala ya shaki
ruwa ruwan ya shiga hancin sa sosai, sai dai
kawai idan yana azumine sai yayi kadan. Amma
yadda mutane suke shafar hancinsu wai da
sunan shaka ruwa wannan baiba.
(4) Facewa: mai alwala zai shaki ruwanne da
hannun dama sai ya sa hannun haku akan
karan hancinsa, sannan sai ya fyato ruwan da
ya shaka.
(5) Shafar Kunne; Mai alwala ya tabbata ya
shafi cikin kunnensa da wajan kunnan, zaka/ki
sanya yatsanka 'yar-manuniya a cikin kunnan
sannan ka babban yatsa a wajan kunnan
sannan sai ka shafa, Dirkashi!.
(6) Sake Taba Ruwa: Alokacin da zaka shafi
kunne shin zaka shafi kunnanne da ragowar
danshin hannuka da ka yi shafar kai da shi? Ko
ko zaka sake taba ruwa na musamman domin
shafar kunne, malamai sun karawa juna san, ko
wanne ka yi ya yi daidai.
(7) Dawo Da Shafar Kai: Ka tsaya ka fahimta,
ita shafar kai farillace, amma dawo da shafar
kai sunnace daga cikin sonnonin alwala.
(8) Jeranto Farillai: Ta yadda zaka kawosu
daya-bayan-daka kamar yadda aka lissafosu,
kada ka dauki na uku ya zama shine na farko
sannan ka biyo shi dana biyar, misali…'.
Wadannan matsayisu bai kai matsayin farillaiba,
amma suna cikin manyan abubuwan da suke
cika alwala.
Mustahabban Alwala:
Wannan shi ke biye da mataki na sunnoni,
kenan sunnoni sun fi mustahabbai karfi,
wadanda suke dukansu biyun farillai na
gabansu, babu daya daga cikin sunnoni ko
mustahabbai da mutum zai yi sakaci da su,
domin kowannanmu so yake ya yi ibada
cikakkiya kammalalliya, to ko tunda hakane bai
kamata yace ai wannan mustahabbine ya
daukeshi kamar wani kankanin abu.
Su mustahabban alwala suna da yawa, amma
yanzu ga kadan daga cikinsu:
(1) Anbaton Allah yace ''Bismillah'' , adaidai
loakcin da zaka fara alwala, amma idan mutum
ya manta saida yake tsakiyar alwalar ya tuna
bakomai sai ya yi a lokacin.
(2) Addu'a bayan kammala alwala, itace kuma
kamar haka:
ﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥْ ﻻَ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺍَﻟﻠﻪُ ﻭَﺣْﺪَﻩُ ﻻَ ﺷَﺮِﻳﻚَ ﻟَﻪُ،
ﻭَﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥَّ ﻣُﺤَﻤَّﺪًﺍ ﻋَﺒْﺪُﻩُ ﻭَﺭَﺳُﻮﻟُﻪُ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺍَﺟْﻌَﻠْﻨِﻲ
ﻣِﻦَ ﺍَﻟﺘَّﻮَّﺍﺑِﻴﻦَ، ﻭَﺍﺟْﻌَﻠْﻨِﻲ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﻤُﺘَﻄَﻬِّﺮِﻳﻦَ .
Ma'ana: ''Ina shaidawa da babu abinbauta da
cancanta sai Allah, kuma shi kadai yake bashi da
abokin tarayya, kuma ina shaidawa lalle (Annabi)
Muhammad bawan Allah ne kuma manzansa ne,
Ya Allah ! ka sanya ni daga cikin masu yawan
tuba, kuma ka sanya ni daga masu neman
tsarkaka.''
(3) Karanta Ruwa : Bawai ana nufin mai alwala
ya shasshafa gabbansa bane, a'a, ana bukatar
ya yi anfani da ruwa amma kada ya malalar da
shi, domin yana daga cikin tsarin musulunci
tattali da tsimi da tanadi.
(4) Gabatar Da Asuwaki: Bayani kuma dama ya
gabata akan asuwaki, ana yi da danye ko da
busasshe, idan bai samuba sai ayi da yatsa,
amma mu sani asuwaki daban kuskurar baki ma
daban. Hakanan kuma ko da mutum lokacin
sallah ya yi kuma amma yana da alwala to
abinda ake so shine ya yi asuwaki.
(5) Wuri Mai Tsarki : An so inda zaka yi alwala
ya zama wurine mai tsarki.
(6) Dama Kafin Hagu : abin nufi shine ka fara
wanke hannun dama kafin hannun hagu,
hakanan ka fara wanke kafar hagu kafin ta
dama.
( 7) Jerantawa: Wato jeranta kowacce sunnah
tare da 'yar-uwarta, kamar fara gabatar da
kuskurar baki kafin shaka ruwa.
(8) Wankewa Sau Uku: Ma'ana wanke wuraran
da ake wankewa sau uku, mu sani wankewa sau
uku zai zama mustahabbine idain wankewar
farko ta game ko ina, amma idan ta farko bata
gamaba to ta biyu tananan amatsayin wajibi,
haka namma idan ta biyun idan bat agama ba
to ta uku tana nan a matsayin wajibi. Ya zama
wajibi mai alwala mace ko namiji ya kula sosai
ya cuccuda inda ya kamata ya sa ruwa ba tare
da barnaba. Amma shi kais au daya ake
shafarsa, ba'a shafar kai sau uku. Sannan kuma
mutum ya tabbata a wadannan wankewa da
akace ya yi sau uku bai kara akan hakan ba, ya
yi iya kokarinsa ya ga guda ukun sun kammala.
Wadannan kadan kenan daga cikin
mustahabban alwala, kuma wadannan bayanai
sun mata kamar yadda suka shafi maza, sai dai
mata su sani gashin kansu da sangalin
hannuwansu duka al'aurane, saboda haka bai
halatta su bayyanar da su ga maza, ken an idan
zaki yi alwala sai ki sami wuri ki kawwame
kanki.
Wadannan bayanai da suka gabata zasu
haskaka mana yadda alwala take, amma hanya
mafi sauki shi ne a yi maka ita a aikace ka gani
domin haka sahabban ma'aikin Allah suka yi, an
tambayi Usman dan Affan dan gane da alwala
sai yasa aka kawo mishi butar alawala ya yi
musu ita a aikace, yace kuma irinta ma'aikin
Allah ce.
Anan nake kira ga dukkanin limamai na juma'a
dana sauran masallatai da kuma malamai a
jami'oi da kwalejin ilimi da kuma malamai a
sakandare da firamare da malaman islamiyyu da
malamai masu karantarwa a masallatai da
masu wa'azi da sauran wadanda abin ya shafa
da su karantar da mutane ita wannan alwalar a
aikace kowa ya gani ya kuma yi tambaya, kada
ka ga kamar kowa ya gane da zarar ka yi ta a
aikace zaka ga abin mamaki, ni na taba gwada
hakan, ita ibada sai an koyawa mutum ba wai
daka kawai shikenan ya iyaba, ko kuma ai shi
iyaye da kakanni duk musulmai ne sabo da haka
ba sai ya koyaba, duk wannan maganace ta
wanda yake nesa da makaranta, kai da ganin
alwalar wani kasan bai je makaranta ba, Allah
ya karba mana ibadummu.
Kammalawa: Lalle wadannan bayanai sun
kara tabbatar mana ashe alwa abace da sai an
tashi tuku domin a koyeta tana da falala da
kuma sharudda sannan ga farillai da sunnoni da
kuma mustahabbai, lalle ka nana bukatar
malamai daga kowanne bangare su tashi tsaye
su karantar da al'umma wannan ibada a aikace,
domin a gudu tare a tsira tare.

TSARKI DA YADDA AKE YINSA

TSARKI DA YADDA AKE
YINSA

Shinfida: Mu sani ya 'yan-uwa masu albarka,
wannan addini na musulunci addinine da yake
cikakken addini ta kowanne bangare, bai takaitu
ga alwala da sallaba kadai, ya shafi kowanne
bangare na rayuwa, kamar tsafta kiwon lafiya
zamantakewa, kasuwanci taimakon juna, tsare-
tsaren gudanarwa dadai sauransu.
A yanzu zamu kawo bayanaine da suka shafi
tsarki, dame-dame ake yiwa tsarki? Me rashin
tsarkin yake jawowa? Ya ladubban yin tsarkin
suke? Ya ake shiga makewayi? Dadai sauran
wadansu batutuwa da suke da alaka da wannan
maudu'i, da fatan Allah ya yi mana jagora ya
kuma fahimtar da mu.
Abubuwan Da Akewa Tsarki: ana yin tsarki ne
daga dukkan abinda ya fito ta daya daga
mafitar guda biyu ko ma ta duka inbanda hutu
(tusa). Kenan ana yiwa fitsari, bayangida
maniyyi maziyyi jinin al'ada….tsarki, kawai dai
idan mutum yana da alwala sai ya yi tusa to
alwalar kawai zai sake ba sai ya dauki butu ya
yi tsarki ba.
Hukuncin Tsarki: Tsarki wajibine, saboda haka
dukkan wanda dayan wadancan abubuwa da
makamantansu suka same shi to dole ya
tabbata ya gabatar da ya yi tsarki.
Abinda Ake Tsarki Da Shi : Abinda ake tsarki da
ashar'ance shine ruwa mai tsarki mai
tsarkakewa, wannan shi ake kira Istinja'u .
Saidai idan mutum bai sami ruwanba sai ya yi
da duwatsu a kalla guda uku, idan ya ga na
ukun ya fito a bushe ba wata laima shikenen,
idan kuma akwai laima to sai ya kara su kai
biyar wuturi ake bukata (3,5,7,9…) wannan kuma
ana yinshi a fitsari ko bayan gida, sannan idan
ka sami ruwa ba sai ka sake ba, wannan
hukunci shi ake kira Istijmari , ka samu ka hada
duka a lokaci guda, misali idan ka yi bayan gida
sai kasa tsinke ko takarda mara rubutu sai ka
share sannan sai ka biyo shi da ruwa. Kenan
ba'a tsarki da yawu (miyau).
Kada asha'afa, idan aka yi la'akari da abinda
ya fita da kuma abinda ya fantsamo maka, za'a
raba tsarki zuwa gida biyu:
(1) Tsarkin Hadasi: Shine tsarkin abinda ya fita
daga dayan mafita guda biyu, kamar fitsari,
maziyyi…'.
(2) Tsarkin Kabasi: Shine tsarkake abinda ya
taba jiki ko tufafi ko kuma wuri, kuma ko
wannensu baya yiwuwa said a ruwa mai tsarki
mai tsarkakewa.
Amma idan aka yi la'akari da girma ko rashin
girma za'a kasa tsarki zuwa gida biyu shima:
(1) Babba wanda ake kira Hadasul Akbar:
Ankira shi babbane domin ba'a tsarkaka daga
gareshi sai an yi wanka, kamar fitar maniyyi, ko
saduwa, ko daukewar jinin al'ada ko na biki.
(2) Karami wanda ake kira Hadasul Asghar:
wanda yake tsarki ko alwala ta wadatar, kamar
fitsari ko maziyyi.
Yadda ake yi: Da farko mutum ya wanke
hannunsa na hagu kafin ya sa a wurin da zai
wanke, domin hannun sa ya koshi da ruwa,
sannan sai ya wanke wurin fitsari. Daga nan
kuma sai ya fara wanke wurin bayan gida
musamman idan ya kaatse, ana bukatar mutum
ya wanke al'aurar sa baki dayanta musamman
idan maziyyi ne ya fita.
Ladubban Zagawa (Fitsari Ko Bayangida):
Akwai tsari na ladubba da musulunci yake da su
a lokacin da mutum ya ke niyyar kewayawa,
wannan zai nuna maka cewa musulunci ya
karade komai:
(1) Anbaton Allah : Ana bukatar kafin ka shiga
ka ambaci Allah domin ba'a anbaton Allah a
makewayi, kuma ka nemi Allah ya tsareka da
sharrin aljanu, domin irin wadannan wurare
matattarace ta su, yace:
ﺑِﺴْﻢِ ﺍَﻟﻠﻪِ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﻋُﻮﺫُ ﺑِﻚَ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﺨُﺒُﺚِ
ﻭَﺍﻟْﺨَﺒَﺎﺋِﺚِ
Ma'ana: Da sunan Allah, Ya Allah lalle ni ina
neman tsarinka (Ka tsareni) daga aljanu maza da
kuma aljanu mata.
Idan kuma zaka fito sai kace:
ﻏُﻔْﺮَﺍﻧَﻚَ، ﺍَﻟْﺤَﻤْﺪُ ﻟﻠﻪِ ﺍَﻟَّﺬِﻱ ﺃَﺫْﻫَﺐَ ﻋَﻨِّﻲ ﺍَﻷَﺫَﻯ
ﻭَﻋَﺎﻓَﺎﻧِﻲ
Ma'ana: (Ina neman) gafarar Ka , Dukkan godiya
ta tabbata ga Allah wanda ya rabani da wannan
kazantar kuma ya bani lafiya.
Ka sani ba'a shiga bayi da dukkan wani da
yake dauke da sunan Allah, kamar zobe, ko
carbi…'. Hakanan kuma ba'a katse bayangida da
dukkan wani abu da yake da sunan Allah.
(2) Fara Gabatar Da Kafar Hagu Lokacin Shiga,
kafar dama kuma lokacin fita.
(3) Ayi A Tsugunne: kada mutum ya yi fitsari
ko bayan gida a tsaye, sai dai idan wurin
kangone ko yana tsoron fitarin ya fallatso masa,
sannan ba wanda zai ganshi ya samu ya yi a
tsaye.
(4) Tabbatuwa A Cikin Sutura: ana bukatar
kada mutum ya yaye al'aurar sa tun yana tsaye,
sai ya tsugunna ya yi dab da kasa sai ya daga
suturarsa, domin ba'a yarda wani ya ga al'aurar
wani ba in ba miji da mataba, amma halin ko
unkula da wasu suke nunawa na bayyanar da
al'aurarsu ga kowa muddin jinsi gudane wannan
baidaceba, sai ka ji wana yace 'Ai duka
mazane, abinda kake da shi ina dashi', wannan
ba koyarwar musulunci bace, haka namma
mata, wannan zai kaika ka ga maza sun tube
suna wanka lokaci guda a dakin wanka guda,
haka namma mata, wai sun dauka abinda yake
haram shine namiji ya ga al'aurar mace ko
mace ta ga al'aurar namiji, kai wani lokaci kana
tafiya a cikin mota sai kai arba da wani
gabjejen kato yana wanka a rafi, wani kuma a
gefan titi ya kafe mashin ko ya je kayan
tallansa, duk wadannan bakewawan halaye
bane, mutum musulmi ya nisance su.
(5) Yafi Bada Karfi A Kafarsa Ta Hagu: Kenan
abinda akafi so shine mutum ya fi bayar da
karfinsa a kan kafarsa ta hagu.
(6) Ya Bude Tsakanin Cinyoyinsa: kenan kada
ya matse, ballantana ya sa matsattsiyar tufa
wacce idan yana fitsari na gaban ne kawai zai
fita, sannan idan ya mayar cikin wando sauran
ya gangaro, Allah ya sawwake.
(7) Ya Nisanci Inda Ruwa Yake: musulunci bai
yadda mutun ya yi fitsari ko bayan gida a inda
ruwa yakeba ko kusa dashi, dan wannan zai
haifar da cututtuka.
(8) Ya Rufe Kansa: Ana son wanda yake
bayangida ya rufe kansa a daidai lokacin da
yake yi, domin koda wani ya yi kuskuren
ganinsa to shi bai ganshiba, abin zai zo da
sauki, amma ba zaka ji dadiba kana bayan gida
ka hada ido da wani, wanda zai iya zama
dalibinka ne ko suruki ko da..,'.
(8) Kada Ayi Magana: anhana mutum yana
bayan gida yana Magana, sai dai idan akwai
dalili mai kwari, kamar ka ga makaho ya nufi
rijiya ko karamin yaro…'.
(9) Kada A Tari Iska: an hana idan mutum zai
yi bayan gida a dawa (daji) an hana ya tari iska,
domin zai bsowa jama'a warin bayan gidansa,
kenan sai ya yi nesa, ya kuma duba ina iska
take kadawa.
(10) Kaucewa Rami: Ba'a yarda idan za ka yi
fitsari ko bayangida ka yi aramiba saidai idan
kai ka haka, domin bakasan mekecikin ramin ba,
takan yiwu akwai mugun abu.
(11) Kaucewa Wuraran Tsinuwa: Wadannan
wurare sune wuraran da mutane suke yawan
tsinema dukkan wanda ya yi musu bayangida a
wurin, wadannan wurare sune:
(a) Inda mutane suke zama su huta, jikin
bangone ko karkashin bishi komadai inane.
(b) Kan hanya: Akwai rashin mutunci mutum ya
zo kan hanya ya gicciya bayangida, wannan
dabi'a musulunci bai yarda da ita ba.
( c ) Mashayarruwa: Hakanan baya cikin
karantarwar musulunci mutum ya zo inda
al'umma suke diban ruwa rafine ko wani gulbi
ko gindin fanfo komadai inane ya aikata wannan
ta'asa. Wadannan wurare uku musulunci ya
hana a aikata wannan danyan aiki a wurin,
domin mutum yana jawa kansa tsinuwa, Allah
ya tsaremu.
(12) Nesa Da Jama'a : ana bukatar dukkan
wanda zai yi bayan gida ya yi nesa da jama'a ta
yadda ba za su ganshiba kuma ba za su ji
nishin shiba, ba zai yi kyauba ace kana bayan
gida mutane suna ganinka ko suna jin nshinka,
ko da a bayan bishiya ko ganyan kargo sai ka
boye, amma sau da yawa mutane suna tafiya a
mota da motar ta tsaya sai ka ga kowa ya
tsaya dab da motar, sannan ba za'a tafi a
barshiba.
(13) Kada Ya Fuskanci Alkibla: wato inda
mutum yake kallo lokacin sallah, kuma kada ya
juya mata baya, wannan idan a dajine, amma
idan a gidane to da sauki.
Abubuwan Da Rashin Tsarki Yake Hanawa:
kamar yadda bayani ya gabata cewar tsarki
wajibine, to mu sani idan mutum bashi da tsarki
bai halatta a gareshi wadannan abubuwanba:
(1) Sallah: Bai halatta ga wanda bashi da tsarki
ba ya yi sallah nafila ko farillah.
(2) Dawafi: Kewayan Ka'aba kenan a birnin
makkah, saboda haka idan mutum yana dawafi
sai ya yi tusa to dawafisa ya warware sai ya
sake alwala domin ita tusa ba'a yi mata tsarki.
(3) Sujjadar Tilawa: Wato sujjadar da mutum
zai yi ida yana karatun Alkur'ani mai girma sai
ya kai wadansu gurare, domin ba shi da tsarki,
dudda malamai sun kawa juna sani akai.
(4) Kabli Ko Ba'adi : Bai halatta ga wanda bashi
da tsarki ba ya yi kabli ko ba'adiba har sai ya yi
tsarki, idan akce kabli ana nufin sujjadar da
mutum zai yi kafin ya yi sallama, amma idan
ake ba'adi to wacce zai yi bayan sallama. Idan
jiya ba'adi ta kamaka sai kuma ka manta baka
yi to ya halatta ka yi ta a yanzu idan kana da
tsarki.
(5) Daukar Alkur'ani Mai Tsarki: idan mutum
bashi da tsarki to sai yi tsarki kafin ya taba
wannan littafi mai tsarki.
Kammalawa: ina fatan wadannan takaitattun
bayanai sun warkar da abinda ake bukata, kuma
sun nuna lallai addinin musulunci gamamman
addinine da ya shafi komai ya kuma yi bayani
akan komai, domin idan yakai bayan gida sai an
nunawa mutum yadda ya kamata ya yi to ashe
wannan ba karamin gata musulunci ya yi mana,
muna godiya ga Allah.

ABUBUWAN DAKE KARYA ALWALA

ABUBUWAN DAKE KARYA
ALWALA

Shinfida: Lalle wannan babi yana da matukar
muhimmanci, domin bayan da kasan alwala to
ya kamata kasan abin da ke warwareta, akan
haka ya ka yiwa kanka hukunci idan zaka yi
sallah ko abinda dole sai da alwala ake yinsa,
saboda haka yana da matukar kyau mu kula da
wadannan hukunce-hukunce. Allah ya yi mana
jagora.
Abubuwan da suke bata alwala sunkasu kashi
biyu; Hadasi da Sababinsa. Abin nufi anan
shine, akwai abinda shi karankan sa yake bata
alwala to wannan shi ake kira Hadasi
(Al'ahdaas) . Akwai kuma wanda shi karankan
sa bai warware alwala amma zai kai ka ga
abinda yake warware alwalar to wannan shi ake
kira, Sabuban Hadasi (Asbabul Ahdas).
To shi hadasin wato abinda yake karya alwala
da karankansa, abubuwane guda shidane, hudu
daga cikinsu suna fitane ta gaba, sune kuma;
Fitsari, Maziyyi, Wadiyyi da kuma Maniyyi.
Wadannan idan suka faru ko dayansu ya faru to
tsarki kawai za'a yi a sake alwala in banda
maniyyi, Wanda shi maniyyi bayan ya bata
alwala sai kuma anyi wanka. Sai kuma guda
biyu daga da suke fita daga dubura, sune kuma;
Bayangida da kuma tusa. Amma shi bayan-gida
tsarki za'a yi sai a sake alwala, sabanin tusa
wacce take ita ba'a yi mata tsarki alwala kawai
za'a sake.
Sai kuma abubuwan da suke sabubbane na
hadasin wadanda yake suna da wasu bayanai,
amma su wadancan da zarar ya diga komai
kankantarsa to ya karya alwala inbanda mai
fama da cutar yoyon-fitsari, wadannan abubuwa
sune;
(1) Bacci: Shi bacci a nan ya kasu kashi hudu;
(a) Dogon bacci mai nauyi, kai tsaye wannan ya
karya alwala.
(b) Takaitaccan bacci mai nauyi, shi ma ya
karya alwala.
(c) Takaitaccan bacci mara nauyi to shi bai
karya alwala ba.
(e) Dogon bacci mara nauyi, bai karya alwala
amma an so a sake ta.
Ma'aunin da ake auna bacci da shi domin a
gane yana da nauyi ko ba shi da nauyi shine;
Idan ka san wanda ya zo da wanda ya tashi to
baccinka bai yi nauyi ba, amma idan baka san
wanda ya zo ba ko wanda ya tashi ba to baccin
ya yi nauyi. Kenan idan kuna fira sai amma
kana gyangyadi sai da ka farka sai kace; ina
wane? Ko; wane yaushe ka zo? To kasan
baccinka ya yi nauyi, Allah ya sa mu dace.
(2) Gushewar Hankali: Idan hankalin mutun ya
gushe ta hanyar hauka ko farfadiya ko suma ko
maye to mu sani alwalarsa ta karye. Kenan idan
mutum ya yi alwala sai ya hau iska ko kuma
suka yi hadari kawai sai ganinsa ya yi a asbiti
ko kuma ya sha ta yi Marisa-ta sha kafso to
alwalar ko wannensu ta karye.
(3) Shafar Azzakari: Idan mutum ya shafi
al'aurarsa kai tsaye tafin hannunsa ya taba
al'aurarsa bawai ta samani riga ko wandoba ko
kuma wani kyalleba to malamai sun karawa
juna sani kan makomar al'walarsa, wadansu
suke ce kawai alwalarsa ta karye, wasu kuma
suka ce idan ya tabane domin ya ji dadi to ta
karye amma idan ba wai ya yi hakanne domin
ya ji dadi ba alwalarsa nanan, wannan maganar
kuwa tana da karfi. Amma dukkanin malamai
sun yi ittifaki kan cewa idan ya taba al'aurarsa
ba kai tsayeba ko dai ta saman wando ko
saman riga ko saman wani kyalle to alwalarsa
nanan daram.
(4) Shafar Mace/Namiji: Idan namiji ya shafi
mace domin ya ji dadi to ko ya ji dadin ko bai ji
ba alwalarsa ta karye, haka kuma al'amari yake
idan mace ta taba namiji domin ta ji dadi to ta
ji dadin ko bata ji ba alwalarta ta karye,
malamai sun kasa shafar zuwa gida hudu;
(a) Idan ya taba domin ya ji dadi kuma ya ji
dadin to alwalar ta karye.
(b) Idan ya taba ba don ya ji dadi ba sai kuma
ya ji dadin to ta karye.
( c) Idan ya taba domin ya ji dadi sai bai ji da
din ba to alwalar ta karye.
(d) Idan ya taba ba domin ya ji dadi ba kuma
bai ji dadinba to alwalarshi tanan daram.
Wadannan bayanai haka mai Ashmawi ya
kawosu. Mu sani wadannan bayanai sun shafi
macema idan ita ta yi.
Akwai wadansu da malamai suka karawa juna
sani akan suna karya alwala ko basa karyawa?,
wadannan kuma sune:
(5) Shakka Akan Hadasi: Idan mutum ya
tabbatar da alwalarsa sai kuma yake kokwanto
ya yi hadasi ko bai yi ba? Kenan bashi da
tabbas? Wasu malamai sukace; Ai da ya yi
kokwanto alwalarsa ta karye domin ba'a sallah
da wani abu na shakku. Wasu malaman kuma
suke: Idan ya tabbatar da yana da alwala sai
daga bayane yake shakka to ai shakka bata ture
abinda yake dahir, saboda haka sukace alwalar
nanan, Allah shine masani.
(6) Ridda: Shine mutum musulmi ya kafirta
(Allah Ya tsaremu). Wadansu malamai sukace
da zarar ya bar musulunci to da zarar alwalar ta
karye, wasu malaman kuma sukace; A'a, ai
ayyukansa da ya yi ba za su baciba sai in ya
mutu bai dawo musulunci ba, wadda alwala na
cikin wadannan ayyukan. Mafi kyawu ga
wadannan abubuwa mutum ya sake alwalar shi
yafi.
Alwala bata baci idan mutum ya yanke farce
(Kunba), ko ya taba marenansa ko duburarsa ko
anyi masa kaho ko ya yi dariya ko amai ko
kuma tuntube har jini ya fita duk alwala bat
abaci saboda wadannan, ko mace ta shafi
gabanta amma idan ta sa yatsa a ciki to wasu
sunce alwalar ta karye. Idan mutum yana jin
fitsari ko tusa ko bayan gida abinda musulunci
ya karantar shine mutum ya je ya biya wannan
bukatar ta shi tukunna, maimakon ya matse.
Kammalawa: Alwala tana da muhimmanci
matuka saboda haka a kiyayeta a san kuma
abinda yake warwareta, kuma wannan yake
nuna mana cewa tunda har alwala za'a ce
akwai abubuwan da suke warwareta dudda ga
laima a jikin mutum amma ace alwalarsa ta
warware to lalle yana da kyau musan kuma
abubuwan da suke warware musulunci domin
kullun mutum ya dinga ba addininsa kariya ta
yadda kada ya warware, Allah yak are mana
addinimmu, amin.

Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna Jahar Neja, Nijeriya.

WANKAN TSARKI(JANABA)...

WANKAN TSARKI
(JANABA)...

Shinfida: Bayan da bayanai suka gabata akan
abinda ya shafi karamin hadasi wanda yake ya
takaitune ga tsarki da kuma alwala, sannan
bayanai suka zo akan abinda ya shafi kadan
daga cikin hukunce-hukuncen alwala, to a
yanzu za'a yi bayani ne akan abinda ya shafi
babban hadasi wanda yake bai tsaya ga tsarki
ko alwalaba a'a, shi tsarkinsa shine ayi wanka
shine an tsarkaka, wadannan abubuwa da suke
wajabta wanka suna da yawa za mu yi iya
kokari damin mu kawo su daki-daki, da fatan
Allah ya yi mana jagora, amin.
(1) Janaba: Janaba dayace daga cikin
abubuwan da suke wajanta wanka, wanda yake
hanyoyin kasantuwa da janaba sune kamar
haka:
(a) Fitar Mani: Idan maniyyi ya fita daga mace
ko namiji to wanka ya wajaba, amma kafin
wankan ya wajaba sai ya zama maniyyin ya
fitane ta hanyar jin dadi, kamar kallo ko wasa
ko tabe-tabe ko jingina…' amma idan ya fita ba
ta hanyar jin dadiba ya fitane ta hanyar wahala,
kamar ya taka wuta ko harbin kunama ko kuma
watar lantarki ta ja shi…' to wannan wanka bai
wajaba a kanshiba saida kawai ya yi alwala. Shi
wannan fitar maniyyi da ake Magana akan shi
ko dai ya fita a farke ko kuma ya fita ana bacci,
idan ya fita ana farke shine ake maganar an ji
dadi ko ba'a ji ba, amma idan ya fita ana
baccine to ba wata maganar jin dadi wanka ya
wajaba.
(b) Shigar Azzakari Cikin Farji: Idan kan kaciyar
namiji ya bace cikin gaban mace to wanka ya
wajaba. Anan ba'a maganar an fitar da mani ko
ba'a fitarba, da zarar hakan ya faru ko macen
ce ta fitar amma namijin bai fitarba ko kuma
namijin ne ya fitar amma macen bada fitar ba
ko ma dukansu basu fitarba wankadai ya
kamasu su duka, da wanda ya fitar da wanda
bai fitarba, tunda ba maganar fitarwa ake yi ba
maganar saduwace, amma inda wasa aka yi ba
saduwa ba to wanda ya fitar shi wanka ya
wajaba a kanshi.
Idan aka yi saduwa sannan aka kara yi to
idan an tashi wanka wanka guda kawai za'a yi,
koda an yi saduwar sau gomane sannan ake so
ayi wanka to wanka guda za'a yi ba wanka
goma ba.
Idan mutum ya sadu da mace kuma yake so
ya jinkirta wankan janaba zuwa an jima to
abinda zai yi shine ya yi tsarki sai ya yi alwala,
domin alwalar tana rage kaifin janaba, sannan
kuma tana kara kuzari lokacin da ake so akara
saduwar.
Idan mutum ya sadu da mace sai bai fitar da
maniyyi ba wanka ya wajaba akanshi kamar
yadda bayini ya gabata, to bayan ya yi wankan
sai kuma ya ga maniyyi ya zubo, to anan idan
wata sabuwar sha'awace ta fitar da wannan
maniyyin wani wankan ya kama shi, amma idan
janabar da ya yi wa wankace maniyyinta ya zo
yanzu to alwala kawai zai yi.
Abayan da suka gabata mun yi bayani na
babbancin maniyyi da kuma maziyyi, sannan
kuma da banbance-banbancen maniyyin mace
da na namiji. Sannan mu sani wadannan
bayanai sun shafi maza da mata, sannan kuma
ka'ida ta musulunci itace bayanin abubuwa a
yadda suke, domin kada a ga maganganun sun
yi tsauri, mahalline na bayanin hukunce-
hukunce.
Fitar maniyyi a farke ko ta hanyar nafarki,
kamar mutum ya yi mafarkin yana saduwa da
mace, ko mace ta yi mafarkin namiji yana
saduwa da ita to wannan al'amari yana tabbatar
da abubuwa kamar haka; abu na farko wannan
wanda ya fitar da maniyyin janaba ta hau
kanshi, abu na biyu; idan wannan shine fitar
maniyyinsa na farko to ya sani daga wannan
lokacin ya balaga, saboda haka hukunce-
hukuncen musulunci sun hau kanshi ko kanta.
Idan mutum ya yi mafarkin yana saduwa da
mace, ko mace ta yi mafarkin ana saduwa da
ita, sannan kuma ya farka bai ga maniyyi ba to
ba wata janaba akanshi, saboda haka ba zai
wanka ba kuma zai yi tsarkiba saboda hakan.
Wadannan kadan kenan daga cikin bayanan
da suka shafi janaba, kuma dole a tashi tsaye
domin a karantar da mutane, wani da ake
Magana da shi cewa yake yi shi bai san idan
mutum ya sadu da matarsa wai sai ya yi
wankaba, wai abinda ya dauka shine wanda ya
yi zina shine wanda zai yi wanka. Wannan
jahilci har ina!.
Abubuwan Da Janaba Ke Hanawa: Bai halatta
ga wanda yake da janaba ba ya shiga
masallaciba, ko kuma ya karanta Alkur'ani ba,
sai aya daya ko biyu domin neman tsari.
Mutumin da yasan ba zai iya taba rowan
sanyi ba to malamai sunce kada ya kusanci
iyalinsa sai ya tanadi abinda zai dumama rowan
dashi, kamar hita, risho ko itace…'.
(2) Daukewar Jinin Al'ada: Abu na biyu cikin
abubuwan da suke wajabta wanka shine
daukewar jinin al'ada, kenan idan jinin al'adar
mace ya dauke to abu na farko dake gabanta
shine wanka. Bayanai akan abinda ya shafi jinin
al'ada da hukunce-hukuncensa da alamar
daukewarshi da izinin Allah za su zo nan gaba,
mudai sani idan jinin al'ada ya dauke to dole
mace ta yi wanka, kuma zuwan jinin al'ada
lamace dake nuna wannan mai jinin ta balaga
musamman ace shine zuwansa na farko a
wurinta, bayanai dai za su zo da izinin Allah.
(3) Daukewar Jinin Biji: Wannan shine abu na
uku daga cikin abubuwan da suke wajabta
wanka, watau daukewar jinni haihuwa, da zarar
mace ta ga jinin haihuwa ya dauke mata ko da
ranar data haihune to wanka ya wajaba akanta
domin ta fara sallah, ba wanda yace sai mai
jego ta yi kwanaki arba'in kafin ta kama sallah,
shima bayai akan jinin biji zai zo da izimin mai
duka shine Allah, kawai mu sani anan daukewar
jinin haihuwa yana wajabta wanka.
(4) Mutuwa: Mutuwa tana wajabta a yiwa
wanda ya mutu wanka, shi kuma bayanai kan
abinda ya shafi wankan da yadda ake yinsa zai
zo ne alokacin da za'a kawo bayanai kan
jana'iza da izinin Allah, kuma Allah ya kaimu
lokacin, abinda ake so a fahimta anan shine
idan mutum ya mutu to dole ayi mishi wanka
sai dai idan shahidine da ya rasu a fagen fama.
(5) Musulunta: Wannan yana cikin abinda
malamai suka karawa juna sani, shin idan
wanda ba musulmiba ya musulunta wajibine sai
ya yi wanka? Wasu sukace wajibine domin
Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su
tabbata a gareshi- ya umarci wasu da suka
musulunta da su yi wanka, su kuma wadanda
sukace ba wajibi bane wankan sunce ba'a
ruwaito cewa Ma'aikin Allah –Tsira da amincin
Allah su tabbata a gareshi- ya umarci dukkan
wadanda suka musulunta da cewa kowa sai ya
yi wanka ba.
Kammalawa: A yanzudai munsan abubuwan
da idan yada daga cikinsu ya faru to wanka ya
wajaba, kuma mun sami takaitaccan bayani
akan abinda ya shafi janaba, kama daga
hanyoyin da ake samunta, bayanan da zasu zo
nan gaba za su kun yadda wankan tsarki yake,
wato wankan janaba da kuma na daukewar jinin
al'ada (haila) da bambance-bancen dake cikin
su, Allah ya kai mu lokacin da sauran kwana da
kuma imani.

Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna Jahar Neja, Nijeriya.

ABUBUWA BAKWAI MASU HALAKARWA.

Abubuwa Bakwai Masu
Halakarwa(Yiwa Mace Mumina
Kazafi)...

Mace Mumina Kazafi : A yanzu za mu yi
ni akan abu na bakwai kuma na karshe cikin
uwa bakwai da Ma'aikin Allah – tsira da
cin Allah su tabbata a gareshi- ya lissafa
abubuwan da suke halakar da wanda yake
uli dasu , wannan abu shine Yiwa Mace
ina Kazafi .
fi Shine: Jifan mutum da aikata alfasha ta
ko kore juna biyu ko ma Da ba tare da ya
r cikakkun shaiduba.
Alokacin da mutum ya jefa kanshi cikin irin
nnan halayya ta kazafi to lalle ya jefa
a cikin halayyar da take halakarwa, domin
kazafi ba karamin bala'ibane, alokacin da
m ai wance mazinaciyace ko ya yi lalata da
o wannan ciknnanata bana mijintabane ko
a/'yarta ai bana mijinta bane to lalle ya
no tsuliyar dodo dole ya kawo cikakkun
u na mutane hudu maza musulmai da zasu
shaida akan hakan, idan kuma mai kawo
uba ko ya kawo basu cikaba to kowanne
m gada cikinsu bulala tamanin (80) za'a yi
, kamar yadda bayanai zasu zo nan gaba
n.
Wannan shiri da musulunci yake dashi
ramin shiri bane domin kare mutunci, masu
agana na cewa mutunci madarane in ya
bai kwasuwa, addinin musulunci yana daga
manyan manufofinsa kare mutunci, wannan
musulunci ya dauki irin wannan mataki
mmamma 'ya mace, domin alokacin da aka
mata suna to gaba daya anbata mata
arta, shi yasa ayoyin da suka yi Magana
kazafi sun anbaci macece basu anbaci
jiba wannanko ba wai dan hukuncin ya sha
n bane a'a hukuncin iri dayane ga duk
a ya yi mace ko namiji kazafi, kuma bai iya
cikakkakun shaiduba, idan ko ya kawo
u da duk abinda Shara'a ke bukata suka
to baza'a kira wannan da sunan kazafiba.
Yiwa mace mumina kazafi bai halattaba
yana cikin abubuwan da suke halakarwa,
da haka dadin fira ko kiyayya kada ta dauki
m ya yiwa wata/wani kazafi ko yasa a yi.
in Da Suka Yi Magana Akan Kazafi: Idan ka
ka kalli ayoyin zaka gansu kashi ukune
duk suna cikin Suratun Nur.
i Na Farko: Ayata: 4-5, Allah Madaukakin
yana cewa: ''Wadanda suke jifan mata masu
nkai (da zina) sannan kuma basu kawo
u huduba to ku yi musu bulala tamanin (80),
kada ku sake karbar shaidarsu har abada,
waddan sune fasiakai. Saidai kawai wadanda
tuba bayan haka kuma suka kyautata to lalle
mai yawan gafarane kuma mai yawan jinkai .''
nan Allah madaukakin sarki ya bayyana
ncin duk mutumin da ya yiwa mace/namiji
fi kuma bai iya kawo shaidu huduba sai
ya bayyana hukuncin da za'a yi masa. Abu
rko bulala tamanin (80), abu na biyu ba za'a
karbar shaidarsaba har'abada, abu na uku
wannan mutumin fasikine. Sai idan ya tuba,
anne malamai suke maganar shin inya tuba
ci gaba da karbar shaidarsa kuma shikenan
a fasiki bane? Amma ko ya tuba sai an yi
i bulala tamanin.
i Na Biyu: Ayoyin da suka yi bayanin
idan da ya yiwa matarshi kazafi kuma bai
awo shaiduba to shi tsinuwa za su yi da
r ta shi, Allah Yana cewa:
''Wadanda kuma suke jifan matansu (da
kuma ya kasance basu da shaidu saidai
kansu, to shaidar dayansu (itace) Rantsuwa
da Allah lalle shi yana cikin masu gaskiya *
tsuwa) ta biyar tsinuwar Allah ta haukanshi in
asance cikin makaryata. * Kuma abinda zai
ayi mata azaba (haddi) shine ta yi Rantsuwa
da Allah cewar lalle shi (mijin) yana cikin
ryata *. (Rantsuwa) ta biyar lalle fushin Allah
bbata akanta in (mijin nata) ya kasance cikin
gaskiya'' Surartun Nur, ayata: 6-8.
Anan Allah madaukakin sarki ya yi bayanin
miji ya yiwa matarshi kazafi kuma bai iya
shaidu huduba to 'Li'ani'' za su yi. Amma
anda ba miji bane to kodai ya kawo sahaidu
ne hudu maza musulmai ko kuma ayi mishi
a tamanin, ba maganar shi wanda aka yiwa
fi wai ya rantse idan ba haka bane, ko kuma
a ya yi kazafin cewa ya rantse duk babu
i shaidu ko bulala tamanin.
Kashi Na Uku: Ayoyin da suka yi Magana
kazafin da aka yiwa mata muminai masu
nkai natsattsu kammalallu to wadannan
yiwa irin wadannan matan kazafi tsine
aka yi duniya da lahira. Allah madaukakin
yana cewa:
''Lalle dukkanini wadanda ke jifan mata
kamun kai gafalallu (daga aikata dukkanin
ha) wadanda suke muminai to an tsine musu
niya da kuma lahira, kuma suna da azaba
irma* Aranar da harsunannu za su bada
a akansu da hannayansu da kuma
uwansu ta sanadiyyar abinda suka kasance
aikatawa* Awannan ranarce Allah zai cika
sakamakonsu na gaskiya, kuma zasu sani
Allah shi wanda yake mai gaskiya kuma mai
anar da abubuwa''. Suratun Nur, ayata: 23-25.
Wannan ya nuna mana shi karankanshi
fin ya kasu kashi-kashi, kashi na farko shine
gama garin mutane wadanda suke suna da
awan halaye da kuma wanda ba'a rasaba,
ka anbaci hukunci yi musu kazafi a kashin
, sai kuma wanda ya kasance tsakanin miji
ata. Sai wannan kashi na uku, wanda mutum
a mace/namiji mai kamun kai mai addini
ttse mumini kawai ya antayo ashar ya
a mata/mashi ya dinga fadan wasu
nganu wanda da za'a tara mishi arzikin
a domin ya kawo shaida akan haka ba zai
. Domin wani ya dauka irin halin da yake
i to kowa haka yake, to kaga bayan ya kasa
wadannan shaidu za'a yi masa hukuncin
fi anan duniya sanna kuma ya jira ranar
ama, domin Allah baya bari a taba bayinsa
warai, Ya Allah ka samu daga cikinsu, ka
u da sharrin masharranta ka tsaremu ka
mana imanimmu, amin.
Kammalawa: Daga takaitattun bayananan
ayyana agaremu yadda musulunci ya dauki
nci da daraja da kima ya karewa kowa
ncinsa musamman 'ya mace, domin idan ba
ba sai kowa ya fadi abinda ya ga dama ko
hi ya fada yana ganin bai huce aci
shiba, amma idan yasan zai sha bulalane to
ya naba'a yasan me zai fada, sai yazama
are mutuncinsa dana zuriyarsa kamar yadda
re mutuncin wani dana ziriyarsa.
Annanne kuma muka zo karshen wannan
a wacce take dauke da sharhin wannan
i da Abu Hurairata ya ruwaito daga wurin
ikin Allah na wadannan abubuwa bakwai
halakarwa, lalle ma'aikin Allah ya isar da
anci kuma tsira da amincin Allah su tabbata
reshi, hakika ta'amuli da wadannan abubuwa
as yana halakarwa kuma wannan kowa ya
ya tabbatar wannan zai kara imanine bisa
i. Akaro na gaba zamu kawo bayanne kuma
nda zasu haskaka mana rayuwarmu da
inmu, Allah ya kaimu wannan lokacin ya
mu da imani, aimn.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna, Jahar Neja Nijeriya.