Wednesday, 19 April 2017

ABUBUWA GUDA ASHIRIN

🌺🌺🌸🌺🌸🌸🌺🌺🌸🌺
```ABUBUWA GUDA (20) DUK WANDA ALLAH YA ALBARKACE SHI DA RAYUWA TARE DA DAYAN MAHAIFANSHI KO DUKAN SU YA KAMATA YA KIYAYE...!!!
🌺🌺🌸🌸🌺🌸🌸🌺🌺🌺

     Dukkan yabo da jin jina da girmamawa sun tabbata ga Allah (S.W.T) wanda ya gwama/hada kadaitashi da biyyaya ga iyaye. Tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta wanda yace “Yardar Allah na tare da yardar iyaye, fushin Allah na tare da fushin iyaye”, da iyalan gidansa da Sahabbansa da wadanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar karshe.

1⃣Yi masu biyayya da da’a ga duk abinda suke so ko suka yi umurni in bai saba ma shari’a ba.

2⃣Nisantar duk abinda zai fusata su ko ya tunzura su.

3⃣Ka tsare mutuncin su da  girmama su a idon jama’a.

4⃣Yi kokari ka yi duk abinda ka san yana faranta ransu koda basu saka ba.

5⃣Ka karba kiransu cikin murmushi, kaje zuwa aikin da suka sanya ka cikin nishadi.

6⃣Kada kayi jayayya dasu ko da a cikin maganar su basu da gaskiya (a maimakon haka ka samu wani lokaci na musamman na lurar dasu kuskuren su a cikin hikima).

7⃣Ka saurare su idan suna Magana kuma kada ka daga masu murya.

8⃣Ka taya su aiki ko da basu neme ka ba.

9⃣Idan dayansu baya da lafiya ka himmatu wajen jinyarsa da kanka.

🔟Bayyana ladabi garesu ko a wurin zama ko tafiya (kada ka saki jiki ko ka mike kafafu ko ka haura sama da su ko kayi tafiya gabansu ta yadda za su ji lallai basu da wani matsayi na girmamawa a gurin ka).

1⃣1⃣Kada ka taba damuwa ko jin ciwon bayyana cewa iyayenka ne (kayi alfahari dasu koda basu da wata daukaka wadda ake kuri da ita).

1⃣2⃣Kada ka bari bukata ta kamasu har su kai ga rokon ka. Ka wadatasu da gwargwado abinda zasu ji dadin rayuwa har su taimaki wani matukar kana da iko.

1⃣3⃣Nuna kulawa da su ta fuskar ziyara koda a wuri daya kuke, idan kuma ba a wuri daya kuke ba to ka ware wani lokaci da zaka rinka tuntubar su, kana samun lokacin fira das u, kana sauraren kokensu da biyan bukatar su.

1⃣4⃣Rinka nuna musu godiya, da cewa duk abinda ka yi musu baka biyasu ba a kan renonka da sukayi.

1⃣5⃣Kada ka bukacesu da abinda basu son baka.

1⃣6⃣Kada ka fifita iyalanka ko ‘ya’yanka akan su.

1⃣7⃣Ka boye masu mafi yawan kyautatawar da ke tsakaninka da iyalanka domin gudun shedan ya sa masu kishi a kan wannan.

1⃣8⃣Idan rashin jituwa ta shiga tsakanin su da iyalinka kada ka taba goyon bayan iyalanka a fili koda su keda gaskiya.

1⃣9⃣Rinka neman addu’arsu kana fada masu bukatunka tare da sanar dasu cewa, addu’arsu tafi  ta kowa kima da saurin karbuwa.

2⃣0⃣Yawaita neman sa albarkarsu a koda yaushe.

COURTESY:
Shababu Ahlissunnah Waljama’ah Tsafe
ZAMFARA STATE
08064607294, 08139348898

P.R.O SHABABUS-SUNNAH TSAFE```

LAA'ILAHA ILALLAH

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*BAYANIN MA'ANAR LAA'ILAHA IL-LALLAHU!!!*
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺

*_001_*

_Rubutawa:_ *Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)*

*بسم الله الرحمن الر حيم*

*الحمد لله رب العالمين، وصلى الله وسلم وبارك على نبينا محمد وعلى آله وصحبه أجمعين.*

```Da farko ya kamata musan cewa ita wannan Kalmar itace ke rabewa tsakanin musulmi da wanda ba musulmi ba!
Wannan Kalmar akan ta aka aiko dukkan Annabawa!
Itace Kalmar dake tabbatar da tsoron Allah na hakika!
Itace igiyar nan mai karfi, wacce duk Wanda ya riketa zata kaishi Aljanna!

Abin lura: Wannan Kalmar ba fadarta a baki ko da halshe tare da jahiltar ma'anarta ke sanya musuluncinka ya inganta ba!

Domin kuwa munafukai suna fadarta a bakunansu, amma kuma Allah yace" suna chan kasan wuta" a suratun nisa'i aya ta 145, tare da cewa suna Sallah suna sadaka, watakila har wurin wa'azi suna halarta.

Abunda ya kamata ga duk wanda ya fadeta, toh ya san ma'anarta har a zuciya ya kudurceta(ma'anarta, sharuddanta, falalarta, da abunda ta kunsa na tauhidi da akeeda) dole ne kaso Kalmar, kaso mai son Kalmar, dole ne ka yaki duk mai adawa da Kalmar ko mai saba mata.

Ita Kalmar LAA'ILAHA- IL-LALLAH! korewa ne da kuma tabbatarwa. Kore ilahantaka ga duk wani wanda ba Allah ba! Koda kuwa Manzo ne, ko Annabi, ko Mala'ika, ko wani mutumin kirki, ko gausi ko waliyyi koma Waye!  Tare da tabbatar da ilahantaka ga Allah shi kadai.

Na daga cikin mas'alolin jahiliyya wanda Annabi Muhammad s.a.w ya saba musu; Bautar mutanen kwarai ta Hanyar Neman biyan bukatunsu da nufin su nema musu ceto a wurin Allah, saboda zatonsu akan cewa Allah na son hakan. Kamar yadda Allah s.w.t yake cewa;
*ويعبدون من دون الله ما لا يضرهم ولا ينفعهم ويقولون هؤلاء شفعؤنا عند الله.* {يونس ١٨}

Ma'ana: "Suna bautar wani wanda ba Allah ba, Wanda bai iya cutar dasu, kuma bai iya amfanar dasu, har ma zakuji suna fada cewa wadancan sune masu cetonmu a wurin Allah"

Wannan ayar in muka lura zatayi aiki ga masu Dariku da yan shi'ah! Saboda suma zakuji suna fadar irin wadannan kalmomin, bari ma, wani lokaci nasu sunfi muni da hadari.

Muna rokon Allah s.w.t ya tabbatar damu akan tauhidi da akeeda Allah ka kara mana Ikhlasi.

Wannan mukaddima ce, amma bayanin zaizo a fitowa ta gaba insha Allahu.

Copyright©
Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)
08064734911```

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???

🌺🍇🍏🌹🌷🌼🌸💐🌺
*AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???*
🌺💐🌸🌼🍇🌷🌹🍏🌺

(001)

Rubutawa: *_Hashim Siraj Uba atstsamawy(ABU SINÃN)_*

بسم الله الرحمن الر حيم

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya chanchanci a bauta masa shi kadai kuma ya hanemu da shirkah, Tsira da Aminci su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad S.A.W wanda ya tsoratar damu daga aikata bidi'ah.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda ganin ya dace mu faɗakar da yan'uwa musamman iyaye da kakanni da ake zalunta da hadisan ƙarya dangane da falalar watan Rajab.

Da farko dai shi watan Rajab yana ɗaya daga cikin watanni masu alfarma wanda aya ta 36 a Suratu taubah tayi bayani.

✏✏✏✏✏✏✏✏
MAGANGANUN MAGABATA AKAN AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI)
✏✏✏✏✏✏✏✏

kai tsaye yanzu ga Wata tambaya da akayi ma Sheikh bin Baaz(R.H) dangane da azumin Rajab(azumin tsofaffi).

An tambayi Sheikh bin Baaz(R.H) akan cewa shin ko yana halatta azumtar watan Rajab (AZUMIN TSOFAFFI) gaba ɗayansa? Domin wasu Malamai suna faɗar cewa: duk wanda ya azumci Rajab, an gafarta mashi zunubbansa koda sun kai yawan kumfar teku, wasu kuma malaman sunyi hani da azumtar watan suna cewa; duk da zamanshi cikin watanni masu alfarma baya halatta a azumce shi baki ɗaya???

Ga amsar da bin Baaz ya bada, yana cewa; " Abun sani kawai shine ba'a shar'anta azumtar watan Rajab ba! Bari ma an karhantashi, abunda ya tabbata shine an shar'anta azumin sha'aban, Manzon Allah S.A.W ya kasance yana yin azumin sha'aban, yana azumtar sha'aban sai kaɗan yake ragewa(Ma'ana, ya a yawaita azumi a Sha'aban), amma Rajab an karhanta yin azumi a cikinsa, azumi a cikinsa yana daga cikin aikin jahiliyya, saboda masu azumtar basu da dalilin azumtar watan!!! 

Hadisan da ake yawo dasu akan falalar watan Rajab basu da asali, bari ma na ƙarya ne waɗanda basu inganta ba, abinda shari'ah ta shar'anta ga musulmai shine suci susha a watan Rajab, sai dai idan ya kasance kana yin azumin nafila tun kafin zuwan watan Rajab wanda su dama shari'ah ta tabbatar dasu, kamar; litinin da Alhamis, Ayyamul-beed da sauransu, wannan yana da kyau kuma babu laifi, amma azumtar watan gaba ɗayansa, ko kuma baka saba yin azumin nafila ba sai da watan ya shigo sai ka fake da azumin nafila ka gabatar da na Rajab wannan shari'ah bata yadda dashi ba.


Wannan itace amsar da sheikh bin Baaz ya bada dangane da azumin tsofaffi na Rajab.

Hadisi ya tabbata daga Aisha matar Annabi Muhammad s.a.w tana cewa:

كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يصوم حتى نقول لايفطر، ويفطر حتى نقول لايصوم، وما رأيته أكثر صياما منه في شعبان.
[صحيح أخرجه البحاري(١٩٦٩)، و مسلم(١١٥٦)].

Ma'ana; Aisha R.A take cewa; "Manzon Allah S.A.W ya kasance yana yin azumi har sai mun ce baya cin abinci! Yana cin abinci har sai munce baya yin azumi(ma'ana yana yin azumi da yawa, haka kuma yana aje azumi ya huta sosai), ban taɓa ganin Manzon Allah S.A.W yana cika azumin wata daya ba sai dai idan ramadhan ne, ban taba ganin watan da yafi azumi a cikinsa ba face sha'aban

[Bukhari da Muslim]

Haka nan Sheikul Islam yqna cewa

ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ " ‏( 25/290 ‏) :
" ﻭﺃﻣﺎ ﺻﻮﻡ ﺭﺟﺐ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ﻓﺄﺣﺎﺩﻳﺜﻪ ﻛﻠﻬﺎ
ﺿﻌﻴﻔﺔ ، ﺑﻞ ﻣﻮﺿﻮﻋﺔ ، ﻻ ﻳﻌﺘﻤﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻋﻠﻰ
ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻬﺎ ، ﻭﻟﻴﺴﺖ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﺮﻭﻯ ﻓﻲ
ﺍﻟﻔﻀﺎﺋﻞ ، ﺑﻞ ﻋﺎﻣﺘﻬﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﺿﻮﻋﺎﺕ ﺍﻟﻤﻜﺬﻭﺑﺎﺕ...

Shaikhul Islam Ibn taimiyyah (RH) y
ace: “Kebance watan rajab da yin azumi,
dukkan hadisan
da su ka zo akan haka da’ifai ne (masu
rauni), bari
ma hadisan karya ne, masu ilimi
basu amfani dasu, domin basu
cikin hadisan
da ake amfani dasu don nuna falalar
aikata abu,  bari ma dukkan su ma
hadisai ne
na karya..”
Duba Majmu’u Fatawa (25/290).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :
" ﻛﻞ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻲ ﺫﻛﺮ ﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻭﺻﻼﺓ ﺑﻌﺾ
ﺍﻟﻠﻴﺎﻟﻲ ﻓﻴﻪ ﻓﻬﻮ ﻛﺬﺏ ﻣﻔﺘﺮﻯ " ﺍﻧﺘﻬﻰ ﻣﻦ " ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ
ﺍﻟﻤﻨﻴﻒ " ‏(ﺹ 96 ‏)

Imam Ibnul Qaiyim (RH) y ace;
“Dukkan hadisan
da suka ambaci azumin watan rajab da
sallatar wasu
darare a cikin sa, hadisai ne na karya kuma
kirkirarru”.
Duba Almanarul Muniif (shafi 96).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺤﺎﻓﻆ ﺍﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﻓﻲ " ﺗﺒﻴﻴﻦ
ﺍﻟﻌﺠﺐ " ‏(ﺹ 11 ‏) :
" ﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ ﻓﻀﻞ ﺷﻬﺮ ﺭﺟﺐ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﺻﻴﺎﻣﻪ
ﻭﻻ ﺻﻴﺎﻡ ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻪ ﻣﻌﻴﻦ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺔ
ﻣﺨﺼﻮﺻﺔ ﻓﻴﻪ ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ﻳﺼﻠﺢ ﻟﻠﺤﺠﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ.

Alhafiz Ibn Hajar Al-Asqalani yake
cewa; “Babu
wani abu da aka ruwaito na falalar
watan Rajab,
ko yin azumi a cikin sa, ko azumtar
wasu adadin
kwanaki ayyanannu, ko tsayuwar
wasu darare
kebantattu”.
Duba Tabyinul Ajab (shafi 11).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺳﻴﺪ ﺳﺎﺑﻖ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ " ﻓﻘﻪ
ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 1/383 ‏) :
" ﻭﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻟﻴﺲ ﻟﻪ ﻓﻀﻞ ﺯﺍﺋﺪ ﻋﻠﻰ ﻏﻴﺮﻩ ﻣﻦ
ﺍﻟﺸﻬﻮﺭ , ﺇﻻ ﺃﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻷﺷﻬﺮ ﺍﻟﺤﺮﻡ , ﻭﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ
ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺃﻥ ﻟﻠﺼﻴﺎﻡ ﻓﻀﻴﻠﺔ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ,
ﻭﺃﻥ ﻣﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻤﺎ ﻻ ﻳﻨﺘﻬﺾ ﻟﻼﺣﺘﺠﺎﺝ ﺑﻪ
" ﺍﻧﺘﻬﻰ

Imam Sayyid Sabiq (RA) yake cewa;
“Azumin
watan rajab bashi da wani fifiko na
falala akan
waninsa cikin watanni, sai dai shi
yana daga cikin
watanni (guda hudu) ma su alfarma,
kuma ba a
samu a cikin sunnah ingatacciya ba cewa
yin azumi a
cikin sa yana da falala kebantacciya,
abunda ya zo
akan haka (ma’ana hadisan da suka
zo) ba a kafa
hujja dasu (domin da’ifai ne)”
Duba Fiqhus-Sunnah (1/383).

ﻭﺳﺌﻞ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻦ ﺻﻴﺎﻡ
ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﻭﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺘﻪ .
ﻓﺄﺟﺎﺏ :
" ﺻﻴﺎﻡ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ
ﻟﻴﻠﺘﻪ ﻭﺗﺨﺼﻴﺺ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺔ , ﻭﻛﻞ ﺑﺪﻋﺔ ﺿﻼﻟﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ " ‏( 20/440 ‏)

An tambayi sheikh Muhammad Salihul Usaimeen
(RH)
dangane da azumi ranar 27 ga watan
rajab da
kuma tsayuwar dararen sa.
Sai ya amsa da cewa:
“Yin azumi ranar 27 ga watan Rajab
da tsayuwar
darensa kebance shi da haka bidi’a
ne, dukkan
bidi’a kuma batace”
Duba Majmu’u fatawa na Usaimeen
(20/440).

   Haka zalika Sayyidina umar R.A ya kasance yana bulala akan wadanda ke kamewa akan azumin Rajab, yana ce musu kuci abinci, wannan watane da ya kasance ake girmamawa a lokacin jahiliyya. [Ibn Abi shaibah ya fitar 3/102] da ibn kathir a cikin musnadil- faruk 1/285]

Haka zalika ibn umar R.A ya kasance idan yaga mutane suna wuce gona da iri akan Rajab, yana kyamar hakan!
[Sahih: ibn abi shaibah ya fitar 3/102]

Ibn Abbas ya kasance yana hani akan azumin Rajab gaba dayansa, saboda kada a maida shi ya zama abunda za'a rinka yi duk shekara, wato a maidashi ya zama idi.
[Sahih; Abdulrazak ya fitar 7854].

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISAN DA SUKA INGANTA AKAN WATAN RAJAB!
✏✏✏✏✏✏✏✏
=  "kuyi axumi a cikinshi kuma kuci abinci a cikinshi.
[Sahih irwa'ul galeel 958]

= Sha'aban yana tsakanin Rajab da Ramadhan, ana shagaltar da mutane akanshi(domin samun saukin Ramadan) a cikin sha'aban ake daukar ayukkan bayi, ina kwadayin/inason kada a daga ayyukana face ina azumi.
[Isnadinsa mai kyau ne, silsilatus-sahiha 1898]

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISSAI DA'IFAI WADANDA MASU AZUMIN RAJAB KE KAFA HUJJA DASU.!!!
✏✏✏✏✏✏✏✏

= A cikin Aljanna akwai wani gulbi, ana kiransa Rajab, ruwansa suna da fari wanda farin yafi na nono, duk wanda yayi azumin Rajab na rana daya, Allah zai shayar dashi daga wannan gulbin.[Silsilatu-dha'ifah 1898]

= Rajab watan Allah, Sha'aban wata na(manzon Allah), Ramadan watan Al'umma ta.
Da'ifi ne, silsilatu-dha'ifah 4400]

= Darare guda biyar ba'a maida Addu'ah: 1. Farkon Daren Rajab. 2. Daren Rabin watan sha'aban. 3. Daren jumu'ah.  4. Daren karamar sallah. 5. Daren babbar sallah.
[Maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 1452]

= Rajab watane mai girma, Allah na lunka lada idan kayi aikin Alkhairi a cikinsa, duk wanda yayi azumin Rajab na kwana daya,kamar yayi azumin shekara. Duk wanda yayi na kwana bakwai, za'a rufe mashi kofofin wutar jahannama bakwai. wanda yayi na kwana takwas, za'a bude mashi kofofin Aljanna takwas. Wanda yayi na kwana sha biyar, mai kira zaiyi kira a sama yace; an gafarta maka abunda ya gabata na laifuka...[maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 5413]

✏✏✏✏✏✏✏✏
RUBABBUN HADISSAN DA YAN SHI'AH KE KAFA HUJJA DASU AKAN FALALAR WATAN RAJAB.
✏✏✏✏✏✏✏✏
Daga Baban hassan (A.S) yace; Annabi Nuhu (A.S) ya tuka jirgin ruwa a farkon watan Rajab, sai ya umurci wadanda ke tare dashi da su azumci wannan ranar, yace; "duk wanda ya azumci wannan ranar Allah zai nisanta shi da wuta na tsawon tafiyar shekara daya.

=Daga Abi Ja'afar, Muhammad ibn Aliyu(A.S) yace; duk wanda yayi azumi a Rajab na rana daya, a farkon Rajab ko tsakiyarsa ko karshensa, Allah ya wajabta mashi shiga Aljanna, kuma Allah zai sanya shi a tare damu a cikin darajojinmu na Ahlul baiti a ranar kiyama, wanda yayi na kwana biyu, Allah zai gafarta mashi duk zunubbanshi da suka gabata, wanda yayi na kwana uku, Allah zai gafarta mashi abunda ya gabatar na zunubi da wanda zaiyi a gaba sannan za'a bashi damar ceton yan uwanshi ma'abota zunubi...

= As-sadik Ja'afar  ibn Muhammad yace; "kada ka bari ranar ashirin da bakwai ga Rajab ta wuce ba tare da ka azumceta ba! Domin a ranar ne aka saukar wa Annabi Muhammad s.a.w Annabta...

Duka wadannan zaka samesu a cikin littafi mai suna FALALAR WATANNI UKU, wanda gingimemen malamin Shi'ah mai suna MUHAMMAD IBN ALIYU IBN HUSSAIN IBN MUSA AL-QUMMY ya rubuta.
Allah ka la'anci qummy.

  A takaice wadannan sune hujjoji na dangane da rashin ingancin azumin Rajab(azumin tsofaffi), duk wanda yake ganin akwai Gyara matukar gyaran nashi ya inganta hadisi ne ko aya ina maraba dashi kwarai da gaske.

Allah ya hadamu dani daku da sauran musulmai a cikin Aljannah.

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH...```


Copyright©
Dalibinku
*_Hashim Suraj Uba Tsamiya {ABU SINÃN}_*
☎08064734911
📞09030201868

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

17-07-1438AH
15-04-2017AC

Wednesday, 5 April 2017

لا إله إلا الله

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*BAYANIN MA'ANAR LAA'ILAHA IL-LALLAHU!!!*
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺

*_001_*

_Rubutawa:_ *Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)*

*بسم الله الرحمن الر حيم*

*الحمد لله رب العالمين، وصلى الله وسلم وبارك على نبينا محمد وعلى آله وصحبه أجمعين.*

```Da farko ya kamata musan cewa ita wannan Kalmar itace ke rabewa tsakanin musulmi da wanda ba musulmi ba!
Wannan Kalmar akan ta aka aiko dukkan Annabawa!
Itace Kalmar dake tabbatar da tsoron Allah na hakika!
Itace igiyar nan mai karfi, wacce duk Wanda ya riketa zata kaishi Aljanna!

Abin lura: Wannan Kalmar ba fadarta a baki ko da halshe tare da jahiltar ma'anarta ke sanya musuluncinka ya inganta ba!

Domin kuwa munafukai suna fadarta a bakunansu, amma kuma Allah yace" suna chan kasan wuta" a suratun nisa'i aya ta 145, tare da cewa suna Sallah suna sadaka, watakila har wurin wa'azi suna halarta.

Abunda ya kamata ga duk wanda ya fadeta, toh ya san ma'anarta har a zuciya ya kudurceta(ma'anarta, sharuddanta, falalarta, da abunda ta kunsa na tauhidi da akeeda) dole ne kaso Kalmar, kaso mai son Kalmar, dole ne ka yaki duk mai adawa da Kalmar ko mai saba mata.

Ita Kalmar LAA'ILAHA- IL-LALLAH! korewa ne da kuma tabbatarwa. Kore ilahantaka ga duk wani wanda ba Allah ba! Koda kuwa Manzo ne, ko Annabi, ko Mala'ika, ko wani mutumin kirki, ko gausi ko waliyyi koma Waye!  Tare da tabbatar da ilahantaka ga Allah shi kadai.

Na daga cikin mas'alolin jahiliyya wanda Annabi Muhammad s.a.w ya saba musu; Bautar mutanen kwarai ta Hanyar Neman biyan bukatunsu da nufin su nema musu ceto a wurin Allah, saboda zatonsu akan cewa Allah na son hakan. Kamar yadda Allah s.w.t yake cewa;
*ويعبدون من دون الله ما لا يضرهم ولا ينفعهم ويقولون هؤلاء شفعؤنا عند الله.* {يونس ١٨}

Ma'ana: "Suna bautar wani wanda ba Allah ba, Wanda bai iya cutar dasu, kuma bai iya amfanar dasu, har ma zakuji suna fada cewa wadancan sune masu cetonmu a wurin Allah"

Wannan ayar in muka lura zatayi aiki ga masu Dariku da yan shi'ah! Saboda suma zakuji suna fadar irin wadannan kalmomin, bari ma, wani lokaci nasu sunfi muni da hadari.

Muna rokon Allah s.w.t ya tabbatar damu akan tauhidi da akeeda Allah ka kara mana Ikhlasi.

Wannan mukaddima ce, amma bayanin zaizo a fitowa ta gaba insha Allahu.

Copyright©
Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)
08064734911```

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

Thursday, 30 March 2017

QARYA ADON YAN SHI'AH

*'KARYA ADDININ YAN SHI'AH!!!*
**

**

**
```Don haka ne ibn Taimiyya a cikin minhajis-sunnah 1/59 yake cewa; Malamai ma'abota ilimi sunyi ittafaki(sun hadu) akan hakaitowa da ruwayoyi da isnadi akan cewa yan Shi'ah(Rafidhawa) makaryata ne na gaske, kuma karya a wajensu dadadden abune ba wai yau suka fara ba.
Haka shima ABU HATIM-ARRAZY yake cewa naji yunus ibn Abdul-a'ala yana cewa; Ash-hab ibn Abdul-aziz  yace: An tambayi IMAMU MALIK akan yan shi'ah? Sai IMAMU MALIK yace; kada kuyi magana dasu! Kada Ku  ruwaito magana ko wani Abu da zai amfani Al'umma daga garesu! Domin su makaryata ne.

Wannan kuwa kowa na iya gasgata hakan a wannan zamani da muke ciki

((YAA KU WADANDA SUKAYI IMANI, KU KARE KAWUNANKU DA IYALANKU DAGA WUTA! WACCE MAKAMASHINTA MUTANE DA DUWATSU))

Allah ka  kare musulmai daga makirci da sharrin yan Shi'ah a duk inda suke```

Copyright©
*Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINÃN)*
📞08064734911☎

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

QARYA ADON YAN SHI'AH

*'KARYA ADDININ YAN SHI'AH!!!*
**

**

**
```Don haka ne ibn Taimiyya a cikin minhajis-sunnah 1/59 yake cewa; Malamai ma'abota ilimi sunyi ittafaki(sun hadu) akan hakaitowa da ruwayoyi da isnadi akan cewa yan Shi'ah(Rafidhawa) makaryata ne na gaske, kuma karya a wajensu dadadden abune ba wai yau suka fara ba.
Haka shima ABU HATIM-ARRAZY yake cewa naji yunus ibn Abdul-a'ala yana cewa; Ash-hab ibn Abdul-aziz  yace: An tambayi IMAMU MALIK akan yan shi'ah? Sai IMAMU MALIK yace; kada kuyi magana dasu! Kada Ku  ruwaito magana ko wani Abu da zai amfani Al'umma daga garesu! Domin su makaryata ne.

Wannan kuwa kowa na iya gasgata hakan a wannan zamani da muke ciki

((YAA KU WADANDA SUKAYI IMANI, KU KARE KAWUNANKU DA IYALANKU DAGA WUTA! WACCE MAKAMASHINTA MUTANE DA DUWATSU))

Allah ka  kare musulmai daga makirci da sharrin yan Shi'ah a duk inda suke```

Copyright©
*Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINÃN)*
📞08064734911☎

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

Wednesday, 29 March 2017

WATAN RAJAB

```WATAN RAJAB

Watan da yan bidi'ah ke sheke ayarsu da rudar jahillai akan azumtar watan gaba daya ko kuma wasu kwanaki na cikin watan.
Irin wannan lokaci ya shigo ace bamu Dan shafa Kansu ba munyi kuskure.
Saboda haka Ku sauraremu bayanan Malamai zaizo akan watan Rajab da bidi'o'in da yan bidi'ah suka kirkira akan watan.

Kudai cigaba da kasance da ABBAN SINAAN a shafukan Sada zumunta na Facebook;
Hashim surajo uba Tsamiya.
Watsapp;
08064734911```

http://abbansinan.WordPress.com
http://hashimtsamiya.blogspot.com
http://abusinan.blogspot.com
atstsamawy@gmail.com