Wednesday, 7 December 2016

IBN TAIMIYYA BAI YARDA DA MAULIDI BA, HASALI YAYI FADA DA ITA...

🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴
*_IBN TAIMIYYA BAI YARDA DA BIDI'AR MAULIDI BA, HASALI MA YAYI FA'DA DA ITA_*
🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳

_001 Fitowa Na daya_

_Rubutawa:_ *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

بسم الله الر حمن الر حيم

```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai, Tsira da amincin Allah su tabbata ga Wanda babu wani Annabi bayansa, tare da iyalan gidansa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka;
Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda Wata 'karya dake yawo a kafofin sadarwa na zamani(social medias) akan cewa ibn taimiyya yace Maulidi halas ne, har ma yace akwai lada ga Wanda yayi. Maganar wacce suke sama mata gindin zama a cikin littafin shehin Malamin mai suna((I'KTIDA'UL SIRA'DUL MUSTAQEEM)).
Kafin bada amsa ga maganar ya kamata masu karatu kusan cewa Malamai ba ma'asumai bane! Suna dai dai suna kuskure.
Amma ga wata magana ta ibn Taimiyya akan maulidi;```
قال ابن تيمية-رحمه الله- ((فإن هذا [يعنى الإحتفال بالمولد] لم يفعله السلف مع قيام المقتضى له وعدم المانع منه، ولو كان هذا خير محضا أو راجحا لكان السلف رضي الله عنهم أحق به منا، فإنهم كانوا أشد محبة لرسول الله صلى الله عليه وسلم وتعظيما له منا، وهم على الخير أحرص، وإنما كمال محبته ةتعظيمه في متابعته، وطاعته واتباع أمره، وإحياء سنته باطنا وظاهرا، ونشر ما بعث به، والجهاد على ذلك بالقلب واليد واللسان، فإن هذه هي طريقة السابقين الأولين من المهاجرين والأنصار والذين اتبعوهم بإحسان...))    {اقتضاء صراط المستقيم ص ٣٥٠ دار ابن الهثيم}

_Ma'ana;_ *_"Ibn Taimiyya -Allah yayi masa Rahama- a cikin littafinsa [Iktida'ul siradul mustakim] yana cewa; Lallai wannan (Bukin maulidi) magabata basu aikatashi ba tare da suna da damar yin hakan kuma babu abunda zai hanasu, da wani aikin Alkhairi ne babba ko kuma mafi rinjaye da magabata-Allah ya yarda dasu- su sukafi cancanta  su aikatashi fiye damu, domin sun fimu son Annabi Muhammad Tsira da Aminci SU tabbata a gareshi da girmamashi kuma sun fi mu kwadayi ga Alkhairi, to amma abin da ke cikakken so da girmamawa ga Annabi shine bin sunnarsa, da yi masa biyayya da bin umurninsa da rayar da sunnarsa a boye da bayyane da kuma watsa abin da aka aikoshi dashi da kuma yin kokarin yadashi da Alkalami da hannu da kuma halshe, kuma wannan shine tafarkin wadanda suka gabacemu daga cikin muhajiruna da Ansar da wadanda suka bisu da kyautatawa._* [Iktida'u siradul mustakim shafi na 350]

   ```wannan shine abin da sheikhul Islam Allah yayi masa rahama ya fada game da bukin maulidi, kuma wannan karara yake cewa bidi'ah ne daga cikin bidi'o'i, Wanda yasa dole muyi yaki dashi.
   Sai dai yan bidi'ah saboda son rai da son zuciya sun bar wannan magana dake nuna cewa maulidi bidi'ah ne, sunyi riko da Abinda yayi dai dai da son rayuwarsu, kamar yadda dama wannan shine Al'adarsu Qur'an ma yayi bayani a cikin suratul [Ali imran aya ta 7]  daman su mutane ne masu son shubuha.
Su kuwa Ahlis Sunnah ba haka suke ba. Imamul wa'ki'i ibn jarrah yake cewa;```
((أهل السنة يكتبون مالهم وما عليهم، وأهل الأهواء يكتبون مالهم)).
[ذم الكلام للهروي ٣٣٨]

_Ma'ana;_ *_"Ahlus sunnah suna rubuta abinda yake hujja a garesu da Wanda yake hujja akansu, amma masu bin son zuciya (YAN BIDI'AH) suna rubuta abinda yake hujja garesu kawai._* [Zammul kalam 338]

```wannan rubutu zai zamo shimfida na warware wannan shubuha, fitowa ta gaba zanyi bayani akan maganar da ibn taimiyya ya fada wanda yan bidi'ah suke ganin cewa hujja ne garesu.
Allah ya karemu daga bin son zuciya da watsi da sunnar Manzon Allah, Allah ya tabbatar da dugaduganmu akan bin sunnah da aiki da sunnah.```


Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*
Https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya
📞08064734911
Http://hashimtsamiya.blogspot.com
atstsamawy@gmail.com

KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD S.A.W KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???

🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD S.A.W KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???*
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺

  _Fitowa ta biyu (002)_

     _Rubutawa;_ *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

*Godiya ta tabbata ga Allah Tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah s.a.w da mutanen gidansa da sahabbansa da duk Wanda yabi tafarkinsa da kyautatawa har tashin kiyama.*

_Bayan haka;_

_Nayi rubutu mai irin wannan take Wanda nace fitowa na gaba yana nan zuwa, to kuma insha Allahu zan cigaba da bada hujja akan haramcin Maulidi da kuma zamanshi bidi'ah abar kyama.  Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi huduba bayan ya godewa Allah, ya nemi taimakonshi da gafararshi daga karshe sai yace;_
(( أما بعد، فإن خير الحديث كتاب الله وخير الهدي هدي محمد صلى الله عليه وسلم وشر الأمور محدثاتها وكل بدعة ضلالة)).

_Ma'ana;_ *_"Bayan haka; Lallai fiyayyen zance shine littafin Allah, kuma fiyayyar shiriya ita ce shiriyar Muhammad s.a.w, kuma mafi sharrin al'amurra sune wadanda aka kirkiro, kuma dukkan bidi'ah bata ce"_* [Muslim ya ruwaito]

```Bayan wannan; yana daga cikin abunda yasa Malamai suka kyamaci bidi'ar Maulidi; bayan zamanshi bidi'ah, akwai haduwa mata da maza da wake wake da amfani da kayan kid'a (Badujala, piano,...) Da shaye shayen abubuwan dake sa maye, da wasu sharrance sharrance, wani lokaci Abunda yafi wadancan yana faruwa, wato shirka da Allah, ta hanyar wuce gona da iri wajen yabon Manzon Allah s.a.w ko waninsa kamar; Tijjani, Inyassi, jelani, Mahadi, Hussain,  yaa Ali, ko waliyi na wheelbarrow. Za kaga ana Addu'ah ana Neman agajinsu da taimakonsu ko fadar cewa Annabi Muhammad s.a.w yasan gaibi ko wani daga cikin waliyyai, wadannan abubuwa duk zaka samu suna faruwa a wajen Maulidi. Shi kuwa Annabin Rahama s.a.w cewa yayi;```
((إياكم والغلو في الدين، فإنما أهلك من كان قبلكم الغلو في الدين)).

_Ma'ana;_ *_"Ku kiyayi yin shishshigi a cikin Addini, saboda babu wani Abu Wanda ya hallaka wadanda suka gabace ku face shishshigi a cikin addini._*

A wani Hadisin Manzon Allah s.a.w cewa yayi;
((لاتطروني كما أطرت النصاري ابن مريم إنما أنا عبد فقولوا: عبدالله ورسوله))

_Ma'ana;_ *_"Kada Ku zurfafa wajen yabo gareni kamar yadda kiristoci suka zurfafa wajen yabo ga Dan Maryam(Annabi isah) ni bawa ne kawai, saboda haka kuce; bawan Allah kuma manzon Allah._* [Bukhari ya ruwaito]

```Abin mamaki shine zaka samu da yawa daga cikin mutane suna kokari wajen halartar wadannan tarurrukan na bidi'ah, kuma suna kare masu yinsu, amma kuma sai kaga basa halartar wuraren Neman ilimi, Inda za'a nuna maka yadda zakabi Allah da Manzonsa ba inda za'a nuna maka falalar karya ta waliyyan karya ba. Babu shakka wannan yana daga cikin raunin imani da kuma karancin basira, kuma yana nuna cewa tsatsa ta rufe zukatansu ta nau'o'in zunubai da sabon Allah.

    Allah ya karemu daga fadawa cikin shirka da bidi'ah da bata.

     SUNNAH SAK

             BIDI'AH SAM

   MAULIDI SAM SAM SAN SAM SAM

Wa'ka:

DA MAULIDI NE ALAMAR SON MANZO

     DAN FODIO DA BA ZAYA CE MAR BIDI'AH BA.```

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*
📞08064734911📞
Https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

Http://hashimtsamiya.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

Monday, 5 December 2016

ANYA KUNASON HUSSAINI???

*ANYA KUNASON HUSSAINI???*

```gaskiya wannan munafunci ne karara!
Shin wai goma ga Wata aka kashe Hussain ko Ashirin ga Wata???

Anya kunason shahada???

Anya kunason Hussaini???

Tsoron me ya hanaku fitowa a ranar goma ga Wata sai yau ashirin ga Wata???

Ko kuna tsoron Ayi fatahu Tsafe ne???

Meyasa kukayi shi tun da safe, sabanin lokuttan baya sai anyi la'asar???

Kunji kunya! Kunji kunya!! Kunji kunya!!!

Allah ya kyauta```

ALHAMDULILLAH.

*ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!!*

```A madadin kwamitin SHABABU AHLIS SUNNAH WALJAMA'AH TSAFE, muna farin cikin sanar daku cewa Mai gida kuma babban malaminmu, patron na wannan kwamiti, wato Sheikh Musa s lawal Tsafe (Abu salih ibn salih) ya samu nasarar lashe jarabawar karo karatu a jami'ar musulunci dake jamhuriyar Niger(digiri na biyu), muna taya Malam da sauran Abokanshi guda hudu murnar lashe wannan jarabawar.  Allah yasa ayo karatu mai amfani Wanda za'azo a cigaba da kwarara manashi a kwakwalenmu har sai mun fara tunbudinshi.

Hashim Surajo Uba Tsamiya ```

SUWAYE AKA KASHE TARE DA HUSSAINI A CIKIN AHLUL BAITI ALLAH YA YARDA DASU.???

*SUWAYE AKA KASHE TARE DA HUSSAINI A CIKIN AHLUL BAITI ALLAH YA YARDA DASU???*

*من قتل مع الحسين من أهل البيت رضي الله عنهم؟؟؟*

*_Yana daga cikin Abunda zakuji yan shi'ah na fada cewa suna son Ahlul baiti! Toh amma Sayyidina Hussain shikadai ne Ahlul baiti??? Sauran Yayan sayyidina Aliyu su ba Ahlul baiti bane???_*

```yana daga cikin soyayyar sayidina Aliyu ga khalifofin da suka gaba ce shi, sanya ma yayanshi sunayensu. Duk Wanda ya sanya ma dan shi sunanka soyayya ne yasa hakan ko gaba???
Daga cikin sunayen yayan sayyidina Aliyu da kuma yayan Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib wadanda aka kashe tare da Hussaini akwai;
√ Abubakar ibn Aliyu ibn Abi dalib! An kasheshi tare da Hussaini a karbala'a. Kai Dan shi'ah ka duba wannan littafi domin ka ganewa idonka; (Muntahal Amãl,1/528) zaka samu cikakken bayani.

√ Umar ibn Aliyu ibn Abi dalib! Shima ya samu shahada a Karbala'a tare da Sayyidina Hussaini. Ka duba littafin (kashful gummah, 1/440)

√ Usman ibn Aliyu ibn  Abi dalib! Shima ya zama shaheedi a karbala'a ka duba littafin (muntahal Amãl, 1/526-527)

Daga cikin wadanda suka samu shahada a Karbala'a akwai yayan sayyidina Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib, daga ciki akwai;

√ Abubakar ibn Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib! Ka duba cikin(Al-irshãd shafi na 186-248 ko kashful gumma, 1/575-580).

√ Umar ibn Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib! Shima Allah ya bashi shahada a karbala'a. Ka duba cikin(Mazãlimu Ahlul baiti, 254 ko i'ilamul wara, 112).

  Wadannan duk suna cikin Ahlul baiti Rasulul-llah, amma da yake Addinin shi'anci an ginashi ne akan karya da yaudara da siyasa. Sai kaji suna Ambaton sunan Hussaini kadai a matsayin Wanda ya samu shahada a Karbala'a. Saboda gabarsu da kiyayyarsu da masu wadannan sunaye!

Kurtugin shi'ah na Tsafe ina mai tabbatar maka cewa; matukar zaka rika gaba da Abubakar! Toh sai ka chanja sunan Uba!
Allah yayi mana tsari da jahilcin yan shi'ah da suke fama dashi, jahillan cikinsu kuma Allah ya cetosu.```

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya_*

SUNNAH NE YIN SALLAH DA TAKALMI

🔈🔉🔊🔈🔉🔊🔈
*SUNNAH NE YIN SALLAH DA TAKALMI, DAGA GROUPS DIN MUKYAUTATA NIYYA!!!*
📣📣📣📣📣📣📣

*Rubutawa:* *_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)_*

*Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa, muna Neman gafararSa, muna Neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, Wanda Allah ya shiryar babu mai iya batar dashi Wanda kuma ya batar babu mai iya shiryar dashi, kuma ina shaidawa babu abin bauta bisa cancanta sai Allah kuma ina shaidawa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne, yabo da godiya sun tabbata ga fiyayyen halitta Wanda  yace Wanda yayi mashi da'a Dan Aljanna ne, Wanda ya saba mashi Dan wuta ne!*
_Bayan haka:_

*وعن أبى سعيد رضى الله عنه قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: "إذا جاء أحدكم المسجد، فلينظر، فإن رأى فى نعليه أذى أو قذرا فليمسحه، وليصل فيهما.*
(أخرجه أبو داود، وصححه ابن خزيمة).

```Hadisi ya tabbata daga Abi sa'id(R.A) yace, Annabi Muhammad s.a.w yace: idan dayanku yayi Nufin zuwa Masallaci to ya duba idan yaga datti ko Wata 'kazanta a takalminshi, to ya goge sannan yayi SALLAH a cikinsu.```

Yan uwa mu lura, Manzon Allah s.a.w cewa yayi: *MU DUBA IDAN MUKA GA WANI DATTI KO KAZANTA MU GOGE MUYI SALLAH A CIKINSU!*  kuma hadisi ingantacce Wanda Abu daud ya fitar a cikin littafinshi kuma ibn khuzaima ya ingantashi. Imamu Nasirudden bn Albany ya ingantashi.
*Imamu Ahmad(imamu Ahlis sunnah waljama'ah) yake cewa: " من رد حديث رسول الله صلى الله عليه وسلم فهو شفا هلكة*
```Ma'ana: Duk Wanda za'ace ga Hadisi ingantacce amma ya tsaya jayayya yana son raddi ga Hadisin, imamu Ahmad yace yana gefen Halaka!

Ma'abota cewa ba'a SALLAH da takalmi ko zaku bamu hujjarku???``` 

*ABU SINAN* ```na jiran yaji rubabbun hujjojinku. Domin yasan inda kuka dogara.```

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*

Http://Hashim141473.mywapblog.com

ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBU BA...!!! 001

*ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAI SAN GAIBU BA...!!!*

*_Fitowa ta daya(01)_*

*_DAGA; Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*
*بسم الله الرحمن الرحيم*

  ```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda baya da Abokin tarayya. Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga farin jekada   Wanda babu wani Annabi bayansa,Annabi Muhammad s.a.w tare da jama'ar gidansa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan takaitaccen rubutu saboda ganin yadda wasu yan bidi'ah ke cusa ma kananan yara Akeedar cewa Annabi yasan gaibu a makarantunsu Na Zawuyya da sauran Majami'oinsu.
Zan takaitu insha Allahu akan Qur'ani da hadisai ingantattu, saboda kada in kawo maganar wani malami na sunnah wani kuma ya kawo man ta Inyass ko wani shehi!
Ga wasu daga cikin Ayoyin Qur'ani dake nuna cewa Annabi baisan gaibu ba.```

*وعنده مفاتح الغيب لايعلمها إلا هو...*
_Ma'ana;_ *_kuma A wajenshi(Allah) makullan gaibu suke babu Wanda ya sansu sai shi(Allah)_*

*A wani wurin kuma Allah S.W.T cewa yayi;*
*_قل لايعلم من في السماوات والأرض الغيب إلا الله، وما يشعرون أيان يبعثون_*

_Ma'ana;_ ```Kace(yã kai Annabi Muhammad s.a.w) babu Wanda yasan gaibu a sama ko a kasa sai Allah, kuma basu San yaushe ne za'a tashesu ba(bayan mutuwa).```

*Idan kuma muka leka a suratu lukman aya ta karshe Allah S.W.T cewa yayi;*
*_إن الله عنده علم الساعة وينزل الغيث ويعلم ما فى الأرحم، وما تدرى نفس ماذ تكسب غدا، وما تدرى نفس بأي أرض تموت، إن الله عليم خبير_*
_Ma'ana;_ *_Lallai a wurin Allah ne Ilimin sa'a yake(Tashin kiyama) kuma shine ke saukar da girgije, kuma yasan Abunda ke cikin mahaifa, kuma babu Wata Rai da tasan Abunda zata Aikata a gobe ko Anjima, babu Wanda yasan a wace kasa ko a wane gari zai  mutu. Lallai Allah masani ne kuma mai bada labari ne._*

```Wadanan Ayoyi da na kawo dukkansu idan ka duba Tafsiran manyan Malamai wadan da ba son Rai a zuciyarsu, zaka samu sunyi cikakken bayani karara, babu boye boye ko shaci fadi, zaka samu babu Wanda ya kawo cewa Annabi yasan Gaibu.
Idan muka dawo a cikin hadissai kuwa, ga hadisi na biyu dake cikin AR'BA'UNA HADITH, Wanda tun bamu da wayo ake karantar damu shi, Hadisin Sayyidina Umar R.A Wanda imamu Muslim ya ruwaito, Lokacin da Mala'ika jibril lokacin da yake yima Annabi Muhammad s.a.w Tambayoyi, daga karshe yake tambayar shi;``` 
*فأخبرني عن الساعة: قال: ما المسئول عنها بأعلم من السائل....*
_Ma'ana;_ *_ka bani Labarin sa'a(Tashin kiyama)? Sai Annabi Muhammad s.a.w yace; Ai Wanda aka tambaya baifi Wanda yayi Tambayar sani ba._*
``` Shin idan  manzon Allah s.a.w yasan gaibu meyasa bai fada masa Ranar da za'ayi tashin kiyama ba???
Daga karshe inason in fadawa yan uwa cewa; Maganar gaskiya Annabi Muhammad s.a.w bai San gaibi ba sai Allah ya sanar dashi ta fuskar wahayi, amma kafin Allah yayi masa wahayi bai sani ba.

  Allah s.w.t Nike Roko da ya karemu da bin son zukatanmu, ya bamu ikon yin koyi da farin jekada Annabi Muhammad s.a.w a dukkanin Rayuwarmu.

Sai mun hadu a fitowa Na biyu insha Allahu```

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*

Shiga link dake kasa mu hadu a Facebook
https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

IYAYENMU NE

*_ALLAH S.W.T YACE; MATAN ANNABI IYAYENMU NE!*_

      *_Amma shi Dan shi'ah yace ba uwayenshi bane yana zaginsu, sai mukace duk Wanda yace ba iyayenshi bane toh mu munsan uwarshi, uwarshi itace hãwuyah, (wuta)_*

```ABU SINAAN```

ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBI BA...!!!

🎙🎙🎙🎙🎙🎙🎙
*ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBU BA...!!!*🎤🎤🎤🎤🎤🎤

*_Fitowa ta biyu(02)_*

*Daga; Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*Godiya ta tabbata ga Allah Wanda ya sanar da Dan Adam Abunda bai sani ba, tsira da Amincin Allah su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w tare da iyalan gidansa da sahabbansa da duk Wanda yabi hanyarsu da kyautatawa har zuwa ranar da kudi da yaya basu da amfani sai Wanda yaje ma Allah da zuciya mai tsoronshi da mika wuya gareshi.*

*_Bayan haka_*

```Nayi rubutu Mai irin wannan taken a sama sai wasu yan bidi'ah da wadanda basu fahimci addini ba suka yo Mani chaa, sai naga dacewar na kara haskaka ma Al'umma domin kowa ya kara gane inda aka nufa.

Da farko dai Menene Ma'anar gaibu???

     Ita dai Kalmar gaibu kalma ce ta larabci, wadda take hawa akan duk abunda ya boyewa sanin mutum, duk abinda tunanin mai tunani ko hankalin mai hankali bazai iya riskarsa ba to shi ake cewa gaibu. Misali; Sanin yaushe zaka mutu, sanin Abinda zai sami rayuwarka a nan gaba, da sanin ranar tashin Kiyama duk suna daga cikin Misalan gaibu. (Nemi rubutun Abokin da'awa a fagen Media Malam Awaisu Al'araby fagge Wanda yayi a 28/04/2015 domin Karin bayani.)
Idan ka fahimci ma'anar gaibu, toh sai mu leka Qur'ani domin mu warware matsalar.
A cikin Qur'ani Allah S.W.T yake cewa;```
*يسئلك الناس عن الساعة، قل إنما علمها عند الله، وما يدريك لعل الساعة تكون قريبا.*
_Ma'ana;_ *_suna tambayarka(Annabi Muhammad s.a.w) akan lokaci(Tashin kiyama), sai Allah yace, kace saninta(Tashin kiyama) yana wurin Allah kadai. Kuma meya sanar dakai watakila ta kasance kusa._*

   ```Wannan ayar koda ace ita kadai aka saukar akan ilimin gaibu to tabbas ta isa hujja akan wadancan yan bidi'ar, abunda mutane basu fahimta ba akan wannan lamarin shine, su yan bidi'ah suna son fakewa da guzuma domin Harbin karsana, idan su ka yarda Almajiransu suka gane cewa Annabi Muhammad s.a.w baisan gaibu ba, sai Wanda Allah ya sanar dashi,idan kuma Allah ya sanar dashi ya tashi daga gaibu zuwa wahayi, toh idan suka fahimci wannan toh zasu gane cewa Ashe wadancan waliyyan na bugi yaudararsu sukeyi, domin sunce Sunsan gaibu, hujjarsu ta cewa haka saboda saboda tijjani da inyass duk jikokin Annabi ne, toh tunda Annabi yasan gaibu toh toh toh ai ai ai shi kuma jikane, saboda haka dole mu haska ma Al'umma domin su fahimci ina gaskiyar take.
  Wata ayar kuma Allah S.W.T cewa yayi;```
*ولا أقول لكم عندى خزائن الله ولا أعلم الغيب...*

_Ma'ana:_ *_(Allah ne da kanshi ya cewa Annabi Muhammad s.a.w ya fadawa mutane cewa) Ban ce muku Taskokin Allah a hannuna suke ba, sannan kuma bansan gaibu ba._*

   ```To anan Abunda zance shine duk Wanda ya fahimci ma'anar gaibu wacce muka ambata a farkon rubutu, to zai fahimci cewa Manzon Allah s.a.w baisan gaibu ba,sai Wanda Allah ya sanar dashi, idan kuma Allah ya sanar dashi ya tashi daga gaibu zuwa wahayi, Allah ya kara fahimtar damu gaskiya ya bamu ikon binta.
Toh yanzu bari mu leka cikin hadisi.```
 
*Hadisi ya tabbata daga ummuna Aisha R.A akan cewa Annabi baisan gaibu ba.*
*عن عائشة رضي الله عنها قالت؛ من حدثك أن محمدا صلى الله عليه وسلم رأى ربه فقد كذب وهو يقول(لاتدركه ألابصار)، ومن حدثك أنه يعلم الغيب فقد كذب وهو يقول لايعلم الغيب إلا الله*

_Ma'ana:_ *_Nana Aisha tace "duk Wanda yace maka Annabi Muhammad s.a.w yaga Allah toh karya yakeyi, sannan duk Wanda yace maka Annabi yasan gaibu to karya yakeyi, domin shi din yana cewa babu Wanda yasan gaibu sai Allah._*[Bukhari 7380,6945, Muslim 457,287]

   ```Toh yan uwa kunji zancen Nana Aisha matar Manzon Allah s.a.w wacce take kusa dashi a koda yaushe, Masu karyata Ahlis sunnah akan wannan zancen to me zakuce akan zancen Nana Aisha??? Nasan indai ka yarda Nana Aisha uwar muminai ce to baza ka karyata taba, domin indai kai mumini ne to uwarka ce, idan kace ba uwarka bace sai muce toh ai munsan wacece uwarka, eh itace hãwuya, Allah ya kyauta. Bari na dakata a nan idan bukatuwar fitowa na uku ta taso, toh a matsayinmu na dalibai zamu kara cewa wani Abu.
Allah ka jikan sheikhul Islam Muhammad ibn Abdulwahab, a cikin Littafinsa kashfus shubuhãt yake cewa;```
*والعامي من الموحدين يغلب ألفا من علماء هؤلاء المشركين، كما قال تعال؛(وإن جندنا لهم الغلبون) [الصافات ١٧٣]*

_Ma'ana;_ *_Mai karamin sani(ilimi) cikin masu kadaita Allah yana rinjayar mutum dubu cikin mushirikan Malaman bidi'ah, kamar yadda Allah yace; Rundunar Allah sune Masu yin nasara. Rundunar Allah sune masu yin nasara da hujja Qur'ani da hadisi, haka kuma suke yin nasara da harshensu._*

```Allah ya tabbatar damu akan sunnar Annabi Muhammad s.a.w ya dawwamar damu a cikin aiki da ita Amiin.```

https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

Copyright©
*Hashim Surajo Uba Tsamiya*
📞08064734911📞

MA'ANAR SAHABI

🎙🎙🎙🎙🎙🎙🎙
*MU WASA KWAKWALWA*
🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤

*_MA'ANAR SAHABI'_* _Wanda ya hadu da Manzon Allah s.a.w yayi imani dashi, ya mutu akan imani! Ka'ida uku kenan._

*_TAMBAYA ANAN ITACE;_* _Wanda ya hadu da Manzon Allah s.a.w baiyi imani dashi ba, sai bayan Annabi ya rasu, sannan yayi imani dashi, kuma ya mutu akan imani, shi kuma meye sunanshi???_

*Amsa nikeso tare da cikakkar hujja, mu hadu a private chat a _08064734711_ ko a Facebook message, ta https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya domin tattaunawa idan ka kawo amsa tare da hujja mai karfi.

*ABU SINÃN* *_Hashim surajo uba Tsamiya_*

العقيدة

♨ﻋﻠﻤﻮﺍ ﺃبناءكم و اخوانكم ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ﺑﺘﻜﺮﺍﺭ ﻫﺬﻩ ﺍﻷﺳﺌﻠﺔ ﻋﻠﻴﻬﻢ♨
🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺
🔴ﺱ /1 ﻣﻦ ﺃﻳﻦ ﻧﺄﺧﺬ ﻋﻘﻴﺪﺗﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ .
🔴ﺱ /2 ﺃﻳﻦ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻓﻲ ﺍﻟﺴﻤﺎﺀ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻌﺮﺵ .
🔴ﺱ /3 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻌﺮﺵ ؟
🔹ﺝ : ( ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻌﺮﺵ ﺍﺳﺘﻮﻯ ) .
🔴ﺱ /4 ﻣﺎ ﻣﻌﻨﻰ ( ﺍﺳﺘﻮﻯ ) ؟
🔹ﺝ : ﻋﻼ ﻭﺍﺭﺗﻔﻊ .
🔴ﺱ /5 ﻟﻤﺎﺫﺍ ﺧﻠﻖ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺠﻦ ﻭﺍﻹﻧﺲ ؟
🔹ﺝ : ﻟﻌﺒﺎﺩﺗﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ .
🔴ﺱ /6 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﺧﻠﻖ ﺍﻟﺠﻦ ﻭﺍﻹﻧﺲ ﻟﻌﺒﺎﺩﺗﻪ ؟
🔹ﺝ : ( ﻭﻣﺎ ﺧﻠﻘﺖ ﺍﻟﺠﻦ ﻭﺍﻹﻧﺲ ﺇﻻ ﻟﻴﻌﺒﺪﻭﻥ ) .
🔴ﺱ /7 ﻣﺎ ﻣﻌﻨﻰ ( ﻳﻌﺒﺪﻭﻥ ) ؟
🔹ﺝ : ﻳﻮﺣﺪﻭﻥ .
🔴ﺱ /8 ﻣﺎ ﻣﻌﻨﻰ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻻ ﻣﻌﺒﻮﺩ ﺑﺤﻖ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ .
🔴ﺱ /9 ﻣﺎ ﺃﻋﻈﻢ ﻋﺒﺎﺩﺓ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ .
🔴ﺱ /10 ﻣﺎ ﺃﻋﻈﻢ ﻣﻌﺼﻴﺔ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻟﺸﺮﻙ .
🔴ﺱ /11 ﻣﺎﻫﻮ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ؟
🔹ﺝ : ﺇﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﺎﻟﻌﺒﺎﺩﺓ .
🔴ﺱ /12 ﻣﺎﻫﻮ ﺍﻟﺸﺮﻙ ؟
🔹ﺝ : ﻋﺒﺎﺩﺓ ﻏﻴﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻊ ﺍﻟﻠﻪ .
🔴ﺱ /13 ﻛﻢ ﺃﻗﺴﺎﻡ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ؟
🔹ﺝ : ﺛﻼﺛﺔ .
🔴ﺱ /14 ﻣﺎﻫﻲ ﺃﻗﺴﺎﻡ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ؟
🔹ﺝ :ﺍﻟﺮﺑﻮﺑﻴﺔ ﻭﺍﻷﻟﻮﻫﻴﺔ ﻭﺍﻷﺳﻤﺎﺀ ﻭﺍﻟﺼﻔﺎﺕ .
🔴ﺱ /15 ﻣﺎ ﺗﻌﺮﻳﻒ ﺗﻮﺣﻴﺪ ﺍﻟﺮﺑﻮﺑﻴﺔ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ ﺃﻓﻌﺎﻟﻪ ﻣﺜﻞ ﺍﻟﺨﻠﻖ ﻭﺍﻟﺮﺯﻕ .
🔴ﺱ /16 ﻣﺎ ﺗﻌﺮﻳﻒ ﺗﻮﺣﻴﺪ ﺍﻷﻟﻮﻫﻴﺔ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﺄﻓﻌﺎﻝ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩ ﻣﺜﻞ ﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻭﺍﻟﺬﺑﺢ ﻭﺍﻟﺴﺠﻮﺩ .
🔴ﺱ /17 ﻫﻞ ﻟﻠﻪ ﺃﺳﻤﺎﺀ ﻭﺻﻔﺎﺕ ؟
🔹ﺝ : ﻧﻌﻢ .
🔴ﺱ /18 ﻣﻦ ﺃﻳﻦ ﻧﺄﺧﺬ ﺃﺳﻤﺎﺀ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺻﻔﺎﺗﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ .
🔴ﺱ /19 ﻫﻞ ﺗﺸﺒﻪ ﺻﻔﺎﺕ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻔﺎﺗﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ﻻ .
🔴ﺱ /20 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺻﻔﺎﺕ ﺍﻟﻠﻪ ﻻ ﺗﺸﺒﻪ ﺻﻔﺎﺗﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ( ﻟﻴﺲ ﻛﻤﺜﻠﻪ ﺷﻲﺀ ﻭﻫﻮ ﺍﻟﺴﻤﻴﻊ ﺍﻟﺒﺼﻴﺮ ) .
🔴ﺱ /21 ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻛﻼﻡ ﻣﻦ ؟
🔹ﺝ : ﻛﻼ‌ﻡ ﺍﻟﻠﻪ .
🔴ﺱ /22 ﻣﻨﺰﻝ ﺃﻡ ﻣﺨﻠﻮﻕ ؟
🔹ﺝ : ﻣﻨﺰﻝ ﻭ ﻫﻮ ﻛﻼﻣﻪ ﺣﻘﻴﻘﺔ ﺑﺤﺮﻑ ﻭ ﺻﻮﺕ .
🔴ﺱ /23 ﻣﺎ ﻫﻮ ﺍﻟﺒﻌﺚ ؟
🔹ﺝ : ﺇﺣﻴﺎﺀ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺑﻌﺪ ﻣﻮﺗﻬﻢ .
🔴ﺱ /24 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﻛﻔﺮ ﻣﻦ ﺃﻧﻜﺮ ﺍﻟﺒﻌﺚ ؟
🔹ﺝ : ( ﺯﻋﻢ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻛﻔﺮﻭﺍ ﺃﻥ ﻟﻦ ﻳﺒﻌﺜﻮﺍ ) .
🔴ﺱ /25 ﻣﺎ ﺍﻟﺪﻟﻴﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﺳﻴﺒﻌﺜﻨﺎ ؟
🔹ﺝ : ( ﻗﻞ ﺑﻠﻰ ﻭﺭﺑﻲ ﻟﺘﺒﻌﺜﻦ ) .
🔴ﺱ /26 ﻛﻢ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻹﺳﻼﻡ ؟
🔹ﺝ : ﺧﻤﺴﺔ .
🔴ﺱ /27ﻛﻢ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻹﻳﻤﺎﻥ ؟
🔹ﺝ : ﺳﺘﺔ .
🔴ﺱ /28ﻛﻢ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻺﺣﺴﺎﻥ ؟
🔹ﺝ : ﻭﺍﺣﺪ .
🔴ﺱ /29 ﻣﺎﺗﻌﺮﻳﻒ ﺍﻺﺳﻼﻡ ؟
🔹ﺝ : ﺍﻻﺳﺘﺴﻼﻡ ﻟﻠﻪ ﺑﺎﻟﺘﻮﺣﻴﺪ ﻭﺍﻻﻧﻘﻴﺎﺩ ﻟﻪ ﺑﺎﻟﻄﺎﻋﺔ ﻭﺍﻟﺒﺮﺍﺀﺓ ﻣﻦ ﺍﻟﺸﺮﻙ ﻭﺃﻫﻠﻪ .
🔴ﺱ /30 ﻣﺎ ﺗﻌﺮﻳﻒ ﺍﻹﻳﻤﭑﻥ ؟
🔹ﺝ : ﺃﻥ ﺗﺆﻣﻦ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻭﻣﻼﺋﻜﺘﻪ ﻭﻛﺘﺒﻪ ﻭﺭﺳﻠﻪ ﻭﺍﻟﻴﻮﻡ ٱﻵخر ﻭﺍﻟﻘﺪﺭ ﺧﻴﺮﻩ ﻭﺷﺮﻩ،
ﻭﺍﻹﻳﻤﭑﻥ ﺇﻋﺘﻘﺎﺩ ﺑﺎﻟﻘﻠﺐ ﻭﻗﻮﻝ ﺑﺎﻟﻠﺴﺎﻥ ﻭﻋﻤﻞ ﺑﺎﻟﺠﻮﺍﺭﺡ ﻳﺰﻳﺪ ﺑﺎﻟﻄﺎﻋﺔ ﻭﻳﻨﻘﺺ ﺑﺎﻟﻤﻌﺼﻴﺔ
.
🔴ﺱ /31 ﻟﻤﻦ ﻧﺬﺑﺢ ﻭﻧﺴﺠﺪ ؟
🔹ﺝ : ﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ .
🔴ﺱ /32 ﻫﻞ ﻳﺠﻮﺯ ﺍﻟﺬﺑﺢ ﻭﺍﻟﺴﺠﻮﺩ ﻟﻐﻴﺮ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﻻ .
🔴ﺱ /33 ﻣﺎﺣﻜﻢ ﺍﻟﺬﺑﺢ ﻭﺍﻟﺴﺠﻮﺩ ﻟﻐﻴﺮ ﺍﻟﻠﻪ ؟
🔹ﺝ : ﺷﺮﻙ ﺃﻛﺒﺮ .
📚 انشرها قدر استطاعتك

ALLAH YA KYAUTA

*_YANXU IDAN AKA CIRE WASU  JAHOHIN DAKE NORTHEAST (BORNO, ADAMAWA, GOMBE, YOBE), BABU JAHAR DA TAFI RASHIN ZAMAN LAFIYA KAMAR ZAMFARA!_* 

```KO MEYA KAWO HAKAN???

A NAWA TUNANIN SHINE HARDA WASA DA SHARI'AH DA MUKEYI ZAI IYA KAWO HAKA!  ANCE ANA SHARI'AR MUSULUNCI, TOH AMMA GA WANI YA SACI HANDSET (WAYA) AN DAURESHI SHEKARU A GIDAN KASO, SHI KUMA WANCAN YA SACI DUKIYAR GWAMNATI(BAITUL MALI) KUSAN BILIYOYAN KUDI, AMMA AN KYALESHI, KUMA MUTANE BÃSUYI MASHI KALLON BARAWO!

ANYA! ANYA!! ANYA!!!

ALLAH YA KYAUTA```

Sunday, 4 December 2016

KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???

🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤
*_KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???_*
🔊🔈🔊🔈🔉🔉🔊

_Fitowa ta daya 001_

_Rubutawa:_ *Hashim Surajo Uba Tsamiya*  *(ABU SINÃN)*

    *_Godiya ta tabbata ga Allah, Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga Manzon Allah s.a.w da mutanen gidansa da  Sahabbansa da wadanda suka bi tafarkinsa._*

_Bayan haka;_

```Naga da cewar nayi wannan rubutun ne saboda yadda naga watan da yan bidi'ah ke sheke ayarsu ya kama, sannan kuma a wannan watane suke rudar jahillai suna batar dasu.
Amsar taken wannan rubutu itace; Bai halasta ayi bikin Maulidin Annabi ko maulidin waninsa daga cikin magabata, saboda yin haka yana daga cikin bidi'o'in da aka kirkiro a cikin addini, domin kuwa Manzon Allah s.a.w bai yiba, haka ma khalifofinshi guda Hudu shiryayyu da sauran sahabbai da wadanda suka bisu da kyautatawa duk basu yi maulidi ba, tare da cewa sunfi kowa sanin Sunnah da kuma aiki da ita, sunfi kowa So da kyaunar Annabi Muhammad s.a.w da kuma biyayya ga shari"'arsa, bisa wadanda suka zo bayansu.
Hadisi ya tabbata daga Annabi Muhammad s.a.w cewa;```
(من أحدث في أمرنا هذا ما ليس منه فهو رد).

_Ma'ana;_ *_Wanda ya kirkiro wani Abu a cikin wannan Al'amari namu(Addininmu) Wanda baya cikinsa, toh wannan Abu an mayar masa dashi.(Baza'a karba ba)_*

_Manzon Allah s.a.w a wani hadisin kuma sai yace;_
عليكم بسنتي وسنة الخلفاء الراشدين المهديين من بعدي، تمسكوا بها وعضوا عليها بالنواجد وإياكم ومحدثات الأمور، فإن كل محدثة بدعة وكل بدعة ضلالة.

_Ma'ana;_ *_Kuyi Riko da sunnah ta da sunnar khalifofi shiryayyu masu shiryarwa a bayana, kuyi riko da ita, kuma Ku cije a kanta da ha'koranku na can ciki, kuma Ku kiyayi kirkirarrun al'amurra, domin dukkan 'kir'kirarren Abu (a cikin Addini) bidi'ah ne, kuma dukkan bidi'ah bata CE._*

  ```A cikin wadannan hadisai biyu, akwai kashedi mai tsanani a kan kirkirar bidi'ah da kuma aiki da ita!
Allah madaukakin sarki ya fada a cikin littafinsa mai tsarki cewa;```
((وما ءاتكم الرسول فخذوه وما نهاكم عنه فانتهوا)).

_Ma'ana;_ *_Abin da Manzon Allah yazo muku dashi to Ku rikeshi, abin da kuma ya haneku ga barinsa, toh Ku hanu. [Al-hashr, aya ta 7]_*
A nan Allah yayi mana umurni da bin manzon Allah ba da yin maulidi ba

A wani wurin kuma sai Allah yace;
((فليحذر الذين يخالفون عن أمره أن تصيبهم فتنة أو يصيبكم عذاب أليم))
_Ma'ana;_ *_Wadanda suke saba wa umurninsa, baza suyi tunanin wata fitina ta samesu ba, ko wata azaba mai radadi ta samesu[An-Nur, aya ta 63]_*
A Wata ayar sai Allah yace;
اليوم أكملت لكم دينكم وأتممت عليكم نعمتي ورضيت لكم الإسلام دينا.

_Ma'ana;_ *_A yau na kammala maku addininku, kuma na cika ni'imata a kanku, kuma na yarda da musulunci ya zama Addini a gareku._*
          [Al-ma'ida aya ya 3]
 
Da kuwa ace maulidi addinine da yazo kafin saukar wannan ayar.

```Ayoyi da suke da irin wannan ma'ana suna da yawa, kuma kirkiro irin wadannan tarurruka na Maulidi yana nuna cewa Allah s.w.t bai cika Addini ba! Kuma Manzon Allah s.a.w bai Isarwa Al'umma da abunda ya kamata suyi aiki dashi ba! (Wanda duk ya fadi haka kuwa to tabbas ya zama ARNE)
Domin kuwa manzon Allah s.a.w a cikin hadisi ingantace yake cewa;
((ما بعث الله من نبي إلا كان حقا عليه أن يدل أمته على خير ما يعلمه لهم، وينذرهم شر ما يعلمه لهم)).

Ma'ana; Allah bai aiko wani Annabi ba, face ya kasance hakki ne akan wannan Annabin ya nuna wa Al'ummarsa Alherin da ya sani garesu, kuma yayi musu gargadi daga sharrin da ya sani garesu. [Muslim]

Wadannan ayoyi da hadissai kawai sun isa su tabbatar mana da cewa Maulidi ba Addinin Annabi Muhammadu bane, ba ya daga cikin hanyoyin shiriya na Addini, Hasali ma BIDI'AH CE abar kyama.

BIDI'AH SAMM

        TAUHIDI SAKKKKK

          MAULIDI SAM SAM SAM SAM SAM```

Sai mun hadu a fitowa na gaba.

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*
📞08064734911
Https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya
Http://hashimtsamiya.blogspot.com

JAWABI AKAN BIDI'AH

JAWABI A KAN BID'A / MAULIDI DAGA MALAMAN MUSULUNCI  /2/

بسم الله الرحمان الرحيم

Da sunan Allah mai rahama mai jin kai, tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzonmu Annabi Muhammad s.a.w, da Iyalensa da Sahabbansa baki daya.

RABE'RABEN BID'A DA RADDIN MALAMAI A KANTA

Masu bibiya idan ba a manta ba a rubutu na farko mun kawo maganganun malamai magabata na kwarai a kan ta'arifin bid'a, yanzu kuma za mu kawo rabe-raben da aka yi mata, da  farkon wanda ya fara rarrabata kashi-kashi da kuma raddin da shaharrun malaman Musulunci  su ka yi wa wannan rabe-raben.

Al'imams Shad'ibiy, Babban malami a Mazhabar  malikiya a cikin littafinsa mai suna AL'I'ITISAM ya ce:

فصل تقسيم العلماء للبدع
وَمِمَّا يُورَدُ فِي هَذَا الْمَوْضِعِ:

أَنَّ الْعُلَمَاءَ قَسَّمُوا الْبِدَعَ بِأَقْسَامِ أَحْكَامِ الشَّرِيعَةِ الْخَمْسَةِ، وَلَمْ يَعُدُّوهَا قِسْمًا وَاحِدًا مَذْمُومًا، فَجَعَلُوا مِنْهَا مَا هُوَ وَاجِبٌ وَمَنْدُوبٌ وَمُبَاحٌ وَمَكْرُوهٌ وَمُحَرَّمٌ. وَبَسَطَ ذَلِكَ الْقَرَافِيُّ بَسْطًا شَافِيًا وَأَصْلُ مَا أَتَى بِهِ مِنْ ذَلِكَ شَيْخُهُ عِزُّ الدِّينِ بْنُ عَبْدِ السَّلَامِ.  وَهَا أَنَا آتِي بِهِ عَلَى نَصِّهِ، فَقَالَ:

Ma'ana:
/Fasalin da zai yi raddi a kan riyawarsu (wasu malamai) cewa bid'a ta kasu kashi biyar/:

Lallai malamai sun rarraba bid'a irin rabe-raben hukuncin shari'a guda biyar, ba su k'irga bid'a a matsayin kashi d'aya abin zargi, sai suka sanya daga cikinta akwai:
1. Bid'a wajiba,
2. Da mustahabbi,
3. Da halastacce,
4. Da makaruhi (k'yamatacce),
5. Da haramtacce. Malam K'ARRAFIY ya yalwata bayani warakakke a kan haka, asalin abin da K'arrafiy ya zo da shi na wannan bayani daga malaminsa ne IZZUDDIN BIN ABDUSSALAM. Ga shi zan so maka da su kamar yadda ya nassanta:

" اعْلَمْ أَنَّ الْأَصْحَابَ فِيمَا رَأَيْتُ مُتَّفِقُونَ عَلَى إِنْكَارِ الْبِدَعِ، نَصَّ عَلَى ذَلِكَ ابْنُ أَبِي زَيْدٍ وَغَيْرُهُ، وَالْحَقُّ التَّفْصِيلُ وَأَنَّهَا خَمْسَةُ أَقْسَامٍ:

قِسْمٌ وَاجِبٌ: وَهُوَ مَا تَنَاوَلَتْهُ قَوَاعِدُ الْوُجُوبِ وَأَدِلَّتُهُ مِنَ الشَّرْعِ; كَتَدْوِينِ الْقُرْآنِ وَالشَّرَائِعِ إِذَا خِيفَ عَلَيْهَا الضَّيَاعُ، فَإِنَّ التَّبْلِيغَ لِمَنْ بَعْدَنَا مِنَ الْقُرُونِ وَاجِبٌ إِجْمَاعًا، وَإِهْمَالُ ذَلِكَ حَرَامٌ إِجْمَاعًا، فَمِثْلُ هَذَا النَّوْعِ لَا يَنْبَغِي أَنْ يُخْتَلَفَ فِي وُجُوبِهِ.

الْقِسْمُ الثَّانِي الْمُحَرَّمُ: وَهُوَ كُلُّ بِدْعَةٍ تَنَاوَلَتْهَا قَوَاعِدُ التَّحْرِيمِ وَأَدِلَّتُهُ مِنَ الشَّرِيعَةِ، كَالْمُكُوسِ، وَالْمُحْدَثَاتِ مِنَ الْمَظَالِمِ، وَالْمُحْدَثَاتِ الْمُنَافِيَةِ لِقَوَاعِدِ الشَّرِيعَةِ; كَتَقْدِيمِ الْجُهَّالِ عَلَى الْعُلَمَاءِ، وَتَوْلِيَةِ الْمَنَاصِبِ الشَّرْعِيَّةِ مَنْ لَا يَصْلُحُ بِطَرِيقِ التَّوْرِيثِ، وَجَعْلِ الْمُسْتَنَدِ فِي ذَلِكَ كَوْنَ الْمَنْصِبِ كَانَ لِأَبِيهِ، وَهُوَ فِي نَفْسِهِ لَيْسَ بِأَهْلٍ.

الْقِسْمُ الثَّالِثُ أَنَّ مِنَ الْبِدَعِ مَا هُوَ مَنْدُوبٌ إِلَيْهِ: وَهُوَ مَا تَنَاوَلَتْهُ قَوَاعِدُ النَّدْبِ وَأَدِلَّتُهُ; كَصَلَاةِ التَّرَاوِيحِ، وَلِإِقَامَةِ صُوَرِ الْأَئِمَّةِ وَالْقُضَاةِ وَوُلَاةِ الْأُمُورِ عَلَى خِلَافِ مَا كَانَ عَلَيْهِ الصَّحَابَةُ رِضْوَانُ اللَّهِ عَلَيْهِمْ; بِسَبَبِ أَنَّ الْمَصَالِحَ وَالْمَقَاصِدَ الشَّرْعِيَّةَ لَا تَحْصُلُ إِلَّا بِعَظَمَةِ الْوُلَاةِ فِي نُفُوسِ النَّاسِ، وَكَانَ النَّاسُ فِي زَمَنِ الصَّحَابَةِ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُمْ مُعْظَمُ تَعْظِيمِهِمْ إِنَّمَا هُوَ بِالدِّينِ وَسَبْقِ الْهِجْرَةِ، ثُمَّ اخْتَلَّ النِّظَامُ، وَذَهَبَ ذَلِكَ الْقَرْنُ، وَجَدَّ قَرْنٌ آخَرُ لَا يُعَظِّمُونَ إِلَّا بِالصُّوَرِ، فَتَعَيَّنَ تَفْخِيمُ الصُّوَرِ حَتَّى تَحْصُلَ الْمَصَالِحُ.

وَقَدْ كَانَ عُمَرُ بْنُ الْخَطَّابِ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ يَأْكُلُ خُبْزَ الشَّعِيرِ وَالْمِلْحِ، وَيَفْرِضُ لِعَامِلِهِ نِصْفَ شَاةٍ كُلَّ يَوْمٍ; لِعِلْمِهِ بِأَنَّ الْحَالَةَ الَّتِي هُوَ عَلَيْهَا دُونَ غَيْرِهِ لَوْ عَمِلَهَا غَيْرُهُ لَهَانَ فِي نُفُوسِ النَّاسِ وَلَمْ يَحْتَرِمُوهُ، وَتَجَاسَرُوا عَلَيْهِ بِالْمُخَالَفَةِ، فَاحْتَاجَ إِلَى أَنْ يَضَعَ غَيْرَهُ فِي صُورَةٍ أُخْرَى تَحْفَظُ النِّظَامَ.

وَلِذَلِكَ لَمَّا قَدِمَ الشَّامَ; وَجَدَ مُعَاوِيَةَ بْنَ أَبِي سُفْيَانَ قَدِ اتَّخَذَ الْحُجَّابَ، وَاتَّخَذَ الْمَرَاكِبَ النَّفِيسَةَ وَالثِّيَابَ الْهَائِلَةَ الْعَلِيَّةَ، وَسَلَكَ مَا سَلَكَهُ الْمُلُوكُ، فَسَأَلَهُ عَنْ ذَلِكَ؟ فَقَالَ: " إِنَّا بِأَرْضٍ نَحْنُ فِيهَا مُحْتَاجُونَ لِهَذَا ". فَقَالَ لَهُ: " لَا آمُرُكَ وَلَا أَنْهَاكَ "، وَمَعْنَاهُ: أَنْتَ أَعْلَمُ بِحَالِكَ: هَلْ أَنْتَ مُحْتَاجٌ إِلَى هَذَا فَيَكُونُ، أَوْ غَيْرُ مُحْتَاجٍ إِلَيْهِ؟
فَدَلَّ ذَلِكَ مِنْ عُمَرَ وَغَيْرِهِ عَلَى أَنَّ أَحْوَالَ الْأَئِمَّةِ وَوُلَاةِ الْأُمُورِ تَخْتَلِفُ بِاخْتِلَافِ الْأَمْصَارِ وَالْقُرُونِ وَأَحْوَالِ أَهْلِهَا، فَكَذَلِكَ يُحْتَاجُ إِلَى تَجْدِيدِ زَخَارِفَ وَسِيَاسَاتٍ لَمْ تَكُنْ قَدِيمَةً، وَرُبَّمَا وَجَبَتْ فِي بَعْضِ الْأَحْوَالِ.

الْقِسْمُ الرَّابِعُ: بِدْعَةٌ مَكْرُوهَةٌ: وَهِيَ مَا تَنَاوَلَتْهُ أَدِلَّةُ الْكَرَاهَةِ مِنَ الشَّرِيعَةِ وَقَوَاعِدِهَا; كَتَخْصِيصِ الْأَيَّامِ الْفَاضِلَةِ أَوْ غَيْرِهَا بِنَوْعٍ مِنَ الْعِبَادَةِ.
وَلِذَلِكَ وَرَدَ فِي الصَّحِيحِ [شَاهِدٌ] خَرَّجَهُ مُسْلِمٌ وَغَيْرُهُ: «أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ نَهَى عَنْ تَخْصِيصِ يَوْمِ الْجُمُعَةِ بِصِيَامٍ، أَوْ لَيْلَةٍ بِقِيَامٍ.»

وَمِنْ هَذَا الْبَابِ الزِّيَادَةُ فِي الْمَنْدُوبَاتِ الْمَحْدُودَاتِ; كَمَا وَرَدَ فِي التَّسْبِيحِ عَقِبَ الْفَرِيضَةِ ثَلَاثًا وَثَلَاثِينَ، فَتَفْعَلُ مِائَةً، وَوَرَدَ صَاعٌ فِي زَكَاةِ الْفِطْرِ، فَيَجْعَلُ - عَشَرَةَ أَصْوُعٍ ; بِسَبَبِ أَنَّ الزِّيَادَةَ فِيهَا إِظْهَارُ الِاسْتِظْهَارِ عَلَى الشَّارِعِ، وَقِلَّةُ أَدَبٍ مَعَهُ، بَلْ شَأْنُ الْعُظَمَاءِ إِذَا حَدَّدُوا شَيْئًا; وُقِفَ عِنْدَهُ وَعُدَّ الْخُرُوجُ عَنْهُ قِلَّةَ أَدَبٍ.
وَالزِّيَادَةُ فِي الْوَاجِبِ أَوْ عَلَيْهِ أَشَدُّ فِي الْمَنْعِ; لِأَنَّهُ يُؤَدِّي إِلَى أَنْ يُعْتَقَدَ أَنَّ الْوَاجِبَ هُوَ الْأَصْلُ وَالْمَزِيدُ عَلَيْهِ.

وَلِذَلِكَ نَهَى مَالِكٌ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ عَنْ إِيصَالِ سِتَّةِ أَيَّامٍ مِنْ شَوَّالٍ; لِئَلَّا يُعْتَقَدَ أَنَّهَا مِنْ رَمَضَانَ.

وَخَرَّجَ أَبُو دَاوُدَ فِي " مُسْنَدِهِ ": أَنَّ رَجُلًا دَخَلَ إِلَى مَسْجِدِ رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، فَصَلَّى الْفَرْضَ، وَقَامَ لِيُصَلِّيَ رَكْعَتَيْنِ، «فَقَالَ لَهُ عُمَرُ بْنُ الْخَطَّابِ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ: اجْلِسْ حَتَّى تَفْصِلَ بَيْنَ فَرْضِكَ وَنَفْلِكَ، فَهَكَذَا مَنْ قَبْلَنَا. فَقَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: أَصَابَ اللَّهُ بِكَ يَا ابْنَ الْخَطَّابِ ; يُرِيدُ عُمَرَ: إِنَّ مَنْ قَبْلَنَا وَصَلُوُا النَّوَافِلَ بِالْفَرَائِضِ، وَاعْتَقَدُوا الْجَمِيعَ وَاجِبًا، وَذَلِكَ تَغْيِيرٌ لِلشَّرَائِعِ، وَهُوَ حَرَامٌ إِجْمَاعًا».

الْقِسْمُ الْخَامِسُ: الْبِدَعُ الْمُبَاحَةُ: وَهِيَ مَا تَنَاوَلَتْهُ أَدِلَّةُ الْإِبَاحَةِ وَقَوَاعِدُهَا مِنَ الشَّرِيعَةِ، كَاتِّخَاذِ الْمَنَاخِلِ لِلدَّقِيقِ، فَفِي الْآثَارِ: أَوَّلُ شَيْءٍ أَحْدَثَهُ النَّاسُ بَعْدَ رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ اتِّخَاذُ الْمَنَاخِلِ ; لِأَنَّ تَلْيِينَ الْعَيْشِ وَإِصْلَاحَهُ مِنَ الْمُبَاحَاتِ، فَوَسَائِلُهُ مُبَاحَةٌ.

فَالْبِدْعَةُ إِذَا عُرِضَتْ تُعْرَضُ عَلَى قَوَاعِدِ الشَّرْعِ وَأَدِلَّتِهِ، فَأَيُّ شَيْءٍ تَنَاوَلَهَا مِنَ الْأَدِلَّةِ وَالْقَوَاعِدِ أُلْحِقَتْ بِهِ، مِنْ إِيجَابٍ أَوْ تَحْرِيمٍ أَوْ غَيْرِهَا، وَإِنْ نُظِرَ إِلَيْهَا مِنْ حَيْثُ الْجُمْلَةِ بِالنَّظَرِ إِلَى كَوْنِهَا بِدْعَةً مَعَ قَطْعِ النَّظَرِ فِيمَا يَتَقَاضَاهَا; كُرِهَتْ; فَإِنَّ الْخَيْرَ كُلَّهُ فِي الِاتِّبَاعِ، وَالشَّرَّ كُلَّهُ فِي الِابْتِدَاعِ انْتَهَى مَا ذَكَرَهُ الْقَرَافِيُّ.
وَذَكَرَ شَيْخُهُ فِي " قَوَاعِدِهِ " فِي فَصْلِ الْبِدَعِ مِنْهَا بَعْدَمَا قَسَّمَ أَحْكَامَهَا إِلَى الْخَمْسَةِ: أَنَّ الطَّرِيقَ فِي مَعْرِفَةِ ذَلِكَ أَنْ تُعْرَضَ الْبِدْعَةُ عَلَى قَوَاعِدِ الشَّرِيعَةِ، فَإِنْ دَخَلَتْ فِي قَوَاعِدِ الْإِيجَابِ; فَهِيَ وَاجِبَةٌ. . . . . . .

إِلَى أَنْ قَالَ: " وَلِلْبِدَعِ الْوَاجِبَةِ أَمْثِلَةٌ:
(أَحَدُهَا): الِاشْتِغَالُ [بِـ] الَّذِي يُفْهَمُ بِهِ كَلَامُ اللَّهِ تَعَالَى وَكَلَامُ رَسُولِهِ، وَذَلِكَ وَاجِبٌ; لِأَنَّ حِفْظَ الشَّرِيعَةِ وَاجِبٌ.
(وَالثَّانِي): حِفْظُ غَرِيبِ الْكِتَابِ وَالسُّنَّةِ مِنَ اللُّغَةِ.
(وَالثَّالِثُ): تَدْوِينُ أُصُولِ الْفِقْهِ.
(وَالرَّابِعُ): الْكَلَامُ فِي الْجَرْحِ وَالتَّعْدِيلِ لِتَمْيِيزِ الصَّحِيحِ مِنَ السَّقِيمِ.

ABIN LURA:
A nan mun fahimci cewa asalin wanda ya rarraba bid'a gida -gida shi ne wannan Malami, wato Izzuddin bin Abdussalam, malami ga Imamul K'arrafiy. Duk wani malami da ka ga  ya rarraba bid'a gida-gida daga  Malam Izzuddin din can ya dakko wannan fahimtar. Babu wani kafinsa, ga kuma raddin da IMAMUS SHA'DIBIY ya yi masa a gaba, bayan ya yi masa adalci ya kawo magarsa cikakkiya kamar yadda ku ka gani a nan, sai Imamus Shadibiy ya ce:

وَالْجَوَابُ:

أَنَّ هَذَا التَّقْسِيمَ أَمْرٌ مُخْتَرَعٌ، لَا يَدُلُّ عَلَيْهِ دَلِيلٌ شَرْعِيٌّ، بَلْ هُوَ نَفْسُهُ مُتَدَافِعٌ; لِأَنَّ مِنْ حَقِيقَةِ الْبِدْعَةِ أَنْ لَا يَدُلَّ عَلَيْهَا دَلِيلٌ شَرْعِيٌّ; لَا مِنْ نُصُوصِ الشَّرْعِ، وَلَا مِنْ قَوَاعِدِهِ.
إِذْ لَوْ كَانَ هُنَالِكَ مَا يَدُلُّ مِنَ الشَّرْعِ عَلَى وُجُوبٍ أَوْ نَدْبٍ أَوْ إِبَاحَةٍ; لَمَا كَانَ ثَمَّ بِدْعَةٌ، وَلَكَانَ الْعَمَلُ دَاخِلًا فِي عُمُومِ الْأَعْمَالِ الْمَأْمُورِ بِهَا أَوِ الْمُخَيَّرِ فِيهَا، فَالْجَمْعُ بَيْنَ [كَوْنِ] تِلْكَ الْأَشْيَاءِ بِدَعًا، وَبَيْنَ كَوْنِ الْأَدِلَّةِ تَدُلُّ عَلَى وُجُوبِهَا أَوْ نَدْبِهَا أَوْ إِبَاحَتِهَا جَمْعٌ بَيْنَ مُتَنَافِيَيْنِ.

أَمَّا الْمَكْرُوهُ مِنْهَا وَالْمُحَرَّمُ; فَمُسَلَّمٌ مِنْ جِهَةِ كَوْنِهَا بِدَعًا لَا مِنْ جِهَةٍ أُخْرَى، إِذْ لَوْ دَلَّ دَلِيلٌ عَلَى مَنْعِ أَمْرٍ أَوْ كَرَاهَتِهِ; لَمْ يُثْبِتْ بِذَلِكَ كَوْنَهُ بِدْعَةً; لِإِمْكَانِ أَنْ يَكُونَ مَعْصِيَةً; كَالْقَتْلِ وَالسَّرِقَةِ وَشُرْبِ الْخَمْرِ وَنَحْوِهَا، فَلَا بِدْعَةَ يُتَصَوَّرُ فِيهَا ذَلِكَ التَّقْسِيمُ أَلْبَتَّةَ، إِلَّا الْكَرَاهِيَةَ وَالتَّحْرِيمَ حَسْبَمَا يُذْكَرُ فِي بَابِهِ.

فَمَا ذَكَرَ الْقَرَافِيُّ عَنِ الْأَصْحَابِ مِنَ الِاتِّفَاقِ عَلَى إِنْكَارِ الْبِدَعِ صَحِيحٌ، وَمَا قَسَّمَهُ فِيهَا غَيْرُ صَحِيحٍ.
وَمِنَ الْعَجَبِ حِكَايَةُ الِاتِّفَاقِ مَعَ الْمُصَادَمَةِ بِالْخِلَافِ وَمَعَ مَعْرِفَتِهِ بِمَا يَلْزَمُهُ فِي خَرْقِ الْإِجْمَاعِ........... الخ

Da Imamus Shad'ibiy ya matsa gaba sai ya bude Sabon fasali ya ce:

الرد على القول بتقسيم البدع إلى أقسام:

وَأَمَّا مَا قَالَهُ عِزُّ الدِّينِ؛ فَالْكَلَامُ فِيهِ عَلَى مَا تَقَدَّمَ:
فَأَمْثِلَةُ الْوَاجِبِ مِنْهَا مِنْ قِبَلِ مَا لَا يَتِمُّ الْوَاجِبُ إِلَّا بِهِ كَمَا قَالَ ـ فَلَا يُشْتَرَطُ أَنْ يَكُونَ مَعْمُولًا بِهِ فِي السَّلَفِ، وَلَا أَنْ يَكُونَ لَهُ أَصْلٌ فِي الشَّرِيعَةِ عَلَى الْخُصُوصِ. وَلِأَنَّهُ مِنْ بَابِ الْمَصَالِحِ الْمُرْسَلَةِ لَا مِنَ البدع.

Ma'ana:
Amma abin da Izzuddin ya fada (na rarraba bid'a), magana a kansa kamar yadda ya gabata: Misalan bid'a wajiba daga ciki yana daga cikin abin da wajibi ba ya cika sai da shi, kamar yadda (Izzuddin) ya Fada: ba a shardanta ya zamo ana amfani da shi ba a baya, bai zamo yana da asali a shari'a ba a kebance. Domin shi yana daga cikin babin abubuwan yau-da-kullum ne ba cikin bid'a ba. Ga dai bayanan da ya yi ta yi nan, saboda k'arancin lokaci fassarasu duka ba zai yiwu min ba a yanzu, Ga sunan:

أَمَّا هَذَا الثَّانِي فَقَدْ تَقَدَّمَ. وَأَمَّا الْأَوَّلُ؛ لَوْ كَانَ ثَمَّ مَنْ يَسِيرُ إِلَى فَرِيضَةِ الْحَجِّ طَيَرَانًا فِي الْهَوَاءِ، أَوْ مَشْيًا عَلَى الْمَاءِ؛ لَمْ يُعَدَّ مُبْتَدِعًا بِمَشْيِهِ كَذَلِكَ؛ لِأَنَّ الْمَقْصُودَ إِنَّمَا هُوَ التَّوَصُّلُ إِلَى مَكَّةَ لِأَدَاءِ الْفَرْضِ، وَقَدْ حَصَلَ عَلَى الْكَمَالِ، فَكَذَلِكَ هَذَا.

عَلَى أَنَّ هَذِهِ أَشْيَاءُ قَدْ ذَمَّهَا بَعْضُ مَنْ تَقَدَّمَ مِنَ الْمُصَنِّفِينَ فِي طَرِيقَةِ التَّصَوُّفِ، وَعَدَّهَا مِنْ جُمْلَةِ مَا ابْتَدَعَ النَّاسُ، وَذَلِكَ غَيْرُ صَحِيحٍ، وَيَكْفِي فِي رَدِّهِ إِجْمَاعُ النَّاسِ قَبْلَهُ عَلَى خِلَافِ مَا قَالَ.
عَلَى أَنَّهُ نُقِلَ عَنِ الْقَاسِمِ بْنِ مُخَيْمِرَةَ: أَنَّهُ ذُكِرَتِ الْعَرَبِيَّةُ، فَقَالَ: " أَوَّلُهَا كِبْرٌ، وَآخِرُهَا بَغْيٌ ".

وَحُكِيَ أَنَّ بَعْضَ السَّلَفِ قَالَ: " النَّحْوُ يُذْهِبُ الْخُشُوعَ مِنَ الْقَلْبِ، (وَ) مَنْ أَرَادَ أَنْ يَزْدَرِيَ النَّاسَ كُلَّهُمْ؛ فَلْيَنْظُرْ فِي النَّحْوِ ".
وَنَقَلَ نَحْوًا مِنْ هَذِهِ.

وَهَذِهِ كُلُّهَا لَا دَلِيلَ فِيهَا عَلَى الذَّمِّ؛ لِأَنَّهُ لَمْ يُذَمَّ النَّحْوُ مِنْ حَيْثُ هُوَ بِدْعَةٌ، بَلْ مِنْ حَيْثُ مَا يُكْتَسَبُ بِهِ أَمْرٌ زَائِدٌ؛ كَمَا يُذَمُّ سَائِرُ عُلَمَاءِ السُّوءِ؛ لَا لِأَجْلِ عُلُومِهِمْ، بَلْ لِأَجْلِ مَا يَحْدُثُ لَهُمْ بِالْعَرَضِ مِنَ الْكِبْرِ بِهِ وَالْعُجْبِ وَغَيْرِهِمَا، وَلَا يَلْزَمُ مِنْ ذَلِكَ كَوْنُ الْعِلْمِ بِدْعَةً.

فَتَسْمِيَةُ الْعُلُومِ الَّتِي يُكْتَسَبُ بِهَا أَمْرٌ مَذْمُومٌ بِدَعًا إِمَّا عَلَى الْمَجَازِ الْمَحْضِ مِنْ حَيْثُ لَمْ يُحْتَجْ إِلَيْهَا أَوَّلًا ثُمَّ احْتِيجَ بَعْدُ، أَوْ مِنْ عَدَمِ الْمَعْرِفَةِ بِمَوْضُوعِ الْبِدْعَةِ، إِذْ مِنَ الْعُلُومِ الشَّرْعِيَّةِ مَا يُدَاخِلُ صَاحِبَهَا الْكِبْرُ وَالزَّهْوُ وَغَيْرُهُمَا، وَلَا يَعُودُ ذَلِكَ عَلَيْهَا بِذَمٍّ.

وَمِمَّا حَكَى بَعْضُ هَذِهِ الْمُتَصَوِّفَةِ عَنْ بَعْضِ عُلَمَاءِ الْخَلَفِ قَالَ: " الْعُلُومُ تِسْعَةٌ، أَرْبَعَةٌ مِنْهَا سُنَّةٌ مَعْرُوفَةٌ مِنَ الصَّحَابَةِ وَالتَّابِعِينَ، وَخَمْسَةٌ مُحْدَثَةٌ لَمْ تَكُنْ تُعْرَفُ فِيمَا سَلَفَ، فَأَمَّا الْأَرْبَعَةُ الْمَعْرُوفَةُ: فَعِلْمُ الْإِيمَانِ، وَعِلْمُ الْقُرْآنِ، وَعِلْمُ الْآثَارِ، وَالْفَتَاوَى، وَأَمَّا الْخَمْسَةُ الْمُحْدَثَةُ: فَالنَّحْوُ، وَالْعَرُوضُ، وَعِلْمُ الْمَقَايِيسِ، وَالْجَدَلِ فِي الْفِقْهِ، وَعِلْمُ الْمَعْقُولِ بِالنَّظَرِ ". انْتَهَى.

وَهَذَا ـ إِنْ صَحَّ نَقْلُهُ ـ فَلَيْسَ أَوَّلًا كَمَا قَالَ؛ فَإِنَّ أَهْلَ الْعَرَبِيَّةِ يَحْكُونَ عَنْ أَبِي الْأَسْوَدِ الدُّؤَلِيِّ: أَنَّ عَلِيَّ بْنَ أَبِي طَالِبٍ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ هُوَ الَّذِي أَشَارَ عَلَيْهِ بِوَضْعِ شَيْءٍ فِي النَّحْوِ حِينَ سَمِعَ أَعْرَابِيًّا قَارِئًا يَقْرَأُ: أَنَّ اللَّهَ بَرِيءٌ مِنَ الْمُشْرِكِينَ وَرَسُولُهُ ـ؛ بِالْجَذرِّ.

وَقَدْ رُوِيَ عَنِ ابْنِ مُلَيْكَةَ: أَنَّ عُمَرَ بْنَ الْخَطَّابِ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ أَمَرَ أَنْ لَا يَقْرَأَ الْقُرْآنَ إِلَّا عَالِمٌ بِاللُّغَةِ، وَأَمَرَ أَبَا الْأَسْوَدِ، فَوَضَعَ النَّحْوَ. وَالْعَرُوضُ مِنْ جِنْسِ النَّحْوِ.

وَإِذَا كَانَتِ الْإِشَارَةُ مِنْ وَاحِدٍ مِنَ الْخُلَفَاءِ الرَّاشِدِينَ؛ صَارَ النَّحْوُ وَالنَّظَرُ فِي الْكَلَامِ الْعَرَبِيِّ مِنْ سُنَّةِ الْخُلَفَاءِ الرَّاشِدِينَ، وَإِنْ سُلِّمَ أَنَّهُ لَيْسَ كَذَلِكَ؛ فَقَاعِدَةُ الْمَصَالِحِ تَعُمُّ عُلُومَ الْعَرَبِيَّةِ، (أَيْ: تَكُونُ مِنْ) قَبِيلِ الْمَشْرُوعِ، فَهِيَ مِنْ جِنْسِ كَتْبِ الْمُصْحَفِ وَتَدْوِينِ الشَّرَائِعِ.

وَمَا ذُكِرَ عَنِ الْقَاسِمِ بْنِ مُخَيْمِرَةَ قَدْ رَجَعَ عَنْهُ؛ فَإِنَّ أَحْمَدَ بْنَ يَحْيَى ثَعْلَبًا، قَالَ: " كَانَ أَحَدُ الْأَئِمَّةِ فِي الدِّينِ يَعِيبُ النَّحْوَ، وَيَقُولُ: أَوَّلُ تَعَلُّمِهِ شُغْلٌ، وَآخِرُهُ بَغْيٌ، يُزْدَرَى بِهِ النَّاسُ، فَقَرَأَ يَوْمًا: إِنَّمَا يَخْشَى اللَّهُ مِنْ عِبَادِهِ الْعُلَمَاءَ؛ (بِرَفْعِ اللَّهِ وَنَصْبِ الْعُلَمَاءِ) فَقِيلَ لَهُ: كَفَرْتَ مِنْ حَيْثُ لَا تَعْلَمُ تَجْعَلُ اللَّهَ يَخْشَى الْعُلَمَاءَ؟ فَقَالَ: لَا طَعَنْتُ عَنْ عِلْمٍ يَؤُولُ إِلَى مَعْرِفَةِ هَذَا أَبَدًا.
قَالَ عُثْمَانُ بْنُ سَعِيدٍ الدَّانِيُّ: " الْإِمَامُ الَّذِي ذَكَرَهُ أَحْمَدُ بْنُ يَحْيَى هُوَ الْقَاسِمُ بْنُ مُخَيْمِرَةَ ".

قَالَ: " وَقَدْ جَرَى لِعَبْدِ اللَّهِ بْنِ أَبِي إِسْحَاقَ مَعَ مُحَمَّدِ بْنِ سِيرِينَ كَلَامٌ، وَكَانَ ابْنُ سِيرِينَ يَنْتَقِصُ النَّحْوِيِّينَ، فَاجْتَمَعَا فِي جِنَازَةٍ، فَقَرَأَ ابْنُ سِيرِينَ إِنَّمَا يَخْشَى اللَّهُ مِنْ عِبَادِهِ الْعُلَمَاءَ؛ بِرَفْعِ اسْمِ اللَّهِ، فَقَالَ لَهُ ابْنُ أَبِي إِسْحَاقَ: كَفَرْتَ يَا أَبَا بَكْرٍ تَعِيبُ عَلَى هَؤُلَاءِ الَّذِينَ يُقِيمُونَ كِتَابَ اللَّهِ؟ فَقَالَ ابْنُ سِيرِينَ: إِنْ كُنْتُ أَخْطَأْتُ؛ فَأَسْتَغْفِرُ اللَّهَ ".

وَأَمَّا عِلْمُ الْمَقَايِيسِ فَأَصْلُهُ فِي السُّنَّةِ، ثُمَّ فِي عِلْمِ السَّلَفِ بِالْقِيَاسِ، ثُمَّ قَدْ جَاءَ فِي ذَمِّ الْقِيَاسِ أَشْيَاءُ حَمَلُوهَا عَلَى الْقِيَاسِ الْفَاسِدِ، وَهُوَ الْقِيَاسُ عَلَى غَيْرِ أَصْلٍ، وَهُوَ عُمْدَةُ كُلِّ مُبْتَدَعٍ.

- وَأَمَّا الْجَدَلُ فِي الْفِقْهِ؛ فَذَلِكَ مِنْ قَبِيلِ النَّظَرِ فِي الْأَدِلَّةِ، وَقَدْ كَانَ السَّلَفُ الصَّالِحُ يَجْتَمِعُونَ لِلنَّظَرِ فِي الْمَسَائِلِ الِاجْتِهَادِيَّةِ الَّتِي لَا نَصَّ فِيهَا لِلتَّعَاوُنِ عَلَى اسْتِخْرَاجِ الْحَقِّ، فَهُوَ مِنْ قَبِيلِ التَّعَاوُنِ عَلَى الْبِرِّ وَالتَّقْوَى، وَمِنْ قَبِيلِ الْمُشَاوَرَةِ الْمَأْمُورِ بِهَا، فَكِلَاهُمَا مَأْمُورٌ بِهِ.

- وَأَمَّا عِلْمُ الْمَعْقُولِ بِالنَّظَرِ؛ فَأَصْلُ ذَلِكَ فِي الْكِتَابِ وَالسُّنَّةِ؛ لِأَنَّ اللَّهَ تَعَالَى احْتَجَّ فِي الْقُرْآنِ عَلَى الْمُخَالِفِينَ لِدِينِهِ بِالْأَدِلَّةِ الْعَقْلِيَّةِ؛ كَقَوْلِهِ: {لَوْ كَانَ فِيهِمَا آلِهَةٌ إِلَّا اللَّهُ لَفَسَدَتَا} [الأنبياء: ٢٢]، وَقَوْلُهُ: {هَلْ مِنْ شُرَكَائِكُمْ مَنْ يَفْعَلُ مِنْ ذَلِكُمْ مِنْ شَيْءٍ} [الروم: ٤٠]، وَقَوْلُهُ: {أَرُونِي مَاذَا خَلَقُوا مِنَ الْأَرْضِ أَمْ لَهُمْ شِرْكٌ فِي السَّمَاوَاتِ} [فاطر: ٤٠]

وَحَكَى عَنْ إِبْرَاهِيمَ عَلَيْهِ السَّلَامُ مُحَاجَّتَهُ لِلْكَفَّارِ بِقَوْلِهِ: {فَلَمَّا جَنَّ عَلَيْهِ اللَّيْلُ رَأَى كَوْكَبًا قَالَ هَذَا رَبِّي} [الأنعام: ٧٦] إِلَخْ. وَفِي الْحَدِيثِ حِينَ ذُكِرَتِ الْعَدْوَى: «فَمَنْ أَعْدَى الْأَوَّلَ؟ ".»
إِلَى غَيْرِ ذَلِكَ مِنَ الْأَدِلَّةِ. فَكَيْفَ يُقَالُ: إِنَّهُ مِنَ الْبِدَعِ؟

- وَقَوْلُ عِزِّ الدِّينِ: " إِنَّ الرَّدَّ عَلَى الْقَدَرِيَّةِ وَكَذَا (غَيْرُهُمْ) مِنْ أَهْلِ الْبِدَعِ مِنَ الْبِدَعِ الْوَاجِبَةِ "، غَيْرُ جَارٍ عَلَى الطَّرِيقِ الْوَاضِحِ، وَلَوْ سُلِّمَ؛ فَهُوَ مِنَ الْمَصَالِحِ الْمُرْسَلَةِ.

وَأَمَّا أَمْثِلَةُ الْبِدَعِ الْمُحَرَّمَةِ؛ فَظَاهِرَةٌ.

وَأَمَّا أَمْثِلَةُ الْمَنْدُوبَةِ؛ فَذَكَرَ مِنْهَا إِحْدَاثَ الرُّبْطِ وَالْمَدَارِسِ:
- فَإِنْ عَنَى بِالرُّبْطِ مَا بُنِيَ مِنَ الْحُصُونِ وَالْقُصُورِ قَصْدًا لِلرِّبَاطِ فِيهَا؛ فَلَا شَكَّ أَنَّ ذَلِكَ مَشْرُوعٌ بِشَرْعِيَّةِ الرِّبَاطِ وَلَا بِدْعَةَ فِيهِ.
وَإِنْ عَنَى بِالرُّبْطِ مَا بُنِيَ لِالْتِزَامِ سُكْنَاهَا قَصْدَ الِانْقِطَاعِ إِلَى الْعِبَادَةِ؛ فَإِنَّ إِحْدَاثَ الرُّبْطِ الَّتِي شَأْنُهَا أَنْ تُبْنَى تَدَيُّنًا لِلْمُنْقَطِعِينَ لِلْعِبَادَةِ - فِي زَعْمِ الْمُحْدَثِينَ - وَيُوقَفُ عَلَيْهَا أَوْقَافٌ يَجْرِي مِنْهَا عَلَى الْمُلَازِمِينَ لَهَا مَا يَقُومُ بِهِمْ فِي مَعَاشِهِمْ مِنْ طَعَامٍ أَوْ لِبَاسٍ وَغَيْرِهِمَا؛ لَا يَخْلُو أَنْ يَكُونَ لَهَا أَصْلٌ فِي الشَّرِيعَةِ أَمْ لَا، فَإِنْ لَمْ يَكُنْ أَصْلٌ؛ دَخَلَتْ فِي الْحُكْمِ تَحْتَ قَاعِدَةِ الْبِدَعِ الَّتِي هِيَ ضَلَالَاتٌ؛ فَضْلًا عَنْ أَنْ تَكُونَ مُبَاحَةً؛ فَضْلًا عَنْ أَنْ تَكُونَ مُنْدُوبًا إِلَيْهَا، وَإِنْ كَانَ لَهَا أَصْلٌ؛ فَلَيْسَ بِبِدْعَةٍ، فَإِدْخَالُهَا تَحْتَ جِنْسِ الْبِدَعِ غَيْرُ صَحِيحٍ.

ثُمَّ إِنَّ كَثِيرًا مِمَّنْ تَكَلَّمَ عَلَى هَذِهِ الْمَسْأَلَةِ مِنَ الْمُصَنِّفِينَ فِي التَّصَوُّفِ تَعَلَّقُوا بِالصُّفَّةِ الَّتِي كَانَتْ فِي مَسْجِدِ رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَجْتَمِعُ فِيهَا فُقَرَاءُ الْمُهَاجِرِينَ، وَهُمُ الَّذِينَ نَزَلَ فِيهِمْ: {وَلَا تَطْرُدِ الَّذِينَ يَدْعُونَ رَبَّهُمْ بِالْغَدَاةِ وَالْعَشِيِّ يُرِيدُونَ وَجْهَهُ} [الأنعام: ٥٢] الْآيَةَ، وَقَوْلُهُ تَعَالَى: {وَاصْبِرْ نَفْسَكَ مَعَ الَّذِينَ يَدْعُونَ رَبَّهُمْ بِالْغَدَاةِ وَالْعَشِيِّ} [الكهف: ٢٨] الْآيَةَ، فَوَصَفَهُمْ (اللَّهُ) بِالتَّعَبُّدِ وَالِانْقِطَاعِ إِلَى اللَّهِ بِدُعَائِهِ قَصْدًا لِلَّهِ خَالِصًا، فَدَلَّ عَلَى أَنَّهُمُ انْقَطَعُوا لِعِبَادَةِ اللَّهِ، لَا يَشْغَلُهُمْ عَنْ ذَلِكَ شَاغِلٌ، فَنَحْنُ إِنَّمَا صَنَعْنَا صُفَّةً مِثْلَهَا أَوْ تُقَارِبُهَا، يَجْتَمِعُ فِيهَا مَنْ أَرَادَ أَنْ يَنْقَطِعَ إِلَى اللَّهِ وَيَلْتَزِمَ الْعِبَادَةَ، وَيَتَجَرَّدَ عَنِ الدُّنْيَا وَالشُّغْلِ بِهَا، وَذَلِكَ كَانَ شَأْنُ الْأَوْلِيَاءِ أَنْ يَنْقَطِعُوا عَنِ النَّاسِ، وَيَشْتَغِلُوا بِإِصْلَاحِ بَوَاطِنِهِمْ، وَيُوَلُّوا وُجُوهَهُمْ شَطْرَ الْحَقِّ، فَهُمْ عَلَى سِيرَةِ مَنْ تَقَدَّمَ.

وَإِنَّمَا يُسَمَّى ذَلِكَ بِدْعَةً بِاعْتِبَارٍ مَا، بَلْ هِيَ سُنَّةٌ، وَأَهْلُهَا مُتَّبِعُونَ لِلسُّنَّةِ، فَهِيَ طَرِيقَةٌ خَاصَّةٌ لِأُنَاسٍ، وَلِذَلِكَ لَمَّا قِيلَ لِبَعْضِهِمْ: فِي كَمْ تَجِبُ الزَّكَاةُ؟ قَالَ: عَلَى مَذْهَبِنَا أَمْ عَلَى مَذْهَبِكُمْ؟ ثُمَّ قَالَ: أَمَّا عَلَى مَذْهَبِنَا؛ فَالْكُلُّ لِلَّهِ، وَأَمَّا عَلَى مَذْهَبِكُمْ؛ فَكَذَا وَكَذَا، أَوْ كَمَا قَالَ.

وَهَذَا كُلُّهُ مِنَ الْأُمُورِ الَّتِي جَرَتْ عِنْدَ كَثِيرٍ مِنَ النَّاسِ هَكَذَا؛ غَيْرَ مُحَقَّقَةٍ، وَلَا مُنَزَّلَةٍ عَلَى الدَّلِيلِ الشَّرْعِيِّ، وَلَا عَلَى أَحْوَالِ الصَّحَابَةِ وَالتَّابِعِينَ.

وَلَا بُدَّ مِنْ بَسْطِ طَرْفٍ مِنَ الْكَلَامِ فِي هَذِهِ الْمَسْأَلَةِ - بِحَوْلِ اللَّهِ - حَتَّى يَتَبَيَّنَ الْحَقُّ فِيهَا لِمَنْ أَنْصَفَ وَلَمْ يُغَالِطْ نَفْسَهُ، وَبِاللَّهِ التَّوْفِيقُ.

Imamus Shad'ibiy ya kore duk wata misali da shubha da Malam Izzuddin ya kawo na a karkasa bid'a da ya yi, wannan na kawo maku ne a dunkule, amma muna nan za Ku ji wani babban Sufi da ya Goya wa Imamus Shad'ibiy baya wajen rusa duk rabe-raben bid'a a wani shahararren littafinsa.

A duba littafin IMAMUS SHAD'IBIY Al'i'itisam (الإعتصام) shafi na 128 had zuwa shafi na 138.

Nan zan dakata da ikon Allah mu hadu a darasi na gaba.

Muhammad Jamilu Zaria.
4/3/1438 h.
  04/12/2016 m.