Sunday, 1 January 2017

ABUBUWA BAKWAI MASU HALAKARWA.

Abubuwa Bakwai Masu
Halakarwa(Yiwa Mace Mumina
Kazafi)...

Mace Mumina Kazafi : A yanzu za mu yi
ni akan abu na bakwai kuma na karshe cikin
uwa bakwai da Ma'aikin Allah – tsira da
cin Allah su tabbata a gareshi- ya lissafa
abubuwan da suke halakar da wanda yake
uli dasu , wannan abu shine Yiwa Mace
ina Kazafi .
fi Shine: Jifan mutum da aikata alfasha ta
ko kore juna biyu ko ma Da ba tare da ya
r cikakkun shaiduba.
Alokacin da mutum ya jefa kanshi cikin irin
nnan halayya ta kazafi to lalle ya jefa
a cikin halayyar da take halakarwa, domin
kazafi ba karamin bala'ibane, alokacin da
m ai wance mazinaciyace ko ya yi lalata da
o wannan ciknnanata bana mijintabane ko
a/'yarta ai bana mijinta bane to lalle ya
no tsuliyar dodo dole ya kawo cikakkun
u na mutane hudu maza musulmai da zasu
shaida akan hakan, idan kuma mai kawo
uba ko ya kawo basu cikaba to kowanne
m gada cikinsu bulala tamanin (80) za'a yi
, kamar yadda bayanai zasu zo nan gaba
n.
Wannan shiri da musulunci yake dashi
ramin shiri bane domin kare mutunci, masu
agana na cewa mutunci madarane in ya
bai kwasuwa, addinin musulunci yana daga
manyan manufofinsa kare mutunci, wannan
musulunci ya dauki irin wannan mataki
mmamma 'ya mace, domin alokacin da aka
mata suna to gaba daya anbata mata
arta, shi yasa ayoyin da suka yi Magana
kazafi sun anbaci macece basu anbaci
jiba wannanko ba wai dan hukuncin ya sha
n bane a'a hukuncin iri dayane ga duk
a ya yi mace ko namiji kazafi, kuma bai iya
cikakkakun shaiduba, idan ko ya kawo
u da duk abinda Shara'a ke bukata suka
to baza'a kira wannan da sunan kazafiba.
Yiwa mace mumina kazafi bai halattaba
yana cikin abubuwan da suke halakarwa,
da haka dadin fira ko kiyayya kada ta dauki
m ya yiwa wata/wani kazafi ko yasa a yi.
in Da Suka Yi Magana Akan Kazafi: Idan ka
ka kalli ayoyin zaka gansu kashi ukune
duk suna cikin Suratun Nur.
i Na Farko: Ayata: 4-5, Allah Madaukakin
yana cewa: ''Wadanda suke jifan mata masu
nkai (da zina) sannan kuma basu kawo
u huduba to ku yi musu bulala tamanin (80),
kada ku sake karbar shaidarsu har abada,
waddan sune fasiakai. Saidai kawai wadanda
tuba bayan haka kuma suka kyautata to lalle
mai yawan gafarane kuma mai yawan jinkai .''
nan Allah madaukakin sarki ya bayyana
ncin duk mutumin da ya yiwa mace/namiji
fi kuma bai iya kawo shaidu huduba sai
ya bayyana hukuncin da za'a yi masa. Abu
rko bulala tamanin (80), abu na biyu ba za'a
karbar shaidarsaba har'abada, abu na uku
wannan mutumin fasikine. Sai idan ya tuba,
anne malamai suke maganar shin inya tuba
ci gaba da karbar shaidarsa kuma shikenan
a fasiki bane? Amma ko ya tuba sai an yi
i bulala tamanin.
i Na Biyu: Ayoyin da suka yi bayanin
idan da ya yiwa matarshi kazafi kuma bai
awo shaiduba to shi tsinuwa za su yi da
r ta shi, Allah Yana cewa:
''Wadanda kuma suke jifan matansu (da
kuma ya kasance basu da shaidu saidai
kansu, to shaidar dayansu (itace) Rantsuwa
da Allah lalle shi yana cikin masu gaskiya *
tsuwa) ta biyar tsinuwar Allah ta haukanshi in
asance cikin makaryata. * Kuma abinda zai
ayi mata azaba (haddi) shine ta yi Rantsuwa
da Allah cewar lalle shi (mijin) yana cikin
ryata *. (Rantsuwa) ta biyar lalle fushin Allah
bbata akanta in (mijin nata) ya kasance cikin
gaskiya'' Surartun Nur, ayata: 6-8.
Anan Allah madaukakin sarki ya yi bayanin
miji ya yiwa matarshi kazafi kuma bai iya
shaidu huduba to 'Li'ani'' za su yi. Amma
anda ba miji bane to kodai ya kawo sahaidu
ne hudu maza musulmai ko kuma ayi mishi
a tamanin, ba maganar shi wanda aka yiwa
fi wai ya rantse idan ba haka bane, ko kuma
a ya yi kazafin cewa ya rantse duk babu
i shaidu ko bulala tamanin.
Kashi Na Uku: Ayoyin da suka yi Magana
kazafin da aka yiwa mata muminai masu
nkai natsattsu kammalallu to wadannan
yiwa irin wadannan matan kazafi tsine
aka yi duniya da lahira. Allah madaukakin
yana cewa:
''Lalle dukkanini wadanda ke jifan mata
kamun kai gafalallu (daga aikata dukkanin
ha) wadanda suke muminai to an tsine musu
niya da kuma lahira, kuma suna da azaba
irma* Aranar da harsunannu za su bada
a akansu da hannayansu da kuma
uwansu ta sanadiyyar abinda suka kasance
aikatawa* Awannan ranarce Allah zai cika
sakamakonsu na gaskiya, kuma zasu sani
Allah shi wanda yake mai gaskiya kuma mai
anar da abubuwa''. Suratun Nur, ayata: 23-25.
Wannan ya nuna mana shi karankanshi
fin ya kasu kashi-kashi, kashi na farko shine
gama garin mutane wadanda suke suna da
awan halaye da kuma wanda ba'a rasaba,
ka anbaci hukunci yi musu kazafi a kashin
, sai kuma wanda ya kasance tsakanin miji
ata. Sai wannan kashi na uku, wanda mutum
a mace/namiji mai kamun kai mai addini
ttse mumini kawai ya antayo ashar ya
a mata/mashi ya dinga fadan wasu
nganu wanda da za'a tara mishi arzikin
a domin ya kawo shaida akan haka ba zai
. Domin wani ya dauka irin halin da yake
i to kowa haka yake, to kaga bayan ya kasa
wadannan shaidu za'a yi masa hukuncin
fi anan duniya sanna kuma ya jira ranar
ama, domin Allah baya bari a taba bayinsa
warai, Ya Allah ka samu daga cikinsu, ka
u da sharrin masharranta ka tsaremu ka
mana imanimmu, amin.
Kammalawa: Daga takaitattun bayananan
ayyana agaremu yadda musulunci ya dauki
nci da daraja da kima ya karewa kowa
ncinsa musamman 'ya mace, domin idan ba
ba sai kowa ya fadi abinda ya ga dama ko
hi ya fada yana ganin bai huce aci
shiba, amma idan yasan zai sha bulalane to
ya naba'a yasan me zai fada, sai yazama
are mutuncinsa dana zuriyarsa kamar yadda
re mutuncin wani dana ziriyarsa.
Annanne kuma muka zo karshen wannan
a wacce take dauke da sharhin wannan
i da Abu Hurairata ya ruwaito daga wurin
ikin Allah na wadannan abubuwa bakwai
halakarwa, lalle ma'aikin Allah ya isar da
anci kuma tsira da amincin Allah su tabbata
reshi, hakika ta'amuli da wadannan abubuwa
as yana halakarwa kuma wannan kowa ya
ya tabbatar wannan zai kara imanine bisa
i. Akaro na gaba zamu kawo bayanne kuma
nda zasu haskaka mana rayuwarmu da
inmu, Allah ya kaimu wannan lokacin ya
mu da imani, aimn.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna, Jahar Neja Nijeriya.

NAJASA DA HUKUNCE HUKUNCETA A MUSULUNCI

NAJASA DA HUKUNCE-
HUKUNCENTA

Bayanda a darasin da ya gabata aka kawo
bayanai da suka shafi ruwa, a yanzu za'a kawo
abubuwan da ake yi da ruwan, akan haka za'a
fara da najasa da yadda ake gusar da ita da
ruwa da sauran hukunce hukuncen ita najasar,
Allah Ya yi mana jagora amin.
Abubuwan Da Suke Najasa:
Na farko: Fitsari. (Na mutum) Na babba ko na
karami na mace ko na namiji, ya fara cin abinci
ko bai faraba. Na biyu: Bayangida (Kashi na
mutum). Na uku: Mushe, shine abinda ya mutu
da karan kansa, ko aka yankashi ta hanyar da
bata musulunci ba. Na hudu: Nonon dabbar da
ta yi mushe. Na biyar: Nonon dabbar da aka
haramta cin ta, kamar nonon karya, ko alade ko
jaka...' Na shida: Fitsarin dabbar da aka
haramta cin ta, kamar fitsarin jaki, ko kare…' Na
bakwai: Kashin dukkanin dabbar da aka
harantata, kamar kashin alade (alhanzir), kashin
jaka/jaki..' Na takwas: Kashi da fitsari na
dukkanin dabbar da take cin najasa. Na tara:
Giya. Na goma: Jini, saboda haka bai halatta a
tari jinin da aka yanka dabba ba wai ace za'a
gasa shi ko a soya ko ayiwa dabbobi abinci da
shi ba domin najasa ne (in banda jinin da ake
samu a cikin dabba bayan anyankata wanda bai
fitaba, ai dakyar a rasa jini a cikin dabba). Na
sha-daya: Ruwan ciwo. Na sha-biyu: Maziyyi,
shi kuma ruwane da yake fari yana da laushi
yana fitane lokacin motsawar sha'awa ta mace
ko namiji ta hanyar wasa ko kallo ko nitsewa
cikin tunani, amma idan sha'awa ta kara
karkafafa to maniyyine ke fita, shi kuma
maniyyi ana jin fitarshi sabanin maziyyi, sannan
shi kuma maniyyi yana da kauri sabanin maziyyi
shi yana da laushine, bayanai za su zo akan shi
nan gaba kada idan Allah Ya yarda. Na sha-uku:
Wadiyyi, shi kuma ruwane fari yana kauri sau da
yawa yana fine akarshen fitsari, ta sanadiyyar
daukar kaya mai nauyi, ko matsanancin sanyi,
ko kullewar ciki. Na sha-hudu: Ragowar ruwa ko
aminci na dabbar da ba'a ci, kamar rowan da
jaki ya sha ya raje, in banda mage. Na goma
sha-biyar: Yawun kare da na alade, ko na
dukkan babbar da ta samu ta hanyar su. Na
goma sha-shida: Amai, alokacin da canza daga
yanayin abinci, kenan idan aka ci abin ci yanzu
sai kuma aka harar da shi wannan harawwar ba
najasa bace. Wadannan sune abubuwan da suke
najasa, amma akwai wadansu da malamai suka
karawa juna sani akansu kan najasa ne ko ba
najasa ne ba, kamar ragowar ruwa na wanda ba
musulmi bane ya sha, hakanan akan maniyyi.
Shidai Maniyyi na namiji: Ruwa ne da yake
fari maikauri yana tunkudar junansa alokacin da
zai fita, idan ka shinshina shi ya yi kama da
hudar dabino, kuma ya yi kusa da kanshin kulli,
amma idan ya bushe yana kasancewa kamar
karnin fasasshan kwai. Wannan shine galibin
yadda maniyyin namiji yake kasancewa, wani
lokacin ya kanzo sabanin wadannan bayanai da
suka gabata. Yana fitane lokacin matsananciyar
sha'awa ta sanadiyyar kallo ko wasa ko
matsanancin tunani ko lokacin saduwa. Shi
kuma Maniyyin mace, shi ma: Ruwane fatsi-fatsi
yana da laushi. Wannan ya tabbatar da cewa
mace ma tana da maniyyi kuma da shi ne da na
namiji Allah Yake halitta da su.
Wasu malamai sunce maniyyi najasa ne
domin yana fitane ta mafitar fitsari wanda yake
shi kuma fitsari najasane, wasu malaman kuma
sukace ba najasa bane domin da shi ne Allah
Ya halicci dan'adam kuma a cikinsu akwai
Annabawa da Manzanni, kenan ya za'a mutum
da Allah ya karramashi da yaukaka shi har ya
fitar da Annabawa da Manzanni ace kuma da
najasa aka yi shi??. Wadannan sune abubuwan
da suke najasa da kuma wadanda malamai suka
yi wa juna Karin fahimta.
Hukuncin Najasa:
Wajibine gusar da najasa daga jiki da tufafi da
wurin da za'a yi sallah, idan mutum yana da
ikon gusar da ita kuma yana sane bai gusar da
ita dinba ya yi sallah da ita to ba shi da sallah.
Addinin musulunci addinin tsaftane abinda
musulunci yake so shine akoda yaushe ka
sance cikin tsarki, mafificin tsarki kuma shi ne
tsarkin zuciya a kakkabeta daga barin shirka da
zalinci da hassada da munafunci da dukkan
wata mummunar dabi'a, idan aka samu tsarkin
zuciya kuma ga tsarkin tufafi da ganganjiki da
kuma mahalli to lalle wannan shi ke nuna
kammaluwar mutum.
Yadda Ake Gusar Da Najasa:
Idan ka ga inda najasar take a jikinka ko a
tufafinka to iya inda yake iya nan zaka kama ka
wanke, sabanin yadda wasu matan suke yi wai
dukkanin tufafin da tasa alokaci da take al'ada
to sai ta wanke su, kama daga dankwali da zani
da riga…' wannan musulunci bai zo da shi ba,
inda kwai kika ga jini iya nan kawai za ki
wanke. Idan kuma najasar ta rikice maka baka
ganta ba, amma ka tabbata akwaita ajikin
tufafin na ka shikenan sai ka wanke tufafin
gabadaya. Amma idan najasa ta fantsamo sai
kake kokwanton ta tabaka ko bata taba ka ba,
kuma kai baka ganta ba kuma ka duba mai
Ahlari yace sai ka yayyafa ruwa a wurin.
Amma kuma idan wani abu ya fallatso maka
sai kake kokwanto wannan abun najasane ko ba
najasa ba ne, to awannan lokaci ba wani
hukunci akanka, ba yayyafa ruwa ballantana
wankewa, domin mafiyawan abubuwa masu
tsarki ne, najasa kadanne shi yasa ake iya
lissafe su.
Idan inda najasar take kuma filine ko bango
ko wani dutse sai aka yi ruwan sama ko kuma
aka kwarara ruwa mai tsarki akai shikenen an
gusar da wannan najasar. Amma idan ta kasace
yawun karene wato karene ya baki a kwano ko
a kwarya to za'a zubar da abinda yake ciki
sannan a wanke sau bakwai sannan asa kasa a
daya daga cikin bakwai din. Amma najasar da
ba wannan ba sai a wanke ya wanku sabanin
yadda ake yi, da yaro ya yi fitsari sai ace wai
za'a yayyafa ruwa alhali wankewa akace a yi,
wani ruwamma da aka yayyafa kamar karawa
fitsarin yawa aka yi, Allah ya sawwake. Ya
zama wajibi a tshi tsaye a gusar da najasa a
tsaftace muhalli, musulmi ya kasance
tsaftattace tsafta cikon addini ai ta fi ace ita
ciko ce, ita sharadice sai mutum ya tsarkaka
daga wadannan najasar ibadar shi zata karbu.
Abubuwan Da Najasa Take Hanawa:
Anan za'a anbaci wadansu abubuwa ne da basu
halatta ga dukkan mara tsarki ya aikata su
saboda darajarsu da matsayinsu, kuma hadasin
babbane ko karami, wadannan abubuwa sune:
(1) Taba Alkur'ani: Bai halatta ga mara tsarki
ya taba Alkur'ani, har sai ya yi tsarki inda so
samune ma ya yi alwala musamman idan ya
kasance ba mai yawan daukan Alkur'ani bane.
(2) Sllah: Hakanan bai halatta ga mara tsaki ya
yi sallah ba farillace ko nafila, har sai ya
tsarkaka ya kuma yi alwala, kamar yadda
Ma'aikin Allah-tsira da amincin Allah su tabbata
a gareshi- yace: '' Allah ba zai karbi sallar wanda
ya yi hadasiba har sai ya yi alwala'' Bukhari:135,
Muslim:225. Hakanan kuma ko da mutum yana
da tsarki amma tufafinsa ko wurin sallar baida
tsarki to delene ya tsarkake su kafin fara sallar,
saidai idan bai saniba ko ya manta cewa a
tufafinsa ko wurin da ya yi sallah akwai najasa
sai kuma da lokacin sallar ya fita sannan ya
gani ko ya tuna to anan ba komai sallar shi ta
yi.
(3) Tawafi: Kuma dukkan mutumin da bashi da
tsarki to bai halatta ya yi Tawafin Ka'aba ba,
daman kuma ananne kadai ake dawafi a sararin
duniyar nan.
Kammalawa: Daga wadannan bayanai da suka
gabata munsan abubuwan da suke najasa ta
yadda ko yanzu akace ka kawo biyar zaka iya
cikin gaggawa, da kuma hanyoyin da akebi
wurin gusar da wannan najasa, wanda yake
gusar da ita din wajibine domin munji abubuwan
da bai halatta mara tsarki ya yi ba, akaro na
gaba zamu kawo bayanai akan wadansu
abubuwa da ake ganinsu kamar najasane alhali
kuma ba najasa bane.

Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna, Jahar Neja Nijeriya.

KURAKURAI A KIRAN SALLAH

KURAKURAI A KIRAN SALLAH
ﺑِﺴْﻢِ ﺍَﻟﻠﻪِ ﺍَﻟﺮَّﺣْﻤَﻦِ ﺍَﻟﺮَّﺣِﻴﻢِ
Gabatarwa:
Dasunan Allah maiyawan rahama
maiyawan jinkai, tsira da amincin Allah su kara
tabbata ga fiyayyan halittar Allah, manzan tsira
Annabi Muhammad da Iyalan Sa da Sahabban
Sa baki daya da wadanda suka bi bayansu da
kyautatawa izuwa ranar sakamako, amin.
Bayan haka, hakika wannan bita da 'yan
uwa suka shirya a Shirin Hasken-Musulunci
anan Minna, fadar Jahar Neja ayau (Alhamis: 4,
ga Ramadan 1432 daidai da 4, Agusta 2011)
lallai tana da matukar muhimmanci musamman
a irin wannan lokaci, wanda yake a fili take irin
gudun mawar da ladanai suke bayarwa a cikin
al'umma baki daya.
Wannan matashiya da zamu tattauna a
kanta maitaken "Kura-Kuran da ake samu a
kiran sallah'' muna fatan ta zama wani abune
da za mu yiwa juna gyara, don gyara kayanka
bai zama sauke mu raba ba, kuma muna so a
wannan haduwa ya zana an magance wadannan
kura-kurai duddacewa ba su ke nanba, amma
har idan muka gane cewa akwai kurakuran
kuma muka dauki hanyoyin gyara to zamu sami
taimakon Allah akai, Allah ya yi mana jagora
amin.
A cikin wadannan kurakurai akwai
wadanda su ke da alaka da maikiran sallah,
akwai kuma wadanda suke da alaka da
ma'anonin kiran sallah ta yadda idan ma'anar ta
canza sai ta maida shi ba kuma kiran sallah ba.
Sannan akwai wadanda suke da alaka da
al'umma baki daya, lalle wanan yana nuna mana
cewa matsayin ladaini a cikin al'umma ba
karamin matsayi bane, muna rokon Allah da
sunayan kyawawa da siffofin sa madaukaka ya
yima jagora amin.
A yanzu za'a dan lissafa wasu daga ciki,
ayi kuma dan karin haske sannan abada
shawarwari.
Akwai wadansu abubuwa da zasu shiga
cikin kura kuran da ake samu a kiran sallah,
kamar:
1. Rashin Kiran Sallah A Farkon Lokacinta:
Kamar yadda malamai suka zayyana bayana a
littafai cewar kiran sallah shi ne: Sanar da
mutane shigar lokacin sallah. Kuma kamar aka
sani kowacce sallah tanada lokacinta kuma
gashi malam ya kara mana bayi ya kuma fito
mana da lokatan fili, wanda rashin kiran sallah a
farkon lokacin ta ya haifar da angama kiran
sallah sai a tada ikama, wanda anasone
tsakanin kiran sallah da tada ikama a sami
tazara ta yadda mara alwala zai yi alwala,
wanda sai ya yi tsarki ya je ya yi tsarki, anan
kenan zamu gane yana daga cikin manyan
ayyukan ladan da lokacin sallah ya yi ya kita
domin ya sanar da al'umma shigar lokacinta.
Babbancin kiran sallah da ikama shine:
Kiran sallah sanar da mutane shigar lokacin
sallah (Ladani kuma shi ya kamata ya fi kowa
tantance lokutan sallah), ita kuma ikama: sanar
da wadanda ke cikin masallaci anfara sallah.
2. Rashin Tantance Lokaci: Ladani ya sani shi
ne mutum na farko da yafi kowa sanin canjin
lokaci da yadda yake karuwa da kuma yadda
yake raguwa, kuma idan zai yi anfani da agogo
kada ya dogara da agogo daya, ya zamana yana
dasu uku ko hudu, rashin wannan wadansu
ladanan suke kiran sallah tsakaddare ko dab da
magariba idan hadari ya rufe rana.
Ladanifa ya sani sallolin mutane da
azuminsu suna ratayene a wuyanshi, miliyoyin
mutane basa shanruwa ko su dakatar da sahur
sai ladan ya kira sallah.
3. Rashin Tsayawa A Koyi Kiran Sallah: wannan
yana daga cikin manyan matsalolin da ake
samu, ta yadda inda za'a kowa ya fadi malamin
da ya koya masa kiran sallah to da anyi zuffa.
Hakan ya haifar da kowa yake yin yadda ya ga
dama, wasuma ka ji da yarukansu suke yi ba da
larabciba.
4. Rashin Tantacce Ladanai A Masallaci:
wannan yasa kowa ya zama ladani, wanda yake
wannan kuwa kuskure ne, wannan baihana a
sami ladanai a masallaci gudaba, su zama biyu
ko uku ko dai gwargwadon abida ya sawwaka
amma tsayyayu, wannan zai sa asan cewa
ladani wane yana kiran sallar asubahine kafin
alfijiri ya keto amma ladani wane sai bayan
alfijiri, kamar yadda ya kasance tsakanin Bilal
da Ibnu ummi maktum Allah ya kara musu
yarda.
5. Rashin Sanin Ma'anonin Kiran Sallah:
wannan ya haifar da abubuwa masu yawa, da
basa cikin addini, misali: Ladani ya kammala
kiran sallah sai yace 'Ayi alwala, a jaddada' inda
yasan ma'anar
ﺣَﻲَّ ﻋَﻠَﻰ ﺍَﻟﺼَّﻼَﺓِ، ﺣَﻲَّ ﻋَﻠَﻰ ﺍَﻟْﻔَﻼَﺡِ
Hayya alas Swalah, Hayya alal Falah da bai fadi
waccar maganarba.
6. Rashin Kula Da Ladubban Sallah: wannan ya
sa sai kaka ladani yana kiran sallah amma sai
kaga kamar yana wani abu da bashi da alaka da
addini, wani lokacin sai ya yi kamar ya juyawa
alkibla baya.
7. Kura kurai a lafuzza : ana samun kurakurai
masu tarin yawa a lafuzzan kiran sallah.
Wadannan kurakurai sun kashi kashi biyu.
(a) Kuskure mai canza ma'ana: irin wadannan
kura-kurai suna fitar da shi daga kiran sallah
kwatakwata ya zama wani abu daban, misali:
ﺍَﻟﻠﻪُ ﺃَﻛْﺒَﺮُ – ﺃَﻛْﺒَﺎﺭُ
(b) Kuskure na bata lafuzza: wanda yake fitar
da shi daga duniyar larabci, misali:
ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥَّ ﻣُﺤَﻤَّﺪًﺍ ﺭﺳﻮﻝُ ﺍﻟﻠﻪِ
Shawarwari:
A takaitaccen wanna jawabi da kuma wadannan
abubuwa dana gani ina bada shwara kamar
haka:
1. Bayar da mintina bayan kiran sallah kafin
tayar da sallah, wannan ko zai tabbatane idan
ankira kowacce sallah a farkon lokacin. Misali
Azahar minti 20 la'asar minti 15 magariba minti
10 lisha minti 15 asuba minti 20.
2. Ladani ya zama yana da agogo kamar uku
banda na wayarshi, kuma ba zaije kiran sallah
ba sai ya duba su duka.
3. Aiki da dukkan abubuwan da aka gabatar a
wannan bita.
4. Gyara inda duk mutum ya ji yana da kuskure.
5. Isar da wadannan bayanai ga wadanda basu
zo wannan bita ba.
6. Ladanai su samara da wata haduwa da zasu
dinga yi lokaci lokaci domin tuntubar juna koda
ko za'a fara a matakin unguwa unguwa ne.
7. Ci gaba da shirya irin wannan bitar lokaci
bayan lokaci
8. Koyon kiran sallah baki da baki daga wurin
malamai masana.
Allah ya gafartamana ya kuma ya fe mana,
Allah ya karbi ayyukammu amin summa amin.
ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻠﻰ ﻧﺒﻴﻨﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ
ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, bayan Ofishin 'Yansanda,
Minna jahar Neja Nijeriya.

ZAGIN AISHA R.A

*ZAGIN AISHA RADHIYALLAHU ANHAA!!!*

*_Imamu Malik RH yace; "Duk Wanda ya zagi Aisha a kashe shi. Sai aka ce mashi saboda me za'a kashe shi? Sai yace; Duk Wanda ya jefe ta(cewa tayi zina) kamar ya sabama (karyata) Qur'ani ne"._*

```Wannan kuma haka yake, hukuncin duk matsiyacin da ya zagi ummuna Aisha, hukuncinsa kisa kuma dole mu yakeshi.
Haka Qur'ani yace uwarmu ce, duk Wanda bai yarda ummuna Aisha uwarsa bace, toh munsan uwarsa ba ta wuce HAAWUYA, Allah ya tsare uwar mutum ta zama HAAWUYA```

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*

DARIQA

BABBAN DALILIN DA YASA HADIN KAI YAKE WANZUWA TSAKANIN SHI'AH DA DARIQU SHINE; SU YAN SHI'AH BASU ZAGIN TIJJANI DA INYASSI DA SAURAN YAN CUWA-CUWAN WALIYYAI!
SU KUMA A AQEEDARSU INDAI BAZAKA ZAGI JIKAN MANZO(TIJJANI) BA! TOH KO KA ZAGI KAKAN(ANNABI MUHAMMAD S.A.W) KO KAYI MASHI KARYA, KO KA ZAGI ABOKAN SHI, KO KA ZAGI MATANSHI, TOH KAI ABOKIN TAFIYA NE!

WANNAN JAHILCI NAKU YAN DARIQU YAYI YAWA! YA KAMATA KUSAN ME KUKEYI!

KUFA KUKE YABA ABOKAN ANNABI A WURIN MAULIDI! AMMA KUMA SABODA ZINDIQANCI IDAN YAN SHI'AH SUN GAYYACEKU NASU MAULIDIN SAI SU ZAGI ABUBAKAR SU ZAGI UMAR SU ZAGI AISHA SU ZAGI HAFSAT, KUNA ZAUNE SAMAN KUJERU DON KAWAI SUN KAWO MAKU JUICE DA LEMU DA SWAN SANNAN BASU TABA TIJJANI DA INYASSI BA! WANNAN ZINDIQANCI YAYI YAWA, YA KAMA KU FARKA DAGA SUMAR DA KUKAYI!

ALLAH YA TSARE MANA IMANINMU.

ABBAN SINAAN
Hashim Surajo Uba Tsamiya

MASJID ABI HURAIRAH TSAFE

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
MASALLACIN ABU HURAIRA YAR'YARA TSAFE

              *NABIYYUR RAHMAH*

*_MASJID ABI HURAIRAH YAR YARA TSAFE_*

*JERANGIYAR KARATUTTUKAN NABIYYUR              RAHMAN.

WANDA MALAM SANI LIMAN TSAFE, (LIMAMIN ABU HURAIRA AREA 2. TSAFE) YA GABATAR A' MASALLACIN ABU HURAIRA YAR'YARA TSAFE, AN SAUKE LITTAFIN CIKIN CASSET ARBA'IN DA (48) ALLAH YA BIYA MALAM AMIN.

Darasi Na 01Nabiyyulrahmah by Malam Sani Liman  tsafe
http://darulfikr.com/s/12024 

Darasi Na 02 Nabiyyulrahmah
http://darulfikr.com/s/12025 

Darasi Na 03 Nabiyyulrahmah
http://darulfikr.com/s/12026 

Darasi Na 04NabiyylRahmah
http://darulfikr.com/s/12027 

Darasi Na 05NabiyyulRahmah
http://darulfikr.com/s/12028

 Darasi Na 06 Nabiyyulrahmah
http://darulfikr.com/s/12029

 Darasi Na 10 Nabiyul Rahmah
http://darulfikr.com/s/12032

 Darasi Na 12 NabiyulRaham by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12030 

Darasi Na 13 NabiyulRahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12031

 Darasi Na 14 NabiyulRahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12034

 Darasi Na 15 NabiyulRahmah By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12033

 Darasi Na 16 NabiyulRahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12035 

Darasi Na 17 NabiylRahmah
http://darulfikr.com/s/12036 

Darasi Na 17 NabiyulRahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12037 

Darasi Na 19 NabiyulRahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12038

 Darasi Na 20 NabiylRahma by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12039

 Darasi Na 21 NabiyulRahmah By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12040 

Darasi Na 22 Nabiyulahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12041

 Darasi Na 23 Nabiyulahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhuraiah
http://darulfikr.com/s/12042

 Darasi Na 24 NabiyulRahmah ByMal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12043

 Darasi Na 25 NabiyulRahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12044

 Darasi Na 26 NabiyulRahmah By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12045 

Darasi Na 29 NabiyulRahmah
http://darulfikr.com/s/12049

 Darasi Na 30 NabiyulRahma
http://darulfikr.com/s/12046 

Darasi Na 31 NabiyulRahma by Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/12047

 Darasi Na 32 NabiyuRahmah By Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12050

 Darasi Na 39 NabiylRahamah by Mal Sani Liman Tsafe
http://darulfikr.com/s/12053

 Darasi Na 40 Nabiyul Rahmah by Mal Sani Liman Tsafe Abuhurairah
http://darulfikr.com/s/12054 

Darasi Na 42 NabiulRahma By Mal Sani Liman
http://darulfikr.com/s/12055 

Darasi Na 47 NabiyuRama by Malam Sani Liman
http://darulfikr.com/s/12060 

Darasi Na 48 NabiyulRahmah By Malam Sani Liman
http://darulfikr.com/s/12061

MUQABALA

*NEW UPDATES 10/08/2016*

*MUQABALA!!!*

Muqabala tsakanin Wani mai suna *TIJJANIYYA INYASSIYYA* account dinshi Na facebook! Tare da number shi: *08094652545*
Sai abokin muqabalar fitinannen yaron nan ta yadda suke cewa wato *HASHIM SURAJO UBA TSAMIYA* da number shi: *08064734911*

Wannan muqabala ta biyo bayan cika bakin da suke yi a shafin sadarwa na Facebook, sai  naga ya dace in kirashi domin muyi magana, Na kuma dauki audio domin mutane suyi hukunci da Kansu.
Muqabalar ta farko mai tsawon 01:28:55
👇�👇�👇�👇�👇�👇�
http://kiwi6.com/file/e0gfczbnen

A lokacin da ya gudu sai Na kara kiranshi mukayi mintuna 11:27secs,
👇�👇�👇�👇�👇�👇�👇�
http://kiwi6.com/file/50bcae4l2e

sai karshen mai tsawon mintuna 11:39secs
👇�👇�👇�👇�👇�👇�👇�👇�
http://kiwi6.com/file/50bcae4l2e

Malam yi hukunci da kanka domin fahimtar Wanda ke kan qur'ani da hadisi.

Hashim Surajo Uba Tsamiya
Http://hashim141473.mywapblog.com