Wednesday, 6 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH002

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*HUBUDAR JUMA'AH DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABI-HURAIRAH AREA II TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

Taken hudubar: *wajabcin neman Shawara a addinin Musulunci kashi na biyu(002)*

Mai gabatarwa: *_Sheikh Sani Liman (ABU-HURAIRAH) Tsafe._*

Shiga links dake kasa domin saukewa.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://kiwi6.com/file/ij1jswtjn6

Masu matsalar browsing zasu iya bi ta wannan Link
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://k003.kiwi6.com/hotlink/ij1jswtjn6/02h

```wannan itace cigaban hudubar da Shehin Malamin ya gabatar a satin da ya gabata, idan son samu ne ka sauraresu gaba daya domin amfanuwa.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi, Mu kuma Allah ya bamu ikon amfani da wannan hudubah.```

Copyright©
*_MASJID ABI HURAIRAH SOCIAL MEDIA TSAFE_*

HUDUBAR JUMA'AH001

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*HUBUDAR JUMA'AH DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABI-HURAIRAH AREA II TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

Taken hudubar: *wajabcin neman Shawara a addinin Musulunci*

Mai gabatarwa: *_Sheikh Sani Liman (ABU-HURAIRAH) Tsafe._*

Shiga links dake kasa domin saukewa.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://kiwi6.com/file/p4cumpwxef

Masu matsalar browsing zasu iya bi ta wannan Link
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://k003.kiwi6.com/hotlink/p4cumpwxef/h

```Akwai cigaban wannan hudubah a sati mai zuwa insha Allahu.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi, Mu kuma Allah ya bamu ikon amfani da wannan hudubah.

Copyright©
_Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU-SINAN)_```
atstsamawy@gmail.com
08064734911

ZUMUNTA A MUSULUNCI

🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

*_TATTARAWA:_*

*MALAM SANI LIMAN (ABU HURAIRAH) TSAFE*

_Fitowa Na biyu(002)_

```Bisimillahir-rahmanir-raheem, Alhamdulillah, bayan bayanin da ya gabata na ABUBUWAN DA WANNAN RUBUTU ya kunsa, yanzu zamu fada cikin bayanin Abu na farko.

MECECE ZUMUNTA???

  Ibn athir yana cewa zumunta tana nufin taimakawa yan uwa na bangaren dangantaka da sarakuta da kula da halayen SU koda kuwa suna zaune a wurare masu nisa koda kuma suna munana maka. A daya bangaren kuma, yanke zumunta yana nufin kishiyar abubuwan da aka ambata a baya.

DA WANE ABU AKE SADAR DA ZUMUNTA???

Ana sadar da zumunta da al'amura masu yawa kamar; Ziyartarsu, bibiyar halayensu, tambaya game dasu, aika masu da kyaututtuka da kuma saukar da kowannensu a matsayin da ya dace dashi(wato su yan uwan da ya kamata a sadar da zumunta garesu), sannan kuma ana Sadar da zumunta da bada sadaka ga fakirai daga cikin su da tausasama mawadatan su da girmama manyansu da kuma tausayama kananan su da masu rauninsu da yawan tambayar halin da suke ciki, ziyartar su da kanka ko ka aika wasika ko kayi amfani da wayar salula.

    Mafi girman abunda ake sadar da zumunta dashi shine; mutum yayi kwadayin kiransu((yan uwansa) zuwa ga shiriya ya umurcesu da aiki mai kyau ya kuma hana su aikata miyagun ayyuka.

   Haka nan zumunta bata da wani kayyadadden lokaci da aka kayyade don sadar da ita. Duk abunda al'ada ingantatta ta tabbatar a matsayin Sada zumunta, ana daukarshi a matsayin haka. Haka kuma duk abunda al'ada ingantatta ta tabbatar a matsayin yanke zumunta to ana daukarshi a matsayin haka.

   Zumunta tana bambanta gwargwadon kusanci da matsayi na wadanda ake sadar da zumuntar zuwa garesu, zumuncin da yake tsakanin uba da dansa ya sha bam-ban da Dan uwa na nesa.

   Bugu da kari, zumunta tana banbanta gwargwadon halayen da su wadanda za'a sadarmawa suke ciki, kamar sadar da zumunta ga marar lafiya da mabukaci ta bambanta da sadarwa ga waninsu. Haka kuma sadarwa ga babba ta banbanta da ta karami

    Haka nan sadar da zumunta yana banbanta ta fuskar bagire, Wanda yake zaune a cikin gari ya banbanta da Wanda yake zaune a wani gari wajen ziyartar shi da tambayar halinda yake ciki, da yimasa sallama ko aika mashi da sakonni.

Zamu tsaya a nan, sai wani lokaci idan Allah ya kaimu insha Allahu.

Allah ya bamu ikon sadar da zumunta gwargwadon iko Amiin.

A gaba zamuyi bayani akan FALALAR SADAR DA ZUMUNTA insha Allahu.

Allah yayi mana jagoranci.

Copyright©
MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA```
+2348064734911

BIDI'AR SHAFAR FUSKA BAYAN KAMMALA ADDU'AH


BIDI'AR SHAFAR FUSKA BAYAN KAMMALA ADDU'A🙏
Ibn Rushud yace: an tambayi imamu malik akan mutumin da yake shafar fuska da tafukansa yayin kammala addu'a bayan ya shinfida tafukan kafin hakan?sai imamu Malik yayi inkarin haka,yace bansan wannan ba. nace (Ibn Rushud) Malik (R)yayi inkarin shafar fuska da tafukan hannu bayan addu'a domin yana ganin yin haka badi'a ne, domin babu wani asar daga manzon Allah yake nuna halaccin hakan kuma ra'yi baida mashiga a cikin
📚(albayan wattahsil 49/18)
Imam Abu Daud yace:naji an tambayi imamu Ahmad akan mutumin da ya ke shafar fuskar sa da hannunsa bayan ya kammala wuturi? Sai ya ce "bantaba jin wannan ba" a wani lokacin ma cewa yayi "bantaba jin wani Abu game da shiba". Abu Daud yace banga imamu Ahmad yana aikata hakan ba(ma'ana:babu wani Abu da ya tabbata daga manzaon Allah akan yin haka, kuma babu wani daya daga cikin magabata da ya aikata  haka.
📚(masa'ilah 102).

SIFFOFIN MACE TA GARI

📜📜📜
SIFFOFIN MACE TAGARI📜📜📜
Shaikhul Islam Ibn Taimiyya yace"mace ta gari tana kasancewa tare da miji nagari tsawon shekaru masu yawa.
Ita ce jindadin sa Wanda manzon Allah(saw) ya fada a cikin hadithi yace"ita duniya wani Dan jindadi/amfani ne kuma mafi alkhairin amafani/jindadin ta ita ce mace mumina wadda idan ka kalle ta sai ta  burgeka, idan kabata  umarni sai ta yi maka da'a, idan kafita kabarta zata  kiyaye ka ga kanta(ba zata ci amarnarka ba).

Itace wadda manzon Allah yayi umarni da ita a cikin  zancen sa lokacin da muhajiruna suka tambaye shi:wace dukiya ya kamata murika? Sai yace: "harshe mai yawan ambaton Allah, da zuciya mai yawan godiya, da MACE TAGARI mai taimakon dayanku bisa imani"
(📚Timidhi ya Ruwaito shi saga Salim ibn Abilja'ad daga  Sauban).

Ita ce wadda kauna/soyayya da tausayi yake tabbata da ita kamar yanda Allah (SWT) ya fada a cikin Alqr'an, radadin rabuwa da ita yafi tsanani sama da na mutuwa,wani lakacin ma yafi tsanani sama da kariyar arziki, yafi tsanani sama da barin wurin zama(gida) musamman idan akwai alaqa a tsakanin su (zumunta) ko kuma suna da  'ya 'ya a tsakanin su wadan da rabuwar zata jefasu cikin yanayi na kunci da  tozarta da kuma  gurbacewar dabi'un  su"
(📚majmu'ul fatawa 35/299)

🕌🕌COMMITTEE FOR SOCIAL MEDIA MASJID ABU HURAIRA TSAFE ZAMFARA STATE (07039140450)

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 007

*GORON SALLAH*1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na takwas(008)_

``` √ AKIDATUL BADA’A.

Akidatul Bada’a rukuni ce daga cikin rukunnan
addinin Shi’a, akidatul bada’a tana nufin Allah
yana yin kuskure a cikin ayyukansa da
maganganunsa. Sai daga baya ya gano kuskure
ne, sai ya canza. Sun sanya ta a cikin rukunnan
addinin su domin su watsar da nassosa na
shari’ar musulunci da nuna duk abunda musulmi
ya yarda da shi to Allah ya canzashi bayan ya
gano kuskurene. A takaice dai a wajen su Allah
yana jahiltar wasu ayyuka da magan-ganunsa,
wanna akidar tana daga cikin mafi munin akidar
su domin suna nuna tozarci da kasawa da jahilci
ga Allah wadanda duk sunkoru ga reshi (SWT).
Shi kuma Mahadin sunnah, ingantacciyar ruwaya
ta zo game da shi cewa yana daga cikin tsatson
Hassan bin Aliyu
(R.A).
Daga karshe yaku bayin Allah, wannan yar
takaitattar nasiha ce da tayi bayani akan micece
Shi’a da miyagun akidunta saboda haka ne
malamai sun yi hukunci cewa ‘Yan Shi’a kafirai
ne, kuma zindikai ne.
Imamu Malik yace “Wanda yake zagin sahabban
Manzon Allah ba shi da rabon muslunci” (Wato
ba musulmi bane)
Imamu Ahmad bin Hambal yana cewa “ba’a
auren mata ‘Yan Shi’a, kuma ba’a cin yankansu
domin sunyi ridda sun bar musulunci. Kaga anan
Imamu Ahmad yana nufin idan har baya halatta a
auri diyan su mata to min babi aula kenan mu
musulmai baya halatta mu basu aure, duk da
cewa addinin muslunci ya halatta auren
ahlulkitabi, wannan yana nuna munin Shi’a sama
da Yahudu da Nasara.
Manufar wannan bayanin bayana nuna karanta
darajar Aliyu ko ahlulbaiti bane, lallai
ahlussunnah suna son Aliyu da ahlulbaiti da
sauran sahabbai. Shi’a ita ce kungiya mafi hadari
ga addinin muslunci, domin suna kashe musulmai
suna kyale masu bautar gumaka, suna zagin
Sahabbai amma a hakika Annabi suke zagi
Imamu San’ani yana cewa “al-ummar musulmi ta
hadu akan kafircin Shi’a Imamiyya
Sheikh bin Baz yace “Shi’a Rafida da kumaini
suna kan shirka babba
Sheikh Albani yace “Lallai abun da kumaini yake
kira akan shi na cewa sahabbai sun juyar da
Qur’ani wannan kafirci ne babu shakka
Don haka babu wadanda sukafi ahlussunnah son
ahlulbaiti da sauran sahabbai da magabata gaba
daya
Kamar yadda Imamu Shafii ya kawo a cikin
diwaninsa
Ya ku ahlulbait Rasulullah, lallai Allah ya farlanta
sonku kamar yadda ya saukar a cikin Qur’anin sa
Ya isheku girman alfahari duk wanda yayi salati
ga Manzon Allah bai sanya kuba to bashi da
salati.

DA WANNAN NE MUKA KAWO KARSHEN
WANNAN RUBUTU, MUNA GODIYA GA MASU
BIBIYARMU A KODA YAUSHE, ALLAH YA
AMFANAR DAMU DA ABUNDA MUKA KARANTA,
YA KARA TSAREMU DAGA MIYAGUN AKEEDU.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 006

*GORON SALLAH* 1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na shida(006)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA IMAMA.

Imama a wajen ‘Yan Shi’a tana dai-dai da
Annabawa a wajen musulmi, don haka ma suka
ce imamansu (12) ma’asumaine (Basu yin laifi)
“Yan Shi’a sun kudurce cewa lallai Imama baza
ta kasan ce ga kowaba sai ga Aliyu da diyan sa
(12) kuma sun sanya wannan a cikin rukunnan
imani suka ce duk wanda yayi kudurin Imama ba
ga Aliyu ko diyansa ba to ya kafirta kafirci mai
girma.
Hakika malaman sunnah sun hadu akan cewa
wadanda suka can-canta da halifanci bayan
Manzon Allah gasu kamar yanda suke a jere: -
Abubakar, Umar, Usman, sannan Aliyu, kuma
haka suke a wajen falala.
Ma’ana: Abubakar shine mafifici, sannan Umar,
sannan Usman, sannan Aliyu. Malaman suka ce
duk wanda yace Aliyu yafi Abubakar da Umar
falala to shi dan bidi’a ne.

√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA ILIMIN FIQIHU.
‘Yan Shi’a sun sabama ahlussunah dangane da
ilimin Fiqihu saboda basu karbar hadisai
ingantattu da sunnoni da aka ruwaito a cikin
littafan sunnah.
‘Yan Shi’a mabukata ne ta bangaren fahimtar
sunnah.
Sun kir-kiri bidi’o’i a cikin kiran sallah kamar
haka:
Suna karawa da Ash-hadu anna Aliyu
Waliyuullah, Madadin Ash-hadu anna
Muhammadarrasulullah
Sun kir-kiri bidi’o’i ta bangaren sallah kamar
haka:
Suna hada sallah ba tare da wani uzuriba
Basu yarda da sallar juma’a ba ko da a zahiri
anga sunayi.
Sun haramta cin zomo
Sun halatta auren mutu’a
Duk wadannan haramunne ga Ijma’in malamai.
ALLAH YA KARA TABBATAR DAMU AKAN
HANYA MADAIDAICIYA.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```