*GORON SALLAH* 1438/2017
*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*
*_WALLAFAR:_* *Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)*
_Fitowa Na shida(006)_
```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA IMAMA.
Imama a wajen ‘Yan Shi’a tana dai-dai da
Annabawa a wajen musulmi, don haka ma suka
ce imamansu (12) ma’asumaine (Basu yin laifi)
“Yan Shi’a sun kudurce cewa lallai Imama baza
ta kasan ce ga kowaba sai ga Aliyu da diyan sa
(12) kuma sun sanya wannan a cikin rukunnan
imani suka ce duk wanda yayi kudurin Imama ba
ga Aliyu ko diyansa ba to ya kafirta kafirci mai
girma.
Hakika malaman sunnah sun hadu akan cewa
wadanda suka can-canta da halifanci bayan
Manzon Allah gasu kamar yanda suke a jere: -
Abubakar, Umar, Usman, sannan Aliyu, kuma
haka suke a wajen falala.
Ma’ana: Abubakar shine mafifici, sannan Umar,
sannan Usman, sannan Aliyu. Malaman suka ce
duk wanda yace Aliyu yafi Abubakar da Umar
falala to shi dan bidi’a ne.
√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA ILIMIN FIQIHU.
‘Yan Shi’a sun sabama ahlussunah dangane da
ilimin Fiqihu saboda basu karbar hadisai
ingantattu da sunnoni da aka ruwaito a cikin
littafan sunnah.
‘Yan Shi’a mabukata ne ta bangaren fahimtar
sunnah.
Sun kir-kiri bidi’o’i a cikin kiran sallah kamar
haka:
Suna karawa da Ash-hadu anna Aliyu
Waliyuullah, Madadin Ash-hadu anna
Muhammadarrasulullah
Sun kir-kiri bidi’o’i ta bangaren sallah kamar
haka:
Suna hada sallah ba tare da wani uzuriba
Basu yarda da sallar juma’a ba ko da a zahiri
anga sunayi.
Sun haramta cin zomo
Sun halatta auren mutu’a
Duk wadannan haramunne ga Ijma’in malamai.
ALLAH YA KARA TABBATAR DAMU AKAN
HANYA MADAIDAICIYA.
HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```
No comments:
Post a Comment