Monday, 15 October 2018

001 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE,
DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na daya 001_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*MUKADDIMA*

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki Wanda ya wajabta mana tsarki, tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya karantar damu yadda zamuyi tsarki.

_Bayan Haka;_
Insha Allahu kamar yadda muka alkawarta muku cewa zamu fara kawo muku karantarwa akan ibada da sauransu, yanzu zamu fara daga yau har zuwa lokacin da muke iyawa insha Allahu.
Mun tsara Abubuwan daki-daki, zamu fara da magana akan tsarki kafin sauran, zamuyi kokarin ganin kullum munyi sau daya, filin tambaya a bude yake insha Allahu.

*TSARKI DA YADDA AKE YINSA A MUSULUNCI*

*Shimfida:*  Mu sani ya 'yan-uwa masu albarka,
wannan addini na musulunci addinine da yake
cikakken addini ta kowane bangare, bai takaitu
ga alwala da sallah ba kawai, ya shafi kowane bangare na rayuwa, kamar tsafta kiwon lafiya
zamantakewa, kasuwanci taimakon juna, tsare-
tsaren gudanarwa dadai sauransu.
A yanzu zamu kawo bayanai da suka shafi tsarki, dame-dame ake yiwa tsarki? Me rashin tsarkin yake jawowa? Ya ladubban yin tsarkin
suke? Ya ake shiga makewayi? Dadai sauran wadansu batutuwa da suke da alaka da wannan
maudu'i, da fatan Allah ya yi mana jagora ya
kuma fahimtar da mu.

*ABUBUWAN DA AKEWA TSARKI:*

Ana yin tsarki ne
daga dukkan abinda ya fito ta daya daga
mafita guda biyu ko ma ta duka inbanda hutu (tusa). Kenan ana yiwa fitsari, bayan gida maniyyi maziyyi jinin al'ada….tsarki, kawai dai idan mutum yana da alwala sai ya yi tusa to
alwalar kawai zai sake ba sai ya dauki buta ya yi tsarki ba.

Insha Allahu zamu dakata anan sai lokaci Na gaba.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim siraj uba ats-tsamawy(ABU-SINAN)*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN:

*MUKYAUTATA NIYYA*
wa.me/+2348064734911

*KARATTUTUKAN MALUMAN SUNNAH*
wa.me/+2349031666613

Monday, 8 October 2018

SHAWARAR UMMU JURAIJ GA YAN UWA MATA

GAREMU MATA,SHAWARA CE KAWAI!!!.

Duba da yanda Allah ya halicce mu ,yasa nake ganin ya kamata mu Dan nutsu kadan mu gane muna da tawaya da kuma matsaloli a tare damu.
Duk inda aka duba koda Asibiti ko wurin magani za a tarar  mata munfi maza damuwa da kuma yawan lalurori.
Haka bangaren shedanci mata munfi yawa.
Sannan bangare tsafi da tsubbu mune a gaba.

Wani Malami Yace  "Idan Namiji ya zama Ustaz za a ga abin kamar wani abu gama gari,amma kafin mace ta zama ustaziya completely sai anci baqar wuya,zaka ganta dai kamar Ustaziya amma daga shedan ya Dan hura ta sai kaga ta zama wata qaramar shaidaniya ko 'Yar bori,amma Duk barnar 'ya mace indai akwai tsoron Allah a tare da ita da kuma ilimi kana fara Mata nasiha da wa'azi zata nutsu sa6anin wacce ta rasa wannan abubuwa guda 2,ita mace dole sai kayi haquri da wasu dabi ah NATA".Kuma na yarda da wannan maganar tasa,haka muke.

Hakan yasa naga ya kamata mudan riqe wannan domin samun nutsuwa a rayuwar mu ta yau da gobe,saboda yanda zamu ga mun zama abubuwan wasan  shaidanu,su shiga jikinmu sanda suka so su kuma fita sanda suka ga dama,Allah ya qare mu da lafiya baki daya.

Ki Tabbatar kina wadannan abubuwan koda kina da lalura ko baki da ita don Allah na roqeki.

*Karanta koda Rabin izu ne na Qur'ani kullum duk kasalarki ko simini 1 ki daure kiyi,a hankali zakiji kina qara yawan karatun idan kika saba,ko kinji kamar kin dauki dala da gwuron dutse idan za kiyi karatun ki fadawa zuciyar taki dole sai kinyi,don wata tace min " idan zata karanta Qur ani ji take kamar zata mutu".

*ki nemi (hisnul Muslim) Littafi ne,ki ajiye akusa dake ki duba a hankali akwai Azkar Wanda za kiyi da safe da kuma Wanda za kiyi da yamma,ko unguwa zaki je kidan  saka shi a jaka idan lokacin yi yayi ki dakko kiyi.

*Idan kika kama ruwa bayan fitsari ki Dan daure kiyi alwala ko ba ko da yaushe ba amma kidan dinga kokartawa kina yi.Zama da alwalan  yana da kyau koda kina Haidha kiyi.

*Yar uwa kina sallame sallar farilla ki karanta ayatul,kursiyyu,falaqi,Naasi,Qul huwal lahu(ikhlas)ko wacce 3,ki Dora da amanar rasul,barinma ki qara da subhanallahi 33,Alhamdulillah33,Allahu akbar33 ,ki yima Annabi (SAW)salati ,nan take zaki ji wani sanyi da nutsuwa aranki.

*Kin farka daga bacci kinyi Addu ah,zaki shiga ban daki kinyi addu'ah,zaki fito kinyi addu ah,zaki zauna kince Bismillah,zaki ci Abinci kinyi addu ah,kin gama ci kinyi Addu ah,zaki sanya tufafi koda bismillah kice,zaki cire Ki ambaci hakan,zaki fita daga gida kinyi addu ah,kin dawo zaki shiga gida kinyi addu ah,komai zaki yi na aiki ko baki iya addu arba,kawai ambaci "Bismillah".

*Ki Dan dinga zama kina Nazarin abubuwan da Ki kasan Haram ne ki kudirce fara ragewa,a hankali sai Allah ya dafa mana,kamar jin kada kada-kade,kallo mara amfani,sai fa muna ragewa Nasan muna son nishadi amma Reduction yayi a rayuwa,kamar zama ba dan kwali duk sai mun dinga kula ,Idan muna zaune bama komai muyi ta istigfari,hailala,salati da sauransu.

Guarantee na baki idan bakya yi ki fara daga yau zaki ji wani chanji na musamman acikin Duniyar ki.Allah yasa mu dace baki daya Ameen.

✍ummu juraij

Monday, 19 March 2018

AZUMIN WATAN RAJAB(SUNNAH KO BIDI'AH)?

🌺🍇🍏🌹🌷🌼🌸💐🌺
*AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???*
🌺💐🌸🌼🍇🌷🌹🍏🌺

Rubutawa: *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

بسم الله الرحمن الر حيم

```Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya chanchanci a bauta masa shi kadai kuma ya hanemu da shirkah, Tsira da Aminci su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w wanda ya tsoratar damu daga aikata bidi'ah.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda ganin ya dace mu fadakar da yan uwa musamman iyaye da kakanni da ake zalunta da hadissan karya, dangane da falalar azumin watan Rajab.

Da farko dai shi watan Rajab yana daya daga watanni masu alfarma wanda aya ta 36 a suratu taubah tayi bayani.

✏✏✏✏✏✏✏✏
MAGANGANUN MAGABATA AKAN AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI)
✏✏✏✏✏✏✏✏

kai tsaye yanzu ga Wata tambaya da akayi ma sheikh bin baaz(R.H) dangane da azumin Rajab(azumin tsofaffi).

An tambayi sheikh bin baaz(R.H) akan cewa shin ko yana halatta azumtar watan Rajab (AZUMIN TSOFAFFI) gaba dayansa? Domin wasu Malamai suna fadar cewa: duk wanda ya azumci Rajab, an gafarta mashi zunubbansa koda sun kai yawan kumfar teku, wasu kuma malaman sunyi hani da azumtar watan suna cewa; duk da zamanshi cikin watanni masu alfarma baya halatta a azumceshi gaba daya???

Ga amsar da bin baaz ya bada, yana cewa; " Abun sani kawai shine ba'a shar'anta azumtar watan Rajab ba! Bari ma an karhantashi, abunda ya tabbata shine an shar'anta azumin sha'aban, manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumin sha'aban, yana azumtar sha'aban sai kadan yake  ragewa, amma Rajab an karhanta yin azumi a cikinsa, azumi a cikinsa yana daga cikin aikin jahiliyya, saboda masu azumtar basu da dalilin azumtar watan!!! Hadisan da ake yawo dasu akan falalar watan Rajab basu da asali, bari ma na karya ne wadanda basu inganta ba, abunda shari'ah ta shar'anta ga musulmai shine suci susha a watan Rajab, sai dai idan ya kasance kana yin azumin nafila tun kafin zuwan watan wanda su dama shari'ah ta tabbatar dasu, kamar; litinin da Alhamis, Ayyamul-beedh da sauransu, wannan yana da kyau kuma babu laifi, amma azumtar watan gaba dayansa, ko kuma baka saba yin azumin nafila ba sai da watan ya shigo sai ka fake da azumin nafila ka gabatar da na Rajab wannan shari'ah bata yadda dashi ba.
Wannan itace amsar da sheikh bin Baaz ya bada dangane da azumin tsofaffi na Rajab.

Hadisi ya tabbata daga Aisha matar Annabi Muhammad s.a.w tana cewa:كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يصوم حتى نقول لايفطر، ويفطر حتى نقول لايصوم، وما رأيته أكثر صياما منه في شعبان.
[صحيح أخرجه البحاري(١٩٦٩)، و مسلم(١١٥٦)].

Ma'ana; Aisha R.A take cewa; "Manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumi har sai nace bai cin abinci! Yana cin abinci har sai nace bai yin azumi(ma'ana yana yin azumi da yawa, haka kuma yana aje azumi ya huta sosai) ban taba ganin Manzon Allah s.a.w yana cika azumin wata daya ba sai dai idan ramadhan ne, ban taba ganin watan da yafi azumi a cikinsa ba face sha'aban.
[Bukhari da Muslim].

ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ " ‏( 25/290 ‏) :
" ﻭﺃﻣﺎ ﺻﻮﻡ ﺭﺟﺐ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ﻓﺄﺣﺎﺩﻳﺜﻪ ﻛﻠﻬﺎ
ﺿﻌﻴﻔﺔ ، ﺑﻞ ﻣﻮﺿﻮﻋﺔ ، ﻻ ﻳﻌﺘﻤﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻋﻠﻰ
ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻬﺎ ، ﻭﻟﻴﺴﺖ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﺮﻭﻯ ﻓﻲ
ﺍﻟﻔﻀﺎﺋﻞ ، ﺑﻞ ﻋﺎﻣﺘﻬﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﺿﻮﻋﺎﺕ ﺍﻟﻤﻜﺬﻭﺑﺎﺕ...

Shaikhul Islam Ibn taimiyyah (RH) y
ace: “Kebance watan rajab da yin azumi,
dukkan hadisan
da su ka zo akan haka da’ifai ne (masu
rauni), bari
ma hadisan karya ne, masu ilimi
basu amfani dasu, domin basu
cikin hadisan
da ake amfani dasu don nuna falalar
aikata abu,  bari ma dukkan su ma
hadisai ne
na karya..”
Duba Majmu’u Fatawa (25/290).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :
" ﻛﻞ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻲ ﺫﻛﺮ ﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻭﺻﻼﺓ ﺑﻌﺾ
ﺍﻟﻠﻴﺎﻟﻲ ﻓﻴﻪ ﻓﻬﻮ ﻛﺬﺏ ﻣﻔﺘﺮﻯ " ﺍﻧﺘﻬﻰ ﻣﻦ " ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ
ﺍﻟﻤﻨﻴﻒ " ‏(ﺹ 96 ‏)

Imam Ibnul Qayyim (RH) yace;
“Dukkan hadisan 
da suka ambaci azumin watan rajab da
sallatar wasu
darare a cikin sa, hadisai ne na karya kuma 
kirkirarru”.
Duba Almanarul Muniif (shafi 96).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺤﺎﻓﻆ ﺍﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﻓﻲ " ﺗﺒﻴﻴﻦ
ﺍﻟﻌﺠﺐ " ‏(ﺹ 11 ‏) :
" ﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ ﻓﻀﻞ ﺷﻬﺮ ﺭﺟﺐ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﺻﻴﺎﻣﻪ
ﻭﻻ ﺻﻴﺎﻡ ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻪ ﻣﻌﻴﻦ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺔ
ﻣﺨﺼﻮﺻﺔ ﻓﻴﻪ ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ﻳﺼﻠﺢ ﻟﻠﺤﺠﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ.

Alhafiz Ibn Hajar Al-Asqalani yake
cewa; “Babu
wani abu da aka ruwaito na falalar
watan Rajab,
ko yin azumi a cikin sa, ko azumtar
wasu adadin
kwanaki ayyanannu, ko tsayuwar
wasu darare
kebantattu”.
Duba Tabyinul ujub (shafi 11).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺳﻴﺪ ﺳﺎﺑﻖ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ " ﻓﻘﻪ
ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 1/383 ‏) :
" ﻭﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻟﻴﺲ ﻟﻪ ﻓﻀﻞ ﺯﺍﺋﺪ ﻋﻠﻰ ﻏﻴﺮﻩ ﻣﻦ
ﺍﻟﺸﻬﻮﺭ , ﺇﻻ ﺃﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻷﺷﻬﺮ ﺍﻟﺤﺮﻡ , ﻭﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ
ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺃﻥ ﻟﻠﺼﻴﺎﻡ ﻓﻀﻴﻠﺔ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ,
ﻭﺃﻥ ﻣﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻤﺎ ﻻ ﻳﻨﺘﻬﺾ ﻟﻼﺣﺘﺠﺎﺝ ﺑﻪ
" ﺍﻧﺘﻬﻰ

Imam Sayyid Sabiq (RA) yake cewa;
“Azumin
watan rajab bashi da wani fifiko na
falala akan
waninsa cikin watanni, sai dai shi
yana daga cikin
watanni (guda hudu) ma su alfarma,
kuma ba a
samu a cikin sunnah ingatacciya ba cewa
yin azumi a
cikin sa yana da falala kebantacciya,
abunda ya zo
akan haka (ma’ana hadisan da suka
zo) ba a kafa
hujja dasu (domin da’ifai ne)”
Duba Fiqhus-Sunnah (1/383).

ﻭﺳﺌﻞ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻦ ﺻﻴﺎﻡ
ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﻭﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺘﻪ .
ﻓﺄﺟﺎﺏ :
" ﺻﻴﺎﻡ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ
ﻟﻴﻠﺘﻪ ﻭﺗﺨﺼﻴﺺ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺔ , ﻭﻛﻞ ﺑﺪﻋﺔ ﺿﻼﻟﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ " ‏( 20/440 ‏)

An tambayi sheikh Muhammad Salihul Usaimeen
(RH)
dangane da azumi ranar 27 ga watan
rajab da
kuma tsayuwar dararen sa.
Sai ya amsa da cewa:
“Yin azumi ranar 27 ga watan Rajab
da tsayuwar
darensa kebance shi da haka bidi’a
ne, dukkan
bidi’a kuma batace”
Duba Majmu’u fatawa na Usaimeen
(20/440).

   Haka zalika Sayyidina umar R.A ya kasance yana bulala akan wadanda ke kamewa akan azumin Rajab, yana ce musu kuci abinci, wannan watane da ya kasance ake girmamawa a lokacin jahiliyya. [Ibn Abi shaibah ya fitar 3/102] da ibn kathir a cikin musnadil- faruk 1/285]

Haka zalika ibn umar R.A ya kasance idan yaga mutane suna wuce gona da iri akan Rajab, yana kyamar hakan!
[Sahih: ibn abi shaibah ya fitar 3/102]

Ibn Abbas ya kasance yana hani akan azumin Rajab gaba dayansa, saboda kada a maida shi ya zama abunda za'a rinka yi duk shekara, wato a maidashi ya zama idi.
[Sahih; Abdulrazak ya fitar 7854].

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISAN DA SUKA INGANTA AKAN WATAN RAJAB!
✏✏✏✏✏✏✏✏
=  "kuyi axumi a cikinshi kuma kuci abinci a cikinshi.
[Sahih irwa'ul galeel 958]

= Sha'aban yana tsakanin Rajab da Ramadhan, ana shagaltar da mutane akanshi(domin samun saukin Ramadan) a cikin sha'aban ake daukar ayukkan bayi, ina kwadayin/inason kada a daga ayyukana face ina azumi.
[Isnadinsa mai kyau ne, silsilatus-sahiha 1898]

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISSAI DA'IFAI WADANDA MASU AZUMIN RAJAB KE KAFA HUJJA DASU.!!!
✏✏✏✏✏✏✏✏

= A cikin Aljanna akwai wani gulbi, ana kiransa Rajab, ruwansa suna da fari wanda farin yafi na nono, duk wanda yayi azumin Rajab na rana daya, Allah zai shayar dashi daga wannan gulbin.[Silsilatu-dha'ifah 1898]

= Rajab watan Allah, Sha'aban wata na(manzon Allah), Ramadan watan Al'umma ta. 
Da'ifi ne, silsilatu-dha'ifah 4400]

= Darare guda biyar ba'a maida Addu'ah: 1. Farkon Daren Rajab

2. Daren Rabin watan sha'aban

3. Daren jumu'ah

 4. Daren karamar sallah

5. Daren babbar sallah

[Maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 1452]

= Rajab watane mai girma, Allah na lunka lada idan kayi aikin Alkhairi a cikinsa, duk wanda yayi azumin Rajab na kwana daya,kamar yayi azumin shekara. Duk wanda yayi na kwana bakwai, za'a rufe mashi kofofin wutar jahannama bakwai. wanda yayi na kwana takwas, za'a bude mashi kofofin Aljanna takwas. Wanda yayi na kwana sha biyar, mai kira zaiyi kira a sama yace; an gafarta maka abunda ya gabata na laifuka...[maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 5413]

✏✏✏✏✏✏✏✏
RUBABBUN HADISSAN DA YAN SHI'AH KE KAFA HUJJA DASU AKAN FALALAR WATAN RAJAB.
✏✏✏✏✏✏✏✏
Daga Baban hassan (A.S) yace; Annabi Nuhu (A.S) ya tuka jirgin ruwa a farkon watan Rajab, sai ya umurci wadanda ke tare dashi da su azumci wannan ranar, yace; "duk wanda ya azumci wannan ranar Allah zai nisanta shi da wuta na tsawon tafiyar shekara daya.

=Daga Abi Ja'afar, Muhammad ibn Aliyu(A.S) yace; duk wanda yayi azumi a Rajab na rana daya, a farkon Rajab ko tsakiyarsa ko karshensa, Allah ya wajabta mashi shiga Aljanna, kuma Allah zai sanya shi a tare damu a cikin darajojinmu na Ahlul baiti a ranar kiyama, wanda yayi na kwana biyu, Allah zai gafarta mashi duk zunubbanshi da suka gabata, wanda yayi na kwana uku, Allah zai gafarta mashi abunda ya gabatar na zunubi da wanda zaiyi a gaba sannan za'a bashi damar ceton yan uwanshi ma'abota zunubi...

= As-sadik Ja'afar  ibn Muhammad yace; "kada ka bari ranar ashirin da bakwai ga Rajab ta wuce ba tare da ka azumceta ba! Domin a ranar ne aka saukar wa Annabi Muhammad s.a.w Annabta...

Duka wadannan zaka samesu a cikin littafi mai suna FALALAR WATANNI UKU, wanda gingimemen malamin Shi'ah mai suna MUHAMMAD IBN ALIYU IBN HUSSAIN IBN MUSA AL-QUMMY ya rubuta.
Allah ka la'anci qummy.

  A takaice wadannan sune hujjoji na dangane da rashin ingancin azumin Rajab(azumin tsofaffi), duk wanda yake ganin akwai Gyara matukar gyaran nashi ya inganta hadisi ne ko aya ina maraba dashi kwarai da gaske.

Allah ya hadamu dani daku da sauran musulmai a cikin Aljannah.

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH...```

Copyright©
Dalibinku
*_Hashim Suraj Uba Tsamiya {ABU SINÃN}_*

☎08064734911
📞09030201868 
    08116194214

http://hashimtsamiya.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

17-07-1438AH
15-04-2017AC

Friday, 16 March 2018

تاريخ وفاة عظماء الاسلام

تاريخ وفاة عظماء الاسلام الذين يكثر السؤال عنهم :
📒محمد صلى الله عليه وسلم 11 هجري
📕 أبو بكر الصديق 13 هجري
📔 عمر بن الخطاب 23 هجري
📙 عثمان بن عفان 35 هجري
📘 علي بن أبي طالب 40 هجري
📗 عائشة بنت أبي بكر 57 هجري
📕 ابن عباس 68 هجري
📔 ابن عمر 73 هجري
📘 سعيد بن المسيب 94 هجري
📙 عمر بن عبد العزيز 101 هجري
📗 الحسن البصري 110 هجري
📕 أبو حنيفه 150هجري
📗 مالك بن أنس 179 هجريه
📘 الشافعي 204 هجري
📕 ابن راهويه 238 هجري
📙 أحمد بن حنبل 241 هجري
📗أحمد بن سعيد الدارمي 253 هجري
📘 عبد الله بن عبد الرحمن الدارمي 255 هجري
📔 البخاري 256 هجري
📕 مسلم 261 هجري
📗 ابن ماجه 273 هجري
📘 أبو داود 275 هجري
📙 الترمذي 279 هجري
📗عثمان بن سعيد الدارمي 280هجري
📔 النسائي 303 هجري
📕 ابن جرير الطبري 310 هجري
📘 ابن خزيمة 311 هجري
📕 ابن حبان 354 هجري
📙 الدارقطني 385 هجري
📔 الحاكم 405 هجري
📗 ابن حزم 456 هجري
📘 البيهقي 458 هجري
📕 ابن عبد البر 463 هجري
📔 الخطيب البغدادي 463 هجري
📗 ابن العربي 543 هجري
📘 ابن رشد الحفيد 595 هجري
📙ابن الجوزي 597 هجري
📔 القرطبي صاحب تفسير الجامع لأحكام القرآن 671 هجري
📕النووي 676 هجري
📗 ابن تيمية 728 هجري
📔 الذهبي 748 هجري
📘 ابن القيم 751 هجري
📙 ابن كثير 774 هجري
📗 ابن رجب 795 هجري
📔 ابن حجر العسقلاني 852 هجري
📗 السيوطي 911 هجري
📘 الأمير الصنعاني 1182 هجري
📕محمد بن عبد الوهاب 1206 هجري
📗الشوكاني 1250 هجري
📔 الألوسي 1342 هجري
📙 ابن سعدي 1376 هجري
📕 الشنقيطي 1393 هجري
📘ابن باز 1419 هجري
📗 الألباني 1420 هجري
📔 ابن عثيمين 1421 هجري
📔مقبل بن هادي الوادعي 1422 هجري

⭕ .. أرسلها للطلاب ..
⭕ .. أرسلها لقروب العائلة ..
💡.. ثقف من حولك من هم
.. عظماء الاسلام
-

Friday, 9 March 2018

INAA ZAKUJE YAN MATA???

INAA ZAKUJE YAN MATA???
Wannan muhadara tana da matukar muhimmanci
wallahi, musamman ga yan mata da kuma
iyayenmu mata, Dan uwa/yar uwa daure ka/ki
sauke wannan muhadara domin Amfanuwa.
� � � � � � � � �
� �
http://kiwi6.com/file/0i4idqba1f
Malamin da ya gabatar da wannan muhadara
shine:- ustaz musa s Lawal (Abu salih ibn salih)
Allah ya bada ikon saurara da kuma amfanu da
abunda mukaji
Hashim surajo uba Tsamiya
08064734911

Saturday, 3 March 2018

KO YANA HALASTA NA AURI DAN SHI'AH???

*KO YA HALASTA IN AURI DAN SHI'AH???*
Tambaya: Assalamu Alaikum, Allah ya karawa
Malam lafiya, nice wani Dan buraza(SHI'AH) ke
'SO' kuma aure yakeso muyi, Malam ya hallata
in aure shi ko kuwa??? Amsa: Wa'alaikumus-
salam, Toh wacce tayi wannan tambayar tana
sone dai mu tona ma shi'ah asiri, abunda zance,
shin kina iya auren Sunday? Ko Friday? Ko
peter? Ko Jonathan? Ko bush? Nasan amsarki
bazata wuce A'A ba, toh lallai haka baya halatta
ki auri Dan shi'ah!!! Saboda dashi da wadancan
basu da bambanci, kai idan ka duba cikin ﻣﻨﻬﺎﺝ
ﺍﻟﺴﻨﺔ Na ibn taimiyya, yake cewa: "kara
bayahude da Dan shi'ah, 'kara banasare
(kirista)da Dan shi'ah!!!" Meye hujja??? Yace
idan ka tambayi bayahude cewa suwaye sukafi
kowa Alkhairi a duniya bayan Annabi musa?
Zasu ce, sahabban Annabi musa, idan ka
tambayi kirista cewa suwaye sukafi kowa
Alkhairi bayan Annabi isah? Zasu ce, mutanen
Annabi isah(Hawariyawa), Amma idan ka
tambayi Dan shi'ah suwaye sukafi kowa sharri a
cikin duniya, zasu ce:sahabban Annabi
Muhammad s.a.w!!! Da wannan ne, sheikhul
Islam yace kara bayahude da Dan shi'ah, kara ba
nasare da Dan shi'ah, bugu da 'kari, koda ace
yayi takiyya ya nuna cewa shi ba Dan shi'ah
bane, sai bayan anbashi auren sannan ya fito da
akeedar, to ya zama wajibi Ga waliyyanki da su
gaggauta raba auren! saboda haka yar uwa
akwai bayani sossai, sai naji wani ja'iri yayi
magana sannan zan kara fito da wasu dalilan
kafircin yan shi'ah. Allah yayi mana jagora.

©copyright: Hashim surajo uba tsamiya(ABU-SINAN)

+2348064734911

http://
hashimtsamiya.blogspot.com

Tuesday, 30 January 2018

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN SHIRKA DA NAU'OINTA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#SHIRKA_DA_NAU'O'INTA

BAYAN mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka hakika banban abunda ALLAH yafi kauna shine riko da tauhidi, Kuma babban abunda ALLAH yafi kin shine shirka!!

ALLAH madaukakin na cewa "KU BAUTA MA ALLAH KADA KU HADA SHI DA KOWA"

lallai yan uwa musulmi mafi girman zunubi shine yin shirka da Allah....

ALLAH madaukakin na cewa yayi "DUK WANDA YAYI SHIRKA DA ALLAH MAKOMAR SHI WUTA (idan ya mutu bai tuba ba)"

Sannan kuma Allah na cewa "LALLAI ALLAH BAYA GAFARTAWA IDAN AKAYI SHIRKA DASHI AMMA YANA GAFARTA WANI LAIFIN WANDA BA SHIRKA BA GA WANDA YASO"

Yan uwa musulmi hakika Allah ya tsoratar da dukkan annabawan da ya aiko game da Shirka,  ALLAH yana cewa "MUNYI WAHAYI GAREKA DA WADANDA SUKA GABACE KA IDAN KAYI SHIRKA LALLAI DUK AYYUKAN KA SUN LALACE"

Yan uwa musulmi mu duba girman Annabawa amma Allah yace masu idan suka yi shirka ayyukan su sun lalace balle mu, Wannan kiran fa ba Allah yana nufin Annabawa ba!!

A'a ana nufin mu, Domin annabawa basu yin shirka...

Yan uwa musulmi idan muka diba musulmi fa yawa sun fadawa shirka da sanin su wasu kuma bada sanin su ba!!

ALLAH madaukakin sarki na cewa "DA YAWAN SUNYI IMANI AMMA SUN HADA ALLAH DA WANI"

Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya gargade mu gargadi mai tsauri yana cewa "lallai abunda nafi tsoratar maku a rayuwar Ku shine shirka karama"

Wata rana Abubakar assidiq radiyyallahu anhu yaje wajen Manzon Allah sai Manzo Allah yace mashi lallai shirka tana nan cikin musulmi, Lallai shirka tafi boyuwa a cikin Ku Sama da tururuwa a saman bakin dutse cikin dare "

Amma ga wata addua da zaka rika karanta wa domin neman kariya kace" YA ALLAH INA ROKONKA KA GAFARTA MANI KA KARENI DAGA SHIRKA "

NAU'OIN SHIRKA

*Rokon kabari, Sau da yawa zaka ga wasu masu karancin islamiyya suna zuwa rokon kabari, Ko aljanu ko waliyai ko annbawa Alaihis salam

Alhalin Allah madaukakin sarki ya haramta hakan har ma ya fada cikin suratul ahkaf cewa" BABU BATACCE IRIN MAI KIRAN WANIN WANIN ALLAH "

Kuma duk musulmi mai imani ya amince cewa kiran WANIN Allah shirka ne, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Roko ibada ne " Dan haka duk wanda ya roki WANIN Allah dan neman biyan wata bukata ko neman kariya hakika yayi shirka!!

* Kudurta cewa wani  na cutar wa...

Sau da yawa idan wani abu yafaru da dan Adam sai ya dora laifin bisa wani abu, Ko dora shi ga wani dalili ko kuma cewa ai wane ne dalili da sauran su...

ALLAH madaukakin sarki yace "IDAN ALLAH YA KAWO MAKA CUTA BABU MAI IYA DEBE MAKA ITA SAI SHI"

*SHIRKA TA HANYAR YIN MAGANA...

sau da dama wasu na fadar wasu maganganu alhalin shirka ce, Kamar cewa 'Taya Allah kiwo yafi Allah na nan'!

Kamar cewa Idan Allah ya yarda tare da wane, Ba' a cewa hakan nan cewa ake yi idan Allah ya yarda sannan wane ya yarda, Kaga dole sai ka fara sanya Allah farko.

Sannan masu cewa mun dogara ga Allah mun dogara gareka,  Huzaifa ya ruwaito cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada Kuce abunda ALLAH yaso da abunda wane yaso"

* JINGINA NI'IMAH GA WANI ABU....

jjngina samuwar Ni'ima ga wani abu kamar aiki, Ko sana'a ko, Alhali yin haka sanya wa Allah kishiya ne, Allah kuma yace "KADA KU SANYA MA ALLAH KISHIYA"

* SIHIRI...

Yanzu yawan yin sihiri ya yawaita cikin musulmi, A yanzu yadda sihiri yazama ruwan dare ya koma wa wasu kamar jini, Saboda yawan yin sihiri har sanya wasu anan Zamfara na Jefa Alqur'ani Mai tsarki cikin makewayi (Toilet) subhannallah...

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yaje wurin boka ko dan sihiri ya karyata abunda aka saukar wa Manzo Allah (Alqur'ani)" 

* YIN RANTSUWA DA WANIN ALLAH...

wasu nada tabi'ar yin rantsuwa da, kaddara ko lokachi ko iyaye da sauran su, Har munzo zamanin da akafi yarda da rantsuwar da akayi ba Allah a ciki...

* IZGILI DA WANI ABUN ADDINI....

wasu kuma nada tabi'ar yin izgili da Abubuwan addini kamar, Gemu hijabi, aswaki, Yawaita sallama da sauran su.

* RATAYA LAYA KO KARHU

Daga cikin musulmi akwai masu tabi'ar daura laya ko karhu ko guru ko qaho da sauran su, Da sunan samun kariya ko wani abu, Wannan duk shirka ne.

*JIBINTAR KAFURAI
wasu nada tabi'ar jibintar kafurai fiye da musulmai, Alhali basu son Allah kuma basu son Manzon Allah.

Tabbas duk wanda ya fada shirka tabbas ya halaka, Duniya da Lahira.

ABUBUWAN DAKE SAMUWAR MAI YIN SHIRKA

- Rayuwar mai shirka tana lala cewa.

- Kullum cikin tashin hankali mai shirka ke kasancewa.

-Cirewar natsuwa daga rayuwa.

- shiga cikin batattu domin Allah yace "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA BACE"

-Rosa ayyukan bawa, Duk wanda yayi shirka ya roza ayyukan shi.  ALLAH madaukakin sarki ya cewa Manzo Allah cewa "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA LALATA AYYUKAN SHI"

-DUSHE HASKE.

duk mai yin shirka Allah zai sanya wa rayuwar shi duhu, Baya taba ganin hasken alkahri.!!

Yan uwa musulmi hakika shirka tana tauye imani, Lallai yazama wajibi garemu muyi watsi da duk abunda zai kowa mana tangarda a cikin imanin mu, Domin samun tsira gobe Kiyama mu da iyalan mu da yan uwan mu baki daya.
. Allah ka albarkaci rayuwar mu baki daya.

Allah kayi mana kariya daga shirka, Ka biya mana bukatun mu na alkhairi, Ya Allah Muna tawasuli da sunayen ka ka biya mana bukatun mu na alkhairi baki daya, Ya Allah kara albarka ga garuruwan mu kabamu lafiya da cikakken zama lahiya ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 01-5-1439
Friday 19-January - 2018 AB