Monday, 15 October 2018

006 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na shida 006_

Gabatarwa: *UMMU SUNAN*

🔸 *DAGA CIKIN ABUBUWAN DAKE WAJABTA WANKA.*

1⃣  ```FITAR DA MINIYYI TA HANYAR SHA'AWA, A CIKIN BARCI KO A FARKE.```

2⃣ ```SADUWA DA IYALI(JIMA'I)```

3⃣ ```FITAR JININ HAILA(Al'ada) KO NA BIQI(Na haihuwa)```

4⃣ ```MUTUWA```

✍ *AL-ALLAMA SHEIKH MUHAMMAD BIN SALIH AL-UTHAIMIN*
(RAHIMAHULLAH) YAKE CEWA;

1⃣ *FITAR DA MANIYYI TA HANYAR SHA'AWA, A CIKIN BARCI KO A FARKE;* Duk Wanda ya fitar da maniyyi a cikin barci, wanka ya wajaba a gareshi, saboda Wanda yake barci yana mafarki, idan mafarkin yasa ya fitar da maniyyi, yana wajaba yayi wanka a kowane hali.

2⃣ *SADUWA(JIMA'I);*
    Idan miji ya sadu da matarshi, yana wajaba wanka a garesu, saboda boyuwar hashafa a cikin al'aurar matarshi, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa;

➡ << Ruwa daga ruwa suke>> Ma'ana: wanka yana wajaba a lokacin da namiji ko mace suka fitar da maniyyi.

➡<< Idan miji ya zauna tsakanin gabobinta guda hudu(matarsa) kuma yaji dadi da ita, wanka ya wajaba a garesu, koda basu fitar da komai ba, wannan matsalar(SADUWA BA TARE DA FITAR DA MANIYYI BA) da yawa daga cikin mutane suna jahiltar wannan hukuncin, ta inda wasu mazan suke amfani da yatsunsu a wajen saduwa da iyalansu ba tare da fitar da maniyyi ba sai suki yin wanka saboda jahilcin dake addabarsu, Malam yace wannan al'amari akwai hadari a cikinsa kwarai da gaske, abunda yake wajibi shine mutum yasan cewa idan ya sadu da iyalansa koda bai fitar da komai ba, wanka ya wajaba a garesu(mijin da matar).

3⃣ *FITAR JININ AL'ADA KO NA HAIHUWA;*
   Ita mace idan HAILA tazo mata sai ta dauke, yana wajaba tayi wanka, saboda fadar Allah S.W.T;
  "KU NISANCI MATA A LOKACIN DA SUKE HAILA, KADA KU KUSANCESU HAR SAI SUNYI TSARKI, IDAN SUNYI TSARKI TOH SAI KUZO MASU TA INDA ALLAH YA UMURCEKU, LALLAI ALLAH YANASON MASU TUBA, KUMA YANASON MASU TSARKAKEWA".
  Da fadar Manzon Allah s.a.w cewa; " MAI HAILA IDAN TA KARE KWANAKIN HAILARTA, DA MATA WADANDA SUKA HAIHU IDAN JINI YA DAUKE MUSU, NA GARESU SUYI WANKA."

  Siffar yadda ake wankan haila da na haihuwa kamar siffar yadda ake na janaba yake, sai dai wasu malaman sun so a wankan haila ko haihuwa ayi da ganyen magarya, saboda shi yafi a wurin tsafta da tsarki.

4⃣ *MUTUWA;* Dalili akan wankan gawa shine fadar Manzon Allah s.a.w cewa; "KU WANKE TA SAU UKU, KO SAU BIYAR KO SAU BAKWAI KO FIYE DA HAKA IDAN KUNGA YIYUWAR HAKAN.....HADITH

Da fadar Manzon Allah s.a.w cewa; " KU WANKE SHI DA RUWA, DA GANYEN MAGARYA, KU RUFESHI DA TUFAFINSA"...(mutumin da ya mutu a arfa a lokacin Manzon Allah s.a.w)

Sai Malamai sukace; Su wadanda suka mutu, wanka Na wajaba garesu, sai sai dai wajabcin yana hawa akan yan uwansu rayayyu, saboda shi Wanda ya mutu komi nashi ya yanke, bazai iya aikata komai ba, saboda haka yan uwansu dake raye su zasu yi musu wanka, kamar yadda Manzon Allah s.a.w ya umurta da yin haka.

▪_________________
◼ *Majmu'u fatawa warrasa'il Na Sheikh Muhammad bin Salih Al-uthaimin, Mujalladi Na sha daya, babin wanka.*

SAI WANI LOKACI NA GABA INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE; *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

005 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na biyar 005_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*ABUBUWAN DA RASHIN TSARKI YAKE HANA AIKATAWA;*

    kamar yadda bayani ya gabata cewar tsarki
wajibine, to mu sani idan mutum bashi da tsarki baya halatta a gareshi ya aikata wadannan abubuwan da zasu zo;

1. *SALLAH:*
    Baya halatta ga wanda bashi da tsarki yayi sallar nafila ko farillah.

2. *SUJJADAR TILAWA:*

  Wato sujjadar da mutum zai yi idan yana karatun Alkur'ani mai girma sai ya kai wadansu gurare, domin ba shi da tsarki, duk da cewa malamai sun karawa juna sani akan wannan.

3. *DAUKAR ALQUR'ANI MAI TSARKI:*
     Idan mutum
bashi da tsarki to sai yayi tsarki kafin ya taba wannan littafi mai tsarki.

Wannan shine abunda ya sawwaka insha Allahu.

*A GABA ZAMUYI BAYANI AKAN HUKUNCIN JININ AL'ADA INSHA ALLAHU*


WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

004 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na hudu 004_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*CIGABA DA KAWO LADUBBAN ZAGAYAWA FITSARI KO BAYAN GIDA*

11. *KAUCEMA RAMI;*
    Ba'a yarda idan za ka yi fitsari ko bayan gida ka yi a rami ba sai dai idan
kai ka haka ramin, domin bakasan mike cikin ramin ba,
takan yiwu akwai mugun abu da zai iya cutar da kai.

12. *KAUCEMA WURAREN TSINUWA;*
    Wadannan wurare sune wuraren da mutane suke yawan
tsinema duk wanda ya yi musu bayan gida a wurin, wadannan wurare sune:
🔹 Inda mutane suke zama su huta, jikin bangone ko karkashin bishiya komadai inane.

🔹 Kan hanya: Akwai rashin mutunci mutum ya
zo kan hanya yayi bayan gida, wannan
dabi'a musulunci bai yarda da ita ba.

🔹 Mashayar ruwa: Hakanan baya cikin
karantarwar musulunci mutum ya zo inda al'umma suke diban ruwa rafi ne ko wani gulbi
ko gindin fanfo koma dai inane ya aikata wannan
ta'asa.
 
      Wadannan wurare uku musulunci ya
hana a aikata wannan danyan aiki a wurin, domin mutum yana jawa kansa tsinuwa, Allah ya tsaremu.

13 *NESA DA JAMA'AH;*
  Ana bukatar dukkan wanda zai yi bayan gida ya yi nesa da jama'a ta
yadda ba za su ganshi ba kuma ba za su ji nishin shi ba, bai dace ace kana bayan
gida mutane suna ganinka ko suna jin nishinka ba,
ko da a bayan bishiya ko ganyan kargo sai ka
boye, amma sau da yawa mutane suna tafiya a mota da motar ta tsaya sai ka ga kowa ya
tsaya dab da motar, sannan ba za'a tafi a barshiba.
14 *KADA KA FUSKANCI ALKIBLA;*
    Wato inda
mutum yake kallo lokacin sallah, kuma kada ya
juya mata baya, wannan idan a dajine, amma
idan a gidane to da sauki babu laifi.

ZAMU TSAYA A NAN SAI LOKACI NA GABA ZAMU KAWO ABUBUWAN DA RASHIN TSARKI YAKE HANA AYI SU INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MAKUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

003 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE,  DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na uku 003_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*LADUBBAN ZAGAYAWA FITSARI KO BAYAN GIDA*

   Akwai tsari da ladubba da musulunci yake da su a lokacin da mutum ya ke niyyar kewayawa, wannan zai nuna maka cewa musulunci yayi bayani akan komai, daga cikin ladubban akwai;

1. *AMBATON SUNAN ALLAH*

  Ana bukatar kafin ka shiga ka ambaci sunan Allah domin ba'a ambaton Allah a makewayi, kuma ka nemi Allah ya tsareka da
sharrin aljanu, domin irin wadannan wurare
matattarace ta su, kafin ka shiga sai ka fadi:
ﺑِﺴْﻢِ ﺍَﻟﻠﻪِ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﻋُﻮﺫُ ﺑِﻚَ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﺨُﺒُﺚِ
ﻭَﺍﻟْﺨَﺒَﺎﺋِﺚِ

Ma'ana: Da sunan Allah, Ya Allah lalle ni ina
neman tsarinka (Ka tsareni) daga sharrin aljanu maza da kuma aljanu mata. Idan kuma zaka fito sai kace:

ﻏُﻔْﺮَﺍﻧَﻚَ، ﺍَﻟْﺤَﻤْﺪُ ﻟﻠﻪِ ﺍَﻟَّﺬِﻱ ﺃَﺫْﻫَﺐَ ﻋَﻨِّﻲ ﺍَﻷَﺫَﻯ
ﻭَﻋَﺎﻓَﺎﻧِﻲ

Ma'ana: Ina neman gafarar Ka , Dukkan godiya
ta tabbata ga Allah wanda ya rabani da wannan
kazantar kuma ya bani lafiya.

Ka sani ba'a shiga bayi da dukkan wani abu da yake dauke da sunan Allah.!!!

2 Fara Gabatar Da Kafar Hagu Lokacin Shiga, kafar dama kuma lokacin fita.

3 *AYI A TSUGUNNE;*  
kada mutum ya yi fitsari ko bayan gida a tsaye, sai dai idan wurin kangone ko yana tsoron fitsarin ya fallatso masa,
sannan ba wanda zai ganshi, sai ya yi a tsaye.

4 *TABBATUWA A CIKIN SUTURA;*
   Ana bukatar kada mutum ya yaye al'aurar sa tun yana tsaye, sai ya tsugunna ya yi dab da kasa sai ya daga
suturarsa, domin ba'a yarda wani ya ga al'aurar
wani ba in ba miji da mataba, amma halin ko
unkula da wasu suke nunawa na bayyanar da
al'aurarsu ga kowa muddin jinsi gudane wannan
bai daceba, sai ka ji wani yace 'Ai duka
mazane, abinda kake da shi ina dashi', wannan
ba koyarwar musulunci bace, haka suma mata, wannan zai kaika ka ga maza sun tube
suna wanka lokaci guda a dakin wanka guda, haka suma mata, wai sun dauka abinda yake
haramun shine namiji ya ga al'aurar mace ko mace ta ga al'aurar namiji, kai wani lokaci kana
tafiya a cikin mota sai kai arba da wani
gabjejen kato yana wanka a rafi, wani kuma a gefen titi ya kafe mashin ko ya aje kayan tallansa, duk wadannan ba kyawawan halaye
bane, mutum musulmi ya nisance su.

5 *MUTUM YAFI BADA KARFI A KAFARSA TA HAGU;*
Kenan abinda akafi so shine mutum ya fi bayar da karfinsa a kan kafarsa ta hagu.

6 *YA BUDE TSAKANIN CINYOYINSA;*
  kenan kada ya matse, ballantana ya sa matsattsiyar tufa
wacce idan yana fitsari na gaban ne kawai zai
fita, sannan idan ya mayar cikin wando sauran
ya gangaro, Allah ya sawake.

7  *NISANTAR INDA RUWA YAKE;*
  musulunci bai
yadda mutum ya yi fitsari ko bayan gida a inda ruwa yakeba ko kusa dashi, dan wannan zai haifar da cututtuka.

8 *ANA SO MUTUM YA RUFE KANSA;*
  Ana son wanda yake bayan gida ya rufe kansa a daidai lokacin da yake yi, domin koda wani ya yi kuskuren ganinsa to shi bai ganshi ba, abin zai zo da
sauki, amma ba zaka ji dadi ba kana bayan gida ka hada ido da wani, wanda zai iya zama
dalibinka ne ko suruki ko da..,'

9 *KADA AYI MAGANA;*
  An hana mutum yana bayan gida yana Magana, sai dai idan akwai
dalili mai kwari, kamar ka ga makaho ya nufi
rijiya ko karamin yaro…'.

10 *KADA A TARI ISKA;*
An hana idan mutum zai yi bayan gida a dawa (daji) an hana ya tari iska,
domin zai busowa jama'a warin bayan gidansa, kenan sai ya yi nesa, ya kuma duba ina iska
take kadawa.
.............

ZAMU TSAYA A NAN SAI LOKACI NA GABA ZAMU KAWO MUKU SAURAN LADDUBBAN INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

002 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na biyu 002_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*HUKUNCIN TSARKI A MUSULUNCI*

     Tsarki wajibine, saboda haka
dukkan wanda dayan wadancan abubuwan da muka lissafa a rubutun daya gabata
suka same shi to dole yayi tsarki.

*ABUNDA AKE TSARKI DASHI:*  
   
   Abinda ake tsarki dashi a shari'ah shine ruwa mai tsarki mai tsarkakewa, wannan shi ake kira Istinja'u .

Saidai idan mutum bai sami ruwan ba sai ya yi da duwatsu a kalla guda uku, idan ya ga na
ukun ya fito a bushe ba wata laima shikenen, idan kuma akwai laima to sai ya kara su kai
biyar wuturi ake bukata (3,5,7,9…) wannan kuma
ana yinshi a fitsari ko bayan gida, sannan idan
ka sami ruwa ba sai ka sake ba, wannan
hukunci shi ake kira Istijmari , ka samu ka hada duka a lokaci guda, misali idan ka yi bayan gida
sai kasa tsinke ko takarda mara rubutu sai ka share sannan sai ka biyo shi da ruwa. Kenan
ba'a tsarki da yawu (miyau).
Kada asha'afa, idan aka yi la'akari da abinda ya fita da kuma abinda ya fantsamo maka, za'a raba tsarki zuwa gida biyu:

(1) Tsarkin Hadasi: Shine tsarkin abinda ya fita daga dayan mafita guda biyu, kamar fitsari,
maziyyi…'.

(2) Tsarkin Kabasi: Shine tsarkake abinda ya taba jiki ko tufafi ko kuma wuri, kuma ko
wannensu baya yiwuwa saida ruwa mai tsarki mai tsarkakewa.
Amma idan aka yi la'akari da girma ko rashin
girma za'a kasa tsarki zuwa gida biyu shima:

(1) Babba wanda ake kira Hadasul Akbar:
Ankira shi babbane domin ba'a tsarkaka daga gareshi sai an yi wanka, kamar fitar maniyyi, ko
saduwa, ko daukewar jinin al'ada ko na biki.

(2) Karami wanda ake kira Hadasul Asghar:
wanda yake tsarki ko alwala ta wadatar, kamar
fitsari ko maziyyi.
Yadda ake yi: Da farko mutum ya wanke
hannunsa na hagu kafin ya sa a wurin da zai
wanke, domin hannun sa ya koshi da ruwa,
sannan sai ya wanke wurin fitsari. Daga nan
kuma sai ya fara wanke wurin bayan gida, ana bukatar mutum
ya wanke al'aurar sa baki dayanta musamman
idan maziyyi ne ya fita.

Insha Allahu zamu dakata anan sai wani lokaci Na gaba zamu tashi bayani akan LADUBBAN SHIGA BAYAN GIDA/MAKEWAYI(TOILET).



WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN:

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

001 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE,
DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na daya 001_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*MUKADDIMA*

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki Wanda ya wajabta mana tsarki, tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya karantar damu yadda zamuyi tsarki.

_Bayan Haka;_
Insha Allahu kamar yadda muka alkawarta muku cewa zamu fara kawo muku karantarwa akan ibada da sauransu, yanzu zamu fara daga yau har zuwa lokacin da muke iyawa insha Allahu.
Mun tsara Abubuwan daki-daki, zamu fara da magana akan tsarki kafin sauran, zamuyi kokarin ganin kullum munyi sau daya, filin tambaya a bude yake insha Allahu.

*TSARKI DA YADDA AKE YINSA A MUSULUNCI*

*Shimfida:*  Mu sani ya 'yan-uwa masu albarka,
wannan addini na musulunci addinine da yake
cikakken addini ta kowane bangare, bai takaitu
ga alwala da sallah ba kawai, ya shafi kowane bangare na rayuwa, kamar tsafta kiwon lafiya
zamantakewa, kasuwanci taimakon juna, tsare-
tsaren gudanarwa dadai sauransu.
A yanzu zamu kawo bayanai da suka shafi tsarki, dame-dame ake yiwa tsarki? Me rashin tsarkin yake jawowa? Ya ladubban yin tsarkin
suke? Ya ake shiga makewayi? Dadai sauran wadansu batutuwa da suke da alaka da wannan
maudu'i, da fatan Allah ya yi mana jagora ya
kuma fahimtar da mu.

*ABUBUWAN DA AKEWA TSARKI:*

Ana yin tsarki ne
daga dukkan abinda ya fito ta daya daga
mafita guda biyu ko ma ta duka inbanda hutu (tusa). Kenan ana yiwa fitsari, bayan gida maniyyi maziyyi jinin al'ada….tsarki, kawai dai idan mutum yana da alwala sai ya yi tusa to
alwalar kawai zai sake ba sai ya dauki buta ya yi tsarki ba.

Insha Allahu zamu dakata anan sai lokaci Na gaba.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim siraj uba ats-tsamawy(ABU-SINAN)*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN:

*MUKYAUTATA NIYYA*
wa.me/+2348064734911

*KARATTUTUKAN MALUMAN SUNNAH*
wa.me/+2349031666613

Monday, 8 October 2018

SHAWARAR UMMU JURAIJ GA YAN UWA MATA

GAREMU MATA,SHAWARA CE KAWAI!!!.

Duba da yanda Allah ya halicce mu ,yasa nake ganin ya kamata mu Dan nutsu kadan mu gane muna da tawaya da kuma matsaloli a tare damu.
Duk inda aka duba koda Asibiti ko wurin magani za a tarar  mata munfi maza damuwa da kuma yawan lalurori.
Haka bangaren shedanci mata munfi yawa.
Sannan bangare tsafi da tsubbu mune a gaba.

Wani Malami Yace  "Idan Namiji ya zama Ustaz za a ga abin kamar wani abu gama gari,amma kafin mace ta zama ustaziya completely sai anci baqar wuya,zaka ganta dai kamar Ustaziya amma daga shedan ya Dan hura ta sai kaga ta zama wata qaramar shaidaniya ko 'Yar bori,amma Duk barnar 'ya mace indai akwai tsoron Allah a tare da ita da kuma ilimi kana fara Mata nasiha da wa'azi zata nutsu sa6anin wacce ta rasa wannan abubuwa guda 2,ita mace dole sai kayi haquri da wasu dabi ah NATA".Kuma na yarda da wannan maganar tasa,haka muke.

Hakan yasa naga ya kamata mudan riqe wannan domin samun nutsuwa a rayuwar mu ta yau da gobe,saboda yanda zamu ga mun zama abubuwan wasan  shaidanu,su shiga jikinmu sanda suka so su kuma fita sanda suka ga dama,Allah ya qare mu da lafiya baki daya.

Ki Tabbatar kina wadannan abubuwan koda kina da lalura ko baki da ita don Allah na roqeki.

*Karanta koda Rabin izu ne na Qur'ani kullum duk kasalarki ko simini 1 ki daure kiyi,a hankali zakiji kina qara yawan karatun idan kika saba,ko kinji kamar kin dauki dala da gwuron dutse idan za kiyi karatun ki fadawa zuciyar taki dole sai kinyi,don wata tace min " idan zata karanta Qur ani ji take kamar zata mutu".

*ki nemi (hisnul Muslim) Littafi ne,ki ajiye akusa dake ki duba a hankali akwai Azkar Wanda za kiyi da safe da kuma Wanda za kiyi da yamma,ko unguwa zaki je kidan  saka shi a jaka idan lokacin yi yayi ki dakko kiyi.

*Idan kika kama ruwa bayan fitsari ki Dan daure kiyi alwala ko ba ko da yaushe ba amma kidan dinga kokartawa kina yi.Zama da alwalan  yana da kyau koda kina Haidha kiyi.

*Yar uwa kina sallame sallar farilla ki karanta ayatul,kursiyyu,falaqi,Naasi,Qul huwal lahu(ikhlas)ko wacce 3,ki Dora da amanar rasul,barinma ki qara da subhanallahi 33,Alhamdulillah33,Allahu akbar33 ,ki yima Annabi (SAW)salati ,nan take zaki ji wani sanyi da nutsuwa aranki.

*Kin farka daga bacci kinyi Addu ah,zaki shiga ban daki kinyi addu'ah,zaki fito kinyi addu ah,zaki zauna kince Bismillah,zaki ci Abinci kinyi addu ah,kin gama ci kinyi Addu ah,zaki sanya tufafi koda bismillah kice,zaki cire Ki ambaci hakan,zaki fita daga gida kinyi addu ah,kin dawo zaki shiga gida kinyi addu ah,komai zaki yi na aiki ko baki iya addu arba,kawai ambaci "Bismillah".

*Ki Dan dinga zama kina Nazarin abubuwan da Ki kasan Haram ne ki kudirce fara ragewa,a hankali sai Allah ya dafa mana,kamar jin kada kada-kade,kallo mara amfani,sai fa muna ragewa Nasan muna son nishadi amma Reduction yayi a rayuwa,kamar zama ba dan kwali duk sai mun dinga kula ,Idan muna zaune bama komai muyi ta istigfari,hailala,salati da sauransu.

Guarantee na baki idan bakya yi ki fara daga yau zaki ji wani chanji na musamman acikin Duniyar ki.Allah yasa mu dace baki daya Ameen.

✍ummu juraij