📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
_Fitowa Na uku 003_
Gabatarwa: *UMMU-SINAN*
*LADUBBAN ZAGAYAWA FITSARI KO BAYAN GIDA*
Akwai tsari da ladubba da musulunci yake da su a lokacin da mutum ya ke niyyar kewayawa, wannan zai nuna maka cewa musulunci yayi bayani akan komai, daga cikin ladubban akwai;
1. *AMBATON SUNAN ALLAH*
Ana bukatar kafin ka shiga ka ambaci sunan Allah domin ba'a ambaton Allah a makewayi, kuma ka nemi Allah ya tsareka da
sharrin aljanu, domin irin wadannan wurare
matattarace ta su, kafin ka shiga sai ka fadi:
ﺑِﺴْﻢِ ﺍَﻟﻠﻪِ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﻋُﻮﺫُ ﺑِﻚَ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﺨُﺒُﺚِ
ﻭَﺍﻟْﺨَﺒَﺎﺋِﺚِ
Ma'ana: Da sunan Allah, Ya Allah lalle ni ina
neman tsarinka (Ka tsareni) daga sharrin aljanu maza da kuma aljanu mata. Idan kuma zaka fito sai kace:
ﻏُﻔْﺮَﺍﻧَﻚَ، ﺍَﻟْﺤَﻤْﺪُ ﻟﻠﻪِ ﺍَﻟَّﺬِﻱ ﺃَﺫْﻫَﺐَ ﻋَﻨِّﻲ ﺍَﻷَﺫَﻯ
ﻭَﻋَﺎﻓَﺎﻧِﻲ
Ma'ana: Ina neman gafarar Ka , Dukkan godiya
ta tabbata ga Allah wanda ya rabani da wannan
kazantar kuma ya bani lafiya.
Ka sani ba'a shiga bayi da dukkan wani abu da yake dauke da sunan Allah.!!!
2 Fara Gabatar Da Kafar Hagu Lokacin Shiga, kafar dama kuma lokacin fita.
3 *AYI A TSUGUNNE;*
kada mutum ya yi fitsari ko bayan gida a tsaye, sai dai idan wurin kangone ko yana tsoron fitsarin ya fallatso masa,
sannan ba wanda zai ganshi, sai ya yi a tsaye.
4 *TABBATUWA A CIKIN SUTURA;*
Ana bukatar kada mutum ya yaye al'aurar sa tun yana tsaye, sai ya tsugunna ya yi dab da kasa sai ya daga
suturarsa, domin ba'a yarda wani ya ga al'aurar
wani ba in ba miji da mataba, amma halin ko
unkula da wasu suke nunawa na bayyanar da
al'aurarsu ga kowa muddin jinsi gudane wannan
bai daceba, sai ka ji wani yace 'Ai duka
mazane, abinda kake da shi ina dashi', wannan
ba koyarwar musulunci bace, haka suma mata, wannan zai kaika ka ga maza sun tube
suna wanka lokaci guda a dakin wanka guda, haka suma mata, wai sun dauka abinda yake
haramun shine namiji ya ga al'aurar mace ko mace ta ga al'aurar namiji, kai wani lokaci kana
tafiya a cikin mota sai kai arba da wani
gabjejen kato yana wanka a rafi, wani kuma a gefen titi ya kafe mashin ko ya aje kayan tallansa, duk wadannan ba kyawawan halaye
bane, mutum musulmi ya nisance su.
5 *MUTUM YAFI BADA KARFI A KAFARSA TA HAGU;*
Kenan abinda akafi so shine mutum ya fi bayar da karfinsa a kan kafarsa ta hagu.
6 *YA BUDE TSAKANIN CINYOYINSA;*
kenan kada ya matse, ballantana ya sa matsattsiyar tufa
wacce idan yana fitsari na gaban ne kawai zai
fita, sannan idan ya mayar cikin wando sauran
ya gangaro, Allah ya sawake.
7 *NISANTAR INDA RUWA YAKE;*
musulunci bai
yadda mutum ya yi fitsari ko bayan gida a inda ruwa yakeba ko kusa dashi, dan wannan zai haifar da cututtuka.
8 *ANA SO MUTUM YA RUFE KANSA;*
Ana son wanda yake bayan gida ya rufe kansa a daidai lokacin da yake yi, domin koda wani ya yi kuskuren ganinsa to shi bai ganshi ba, abin zai zo da
sauki, amma ba zaka ji dadi ba kana bayan gida ka hada ido da wani, wanda zai iya zama
dalibinka ne ko suruki ko da..,'
9 *KADA AYI MAGANA;*
An hana mutum yana bayan gida yana Magana, sai dai idan akwai
dalili mai kwari, kamar ka ga makaho ya nufi
rijiya ko karamin yaro…'.
10 *KADA A TARI ISKA;*
An hana idan mutum zai yi bayan gida a dawa (daji) an hana ya tari iska,
domin zai busowa jama'a warin bayan gidansa, kenan sai ya yi nesa, ya kuma duba ina iska
take kadawa.
.............
ZAMU TSAYA A NAN SAI LOKACI NA GABA ZAMU KAWO MUKU SAURAN LADDUBBAN INSHA ALLAHU.
WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*
DOMIN SHIGA GROUPS DIN;
*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911
*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613
No comments:
Post a Comment