Monday, 15 October 2018

006 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na shida 006_

Gabatarwa: *UMMU SUNAN*

🔸 *DAGA CIKIN ABUBUWAN DAKE WAJABTA WANKA.*

1⃣  ```FITAR DA MINIYYI TA HANYAR SHA'AWA, A CIKIN BARCI KO A FARKE.```

2⃣ ```SADUWA DA IYALI(JIMA'I)```

3⃣ ```FITAR JININ HAILA(Al'ada) KO NA BIQI(Na haihuwa)```

4⃣ ```MUTUWA```

✍ *AL-ALLAMA SHEIKH MUHAMMAD BIN SALIH AL-UTHAIMIN*
(RAHIMAHULLAH) YAKE CEWA;

1⃣ *FITAR DA MANIYYI TA HANYAR SHA'AWA, A CIKIN BARCI KO A FARKE;* Duk Wanda ya fitar da maniyyi a cikin barci, wanka ya wajaba a gareshi, saboda Wanda yake barci yana mafarki, idan mafarkin yasa ya fitar da maniyyi, yana wajaba yayi wanka a kowane hali.

2⃣ *SADUWA(JIMA'I);*
    Idan miji ya sadu da matarshi, yana wajaba wanka a garesu, saboda boyuwar hashafa a cikin al'aurar matarshi, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa;

➡ << Ruwa daga ruwa suke>> Ma'ana: wanka yana wajaba a lokacin da namiji ko mace suka fitar da maniyyi.

➡<< Idan miji ya zauna tsakanin gabobinta guda hudu(matarsa) kuma yaji dadi da ita, wanka ya wajaba a garesu, koda basu fitar da komai ba, wannan matsalar(SADUWA BA TARE DA FITAR DA MANIYYI BA) da yawa daga cikin mutane suna jahiltar wannan hukuncin, ta inda wasu mazan suke amfani da yatsunsu a wajen saduwa da iyalansu ba tare da fitar da maniyyi ba sai suki yin wanka saboda jahilcin dake addabarsu, Malam yace wannan al'amari akwai hadari a cikinsa kwarai da gaske, abunda yake wajibi shine mutum yasan cewa idan ya sadu da iyalansa koda bai fitar da komai ba, wanka ya wajaba a garesu(mijin da matar).

3⃣ *FITAR JININ AL'ADA KO NA HAIHUWA;*
   Ita mace idan HAILA tazo mata sai ta dauke, yana wajaba tayi wanka, saboda fadar Allah S.W.T;
  "KU NISANCI MATA A LOKACIN DA SUKE HAILA, KADA KU KUSANCESU HAR SAI SUNYI TSARKI, IDAN SUNYI TSARKI TOH SAI KUZO MASU TA INDA ALLAH YA UMURCEKU, LALLAI ALLAH YANASON MASU TUBA, KUMA YANASON MASU TSARKAKEWA".
  Da fadar Manzon Allah s.a.w cewa; " MAI HAILA IDAN TA KARE KWANAKIN HAILARTA, DA MATA WADANDA SUKA HAIHU IDAN JINI YA DAUKE MUSU, NA GARESU SUYI WANKA."

  Siffar yadda ake wankan haila da na haihuwa kamar siffar yadda ake na janaba yake, sai dai wasu malaman sun so a wankan haila ko haihuwa ayi da ganyen magarya, saboda shi yafi a wurin tsafta da tsarki.

4⃣ *MUTUWA;* Dalili akan wankan gawa shine fadar Manzon Allah s.a.w cewa; "KU WANKE TA SAU UKU, KO SAU BIYAR KO SAU BAKWAI KO FIYE DA HAKA IDAN KUNGA YIYUWAR HAKAN.....HADITH

Da fadar Manzon Allah s.a.w cewa; " KU WANKE SHI DA RUWA, DA GANYEN MAGARYA, KU RUFESHI DA TUFAFINSA"...(mutumin da ya mutu a arfa a lokacin Manzon Allah s.a.w)

Sai Malamai sukace; Su wadanda suka mutu, wanka Na wajaba garesu, sai sai dai wajabcin yana hawa akan yan uwansu rayayyu, saboda shi Wanda ya mutu komi nashi ya yanke, bazai iya aikata komai ba, saboda haka yan uwansu dake raye su zasu yi musu wanka, kamar yadda Manzon Allah s.a.w ya umurta da yin haka.

▪_________________
◼ *Majmu'u fatawa warrasa'il Na Sheikh Muhammad bin Salih Al-uthaimin, Mujalladi Na sha daya, babin wanka.*

SAI WANI LOKACI NA GABA INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE; *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

No comments: