Wednesday, 7 December 2016

IBN TAIMIYYA BAI YARDA DA MAULIDI BA, HASALI YAYI FADA DA ITA...

🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴
*_IBN TAIMIYYA BAI YARDA DA BIDI'AR MAULIDI BA, HASALI MA YAYI FA'DA DA ITA_*
🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳

_001 Fitowa Na daya_

_Rubutawa:_ *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

بسم الله الر حمن الر حيم

```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai, Tsira da amincin Allah su tabbata ga Wanda babu wani Annabi bayansa, tare da iyalan gidansa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka;
Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda Wata 'karya dake yawo a kafofin sadarwa na zamani(social medias) akan cewa ibn taimiyya yace Maulidi halas ne, har ma yace akwai lada ga Wanda yayi. Maganar wacce suke sama mata gindin zama a cikin littafin shehin Malamin mai suna((I'KTIDA'UL SIRA'DUL MUSTAQEEM)).
Kafin bada amsa ga maganar ya kamata masu karatu kusan cewa Malamai ba ma'asumai bane! Suna dai dai suna kuskure.
Amma ga wata magana ta ibn Taimiyya akan maulidi;```
قال ابن تيمية-رحمه الله- ((فإن هذا [يعنى الإحتفال بالمولد] لم يفعله السلف مع قيام المقتضى له وعدم المانع منه، ولو كان هذا خير محضا أو راجحا لكان السلف رضي الله عنهم أحق به منا، فإنهم كانوا أشد محبة لرسول الله صلى الله عليه وسلم وتعظيما له منا، وهم على الخير أحرص، وإنما كمال محبته ةتعظيمه في متابعته، وطاعته واتباع أمره، وإحياء سنته باطنا وظاهرا، ونشر ما بعث به، والجهاد على ذلك بالقلب واليد واللسان، فإن هذه هي طريقة السابقين الأولين من المهاجرين والأنصار والذين اتبعوهم بإحسان...))    {اقتضاء صراط المستقيم ص ٣٥٠ دار ابن الهثيم}

_Ma'ana;_ *_"Ibn Taimiyya -Allah yayi masa Rahama- a cikin littafinsa [Iktida'ul siradul mustakim] yana cewa; Lallai wannan (Bukin maulidi) magabata basu aikatashi ba tare da suna da damar yin hakan kuma babu abunda zai hanasu, da wani aikin Alkhairi ne babba ko kuma mafi rinjaye da magabata-Allah ya yarda dasu- su sukafi cancanta  su aikatashi fiye damu, domin sun fimu son Annabi Muhammad Tsira da Aminci SU tabbata a gareshi da girmamashi kuma sun fi mu kwadayi ga Alkhairi, to amma abin da ke cikakken so da girmamawa ga Annabi shine bin sunnarsa, da yi masa biyayya da bin umurninsa da rayar da sunnarsa a boye da bayyane da kuma watsa abin da aka aikoshi dashi da kuma yin kokarin yadashi da Alkalami da hannu da kuma halshe, kuma wannan shine tafarkin wadanda suka gabacemu daga cikin muhajiruna da Ansar da wadanda suka bisu da kyautatawa._* [Iktida'u siradul mustakim shafi na 350]

   ```wannan shine abin da sheikhul Islam Allah yayi masa rahama ya fada game da bukin maulidi, kuma wannan karara yake cewa bidi'ah ne daga cikin bidi'o'i, Wanda yasa dole muyi yaki dashi.
   Sai dai yan bidi'ah saboda son rai da son zuciya sun bar wannan magana dake nuna cewa maulidi bidi'ah ne, sunyi riko da Abinda yayi dai dai da son rayuwarsu, kamar yadda dama wannan shine Al'adarsu Qur'an ma yayi bayani a cikin suratul [Ali imran aya ta 7]  daman su mutane ne masu son shubuha.
Su kuwa Ahlis Sunnah ba haka suke ba. Imamul wa'ki'i ibn jarrah yake cewa;```
((أهل السنة يكتبون مالهم وما عليهم، وأهل الأهواء يكتبون مالهم)).
[ذم الكلام للهروي ٣٣٨]

_Ma'ana;_ *_"Ahlus sunnah suna rubuta abinda yake hujja a garesu da Wanda yake hujja akansu, amma masu bin son zuciya (YAN BIDI'AH) suna rubuta abinda yake hujja garesu kawai._* [Zammul kalam 338]

```wannan rubutu zai zamo shimfida na warware wannan shubuha, fitowa ta gaba zanyi bayani akan maganar da ibn taimiyya ya fada wanda yan bidi'ah suke ganin cewa hujja ne garesu.
Allah ya karemu daga bin son zuciya da watsi da sunnar Manzon Allah, Allah ya tabbatar da dugaduganmu akan bin sunnah da aiki da sunnah.```


Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*
Https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya
📞08064734911
Http://hashimtsamiya.blogspot.com
atstsamawy@gmail.com

KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD S.A.W KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???

🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*KO YANA HALASTA YIN BIKIN MAULIDIN ANNABI MUHAMMAD S.A.W KO WANI DAGA CIKIN MAGABATA...!!!???*
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺

  _Fitowa ta biyu (002)_

     _Rubutawa;_ *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

*Godiya ta tabbata ga Allah Tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah s.a.w da mutanen gidansa da sahabbansa da duk Wanda yabi tafarkinsa da kyautatawa har tashin kiyama.*

_Bayan haka;_

_Nayi rubutu mai irin wannan take Wanda nace fitowa na gaba yana nan zuwa, to kuma insha Allahu zan cigaba da bada hujja akan haramcin Maulidi da kuma zamanshi bidi'ah abar kyama.  Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi huduba bayan ya godewa Allah, ya nemi taimakonshi da gafararshi daga karshe sai yace;_
(( أما بعد، فإن خير الحديث كتاب الله وخير الهدي هدي محمد صلى الله عليه وسلم وشر الأمور محدثاتها وكل بدعة ضلالة)).

_Ma'ana;_ *_"Bayan haka; Lallai fiyayyen zance shine littafin Allah, kuma fiyayyar shiriya ita ce shiriyar Muhammad s.a.w, kuma mafi sharrin al'amurra sune wadanda aka kirkiro, kuma dukkan bidi'ah bata ce"_* [Muslim ya ruwaito]

```Bayan wannan; yana daga cikin abunda yasa Malamai suka kyamaci bidi'ar Maulidi; bayan zamanshi bidi'ah, akwai haduwa mata da maza da wake wake da amfani da kayan kid'a (Badujala, piano,...) Da shaye shayen abubuwan dake sa maye, da wasu sharrance sharrance, wani lokaci Abunda yafi wadancan yana faruwa, wato shirka da Allah, ta hanyar wuce gona da iri wajen yabon Manzon Allah s.a.w ko waninsa kamar; Tijjani, Inyassi, jelani, Mahadi, Hussain,  yaa Ali, ko waliyi na wheelbarrow. Za kaga ana Addu'ah ana Neman agajinsu da taimakonsu ko fadar cewa Annabi Muhammad s.a.w yasan gaibi ko wani daga cikin waliyyai, wadannan abubuwa duk zaka samu suna faruwa a wajen Maulidi. Shi kuwa Annabin Rahama s.a.w cewa yayi;```
((إياكم والغلو في الدين، فإنما أهلك من كان قبلكم الغلو في الدين)).

_Ma'ana;_ *_"Ku kiyayi yin shishshigi a cikin Addini, saboda babu wani Abu Wanda ya hallaka wadanda suka gabace ku face shishshigi a cikin addini._*

A wani Hadisin Manzon Allah s.a.w cewa yayi;
((لاتطروني كما أطرت النصاري ابن مريم إنما أنا عبد فقولوا: عبدالله ورسوله))

_Ma'ana;_ *_"Kada Ku zurfafa wajen yabo gareni kamar yadda kiristoci suka zurfafa wajen yabo ga Dan Maryam(Annabi isah) ni bawa ne kawai, saboda haka kuce; bawan Allah kuma manzon Allah._* [Bukhari ya ruwaito]

```Abin mamaki shine zaka samu da yawa daga cikin mutane suna kokari wajen halartar wadannan tarurrukan na bidi'ah, kuma suna kare masu yinsu, amma kuma sai kaga basa halartar wuraren Neman ilimi, Inda za'a nuna maka yadda zakabi Allah da Manzonsa ba inda za'a nuna maka falalar karya ta waliyyan karya ba. Babu shakka wannan yana daga cikin raunin imani da kuma karancin basira, kuma yana nuna cewa tsatsa ta rufe zukatansu ta nau'o'in zunubai da sabon Allah.

    Allah ya karemu daga fadawa cikin shirka da bidi'ah da bata.

     SUNNAH SAK

             BIDI'AH SAM

   MAULIDI SAM SAM SAN SAM SAM

Wa'ka:

DA MAULIDI NE ALAMAR SON MANZO

     DAN FODIO DA BA ZAYA CE MAR BIDI'AH BA.```

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*
📞08064734911📞
Https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

Http://hashimtsamiya.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

Monday, 5 December 2016

ANYA KUNASON HUSSAINI???

*ANYA KUNASON HUSSAINI???*

```gaskiya wannan munafunci ne karara!
Shin wai goma ga Wata aka kashe Hussain ko Ashirin ga Wata???

Anya kunason shahada???

Anya kunason Hussaini???

Tsoron me ya hanaku fitowa a ranar goma ga Wata sai yau ashirin ga Wata???

Ko kuna tsoron Ayi fatahu Tsafe ne???

Meyasa kukayi shi tun da safe, sabanin lokuttan baya sai anyi la'asar???

Kunji kunya! Kunji kunya!! Kunji kunya!!!

Allah ya kyauta```

ALHAMDULILLAH.

*ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!!*

```A madadin kwamitin SHABABU AHLIS SUNNAH WALJAMA'AH TSAFE, muna farin cikin sanar daku cewa Mai gida kuma babban malaminmu, patron na wannan kwamiti, wato Sheikh Musa s lawal Tsafe (Abu salih ibn salih) ya samu nasarar lashe jarabawar karo karatu a jami'ar musulunci dake jamhuriyar Niger(digiri na biyu), muna taya Malam da sauran Abokanshi guda hudu murnar lashe wannan jarabawar.  Allah yasa ayo karatu mai amfani Wanda za'azo a cigaba da kwarara manashi a kwakwalenmu har sai mun fara tunbudinshi.

Hashim Surajo Uba Tsamiya ```

SUWAYE AKA KASHE TARE DA HUSSAINI A CIKIN AHLUL BAITI ALLAH YA YARDA DASU.???

*SUWAYE AKA KASHE TARE DA HUSSAINI A CIKIN AHLUL BAITI ALLAH YA YARDA DASU???*

*من قتل مع الحسين من أهل البيت رضي الله عنهم؟؟؟*

*_Yana daga cikin Abunda zakuji yan shi'ah na fada cewa suna son Ahlul baiti! Toh amma Sayyidina Hussain shikadai ne Ahlul baiti??? Sauran Yayan sayyidina Aliyu su ba Ahlul baiti bane???_*

```yana daga cikin soyayyar sayidina Aliyu ga khalifofin da suka gaba ce shi, sanya ma yayanshi sunayensu. Duk Wanda ya sanya ma dan shi sunanka soyayya ne yasa hakan ko gaba???
Daga cikin sunayen yayan sayyidina Aliyu da kuma yayan Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib wadanda aka kashe tare da Hussaini akwai;
√ Abubakar ibn Aliyu ibn Abi dalib! An kasheshi tare da Hussaini a karbala'a. Kai Dan shi'ah ka duba wannan littafi domin ka ganewa idonka; (Muntahal Amãl,1/528) zaka samu cikakken bayani.

√ Umar ibn Aliyu ibn Abi dalib! Shima ya samu shahada a Karbala'a tare da Sayyidina Hussaini. Ka duba littafin (kashful gummah, 1/440)

√ Usman ibn Aliyu ibn  Abi dalib! Shima ya zama shaheedi a karbala'a ka duba littafin (muntahal Amãl, 1/526-527)

Daga cikin wadanda suka samu shahada a Karbala'a akwai yayan sayyidina Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib, daga ciki akwai;

√ Abubakar ibn Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib! Ka duba cikin(Al-irshãd shafi na 186-248 ko kashful gumma, 1/575-580).

√ Umar ibn Hassan ibn Aliyu ibn Abi dalib! Shima Allah ya bashi shahada a karbala'a. Ka duba cikin(Mazãlimu Ahlul baiti, 254 ko i'ilamul wara, 112).

  Wadannan duk suna cikin Ahlul baiti Rasulul-llah, amma da yake Addinin shi'anci an ginashi ne akan karya da yaudara da siyasa. Sai kaji suna Ambaton sunan Hussaini kadai a matsayin Wanda ya samu shahada a Karbala'a. Saboda gabarsu da kiyayyarsu da masu wadannan sunaye!

Kurtugin shi'ah na Tsafe ina mai tabbatar maka cewa; matukar zaka rika gaba da Abubakar! Toh sai ka chanja sunan Uba!
Allah yayi mana tsari da jahilcin yan shi'ah da suke fama dashi, jahillan cikinsu kuma Allah ya cetosu.```

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya_*

SUNNAH NE YIN SALLAH DA TAKALMI

🔈🔉🔊🔈🔉🔊🔈
*SUNNAH NE YIN SALLAH DA TAKALMI, DAGA GROUPS DIN MUKYAUTATA NIYYA!!!*
📣📣📣📣📣📣📣

*Rubutawa:* *_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)_*

*Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa, muna Neman gafararSa, muna Neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, Wanda Allah ya shiryar babu mai iya batar dashi Wanda kuma ya batar babu mai iya shiryar dashi, kuma ina shaidawa babu abin bauta bisa cancanta sai Allah kuma ina shaidawa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne, yabo da godiya sun tabbata ga fiyayyen halitta Wanda  yace Wanda yayi mashi da'a Dan Aljanna ne, Wanda ya saba mashi Dan wuta ne!*
_Bayan haka:_

*وعن أبى سعيد رضى الله عنه قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: "إذا جاء أحدكم المسجد، فلينظر، فإن رأى فى نعليه أذى أو قذرا فليمسحه، وليصل فيهما.*
(أخرجه أبو داود، وصححه ابن خزيمة).

```Hadisi ya tabbata daga Abi sa'id(R.A) yace, Annabi Muhammad s.a.w yace: idan dayanku yayi Nufin zuwa Masallaci to ya duba idan yaga datti ko Wata 'kazanta a takalminshi, to ya goge sannan yayi SALLAH a cikinsu.```

Yan uwa mu lura, Manzon Allah s.a.w cewa yayi: *MU DUBA IDAN MUKA GA WANI DATTI KO KAZANTA MU GOGE MUYI SALLAH A CIKINSU!*  kuma hadisi ingantacce Wanda Abu daud ya fitar a cikin littafinshi kuma ibn khuzaima ya ingantashi. Imamu Nasirudden bn Albany ya ingantashi.
*Imamu Ahmad(imamu Ahlis sunnah waljama'ah) yake cewa: " من رد حديث رسول الله صلى الله عليه وسلم فهو شفا هلكة*
```Ma'ana: Duk Wanda za'ace ga Hadisi ingantacce amma ya tsaya jayayya yana son raddi ga Hadisin, imamu Ahmad yace yana gefen Halaka!

Ma'abota cewa ba'a SALLAH da takalmi ko zaku bamu hujjarku???``` 

*ABU SINAN* ```na jiran yaji rubabbun hujjojinku. Domin yasan inda kuka dogara.```

*_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*

Http://Hashim141473.mywapblog.com

ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAISAN GAIBU BA...!!! 001

*ANNABI MUHAMMAD S.A.W BAI SAN GAIBU BA...!!!*

*_Fitowa ta daya(01)_*

*_DAGA; Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINAAN)_*
*بسم الله الرحمن الرحيم*

  ```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda baya da Abokin tarayya. Tsira da Amincin Allah SU tabbata ga farin jekada   Wanda babu wani Annabi bayansa,Annabi Muhammad s.a.w tare da jama'ar gidansa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan takaitaccen rubutu saboda ganin yadda wasu yan bidi'ah ke cusa ma kananan yara Akeedar cewa Annabi yasan gaibu a makarantunsu Na Zawuyya da sauran Majami'oinsu.
Zan takaitu insha Allahu akan Qur'ani da hadisai ingantattu, saboda kada in kawo maganar wani malami na sunnah wani kuma ya kawo man ta Inyass ko wani shehi!
Ga wasu daga cikin Ayoyin Qur'ani dake nuna cewa Annabi baisan gaibu ba.```

*وعنده مفاتح الغيب لايعلمها إلا هو...*
_Ma'ana;_ *_kuma A wajenshi(Allah) makullan gaibu suke babu Wanda ya sansu sai shi(Allah)_*

*A wani wurin kuma Allah S.W.T cewa yayi;*
*_قل لايعلم من في السماوات والأرض الغيب إلا الله، وما يشعرون أيان يبعثون_*

_Ma'ana;_ ```Kace(yã kai Annabi Muhammad s.a.w) babu Wanda yasan gaibu a sama ko a kasa sai Allah, kuma basu San yaushe ne za'a tashesu ba(bayan mutuwa).```

*Idan kuma muka leka a suratu lukman aya ta karshe Allah S.W.T cewa yayi;*
*_إن الله عنده علم الساعة وينزل الغيث ويعلم ما فى الأرحم، وما تدرى نفس ماذ تكسب غدا، وما تدرى نفس بأي أرض تموت، إن الله عليم خبير_*
_Ma'ana;_ *_Lallai a wurin Allah ne Ilimin sa'a yake(Tashin kiyama) kuma shine ke saukar da girgije, kuma yasan Abunda ke cikin mahaifa, kuma babu Wata Rai da tasan Abunda zata Aikata a gobe ko Anjima, babu Wanda yasan a wace kasa ko a wane gari zai  mutu. Lallai Allah masani ne kuma mai bada labari ne._*

```Wadanan Ayoyi da na kawo dukkansu idan ka duba Tafsiran manyan Malamai wadan da ba son Rai a zuciyarsu, zaka samu sunyi cikakken bayani karara, babu boye boye ko shaci fadi, zaka samu babu Wanda ya kawo cewa Annabi yasan Gaibu.
Idan muka dawo a cikin hadissai kuwa, ga hadisi na biyu dake cikin AR'BA'UNA HADITH, Wanda tun bamu da wayo ake karantar damu shi, Hadisin Sayyidina Umar R.A Wanda imamu Muslim ya ruwaito, Lokacin da Mala'ika jibril lokacin da yake yima Annabi Muhammad s.a.w Tambayoyi, daga karshe yake tambayar shi;``` 
*فأخبرني عن الساعة: قال: ما المسئول عنها بأعلم من السائل....*
_Ma'ana;_ *_ka bani Labarin sa'a(Tashin kiyama)? Sai Annabi Muhammad s.a.w yace; Ai Wanda aka tambaya baifi Wanda yayi Tambayar sani ba._*
``` Shin idan  manzon Allah s.a.w yasan gaibu meyasa bai fada masa Ranar da za'ayi tashin kiyama ba???
Daga karshe inason in fadawa yan uwa cewa; Maganar gaskiya Annabi Muhammad s.a.w bai San gaibi ba sai Allah ya sanar dashi ta fuskar wahayi, amma kafin Allah yayi masa wahayi bai sani ba.

  Allah s.w.t Nike Roko da ya karemu da bin son zukatanmu, ya bamu ikon yin koyi da farin jekada Annabi Muhammad s.a.w a dukkanin Rayuwarmu.

Sai mun hadu a fitowa Na biyu insha Allahu```

Copyright©
*_Hashim Surajo Uba Tsamiya (ABU SINAAN)_*

Shiga link dake kasa mu hadu a Facebook
https://mobile.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya