Friday, 29 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN; MUHIMMANCIN SALLAR DARE

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

Bayan mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka yau khudbar mu zata yi magana ne game da #MUHIMMANCIN_SALLAR_DARE (kiyamul laili)

Yan uwa musulmi a makon da ya gabata munyi khuduba ne game da sallar nafila..

To yau in sha Allah Zamu yi magana ne game da Sallar Dare wato kiyamul laili.

Hakika Allah ya yabi masu yin sallar dare a cikin suratul sajadah, "ALLAH ya kan rokon sa kuma suna ciyar da abunda muka basu,  Suna tashi sallar dare,  suna da makoma ta kwarai"

Hakika saboda kaunar mu da Allah yake yi  ya bamu damar aikata ibadu kala kala har ma yakan bamu lada idan mun aikata.

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Mafificiyar sallah itace sallar nafila bayan ta sai sallar dare"

Hakama Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana cewa "Sallar da Allah yafi so itace sallar dare"

Yan uwa musulmi masu albarka lallai wannan sallar wato sallar dare tana karawa ihlasi.

Hakika tsayuwa cikin dare yana karawa bawa tsoron Allah da natsuwa, Hakama duk ranar da dan Adam yayi sallah to zaiji natsuwa da kwanciyar hankali.

Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace ma sahabin sa "In fada maka wata hanyar alkhairi??
Sai sahabin yace eh, Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace 'Ka yawaita azumin nafila, Da sadaqah domin sadaqah tana cinye zunubai kamar yadda ruwa suke kashe wuta sai kuma ka lizimci sallar dare"

Yan uwa musulmi masu albarka muhimmancin sallar dare baya misaltuwa, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "ALLAH yayi rahama ga wanda ya tashi yayi sallar dare"

Hakika yan uwa musulmi sallar dare tana cikin salloli masu karawa dan Adam ihklas.

Manzo sallal lahu alaihi wassalam shine baban abun koyi garemu baki daya, Hakika Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya kasance yana tsayuwar dare har kafasun sa su fara tsagewa har Aisha radiyyallahu anha tace masa miyasa kana Manzo Allah kake Ibadah kamar haka??

Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace Shin bazan zamo bawa mai godiya ba??

Yan uwa musulmi masu albarka hakika yawan yin sallar dare yana kauda bala'oi da musibuh.

Sallar Dare tana gyara halaye kuma tana gyara halaye.

Ibn hajr asqalani yace 'Ita sallar dare tana wanke zukata'

Saboda muhimmancin sallar dare Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya hore mu da yin sallar dare inda yake cewa "NA hore Ku da sallar dare domin tana share zukata"

Hakika sallar dare tana kara lafiya da kwarin jiki,

Ina wadanda basu da lafiya likita yace sai sun rika motsa jiki duk safiya???

To ga exercise daga likitan likitoci Manzo sallal lahu alaihi wassalam idan har ka tsarkake niya to hakika Allah zai baka lafiya da yardar sa.

Ibn Salam ya ruwaito daga cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Ku yada sallama a tsakanin ku Ku raba Sadakar abinci Ku sada zumunta kuyi sallar dare"

Duk mai kokarin sallar dare Allah zai haska zuciyar sa....

Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana baiwa sahabbai labari cewa "A cikin aljannah akwai wasu benaye masu tsawo ana ganin abunda ke ciki saboda tsabar hasken su a wata ruwayar har matan da suke ciki ya kwatanta, Sai wani mutanen karkara yace ya Manzo Allah wake da wadannan benayen??
Sai Manzo Allah yace na wadanda suka iya magana ne (Magana mai kyau Sadaka ce) da wanda ya sada zumunci da wanda ya yawaita azumi da wanda ya lizimci sallar dare "

ALLAH Ya umarci Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya tashi yayi sallar dare" KA TASHI KAYI SALLAR DARE KA ROKI UBANGIJIN KA "

Manzo sallal lahu lahu alaihi yayi addu'a ga wanda ya tada iyalinsa suka yi sallar dare.

Idan mata ta tashi zatayi to tana iya tada mijinta Shima idan bai tashi ba tana iya yayyafa masa ruwa amma idan babu matsala 😁

Yan uwa musulmi masu albarka saboda muhimmancin sallar dare Umar bn Khaddab ya kasance yana tada iyalinsa suyi sallah a karshen dare.

Hakika ALLAH yana sauka a sulisin dare a saman duniyar nan yana cewa "INA MASU NEMAN GAFARA INYI MASU INA MASU NEMAN BIYAN BUKATA IN BIYA MASHI??"

Yan uwa musulmi a yanzu mun bar sallar dare sai a lokachin azumin ramadana.

Idan baka iya tashi da dare to kana iya yin sallar ka bayan isha'i.

Yan uwa musulmi lokachin da yakamata muyi sallar shine misalin karfe 2,3,4 domin shine sulisin dare.

A yanzu muna ganin yadda a duniyance kowa yana neman hanyar rayuwa, Kama daga bidar kudi da sauran su.

Ita lahira babu batun kudi ko wani abu hakika yakamata mu maida hankali dan lahirar mu.

Lallai kada mu kuskura shaidan yayi tasiri garemu.

Mai hankali ne wanda keyi lahirar sa tanadi kafin yaje.

ALLAH Ka taimakemu da taimakon ka ya ubangiji ka yafe mana kurakuren mu.
Ya Allah ka biya mana bukatun mu kayi rahama ga mamatan mu ya amintar damu daga abunda muke tsoro.

(Dan Adam ajizi ne Allah ka gafarta mana abunda muka yi kuskure)

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 10-Rabi'ul akheer-1439
29 Friday -December-2017 AB

Sunday, 24 December 2017

AN GABATAR DA DAURA KASHI NA FARKO MAI TAKEN; BAYYANA KIRKIRARRUN KARYA DA AKE JINGINAWA IBN TAIMIYYA AKAN HALASCIN MAULUDI.

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*MASJID ABU-HURAIRAH YAR YARA TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

```AN GABATAR DA DAURA KASHI NA FARKO MAI TAKEN; BAYYANA KIRKIRARRUN KARAI-RAYI DA AKA JINGINA GA SHEIKHUL ISLAM IBN TAIMIYYA AKAN HALASCIN MAULUDI...

   Daurar wadda Sheikh Sani Liman (ABU HURAIRAH) Tsafe ya gabatar,  bayan Malam yayi khudubatul haaja, yayi sallama ga Yan uwa musulmai da suka taru a wajen.

  Sheikh sani Liman ya cigaba da cewa; abunda ya hada mu a wannan waje shine domin mu tattauna abunda ya shafi bukukuwan maulidi, muna yima Yan uwa musulmi maraba da karba wannan kira da sukayi, suka nuna cewa su lallai su mazajen sunnah ne, masu jira ace Sunnah tayi kira domin su amsa kiran.

  Sheikh Sani ya cigaba da cewa; Yan uwa kafin mu shiga cikin wannan littafin akwai wata shimfida da nikeson in gabatar, domin ta zamo mana haske a tafiyarmu ta Sunnah...

   Yan uwa musulmi ahlus-sunnah da muka taru a wannan masallaci bisa wannan muna saba ya kamata mu San cewa shi Ahlus-sunnah duk inda ya samu kansa to wajibi ne gareshi yayi fada da Bidi'ah!

Sheikh yace, shi fada da Bidi'ah ana yinsa ne ta hanyoyi guda biyu.

*HANYA TA FARKO:*
Fadakar da al'umma akan Bidi'ah a kowane lokaci, a kowane zamani, yadda dan Bidi'ah baiji kunyar jajircewa wajen dabbaka bidi'ashi ba, toh ai mu yafi cancanta ace mun jajirce wajen tabbatar da Sunnah, kada mu dauka cewa bidi'ar mauludi ita kadai ce zamu tsaya akanta! A'a Na daga cikin bidi'oin da ya kamata muyi fada dasu; Fadar ''SADAKHALLAHUL-AZEEM" bayan kammala karatun Qur'ani! Wannan Bidi'ah ne!!!   Na gaba shine; Fadar "AMIIN WA'ALAIKUMUS-SALAM" a wajen maida sallama, kara AMIIN Bidi'ah ne!!! da wasu daga cikin bidi'oin da basu da bambanci da bidi'ar mauludi.

Sheikh Liman yace ya kamata mu zauna mu zakulo wadannan bidi'oin domin a bayyanawa al'umma, kamar yadda babban Malami Sheikh Usman bin fodiyo ya rubuta littafi akan irin wadannan bidi'oin.

Sheikh Sani Liman ya cigaba da cewa; ba wai dole sai a irin wannan zaman bane zamu rika yakar Bidi'ah! Muna da masallatai, da makarantun islamiyyu da sauran wurare, idan ya zamana cewa ana yima bidi'ah tsirara a irin wadannan wurare a koda yaushe, babu shakka ma'abota Bidi'ah zasu ji tsoron  bayyana bidi'arsu, kuma zasu rikice.

*HANYA TA BIYU:*
hanya ta biyu da ake yakar bidi'ah shine riko da Sunnah, da dabbaka Sunnah, saboda idan Ahlus-sunnah mukayi rauni wurin riko da Sunnar Manzon Allah s.a.w, bamu koyi dashi a wajen maganganunmu da mu'amalarmu da wajen sutura da kasuwanci da sauransu, toh an samu matsala!  Ashe kenan yana daya daga cikin hanyoyin fada da bidi'ah raya Sunnah, saboda Annabi ya kira raya Sunnah a matsayin raya addini ne, saboda haka ya zama wajibi akan Ahlus-sunnah ya raya Sunnah! Abar jin kunyar aje gemu ko dage wando da sauransu.

Sheikh Liman yace, wannan ita ce wasiyya ta gareku...


   Sai Malam ya shilla akan maganar abunda ya taramu a wajen, Malam ya sukwane akan maganar bidi'ah, har ya kawo hadissai dake nuna cewa wajibi ne mu kyamaci bidi'ah, sannan ya kawo mana ayoyi dake nuna wajabcin biyayya ga manzon Allah s.a.w, ya kuma kawo mana manyan malaman musulunci da sukayi suka akan mauludi suka ce ba addini bane.

Bayan Malam ya gama wannan jawabin sai yace kai tsaye sunan littafin da zamu karanta;
تبيين كذب المفتري بما نسب إلى شيخ الإسلام ابن تيمية من استحسان الاحتفال بالمولد النبوي صلى الله عليه وسلم.
Wanda babban malaminmu na jahar zamfara Sheikh Muhammad kabir ibn umar Al-marwy(ABU SUMAYYA) ya rubuta.

Daga nan sai sheikh Sani Liman yayi mana bayanin irin kokarin da marubucin littafin yakeyi wajen baiwa sunnar Annabi kariya, da wasu ayyukan da yake yima Sunnah, malam yayi mana bayanin marubucin littafin sosai, inda har ya fada mana wasu daga cikin littafan da ya rubuta.  Na daga cikin littafan da malamin ya rubuta wanda sheikh sani ya ambata akwai;

√ TUHUFATUL AKHYAAR, BIMA'ARIFATI MALA ASLA LAHU MINAL-AKHBAR.

√ MASHAYIKHIS-SUFIYYA YAKULUNA ALLAHU FISSAMÃ(malaman sufaye sun tabbatar da cewa Allah yana sama)

√ ITTIHAFIL MU'UMININA BIT-TAKHRIJI AHADISI BUGYATUL MUSLIMEENA.

√ AHSANUL-AQAWEEL FI ISBATIS- SUNNIYATI LUBSIS-SARAWEEL, WAR-RADDU ALA MAN ZA'AMA ANNAHU BIDI'AH(wannan raddi ne ga katon dan Bidi'ah Abduljabbar akan littafin da ya rubuta ya nuna cewa sa wando Bidi'ah ne).

√ KASHFUZ-ZUNUN FI TAFSIRI QAULIHI TA'ALA;  ﻗُﻞْ ﺑِﻔَﻀْﻞِ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﻭَﺑِﺮَﺣْﻤَﺘِﻪِ ﻓَﺒِﺬَٰﻟِﻚَ ﻓَﻠْﻴَﻔْﺮَﺣُﻮﺍ ﻫُﻮَ ﺧَﻴْﺮٌ
ﻣِّﻤَّﺎ ﻳَﺠْﻤَﻌُﻮﻥ

Da wasu littafai kusan sha uku da Malam ya ambata kuma ya ba daliban ilimi shawarar su nemesu domin amfanuwa.
Daga nan ne Sheikh yaja burki saboda lokaci da yayi halinsa, malam yace a kashi na biyu zamu shiga cikin littafin ne kai tsaye.```

Ga masu bukatar audio Na wannan Daura suna iya garzayawa a dandalin sunnah Na darulfikr.com a folder Malam zasu sameshi a cikin muhadara insha Allahu.

Allah ya sakawa marubucin wannan littafi da Alkhairi dashi da Sheikh Sani Liman da ya zakulo littafin domin fadakar da al'umma.

Sai mun hadu a fitowa Na gaba insha Allahu.



*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA COMMITTEE*
+2348064734911

05-04-1439AH
24-12-2017AC

Friday, 22 December 2017

HUDUBAR JUMU'AH MAI TAKEN, HUKUNCIN BIKIN KIRSIMETI DA SABUWAR SHEKARA A MUSULUNCI.

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

Bayan mukaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka a yau khudbar mu zata yi magana ne game da hukuncin #BIKIN_KIRISMETI_DA_SABUWAR_SHEKARA_GA_MUSULMI

Yan uwa musulmi masu albarka mu girmama ubangiji Allah kuma mu gode masa game da ni'imar shi garemu ta musulunci, Kuma mu gode masa bisa ga alkawarin sa na kare addinin musulunci daga duk wani sharri!

Yan uwa musulmi masu albarka hakika riko da addini dole kuma wajibi haka ma dole rokon ALLAH mutun ya zama musulunci shine addinin shi har zuwa karshen rayuwar shi.

Hakika Allah madaukakin sarki ya zaba mana musulunci ya zama addinin mu kamar yadda yake fada cewa "NA ZABA MASU MUSULUNCI YA ZAMA ADDININ KU"

Hakika shi addinin musulunci ya cika kuma ya kammalo kuma ta tanadi dokoki da ka'idodi, Babu wani bangaren rayuwar mu da musulunci ya kyale, Kama daga

- mu'amula 'Musulunci ya tsara yadda za' a yi mu'amula.

-Siyasa hatta ita ma musulunci ya tsara yadda za'a yi ta a cikin tsafta.

-Ibadah tabbas musulunci ya tsara yadda za'a Ibadah baki daya.

Da sauransu.

Shi musulunci addini ne wayyaye wamda yake dai dai da kowane irin zamani, Kamar yadda Allah madaukakin sarki ke cewa "MUN SAUKAR MAKA DA LITTAFI NE DAN BAYANI GAME DA KOMAI"

Yan uwa musulmi masu albarka kada mu yadda muyi wani abu da zai kaskantar da addinin mu, Ko yaya abun yake komai yadda muke kallo shi karami!!

Yan uwa musulmi a yanzu wani abun takaici da ban tsoro dake faruwa tsakanin musulmi shine yadda zaka ga wai musulmi na bikin kirismeti, Har yana zuwa wuraren su yana taya su murna yana nishadi da annashuwa.

Har takai ga wasu jahilai daga cikin musulmi na cewa 'Ai babu banbanci tsakanin musulmi da kirista !!!

Har suna cewa ai duniya yanzu ta waye, Kai har masu cewa wai ai duk Allah ne ya saukar da musulunci da kiristanci  Subhannallah!!!

To fadin wannan maganar fa kafirci ne, Allah ne yace "ALLAH YA KAFIRTA MASU CEWA ALLAH UKU NE"

A wani Wuri kuma yace "WALLAHI ALLAH YA KAFIRTA MASU CEWA ISAH (ALAIHIS SALAM) DAN ALLAH NE!!"

ALLAH madaukakin sarki ya gargade mu da so da kaunar kafurai tun daga yahudawa na nasarawa wato kirista...

Yana cewa "YAKU WADANDA SUKAYI IMANI KADA KU RIKI  YAHUDU DA NASARA A MATSAYIN MAJIBINTA DUK WANDA YA RIKE SU (MAJIBINTA)  TO YANA TARE DASU LALLAI ALLAH BAYA SHIRYAR DA AZZALUMAI"

Hakama Allah madaukakin sarki yana kara cewa "KAI MUSULMI YAHUDU KO NASARA BASU TABA YARDA DA DA KAI HAR SAI KA ZAMO DAGA CIKIN SU (wato ka koyi dabi'unsu)"

Yan uwa musulmi ana samun wasu musulmi na zuwa wajen kafurai har suna cewa murnar haihuwar Annabi Isah Alaihis salam, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yayi kama da kiristoci to yana cikin su"

Zama da kiristoci a lalura babu laifi sai dai dole ne a kiyaye duk wata alaka wadda data danganci addinin ka.

Yan uwa musulmi Ibn taimiyah yana cewa 'Abunda kiristoci keyi a addinin Annabi Isah Alaihis salam haramun ne!!!

Yan uwa musulmi masu albarka ma' abota ilmi sunyi gargadi game da taya kafurai murna.

Umar bn Khaddab khalifan Manzo sallal lahu alaihi wassalam na biyu yana cewa 'Kada musulmi su kuskura yaje wajen da kiristoci ke bukukuwan su domin Allah yana saukar da fushin sa a nan to idan musulmi yaje wurin abun na iya faruwa dashi "

Kada ka kuskura wani ya jaka ko ya rude ka cewa wai ai duk ana tare ko kuma kasa daya jama'a daya wallahi kada ko sau daya kaje wajen da kafurai ke yin bukukuwan su!

Su kafurai basu son Allah basu son Manzo sallal lahu alaihi wassalam duk abunda zasu fada maka karya ne kuma adawar ka tana cikin jinin su da rayuwar su

SABUWAR SHEKARA  (NEW YEAR)

Bayan kwana ki kuma kiristoci na bikin sabuwar shekara, Kuma abun takaici kaga musulmi na murna da annashuwa cewa sabuwar shekara ta kama!!

Har zakaga musulmi na turawa a yanar gizo cewa happy new year

Wannan abun takaici ne matuka!!

Shin musulmi sun manta da ainihin shekarar su??

Wai har ana samun musulmi wanda zaka tambaya yau naga ga watan musulunci ya kasa fada??

Wannan abun takaici ne!!!

Lallai wajibi mu fifita amfani da kwanan watan musulunci fiye da nasu, Watanni musulunci a bayyane suke kuma akwai dalilin saukar dasu Allah madaukakin sarki yana cewa "SUNA TAMBAYAR KA GAME DA JINJIRIN WATA MUN SANYA WANNAN NE DAN SANIN LOKACHIN IBADAH DA AIKIN HAJJI"

hakama madaukakin sarki na cewa "ADADIN WATANNI A WURIN ALLAH SUNE GUDA GOMA SHA BIYU AKWAI HUDU MAFI FALALA A CIKIN SU"

kenan ga manu Zamu dauki na wasu??

Amfani da watan ni kafurai sai lalura da kuma dole!!

Kada mu dauka cewa amfani da watan musulunci al'ada ne...... A'a addini ne.

Muna tawasuli da sunayen Allah dari ba daya ya shiryar damu hanya madaidaiciya ya biya bukatun mu na alkhairi.

Allah ka taimaki yan uwa musulmi dake zirin gaza ka kaskantar da yahudawa da masu goya masu Baya.

Allah ka amintar damu Kabamu lafiya d zama lafiya ya ubangiji kayi rahama ga mamatan mu.

Ya ubangiji kayi albarka da bunkasa kasashen mu da jahar mu da garin mu baki daya.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 2-Rabi'ul thani-1439
Friday 22-December - 2017 AB

Monday, 18 December 2017

TARIHIN RASUWAR MANYAN MUTANE, MASU DARAJA A CIKIN MUSULUNCI, WADANDA AKE YAWAN TAMBAYA A KANSU.

🗓 *TARIHIN RASUWAR MANYAN MUTANE, MASU DARAJA A CIKIN MUSULUNCI, WADANDA AKE YAWAN TAMBAYA A KANSU*




📒 ```Annabi Muhammad (salallahu alaihi wasallam) ya rasu a shekara ta 11AH

📕 Abubakar sideeq R.A shekara ta 13AH


📔 Umar bin khaddab R.A shekara ta 23AH

📙 Usman bin Affan R.A shekara ta 23AH

📘 Aliyu bn Abi dalib R.A shekara ta 40AH

📗 Aisha bintu Abubakar R.Anha  shekara ta 57AH


📕 Abdullahi bn Abbas R.A shekara ta 68AH

📔 Abdullahi bn umar R.A shekara ta  73AH

📘 Sa'eed Ibnul musayyib R.H shekara ta 94AH

📙 Umar ibn Abdulaziz R.H shekara ta 101AH

📗 Hasanul busri R.H shekara ta 110AH

📕 Abu Hanifa R.H shekara ta 150AH

📗 Malik ibn Anas R.H shekara ta 79AH

📘 Shafi'i R.H shekara ta 204AH

📕 Ibn Rahawiya R.H shekara ta 238AH

📙 Ahmad ibn Hambal R.H shekara ta 241AH

📗 Ahmad Ibn sa'eed AD-DARUMY R.H shekara ta 253AH

📘 Abdullahi Ibn Abdulrahman AD-DARUMY R.H shekara ta 255AH


📔 imamul Bukhary R.H shekara ta 256AH



📕 Imam Muslim R.H shekara ta 261AH


📗 Ibn majah R.H shekara ta 273AH



📘 Abu daud R.H shekara ta 275AH



📙 Tirmidhi R.H shekara ta 279AH

📗 Usman bin sa'eed AD-DARUMY R.H shekara ta 280AH



📗 imamun nasa'i R.H shekara ta 303AH



📔 Ibn jareer AD-DABARY R.H shekara ta 310AH

📘 Ibn khuzaimah R.H shekara ta 311AH


📕 Ibn Hibban R.H shekara ta 354AH


📙 Imamu DARAQUDUNY R.H shekara ta 385AH


📔 imam Hakim R.H shekara ta 405AH


📗 Ibn hazam R.H shekara ta 456AH


📘 BaihaQy R.H shekara ta 458AH


📕 Ibn Abdulbarr R.H shekara ta 463AH


📔 khadeebul baghadady R.H shekara ta 463AH


📗 Ibnul Araby R.H shekara ta 543AH


📘 Ibn rushid R.H shekara ta 595AH

📙 Ibnul jauzy R.H shekara ta 597AH

📔 Alkurduby(mai littafin الجامع لأحكام القرآن) R.H shekara ta 671AH


📕 Imamun-Nawawy R.H shekara ta 676AH

📗 Ibn Taimiyya R.H shekara ta 728AH

📔 Imamuz-Zahaby R.H shekara ta 748AH

📘 Ibnul kayyim R.H shekara ta 751AH


📙 Ibn Katheer R.H shekara ta 774AH


📗 Ibn Rajab R.H shekara ta 795AH


📔 Ibn Hajar AL-ASQALANY R.H shekara ta 852AH


📗 Imamus - suyudy R.H shekara ta 911AH


📘 Ameerus - san'any R.H shekara ta 1182AH



📕 Muhammad Ibn Abdulwahab R.H shekara ta 1206AH



📗 Imamush -shaukany R.H shekara ta 1250AH


📔 AL-ALUSY R.H shekara ta 1342AH


📙 Ibn Sa'ady R.H shekara ta 1376AH


📕 SHANQIDY R.H shekara ta 1393AH


📘 Ibn baz R.H shekara ta 1419AH


📗 Albany R.H shekara ta 1420AH


📔 Ibn uthaimin R.H shekara ta 1421AH

📕 Abdullahi bn Abdulrahman bn jibreen R.H shekara ta 1430AH


⭕ Ku tura ta zuwa ga daliban ilimi

⭕ Ku tura ta zuwa ga wadanda Luke kusa dasu domin mu hadu wurin amfanuwa.


FASSARAWA:
_HASHIM IBN SURAJ IBN UBA (ABU~SINAN)_```
+2348064734911

http://hashimtsamiya.blogspot.com/

atstsamawy@gmail.com

MUHADARAMUHADARA

📀📀📀📀📀📀📀📀📀
*MUSLIM UMMAH WELFARE AND DA'AWAH ASSOCIATION TSAFE*
💿💿💿💿💿💿💿💿💿


*WA'AZIN DA AKA  GUDANAR A RANAR  ASABAR  27/RABIU AUWAL/1439)*

*DAGA BAKIN SHUGABAN KWAMITIN: (MALAM IBRAHIM MUHAMMAD FILO) TSAFE*

*MAUDU'IN KARATUN SHINE:--- WAJABCIN NEMAN ILMI DA AIKI DA SHI*

Shiga Link dake kasa domin saukewa

💽💽💽💽💽💽💽💽💽💽
http://darulfikr.com/s/37564

*AYI SAURARO LAFIYA CIKIN SAUTI MAI KYAU*

Kasance da darulfikr.com a koda yaushe, domin samun KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH.

#ABBAN_SINAN
+2348064734911

Friday, 15 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN; MUHIMMANCIN NAFILA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH   DAGA MASJID ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon  limam Sani Abi hurairah Tsafe ya gabatar da khudbar ne akan #MUHIMMANCIN_NAFILAH

Bayan mukaddimah......

Yan uwa musulmi masu albarka hakika gaskiyar zance shine Alqur'ani Mai tsarki, Mafi kyawun shiriya itace shiriya ta Annabi Muhammadu sallal lahu alaihi wassalam, Mafi sharrin ayyuka shine kirkirar abu ga addini.

Yan uwa musulmi masu albarka ina maku Nasiha tare da ni kaina da muji tsoron ALLAH domin jin tsoron ALLAH shine jagora ga rayuwar mu, ALLAH yana fada cikin suratul kasas cewa "WANNAN GIDAN NA LAHIRA MU SANYA SHINE GA MASU TSORON ALLAH HAKIKA AQIBA MAI KYAU ITA KUWA AQIBA MAI KYAU TANA GA MASU TSORON ALLAH"

Saboda kaunar da ALLAH keyi mana ya sanya mana abubuwa da Zamu amfana dasu, kamar nafilfili da sauransu,  Nafila ta sallah tana Matukar muhimmancin ga ibada,

Yan uwa musulmi masu albarka sallah itace abunda za'a fara bincike a gobe Kiyama, Manzo sallal lahu alaihi wassalam na cewa "Farkon abunda za'a yiwa dan Adam hisabi akanshi shine sallah idan tayi kyau to dan Adam ya dace idan kuma an samu matsala sai ALLAH ya umarci mala'iku su binciki shin akwai nafila?
Idan akwai to sai ayi amfani da ita wajen cike sallar farilla"

Haka ma a azumi da zakkah sai a diba idan akwai wakafi da sauran ibadu!!

Kenan koda a wannan hadisin muka tsaya lallai zamu fahimci cewa nafila nada matukar muhimmanci.

A wajen yin ibadar sallah ana bukatar natsuwa sosai Ibn Abbas ya ruwaito yace" Sai kana da natsuwa sannan sallahr ka zata karbu "

Yan uwa musulmi masu albarka yawan yin nafila yana sa mutun yazama abokin Manzo sallal lahu alaihi wassalam a gidan aljannah

Akwai wani sahabin Manzo sallal Sallal lahu alaihi wassalam idan Annabi zai yi alwala sai sahabin ya dauki talkaman Annabi ya rike a hannunsa hakama idan Manzo sallal lahu alaihi wassalam zai yi sallah yakan tsaya har sai Annabi ya fito, Wata rana sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya tambaye shi mi kake bukata inyi maka??

Sai yace ina so in zama abokin ka a gidan aljannah.....

Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace to ka taimake ni da yin nafila a koda yaushe. "

Yan uwa musulmi masu albarka yawaita nafila na kara kusan tar da dan Adam ga ubangiji, ALLAH madaukakin sarki na cewa" BAWA BAZAI GUSHE YANA SUJJADAH HAR SAI NA SOSHI "

Yan uwa musulmi masu albarka yawaita yin nafila kara maka kusanci da ubangiji ALLAH

Abdullahi bn Umar ya ruwaito cewa" Kafin sallar azahar kayi raka'a 2 bayan sallar kuma kayi 2 la'asar kayi 2 bayan ta kayi 2 hakama a magrib da isha'i hakama a sallar asuba kafin ta wato sallar fajir "

Haka ma Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Duk wanda yake yawaita yin nafila raka'a 12 a rana ALLAH zai gina mashi gida a aljannah "

Haka ma Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana cewa" Kuyi raka'a 2 kafin magrib ya fadi haka har sau uku amma ga wanda yake sa hali "

Haka ma Aisha radiyyallahu anha ta ruwaito cewa" Manzo sallal lahu alaihi wassalam bai taba barin nafila ba a lokachin sallar asuba ba "

Yan uwa musulmi masu albarka hadisin dake magana game da ba'a sallah bayan la'asar na nufin idan an dade da gama sallar ne.

Daga cikin nafilolin da ake bukatar yawaita aikatawa akwai sallar duha wato ita anayi ta ne da safe, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Dan Adam yana da gabobi guda 360 ana bukatar a kullum kabada Sadaka kwatan kwacin haka sai sahabbai suka ce to idan baka da kudin bada Sadakar??  Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace to ka tsaftace massallaci (kamar shara ko kuma dauke wani tsinke) koda ma ace ka gaza haka to kayi sallar duha "

Yan uwa musulmi masu albarka hakika addinin musulunci yana da Matukar dadi da kuma garabasa ga wani hadisi daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam cewa

" Duk wanda ya fito daga gida yayi aikatawa zaije massallaci to ana rubuta mashi ladar aikin hajji da umrah "

Hakika yan uwa musulmi idan muka yawaita yin nafila za'a rubuta sunayen mu cikin illiyun

Yan uwa musulmi bayan sallar asuba yana da kyau mu rika zaunawa koda awa guda ko biyu ne Muna yin tasbih domin falalar dake ciki, Hadisi daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam na cewa "Bayan kammala sallar asuba ka zauna har rana ta fito kana da ladar aikin hajji cikakke cikakke cikakke!!

Yan uwa musulmi dole ne mu rage yawan zama ana hira ana surutu fiye da awa guda alhali zaman baida wani amfani garemu,

Imam Muslim ya ruwaito daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam cewa "Dayanku bazai yi alwala yana jiran sallah ba face wuta ta haramta gareshi!!"

Yan uwa musulmi kunji falala mai kyau kenan masu zuwa massallaci da Wuri suna jiran limam sun samu shiga a wannan.

Sannan kuma yan uwa musulmi yana da kyau mu yawaita yin nafila a gidajen mu domin Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada mu maida gidajen mu kamar makabartu (Domin ba'a sallah a makabarta)

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Mafificin nafila itace nafillar da akayi a gida "

Yan uwa musulmi kada mu rangwantar da kawunan mu mu kashe jikin mu da hira da surutai marar sa amfani domin wallahi akwai ranar da Zamu nemi ina ma ace Zamu yi aiki koda na kwayar zarra ne!!

Akwai falala mai yawa a cikin sallar nafila, Manzo sallal lahu alaihi wassalam "SALLAR fajir (Kafin asuba) tafi duniya da abunda ke cikin ta"


To yan uwa musulmi kunji fa......

Tabi'ai da sahabbai sun kasance idan wani yayi laifi yana zuwa yayi nafila ya roki Allah ya gafarta masa.

*Sallar nafila tana daga Darajar dan Adam a wurin ALLAH

Hakika sahabbai da Tabi'ai suna yawaita yin nafila domin tsannanin koyi da Annabi, Saboda Annabi ya karantar dasu kuma yayi a gaban su har ma ya kwadaitar da wannan ibadar.

Yawaita nafila yana kawo abubuwa kamar haka :

*Gidan mutun yana albarka

*Darajar dan Adam tana karuwa

*Yana sanya mutun yazama abokin Manzo sallal lahu alaihi wassalam a gidan aljannah.

*Nafila na zama abokiyar hira ga dan Adam a cikin kabari.

*Zai kara maka son ALLAH

*Tana maida dan Adam yazama mutanen kirki.

*Samun ladar aikin hajji da umrah

*Kankarewar Zunubai.!!

Yan uwa musulmi masu albarka a yadda duniya ta chanza a yanzu dole ne mu rungumi koyar wa Manzo sallal lahu alaihi wassalam da duk abubuwan da ya karantar damu.

ALLAH ka gafarta mana kayi mana rahama kabamu lafiya da zaman lafiya, Ya ubangiji ALLAH kayi rahama garemu ka biya mana bukatun mu ka haskaka rayuwar mu, Ameen

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 20-Rabi'ul auwal-1439
Friday 15-December-2017 AB

Friday, 8 December 2017

HUDUBAH MAI TAKEN LOKACIN SANYI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon limamin  Massallacin Jumu'a na Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na Liman'

Yayi Hudubar Sane Akan #LOKACHIN_HUNTURU

Bayan mukkaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka a yau Khudbar mu zatayi magana ne game da halin da muke ciki, Watau yanayi na hunturu da sanyi da kadawar iska.

Idan muka diba lokachin da muka fito na baya zamu ga cewa lallai yanayi yayi matukar chanzawa, Hakika yan uwa musulmi chanzawar lokachi wani sababi ne ga mai imani da zai kara masa imani, Da kara maida kai ga ALLAH Da jajircewa ga biyar sa!

ALLAH Madaukakin sarki cikin hikimar sa da yarda sa yana shata mana zuwan wannan lokachin duk shekara.

Ibn kaiyumul jauzi yana cewa 'Idan aka lura da yadda ALLAH juya lokutta zamu fahimci cewa akwai wata maslaha dake cikin yin hakan'

Idan da yaso sai ya barmu da lokachi daya ko zafi kawai ko sanyi kawai ko kuma ruwan sama kawai!

Yan uwa musulmi masu albarka ina maku wasiya dani da ku da muji tsoron ALLAH, Hakika da tsoron ALLAH Ne zukata ke kamuwa da natsuwa kuma ake fahimta ayoyi da manufofin ubangiji.

ALLAH Madaukakin sarki na cewa "SUNE (Masu imani) MASU DIBA YADDA MUKE JUYA AKAN LAMURA HAKIKA SUN SAMU IMANI KUMA SUNE MASU AMBATON ALLAH BA DARE BA RANA "

Hakama ALLAH S.W.T Na cewa "LALLAH JUYAWAR DARE DA YINI AYAH CE GA MASU IMANI"

Shi wannan lokachin na sanyi ALLAH Madaukakin sarki ne ya kaddaro shi da haka, Domin wuta ce keyin lumfashi!!

Ga hadisi daga Manzo s.a.w "Wata rana wuta takai kara ga ALLAH S.W.T Cewa wani sashen ta yana cin sashen ta sai ALLAH Yabata dama cewa ta rika numfashi wato taja iska (shine muke samun lokachin sanyi) sannan ta saki numfashi (shine lokachin zahi)"

Iman hasanul busariy na cewa 'ALLAH Ya tanadar da wannan lokutta ne dan tunatar damu game da kiyama, Domin idan nukaji sanyi yayi yawa sai mu tuna cewa sanyin azaba da kiyama yafi na duniya, Hakama zafi na duniya bai kai zahin kiyama ba"

Abdullahi dan Mas'ud r.a ya kasance idan sanyi yazo yana cewa 'Maraba da zuwan sanyi maraba da zuwan sanyi idan aka tambaye shi miye dalilin shi na fadar haka sai yace 'Lokachin sanyi lokachi ne da dare keda tsawo (Ana samun damar yin ibadah da kusantar ALLAH) Rana kuma batada tsawo ana yawaita azumi'

Yan uwa musulmi masu albarka lokachin hunturu yana da HUKUNCE HUKUNCEN sa..

*Yin alwala da kyau-Yazama wajibi mu kiyaye yadda muke alwala a lokachin sanyi, Domin muna sanya manya kaya kuma wajen alwala zakaga wasu saboda kaya masu nauyi basu yin alwala da kyau.

Manzo s.a.w "Yaga wasu na alwala amma basu shafawa yadda yakama sai Manzo s.a.w yace 'Boni ya tabbata ga masu alwala basu cikawa ' "

Babu laifi saboda sanyi ayi alwala da ruwan zafi wajen yin alwala.

*Ana son tuna saukin da shari'ah ta kawo mana, Ya halatta shafa sama safa ko takalma ko huffi, Idan har anyi alwala kafin a sanya safar ko takalman.

Mugira ya ruwaito hadisi kuma an ruwaito shi a sunnanin dauda cewa "Manzo s.a.w yana shafa saman khuffi amma idan yayi alwala,

Hakama wata rana Manzo s.a.w zai yi alwala sai Mugira yazo zai cire masa takalma sai Manzo s.a.w yace kabarshi domin nayi alwala kafin insa!

Larabawa na cewa lokachin sanyi namiji zahi kuma macce, Saboda yanayin karfin su ba daya ba.

A zamanin khalifan Manzo s.a.w na biyu wato Umar bn Khattab r.a yana kewa yawa cikin gari yana cewa 'Sanyi yazo sanyi makiyin mu ne dan haka mu tanadi kayan kariya kamar manya barguna da sauran kayan kariya daga sanyi'

Yaku yan uwa musulmi masu albarka, Hakika Umar r.a ya kasance yana taimakon marar sa galihu da kayan rufe jiki dan kariya daga sanyi.

Anan muna kira ga yan uwa musulmi da mu taimaki yan uwa marayu da makwabta da sauran mara sa galihu, Da kuma kula da iyali da kananan yara a tanadar masu kayan sanya kada mu barsu kamar  dabbobi domin zai iya yin illah garesu.

*Yawaita bautar ALLAH, Hunturu lokachi da dan Adam ke samun lafiya da walwala da kebantuwa daga mutane, Domin ko doguwar hirar da ake yi ragewa ake yi, Zaka fito karfe goma ka tarar babu kowa,

Dan haka sai muyi amfani da wanoan lokachin wajen bautar ALLAH ba yawan bacci ba.

*Mu rika cika alwala, Manzo s.a.w na cewa "Cika alwala ne mafi so a yanzu (Lokachin hunturu).

*Dumama jiki dan samun sauki, Sai dai yana da kyau musulmi ayi hattara sosai, Domin kada mu ajiye wuta ta rika kwana a dakunan mu.

Abul musa al'ashry ya ruwaito cewa "Wata rana ayi gobara a Madinah sai aka fadawa Manzo s.a.w sai yace 'Wannan wutar makiyar muce mu daina aje ta a dakunan mu'!!

Dan haka da zarar zamu kwanta sai mu kashe wuta a fito da ita waje,

Yan uwa musulmi mu taimaki yan uwa marar sa galihu, Mu taimaki marar kayan sanyawa.

Lallai ALLAH Na taimakon bawa, Matukar yana taimakon yan uwansa.

ALLAH Ka taimakemu da taimaka, Ka karemu da kariyar ka.

Ya ALLAH Ka biya mana bukatun mu na alkahri ka kiyaye mu kuma ka tsare mu.

Ya ubangiji kayi rahama garemu da iyayen mu.

Ya ubangiji ka zaunar damu lafiya, Ka albarka ci garin mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 19-Rabi'ul auwal-1439
Friday 18-December-2017 AB