Monday, 19 March 2018

AZUMIN WATAN RAJAB(SUNNAH KO BIDI'AH)?

🌺🍇🍏🌹🌷🌼🌸💐🌺
*AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???*
🌺💐🌸🌼🍇🌷🌹🍏🌺

Rubutawa: *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

بسم الله الرحمن الر حيم

```Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya chanchanci a bauta masa shi kadai kuma ya hanemu da shirkah, Tsira da Aminci su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w wanda ya tsoratar damu daga aikata bidi'ah.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda ganin ya dace mu fadakar da yan uwa musamman iyaye da kakanni da ake zalunta da hadissan karya, dangane da falalar azumin watan Rajab.

Da farko dai shi watan Rajab yana daya daga watanni masu alfarma wanda aya ta 36 a suratu taubah tayi bayani.

✏✏✏✏✏✏✏✏
MAGANGANUN MAGABATA AKAN AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI)
✏✏✏✏✏✏✏✏

kai tsaye yanzu ga Wata tambaya da akayi ma sheikh bin baaz(R.H) dangane da azumin Rajab(azumin tsofaffi).

An tambayi sheikh bin baaz(R.H) akan cewa shin ko yana halatta azumtar watan Rajab (AZUMIN TSOFAFFI) gaba dayansa? Domin wasu Malamai suna fadar cewa: duk wanda ya azumci Rajab, an gafarta mashi zunubbansa koda sun kai yawan kumfar teku, wasu kuma malaman sunyi hani da azumtar watan suna cewa; duk da zamanshi cikin watanni masu alfarma baya halatta a azumceshi gaba daya???

Ga amsar da bin baaz ya bada, yana cewa; " Abun sani kawai shine ba'a shar'anta azumtar watan Rajab ba! Bari ma an karhantashi, abunda ya tabbata shine an shar'anta azumin sha'aban, manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumin sha'aban, yana azumtar sha'aban sai kadan yake  ragewa, amma Rajab an karhanta yin azumi a cikinsa, azumi a cikinsa yana daga cikin aikin jahiliyya, saboda masu azumtar basu da dalilin azumtar watan!!! Hadisan da ake yawo dasu akan falalar watan Rajab basu da asali, bari ma na karya ne wadanda basu inganta ba, abunda shari'ah ta shar'anta ga musulmai shine suci susha a watan Rajab, sai dai idan ya kasance kana yin azumin nafila tun kafin zuwan watan wanda su dama shari'ah ta tabbatar dasu, kamar; litinin da Alhamis, Ayyamul-beedh da sauransu, wannan yana da kyau kuma babu laifi, amma azumtar watan gaba dayansa, ko kuma baka saba yin azumin nafila ba sai da watan ya shigo sai ka fake da azumin nafila ka gabatar da na Rajab wannan shari'ah bata yadda dashi ba.
Wannan itace amsar da sheikh bin Baaz ya bada dangane da azumin tsofaffi na Rajab.

Hadisi ya tabbata daga Aisha matar Annabi Muhammad s.a.w tana cewa:كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يصوم حتى نقول لايفطر، ويفطر حتى نقول لايصوم، وما رأيته أكثر صياما منه في شعبان.
[صحيح أخرجه البحاري(١٩٦٩)، و مسلم(١١٥٦)].

Ma'ana; Aisha R.A take cewa; "Manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumi har sai nace bai cin abinci! Yana cin abinci har sai nace bai yin azumi(ma'ana yana yin azumi da yawa, haka kuma yana aje azumi ya huta sosai) ban taba ganin Manzon Allah s.a.w yana cika azumin wata daya ba sai dai idan ramadhan ne, ban taba ganin watan da yafi azumi a cikinsa ba face sha'aban.
[Bukhari da Muslim].

ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ " ‏( 25/290 ‏) :
" ﻭﺃﻣﺎ ﺻﻮﻡ ﺭﺟﺐ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ﻓﺄﺣﺎﺩﻳﺜﻪ ﻛﻠﻬﺎ
ﺿﻌﻴﻔﺔ ، ﺑﻞ ﻣﻮﺿﻮﻋﺔ ، ﻻ ﻳﻌﺘﻤﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻋﻠﻰ
ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻬﺎ ، ﻭﻟﻴﺴﺖ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﺮﻭﻯ ﻓﻲ
ﺍﻟﻔﻀﺎﺋﻞ ، ﺑﻞ ﻋﺎﻣﺘﻬﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﺿﻮﻋﺎﺕ ﺍﻟﻤﻜﺬﻭﺑﺎﺕ...

Shaikhul Islam Ibn taimiyyah (RH) y
ace: “Kebance watan rajab da yin azumi,
dukkan hadisan
da su ka zo akan haka da’ifai ne (masu
rauni), bari
ma hadisan karya ne, masu ilimi
basu amfani dasu, domin basu
cikin hadisan
da ake amfani dasu don nuna falalar
aikata abu,  bari ma dukkan su ma
hadisai ne
na karya..”
Duba Majmu’u Fatawa (25/290).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :
" ﻛﻞ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻲ ﺫﻛﺮ ﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻭﺻﻼﺓ ﺑﻌﺾ
ﺍﻟﻠﻴﺎﻟﻲ ﻓﻴﻪ ﻓﻬﻮ ﻛﺬﺏ ﻣﻔﺘﺮﻯ " ﺍﻧﺘﻬﻰ ﻣﻦ " ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ
ﺍﻟﻤﻨﻴﻒ " ‏(ﺹ 96 ‏)

Imam Ibnul Qayyim (RH) yace;
“Dukkan hadisan 
da suka ambaci azumin watan rajab da
sallatar wasu
darare a cikin sa, hadisai ne na karya kuma 
kirkirarru”.
Duba Almanarul Muniif (shafi 96).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺤﺎﻓﻆ ﺍﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﻓﻲ " ﺗﺒﻴﻴﻦ
ﺍﻟﻌﺠﺐ " ‏(ﺹ 11 ‏) :
" ﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ ﻓﻀﻞ ﺷﻬﺮ ﺭﺟﺐ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﺻﻴﺎﻣﻪ
ﻭﻻ ﺻﻴﺎﻡ ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻪ ﻣﻌﻴﻦ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺔ
ﻣﺨﺼﻮﺻﺔ ﻓﻴﻪ ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ﻳﺼﻠﺢ ﻟﻠﺤﺠﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ.

Alhafiz Ibn Hajar Al-Asqalani yake
cewa; “Babu
wani abu da aka ruwaito na falalar
watan Rajab,
ko yin azumi a cikin sa, ko azumtar
wasu adadin
kwanaki ayyanannu, ko tsayuwar
wasu darare
kebantattu”.
Duba Tabyinul ujub (shafi 11).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺳﻴﺪ ﺳﺎﺑﻖ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ " ﻓﻘﻪ
ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 1/383 ‏) :
" ﻭﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻟﻴﺲ ﻟﻪ ﻓﻀﻞ ﺯﺍﺋﺪ ﻋﻠﻰ ﻏﻴﺮﻩ ﻣﻦ
ﺍﻟﺸﻬﻮﺭ , ﺇﻻ ﺃﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻷﺷﻬﺮ ﺍﻟﺤﺮﻡ , ﻭﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ
ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺃﻥ ﻟﻠﺼﻴﺎﻡ ﻓﻀﻴﻠﺔ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ,
ﻭﺃﻥ ﻣﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻤﺎ ﻻ ﻳﻨﺘﻬﺾ ﻟﻼﺣﺘﺠﺎﺝ ﺑﻪ
" ﺍﻧﺘﻬﻰ

Imam Sayyid Sabiq (RA) yake cewa;
“Azumin
watan rajab bashi da wani fifiko na
falala akan
waninsa cikin watanni, sai dai shi
yana daga cikin
watanni (guda hudu) ma su alfarma,
kuma ba a
samu a cikin sunnah ingatacciya ba cewa
yin azumi a
cikin sa yana da falala kebantacciya,
abunda ya zo
akan haka (ma’ana hadisan da suka
zo) ba a kafa
hujja dasu (domin da’ifai ne)”
Duba Fiqhus-Sunnah (1/383).

ﻭﺳﺌﻞ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻦ ﺻﻴﺎﻡ
ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﻭﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺘﻪ .
ﻓﺄﺟﺎﺏ :
" ﺻﻴﺎﻡ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ
ﻟﻴﻠﺘﻪ ﻭﺗﺨﺼﻴﺺ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺔ , ﻭﻛﻞ ﺑﺪﻋﺔ ﺿﻼﻟﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ " ‏( 20/440 ‏)

An tambayi sheikh Muhammad Salihul Usaimeen
(RH)
dangane da azumi ranar 27 ga watan
rajab da
kuma tsayuwar dararen sa.
Sai ya amsa da cewa:
“Yin azumi ranar 27 ga watan Rajab
da tsayuwar
darensa kebance shi da haka bidi’a
ne, dukkan
bidi’a kuma batace”
Duba Majmu’u fatawa na Usaimeen
(20/440).

   Haka zalika Sayyidina umar R.A ya kasance yana bulala akan wadanda ke kamewa akan azumin Rajab, yana ce musu kuci abinci, wannan watane da ya kasance ake girmamawa a lokacin jahiliyya. [Ibn Abi shaibah ya fitar 3/102] da ibn kathir a cikin musnadil- faruk 1/285]

Haka zalika ibn umar R.A ya kasance idan yaga mutane suna wuce gona da iri akan Rajab, yana kyamar hakan!
[Sahih: ibn abi shaibah ya fitar 3/102]

Ibn Abbas ya kasance yana hani akan azumin Rajab gaba dayansa, saboda kada a maida shi ya zama abunda za'a rinka yi duk shekara, wato a maidashi ya zama idi.
[Sahih; Abdulrazak ya fitar 7854].

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISAN DA SUKA INGANTA AKAN WATAN RAJAB!
✏✏✏✏✏✏✏✏
=  "kuyi axumi a cikinshi kuma kuci abinci a cikinshi.
[Sahih irwa'ul galeel 958]

= Sha'aban yana tsakanin Rajab da Ramadhan, ana shagaltar da mutane akanshi(domin samun saukin Ramadan) a cikin sha'aban ake daukar ayukkan bayi, ina kwadayin/inason kada a daga ayyukana face ina azumi.
[Isnadinsa mai kyau ne, silsilatus-sahiha 1898]

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISSAI DA'IFAI WADANDA MASU AZUMIN RAJAB KE KAFA HUJJA DASU.!!!
✏✏✏✏✏✏✏✏

= A cikin Aljanna akwai wani gulbi, ana kiransa Rajab, ruwansa suna da fari wanda farin yafi na nono, duk wanda yayi azumin Rajab na rana daya, Allah zai shayar dashi daga wannan gulbin.[Silsilatu-dha'ifah 1898]

= Rajab watan Allah, Sha'aban wata na(manzon Allah), Ramadan watan Al'umma ta. 
Da'ifi ne, silsilatu-dha'ifah 4400]

= Darare guda biyar ba'a maida Addu'ah: 1. Farkon Daren Rajab

2. Daren Rabin watan sha'aban

3. Daren jumu'ah

 4. Daren karamar sallah

5. Daren babbar sallah

[Maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 1452]

= Rajab watane mai girma, Allah na lunka lada idan kayi aikin Alkhairi a cikinsa, duk wanda yayi azumin Rajab na kwana daya,kamar yayi azumin shekara. Duk wanda yayi na kwana bakwai, za'a rufe mashi kofofin wutar jahannama bakwai. wanda yayi na kwana takwas, za'a bude mashi kofofin Aljanna takwas. Wanda yayi na kwana sha biyar, mai kira zaiyi kira a sama yace; an gafarta maka abunda ya gabata na laifuka...[maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 5413]

✏✏✏✏✏✏✏✏
RUBABBUN HADISSAN DA YAN SHI'AH KE KAFA HUJJA DASU AKAN FALALAR WATAN RAJAB.
✏✏✏✏✏✏✏✏
Daga Baban hassan (A.S) yace; Annabi Nuhu (A.S) ya tuka jirgin ruwa a farkon watan Rajab, sai ya umurci wadanda ke tare dashi da su azumci wannan ranar, yace; "duk wanda ya azumci wannan ranar Allah zai nisanta shi da wuta na tsawon tafiyar shekara daya.

=Daga Abi Ja'afar, Muhammad ibn Aliyu(A.S) yace; duk wanda yayi azumi a Rajab na rana daya, a farkon Rajab ko tsakiyarsa ko karshensa, Allah ya wajabta mashi shiga Aljanna, kuma Allah zai sanya shi a tare damu a cikin darajojinmu na Ahlul baiti a ranar kiyama, wanda yayi na kwana biyu, Allah zai gafarta mashi duk zunubbanshi da suka gabata, wanda yayi na kwana uku, Allah zai gafarta mashi abunda ya gabatar na zunubi da wanda zaiyi a gaba sannan za'a bashi damar ceton yan uwanshi ma'abota zunubi...

= As-sadik Ja'afar  ibn Muhammad yace; "kada ka bari ranar ashirin da bakwai ga Rajab ta wuce ba tare da ka azumceta ba! Domin a ranar ne aka saukar wa Annabi Muhammad s.a.w Annabta...

Duka wadannan zaka samesu a cikin littafi mai suna FALALAR WATANNI UKU, wanda gingimemen malamin Shi'ah mai suna MUHAMMAD IBN ALIYU IBN HUSSAIN IBN MUSA AL-QUMMY ya rubuta.
Allah ka la'anci qummy.

  A takaice wadannan sune hujjoji na dangane da rashin ingancin azumin Rajab(azumin tsofaffi), duk wanda yake ganin akwai Gyara matukar gyaran nashi ya inganta hadisi ne ko aya ina maraba dashi kwarai da gaske.

Allah ya hadamu dani daku da sauran musulmai a cikin Aljannah.

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH...```

Copyright©
Dalibinku
*_Hashim Suraj Uba Tsamiya {ABU SINÃN}_*

☎08064734911
📞09030201868 
    08116194214

http://hashimtsamiya.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

17-07-1438AH
15-04-2017AC

Friday, 16 March 2018

تاريخ وفاة عظماء الاسلام

تاريخ وفاة عظماء الاسلام الذين يكثر السؤال عنهم :
📒محمد صلى الله عليه وسلم 11 هجري
📕 أبو بكر الصديق 13 هجري
📔 عمر بن الخطاب 23 هجري
📙 عثمان بن عفان 35 هجري
📘 علي بن أبي طالب 40 هجري
📗 عائشة بنت أبي بكر 57 هجري
📕 ابن عباس 68 هجري
📔 ابن عمر 73 هجري
📘 سعيد بن المسيب 94 هجري
📙 عمر بن عبد العزيز 101 هجري
📗 الحسن البصري 110 هجري
📕 أبو حنيفه 150هجري
📗 مالك بن أنس 179 هجريه
📘 الشافعي 204 هجري
📕 ابن راهويه 238 هجري
📙 أحمد بن حنبل 241 هجري
📗أحمد بن سعيد الدارمي 253 هجري
📘 عبد الله بن عبد الرحمن الدارمي 255 هجري
📔 البخاري 256 هجري
📕 مسلم 261 هجري
📗 ابن ماجه 273 هجري
📘 أبو داود 275 هجري
📙 الترمذي 279 هجري
📗عثمان بن سعيد الدارمي 280هجري
📔 النسائي 303 هجري
📕 ابن جرير الطبري 310 هجري
📘 ابن خزيمة 311 هجري
📕 ابن حبان 354 هجري
📙 الدارقطني 385 هجري
📔 الحاكم 405 هجري
📗 ابن حزم 456 هجري
📘 البيهقي 458 هجري
📕 ابن عبد البر 463 هجري
📔 الخطيب البغدادي 463 هجري
📗 ابن العربي 543 هجري
📘 ابن رشد الحفيد 595 هجري
📙ابن الجوزي 597 هجري
📔 القرطبي صاحب تفسير الجامع لأحكام القرآن 671 هجري
📕النووي 676 هجري
📗 ابن تيمية 728 هجري
📔 الذهبي 748 هجري
📘 ابن القيم 751 هجري
📙 ابن كثير 774 هجري
📗 ابن رجب 795 هجري
📔 ابن حجر العسقلاني 852 هجري
📗 السيوطي 911 هجري
📘 الأمير الصنعاني 1182 هجري
📕محمد بن عبد الوهاب 1206 هجري
📗الشوكاني 1250 هجري
📔 الألوسي 1342 هجري
📙 ابن سعدي 1376 هجري
📕 الشنقيطي 1393 هجري
📘ابن باز 1419 هجري
📗 الألباني 1420 هجري
📔 ابن عثيمين 1421 هجري
📔مقبل بن هادي الوادعي 1422 هجري

⭕ .. أرسلها للطلاب ..
⭕ .. أرسلها لقروب العائلة ..
💡.. ثقف من حولك من هم
.. عظماء الاسلام
-

Friday, 9 March 2018

INAA ZAKUJE YAN MATA???

INAA ZAKUJE YAN MATA???
Wannan muhadara tana da matukar muhimmanci
wallahi, musamman ga yan mata da kuma
iyayenmu mata, Dan uwa/yar uwa daure ka/ki
sauke wannan muhadara domin Amfanuwa.
� � � � � � � � �
� �
http://kiwi6.com/file/0i4idqba1f
Malamin da ya gabatar da wannan muhadara
shine:- ustaz musa s Lawal (Abu salih ibn salih)
Allah ya bada ikon saurara da kuma amfanu da
abunda mukaji
Hashim surajo uba Tsamiya
08064734911

Saturday, 3 March 2018

KO YANA HALASTA NA AURI DAN SHI'AH???

*KO YA HALASTA IN AURI DAN SHI'AH???*
Tambaya: Assalamu Alaikum, Allah ya karawa
Malam lafiya, nice wani Dan buraza(SHI'AH) ke
'SO' kuma aure yakeso muyi, Malam ya hallata
in aure shi ko kuwa??? Amsa: Wa'alaikumus-
salam, Toh wacce tayi wannan tambayar tana
sone dai mu tona ma shi'ah asiri, abunda zance,
shin kina iya auren Sunday? Ko Friday? Ko
peter? Ko Jonathan? Ko bush? Nasan amsarki
bazata wuce A'A ba, toh lallai haka baya halatta
ki auri Dan shi'ah!!! Saboda dashi da wadancan
basu da bambanci, kai idan ka duba cikin ﻣﻨﻬﺎﺝ
ﺍﻟﺴﻨﺔ Na ibn taimiyya, yake cewa: "kara
bayahude da Dan shi'ah, 'kara banasare
(kirista)da Dan shi'ah!!!" Meye hujja??? Yace
idan ka tambayi bayahude cewa suwaye sukafi
kowa Alkhairi a duniya bayan Annabi musa?
Zasu ce, sahabban Annabi musa, idan ka
tambayi kirista cewa suwaye sukafi kowa
Alkhairi bayan Annabi isah? Zasu ce, mutanen
Annabi isah(Hawariyawa), Amma idan ka
tambayi Dan shi'ah suwaye sukafi kowa sharri a
cikin duniya, zasu ce:sahabban Annabi
Muhammad s.a.w!!! Da wannan ne, sheikhul
Islam yace kara bayahude da Dan shi'ah, kara ba
nasare da Dan shi'ah, bugu da 'kari, koda ace
yayi takiyya ya nuna cewa shi ba Dan shi'ah
bane, sai bayan anbashi auren sannan ya fito da
akeedar, to ya zama wajibi Ga waliyyanki da su
gaggauta raba auren! saboda haka yar uwa
akwai bayani sossai, sai naji wani ja'iri yayi
magana sannan zan kara fito da wasu dalilan
kafircin yan shi'ah. Allah yayi mana jagora.

©copyright: Hashim surajo uba tsamiya(ABU-SINAN)

+2348064734911

http://
hashimtsamiya.blogspot.com

Tuesday, 30 January 2018

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN SHIRKA DA NAU'OINTA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#SHIRKA_DA_NAU'O'INTA

BAYAN mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka hakika banban abunda ALLAH yafi kauna shine riko da tauhidi, Kuma babban abunda ALLAH yafi kin shine shirka!!

ALLAH madaukakin na cewa "KU BAUTA MA ALLAH KADA KU HADA SHI DA KOWA"

lallai yan uwa musulmi mafi girman zunubi shine yin shirka da Allah....

ALLAH madaukakin na cewa yayi "DUK WANDA YAYI SHIRKA DA ALLAH MAKOMAR SHI WUTA (idan ya mutu bai tuba ba)"

Sannan kuma Allah na cewa "LALLAI ALLAH BAYA GAFARTAWA IDAN AKAYI SHIRKA DASHI AMMA YANA GAFARTA WANI LAIFIN WANDA BA SHIRKA BA GA WANDA YASO"

Yan uwa musulmi hakika Allah ya tsoratar da dukkan annabawan da ya aiko game da Shirka,  ALLAH yana cewa "MUNYI WAHAYI GAREKA DA WADANDA SUKA GABACE KA IDAN KAYI SHIRKA LALLAI DUK AYYUKAN KA SUN LALACE"

Yan uwa musulmi mu duba girman Annabawa amma Allah yace masu idan suka yi shirka ayyukan su sun lalace balle mu, Wannan kiran fa ba Allah yana nufin Annabawa ba!!

A'a ana nufin mu, Domin annabawa basu yin shirka...

Yan uwa musulmi idan muka diba musulmi fa yawa sun fadawa shirka da sanin su wasu kuma bada sanin su ba!!

ALLAH madaukakin sarki na cewa "DA YAWAN SUNYI IMANI AMMA SUN HADA ALLAH DA WANI"

Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya gargade mu gargadi mai tsauri yana cewa "lallai abunda nafi tsoratar maku a rayuwar Ku shine shirka karama"

Wata rana Abubakar assidiq radiyyallahu anhu yaje wajen Manzon Allah sai Manzo Allah yace mashi lallai shirka tana nan cikin musulmi, Lallai shirka tafi boyuwa a cikin Ku Sama da tururuwa a saman bakin dutse cikin dare "

Amma ga wata addua da zaka rika karanta wa domin neman kariya kace" YA ALLAH INA ROKONKA KA GAFARTA MANI KA KARENI DAGA SHIRKA "

NAU'OIN SHIRKA

*Rokon kabari, Sau da yawa zaka ga wasu masu karancin islamiyya suna zuwa rokon kabari, Ko aljanu ko waliyai ko annbawa Alaihis salam

Alhalin Allah madaukakin sarki ya haramta hakan har ma ya fada cikin suratul ahkaf cewa" BABU BATACCE IRIN MAI KIRAN WANIN WANIN ALLAH "

Kuma duk musulmi mai imani ya amince cewa kiran WANIN Allah shirka ne, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Roko ibada ne " Dan haka duk wanda ya roki WANIN Allah dan neman biyan wata bukata ko neman kariya hakika yayi shirka!!

* Kudurta cewa wani  na cutar wa...

Sau da yawa idan wani abu yafaru da dan Adam sai ya dora laifin bisa wani abu, Ko dora shi ga wani dalili ko kuma cewa ai wane ne dalili da sauran su...

ALLAH madaukakin sarki yace "IDAN ALLAH YA KAWO MAKA CUTA BABU MAI IYA DEBE MAKA ITA SAI SHI"

*SHIRKA TA HANYAR YIN MAGANA...

sau da dama wasu na fadar wasu maganganu alhalin shirka ce, Kamar cewa 'Taya Allah kiwo yafi Allah na nan'!

Kamar cewa Idan Allah ya yarda tare da wane, Ba' a cewa hakan nan cewa ake yi idan Allah ya yarda sannan wane ya yarda, Kaga dole sai ka fara sanya Allah farko.

Sannan masu cewa mun dogara ga Allah mun dogara gareka,  Huzaifa ya ruwaito cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada Kuce abunda ALLAH yaso da abunda wane yaso"

* JINGINA NI'IMAH GA WANI ABU....

jjngina samuwar Ni'ima ga wani abu kamar aiki, Ko sana'a ko, Alhali yin haka sanya wa Allah kishiya ne, Allah kuma yace "KADA KU SANYA MA ALLAH KISHIYA"

* SIHIRI...

Yanzu yawan yin sihiri ya yawaita cikin musulmi, A yanzu yadda sihiri yazama ruwan dare ya koma wa wasu kamar jini, Saboda yawan yin sihiri har sanya wasu anan Zamfara na Jefa Alqur'ani Mai tsarki cikin makewayi (Toilet) subhannallah...

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yaje wurin boka ko dan sihiri ya karyata abunda aka saukar wa Manzo Allah (Alqur'ani)" 

* YIN RANTSUWA DA WANIN ALLAH...

wasu nada tabi'ar yin rantsuwa da, kaddara ko lokachi ko iyaye da sauran su, Har munzo zamanin da akafi yarda da rantsuwar da akayi ba Allah a ciki...

* IZGILI DA WANI ABUN ADDINI....

wasu kuma nada tabi'ar yin izgili da Abubuwan addini kamar, Gemu hijabi, aswaki, Yawaita sallama da sauran su.

* RATAYA LAYA KO KARHU

Daga cikin musulmi akwai masu tabi'ar daura laya ko karhu ko guru ko qaho da sauran su, Da sunan samun kariya ko wani abu, Wannan duk shirka ne.

*JIBINTAR KAFURAI
wasu nada tabi'ar jibintar kafurai fiye da musulmai, Alhali basu son Allah kuma basu son Manzon Allah.

Tabbas duk wanda ya fada shirka tabbas ya halaka, Duniya da Lahira.

ABUBUWAN DAKE SAMUWAR MAI YIN SHIRKA

- Rayuwar mai shirka tana lala cewa.

- Kullum cikin tashin hankali mai shirka ke kasancewa.

-Cirewar natsuwa daga rayuwa.

- shiga cikin batattu domin Allah yace "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA BACE"

-Rosa ayyukan bawa, Duk wanda yayi shirka ya roza ayyukan shi.  ALLAH madaukakin sarki ya cewa Manzo Allah cewa "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA LALATA AYYUKAN SHI"

-DUSHE HASKE.

duk mai yin shirka Allah zai sanya wa rayuwar shi duhu, Baya taba ganin hasken alkahri.!!

Yan uwa musulmi hakika shirka tana tauye imani, Lallai yazama wajibi garemu muyi watsi da duk abunda zai kowa mana tangarda a cikin imanin mu, Domin samun tsira gobe Kiyama mu da iyalan mu da yan uwan mu baki daya.
. Allah ka albarkaci rayuwar mu baki daya.

Allah kayi mana kariya daga shirka, Ka biya mana bukatun mu na alkhairi, Ya Allah Muna tawasuli da sunayen ka ka biya mana bukatun mu na alkhairi baki daya, Ya Allah kara albarka ga garuruwan mu kabamu lafiya da cikakken zama lahiya ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 01-5-1439
Friday 19-January - 2018 AB

HUDUBA MAI TAKEN DUKIYA DA FITINAR TA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#DUKIYA_DA_FITINONIN_DAKE_TARE_DA_ITA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

BAYAN mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka lallai mu sani fitunun dake cikin dukiya suna da matukar yawa, Kamar yadda Allah madaukakin sarki ya fada.

Yan uwa musulmi muji tsoron Allah mu tuna lallai kudin dake hannu mu yabamu su ne matsayin Jarabawa!! ALLAH Ya fada cikin suratul anfal cewa "YAYAN KU DA DUKIYOYIN KU FITINA NE GAREKU"

Hakama Allah madaukakin sarki ya fada cikin suratul Tagabun cewa "LALLAI DUKIYOYIN DA YAYA FITINA NE GAREKU"

Yan uwa musulmi idan akace dukiya ana nufin kudi ko wata kadara...

Saboda falalar Allah garemu ya halasta mana hanyar samun dukiya, Allah ya bamu hanyoyin samun dukiya da matukar yawa, Hanyoyin samun dukiya ta halal kashi 99% ne saura kashi daya kuma ne na haram!!
Kunga Allah yayi mana adalci...

Akwai kashe kashen neman halal -

Akwai mutane masu dagewa wajen neman halal, Suna nema tsakanin su da Allah, To wannan Allah yasanya albarka a ciki.

Akwai wanda kuma bayan kyautata neman shi babu ruwan shi da halal da haram, To wannan shine dukiyar ke zaman mashi bala'i, Koda anyi Sadaka ko hajjji ko umrah babu lada..

IDAN AN SAMU DUKIYAR to yaya zaka kashe ta??

Yan uwa musulmi akwai wanda ke zama abokin shi itace dukiya, Ya maida zancen shi kudi mafarkin ki shi kudi, Komai dai maganar kudi...

Alhali abunda ake bukata idan ka rike kudi ka dauke su a hannun ka ba'a zuciyar ka ba, Idan har kasanya kudi a zuciyar ka to lallai ka kama hanyar yin asara...

Yan uwa musulmi masu albarka hakika musulmi na kwarai shine wanda kudi basu hana shi bin Allah basu hana shi neman ilmi ko yin ibada.

Yan uwa musulmi hakika ranar kiyama kafin kowa ya shiga aljannah sai an tambaye shi game da dukiya!

Ina kasamo??
Ina ka aje??
Ina ka kashe??

Wallahi tallahi sai anyi mana wannan tambayoyin 😰😰

Hakika Allah madaukakin sarki ya halicce mu dan mu bauta mashi, Neman halal ne amma ba ido rufe ba 😇😇

Akwai wadanda suke da dukiyar mai yawa, Basu taimakon kowa basu taimakon addinin musulunci, Duk shelar da za'a yi na neman taimako ga addini amma babu ruwan shi...

Babu taimakon addini babu taimakon yan uwa ko makwabta kai wasu ma har iyalin su 😴

Akwai kuma masu almubazaranci da kudi, Komai suka samu nan take zasu kashe, Sai dai duk inda ake neman raya wata bidi'ah to zai bada gudunmuwa!!

Ire iren wannan duk makomar su wuta...

Akwai kuma masu riya, Wato zasu bada Kyauta da Sadaka amma ba dan Allah ba dan kawai ace wane yana da kokari!!

Yan uwa musulmi masu albarka hakika babu wanda zai tsira daga sharrin shaitan sai wanda ya nema ta halal kuma ya kashe ta halal, aka taimaki addini aka taimaki jama'a da marar sa galihu da marayu da sauran mabukata...

Lallai wadannan mutanen Allah yana son su jama'a ma suna son su kamar yadda Allah yake fada cewa cikin suratul furqan "SUNE IDAN ZASU CIYAR BASU TUNANIN KOMAI BASU HAUFI SUNA CIYARWA DAGA ABUNDA ALLAH YA AZURTA SU"

Yan uwa musulmi masu albarka hakika mu sani dukiyar nan aro ce Allah ya bamu, Duk abunda muka samu anan wallahi duk anan Zamu barshi!!

Dama munzo babu ko sisi babu kaciya babu riga babu wando, Haka kuma Zamu koma.

Yan uwa musulmi kada mu bari abunda ke karewa ya rude mu, Har muyi asara...

Shaitan yakan rudemu da aikata abunda ALLAH ya haramta, Kamar cha cha, Kamar zalunci kamar sata kamar cin hanci da rashawa, Yanzu ma'aikatan gwamnati sun lalace sun kowa yafi son inda ake kwasar dukiyar kasa!!

Yan kasuwa sun lalace sun koma mayaudara kasuwanci ya koma kamar na jahiliya.

Yan uwa musulmi Allah fa ya haramta mana cin dukiyar mutane ya haramta mana zubar da jini da cin mutuncin musulmi!!

Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya barranta da masu zalunci "BAYA TARE DAMU MAI YIN ALGUSU"

Yan uwa musulmi wajibi ne Mumini ya kaucewa zaluntar dan uwa musulmi kamar yadda baka son a cuce ka!!

Shi zalunci bai takaita ba kan yan kasuwa ko barayi, A'a akwai wanda ake ba rance bai biya ko kuma kasuwanci da yaudara.

Akwai wadanda kudi ke sanyawa girman kai da fankama, Inda Allah ya sanya kowa ya zam mai arziki da mun zama masu girman kai.

Da yawa wadanda Allah yaba dukiya tana zama sanadin hakalar shi.

Yan uwa musulmi duk wasu kudi da motoci da gidaje abun tambaya ne,

Kada mu manta fadar Allah garemu cewa "KUDI DA YAYA FITINA NE GAREKU"

ALLAH Ya gafarta mana yayi mana rahama, Ya ubangiji ya bamu dukiya mai albarka ta halal, Ya ubangiji ka biya mana bukatun mu na alkhairi ka yafe mana kurakuren mu ka gafarta wa mamatan mu, Ameen ya rabb.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 7-5-1439
Friday 26-January - 2018 AB

Saturday, 27 January 2018

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN SHIRKA DA NAU'OINTA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

#SHIRKA_DA_NAU'O'INTA

BAYAN mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka hakika banban abunda ALLAH yafi kauna shine riko da tauhidi, Kuma babban abunda ALLAH yafi kin shine shirka!!

ALLAH madaukakin na cewa "KU BAUTA MA ALLAH KADA KU HADA SHI DA KOWA"

lallai yan uwa musulmi mafi girman zunubi shine yin shirka da Allah....

ALLAH madaukakin na cewa yayi "DUK WANDA YAYI SHIRKA DA ALLAH MAKOMAR SHI WUTA (idan ya mutu bai tuba ba)"

Sannan kuma Allah na cewa "LALLAI ALLAH BAYA GAFARTAWA IDAN AKAYI SHIRKA DASHI AMMA YANA GAFARTA WANI LAIFIN WANDA BA SHIRKA BA GA WANDA YASO"

Yan uwa musulmi hakika Allah ya tsoratar da dukkan annabawan da ya aiko game da Shirka,  ALLAH yana cewa "MUNYI WAHAYI GAREKA DA WADANDA SUKA GABACE KA IDAN KAYI SHIRKA LALLAI DUK AYYUKAN KA SUN LALACE"

Yan uwa musulmi mu duba girman Annabawa amma Allah yace masu idan suka yi shirka ayyukan su sun lalace balle mu, Wannan kiran fa ba Allah yana nufin Annabawa ba!!

A'a ana nufin mu, Domin annabawa basu yin shirka...

Yan uwa musulmi idan muka diba musulmi fa yawa sun fadawa shirka da sanin su wasu kuma bada sanin su ba!!

ALLAH madaukakin sarki na cewa "DA YAWAN SUNYI IMANI AMMA SUN HADA ALLAH DA WANI"

Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya gargade mu gargadi mai tsauri yana cewa "lallai abunda nafi tsoratar maku a rayuwar Ku shine shirka karama"

Wata rana Abubakar assidiq radiyyallahu anhu yaje wajen Manzon Allah sai Manzo Allah yace mashi lallai shirka tana nan cikin musulmi, Lallai shirka tafi boyuwa a cikin Ku Sama da tururuwa a saman bakin dutse cikin dare "

Amma ga wata addua da zaka rika karanta wa domin neman kariya kace" YA ALLAH INA ROKONKA KA GAFARTA MANI KA KARENI DAGA SHIRKA "

NAU'OIN SHIRKA

*Rokon kabari, Sau da yawa zaka ga wasu masu karancin islamiyya suna zuwa rokon kabari, Ko aljanu ko waliyai ko annbawa Alaihis salam

Alhalin Allah madaukakin sarki ya haramta hakan har ma ya fada cikin suratul ahkaf cewa" BABU BATACCE IRIN MAI KIRAN WANIN WANIN ALLAH "

Kuma duk musulmi mai imani ya amince cewa kiran WANIN Allah shirka ne, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Roko ibada ne " Dan haka duk wanda ya roki WANIN Allah dan neman biyan wata bukata ko neman kariya hakika yayi shirka!!

* Kudurta cewa wani  na cutar wa...

Sau da yawa idan wani abu yafaru da dan Adam sai ya dora laifin bisa wani abu, Ko dora shi ga wani dalili ko kuma cewa ai wane ne dalili da sauran su...

ALLAH madaukakin sarki yace "IDAN ALLAH YA KAWO MAKA CUTA BABU MAI IYA DEBE MAKA ITA SAI SHI"

*SHIRKA TA HANYAR YIN MAGANA...

sau da dama wasu na fadar wasu maganganu alhalin shirka ce, Kamar cewa 'Taya Allah kiwo yafi Allah na nan'!

Kamar cewa Idan Allah ya yarda tare da wane, Ba' a cewa hakan nan cewa ake yi idan Allah ya yarda sannan wane ya yarda, Kaga dole sai ka fara sanya Allah farko.

Sannan masu cewa mun dogara ga Allah mun dogara gareka,  Huzaifa ya ruwaito cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada Kuce abunda ALLAH yaso da abunda wane yaso"

* JINGINA NI'IMAH GA WANI ABU....

jjngina samuwar Ni'ima ga wani abu kamar aiki, Ko sana'a ko, Alhali yin haka sanya wa Allah kishiya ne, Allah kuma yace "KADA KU SANYA MA ALLAH KISHIYA"

* SIHIRI...

Yanzu yawan yin sihiri ya yawaita cikin musulmi, A yanzu yadda sihiri yazama ruwan dare ya koma wa wasu kamar jini, Saboda yawan yin sihiri har sanya wasu anan Zamfara na Jefa Alqur'ani Mai tsarki cikin makewayi (Toilet) subhannallah...

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yaje wurin boka ko dan sihiri ya karyata abunda aka saukar wa Manzo Allah (Alqur'ani)" 

* YIN RANTSUWA DA WANIN ALLAH...

wasu nada tabi'ar yin rantsuwa da, kaddara ko lokachi ko iyaye da sauran su, Har munzo zamanin da akafi yarda da rantsuwar da akayi ba Allah a ciki...

* IZGILI DA WANI ABUN ADDINI....

wasu kuma nada tabi'ar yin izgili da Abubuwan addini kamar, Gemu hijabi, aswaki, Yawaita sallama da sauran su.

* RATAYA LAYA KO KARHU

Daga cikin musulmi akwai masu tabi'ar daura laya ko karhu ko guru ko qaho da sauran su, Da sunan samun kariya ko wani abu, Wannan duk shirka ne.

*JIBINTAR KAFURAI
wasu nada tabi'ar jibintar kafurai fiye da musulmai, Alhali basu son Allah kuma basu son Manzon Allah.

Tabbas duk wanda ya fada shirka tabbas ya halaka, Duniya da Lahira.

ABUBUWAN DAKE SAMUWAR MAI YIN SHIRKA

- Rayuwar mai shirka tana lala cewa.

- Kullum cikin tashin hankali mai shirka ke kasancewa.

-Cirewar natsuwa daga rayuwa.

- shiga cikin batattu domin Allah yace "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA BACE"

-Rosa ayyukan bawa, Duk wanda yayi shirka ya roza ayyukan shi.  ALLAH madaukakin sarki ya cewa Manzo Allah cewa "DUK WANDA YAYI SHIRKA YA LALATA AYYUKAN SHI"

-DUSHE HASKE.

duk mai yin shirka Allah zai sanya wa rayuwar shi duhu, Baya taba ganin hasken alkahri.!!

Yan uwa musulmi hakika shirka tana tauye imani, Lallai yazama wajibi garemu muyi watsi da duk abunda zai kowa mana tangarda a cikin imanin mu, Domin samun tsira gobe Kiyama mu da iyalan mu da yan uwan mu baki daya.
. Allah ka albarkaci rayuwar mu baki daya.

Allah kayi mana kariya daga shirka, Ka biya mana bukatun mu na alkhairi, Ya Allah Muna tawasuli da sunayen ka ka biya mana bukatun mu na alkhairi baki daya, Ya Allah kara albarka ga garuruwan mu kabamu lafiya da cikakken zama lahiya ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 01-5-1439
Friday 19-January - 2018 AB