Monday, 15 October 2018

009 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na Tara 009_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*TABBATUWAR JININ AL'ADA;*
     Shifa abinda ya
shafi jinin al'ada al'amari ne da Allah madaukain sarki ya yi bayaninsa a cikin Alkur'ani mai girma, Allah yana cewa:

```''Kuma suna tambayarka dangane da al'ada,
Kace: Shidinnan cutane, ku nisanci (saduwa da) mata a lokacin al'ada, kada ku kusance su har sai sun yi tsarki (Jinin ya dauke), idan suka tsarkaka
(suka yi wanka) to ku je musu ta inda Allah ya umarceku, Lalle Allah yana son masu yawan tuba
kuma yana son masu tsarkaka''.```
*[Bakara, ayata:222.]*

Haka kuma ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yace; ```(Wannan)
Wani abune da Allah ya dorawa mata 'ya'yan
Adam''.```
> Ashe ba shaci-fadin da ake cewa bane ai sanadiyyar da yasa mata suke al'ada shine wannan ganyan bishiyar da Nana Hawwa'u ta ci
a gidan aljanna, amma Annabi Adam mala'ikane
ya rike masa makoshi(makogaro) sai ya amayar da ganyen shi yasa maza basa yi.
   Wannan labarin bashi da kanshin gaskiya domin ayoyin Alkur'ani sun tabbatar da Annabi Adam ya ci itaciyar.

Shifa jinin al'ada kada amanta jini ne da yake fitowa daga can cikin mahaifa a lokuta sanannu,
Allah madaukakin Sarki ya halicceshi domin ya zama abinci ga yaro a lokacin da yake cikin mahaifiyarsa domin inda zai yi tarayya da
mahaifiiyar ta shi a abincin da take ci to da karfinta ya ragu sosai, sai Allah ya sanya shi ya zama abinci ga reshi, shi yasa dakyar kaga
mace tanada juna biyu (ciki) kuma tana al'ada.

Idan kuma ta haihu sai Allah ya mayar dashi nono jaririn yana sha amatsayin abinci, shi yasa kadan ake samun matan da suke shayarwa kuma suna al'ada. Idan ya zamana mace bata
da juna biyu (ciki) kuma bata shayarwa sai ya
kasance ba inda zaije(jinin al'adar) to shine sai ya taru a
mahaifarta, shine mafi yawancin lokuta yake fita a kowanne wata cikin kwanuka shida ko
bakwai, ya kan karu ko ya ragu akan hakan (kamar yadda bayanai za su zo da izinin Allah).

ZAMU TUQE A NAN SAI LOKACI NA GABA INDA ZAMUYI BAYANI AKAN KARKASUWAR MATA AKAN JININ AL'ADA INSHA ALLAHU

ALLAH YAYI MANA JAGORA

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE;

✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy ( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

No comments: