*KWAMITIN HARKOKIN ADDINI DA ZAMANTAKEWA NA MASALLACIN ABU HURAIRAH TSAFE*
*LADUBBAN NEMAN ILIMI DA BADA ILIMI*
✅ *IKHLASI:*
yi don Allah, mai neman ilimi da malamin dake bada ilimi ya zama dukan su sunayi don Allah, domin neman yaddar Allah. Rasulullahi (S.A.W) yace "Duk wanda ya nemi ilimi don neman yaddar Allah, daga baya ya canza niyarsa don neman duniya, ba zaiji kanshin Al-Janna ba" *(Abu Dawuud: 3664)*
✅ *NIYYAR DAUKE JAHILCI:*
Duk wanda zai nemi ilimi ko zai bada ilimi ya zamanto don ya dauke ma kansa jahilci da waninisa. Imam Ahmad Bin Hambali Yace "Shi ilimi babu abun dake dai-dai dashi ga daraja musamman ga wanda ya kyautata niyar sa". Dalibansa sukace kamar yaya? Yace "Wanda yayi da manufa (Niyar) ya dauke makansa jahilci ko waninsa"
✅ *NEMAN ILIMI DA MANUFAR KARE ADDINI:*
Ya kamata ga mai bada ilimi ko dalibi ya kasance da manufar ba addini kariya ya keyi, Rasulullahi (S.A.W) yace: "Yaku wanda sukayi imani ku kasance masu taimakon addinin Allah, *Q: Suratul Saffi;14".*
✅ *AIKI DA ILIMI:* Na daga cikin ladubban ilimi ga malami da dalibi aiki da ilimi Rasulullahi (S.A.W) yace Alqur'ani hujjane gareka ko akan ka” *(Muslim: 223)* hujjane gare ka in kayi aiki dashi kashiga Aljanna. Akan ka in bakayi aiki dashi ba ka shiga wuta.
✅ *HAKURI:*
Dole ne malami da mai neman ilimi suyi hakuri: malami yayi hakuri wajen bada ilimi, dalibi yayi hakuri wajen neman ilimi. Hakuri kan neman ilimi ya kasu gida ukku (3):
1. Hakuri da talauci da yinwa
2. Hakuri akan dagewa har sai ka samu
3. Rashin yanke kauna ga abin da kake nema
Imam Ahmad bin Hambali yace Na shekara tara (9) ina karatun *Kitabul Haid* har saida na gane shi
✅ *TAWALIU DA NISANTAR GIRMAN KAI:*
Ana son malami da dalibi su sanya tawali'u da nisantar girman kai ga abin da suke nema. Imam Mujahid yace Mai girman kai ko mai kunya baya samun ilimi.
✅ *TAFIYA DON NEMAN ILIMI:*
Wajibi ne ga malami ko dalibin ilimi da suyi tafiya don neman ilimi musamman ilimin da babu a inda suke. Rasulullahi (S.A.W) yace Neman ilimi wajibine ga dukkan musulmi” *(Muslim)*
✅ *RASHIN KARBAR ILIMI GA DAN BIDI'AH:*
Bai halitta ga dalibi ya nemi ilimi ga dan bidi'ah, yan bidi'ah sune wadanda suke saba ma gaskiya kuma suka kirkira abubuwan da musulunci bai zo dasu ba, kamar: Yan shi'ah, Khawarij, da sauran darikun Sufaye.
Muhd Bin Sirin yace: Kada ku kuskura ku zauna da yan bidi'ah kada kuyi karatu garesu kar ku sauraresu domin Ahlis-sunnah sunyi ittifaki a kaurace masu da kuma nesa dasu”.
Allah ya bamu ilimi Mai amfani Kuma Mai albarka 🤲🤲🤲
*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA COMMITTEE*
+2348064734911
https://fb.me/masjidabuhurairahtsafe
No comments:
Post a Comment