Wednesday, 6 December 2017

MU'AWUYA BN ABU SUFYAN

*BABU MAI ZAGIN MU'AWUYYA SAI KAFIRI FASIQI MUNAFUKI!!!*

```GA KADAN DAGA CIKIN TARIHINSHI DA
NASABARSHI DA KHALIFANCISA!!!
.
.
.
Nasaba Da Sarakutar Mu’awiya binu Abi
Sufyan(RA).

Shi ne Mu’awiya dan Abu Sufyan (sunansa
Sakhar) dan Harb dan Umayya.

   Ya fito daga
gidan Banu Umayya, dangin Sarkin Musulmi
Usmanu(RA). Mahaifinsa Abu Sufyan ya jagoranci
mushirikan Makka a cikin adawarsu ga
Musulunci da yaqoqansu ga Annabi(SAW).

Ya
musulunta shi da mahaifinsa bayan bude Makka
kuma ya halarci yaqin Hunain tare da Annabi
(SAW).

Ya kasance daga cikin marubutan
Annabi(SAW) kuma Manzo(SAW) ya auri ‘yar
uwarsa Ummu Habiba Ramla diyar Abu
Sufyan, Allah ya yarda da ita.

    Mu’awiya(RA) mutum ne da ya laqanci qulle-
qullen siyaa.

Umar binul
Khaddab ya nada shi a kan wani bangare na
qasar Sham kuma Usmanu binu Affan ya game
masa mulkin Sham baki daya. Mu’awiya ya ja
da Sarkin Musulmi Ali(RA) a lokacin da ya qi
ya yi mubaya’a sai har Ali ya zaqulo wadanda
suka kashe Usmanu daga cikin rundunarsa ya
hukunta su. A sakamakon haka, yaqin Siffain
ya auku tsakanin Ali da Mu’awiya. Bayan da
aka samu qiqi-qaqa a qarshen wannan yaqin,
Mu’awiya ya yi amfani da iya janhurunsa na
siyasa ya yi qarfi, a yayin da Ali ya yi rauni,
kuma rundunarsa ta wargaje a sakamakon
ficewar Khawarijawa daga cikinta. Ali(RA) ya
shagala da yaqar Khawarijawa, abinda ya
qara masa rauni, a lokacin da shi kuma
Mu’awiya ya qara qarfi da kama qasa a cikin
lamarinsa. Ana cikin haka ne Khawarijawa
suka shirya maqarqashiyar kashe Ali da
Mu’awiya, Allah ya yarda da su, wai domin su
hade kan Musulmi kuma su yi maganin fitina.
Amma Mu’awiya ya tsallake wannan
maqarqashiya da qaddarar Allah; shi kuwa sayyidina Ali(R.A)
da aka qaddara masa qarar kwana ya yi
shahada. Bayan rasuwar Sarkin Musulmi Ali
(RA), magoya bayansa sun yi mubaya’a ga
dansa Hassan(RA) wanda ya zama khalifa na
tsawon wata shida.
Hassan binu Ali(RA) ya yi tunanin ya kai
qarshen jayayya da Mu’awiya wacce ya gada
daga mahaifinsa. Don haka ya dauki matakin yin
sulhu da Mu’awiya kuma ya sakar masa lamarin shugabancin al’umma
domin tsai da zubar da jinin Musulmi a
junansu. Da wannan ne Mu’awiya ya zama
Sarkin Musulmi kuma dukkan bangarori suka
shiga qarqashin da’arsa, in banda
Khawarijawa wadanda suka ci gaba da yaqar
sa. Kuma da wannan sulhu ne aka kai
qarshen zamanin Khulafa’ur Rashidun kuma
aka fara zamanin khalifofin Banu Umayya.
Wannan ya faru a shekara ta 40 bayan hijira,
shekarar da akewa laqabi da Amal Jama’a,
watau shekarar hadin kai, saboda haduwar
al’umma a kan Mu’awiya(RA).
Mu’awiya binu Abi Sufyan ya yi shekara
ishirin yana gwamnan Sham, kuma ya shekara
ishirin yana khalifa. Ya rasu a shekara ta 60
bayan hijira, yana da shekaru saba’in da
takwas a duniya.
Sarkin Musulmi Mu’awiya ya auri Fakhitatu
diyar Qurza, ta haifa masa Abdurrahman da
Abdullahi. Haka nan, ya auri Maisun diyar
Badajal wacce ta haifa masa dansa Yazid
wanda ya gaje shi a matsayin khalifa. Mun
gabatar da bayani cewa gidan su Mu’awiya,
Banu Umayya, surukan Annabi(SAW) ne. Ya
aurar da diyansa mata uku ga ‘ya’yan wannan
gida. Su ne Zainab ya aurar da ita ga Abul
Aas binu Rabi da kuma Ruqayya da Ummu
Kulthum ya aurar da su ga Usmanu binu
Affan. Kamar yadda shi kuma ya auri ‘yar
uwar Mu’awiya, watau Ramla wacce akewa
alkunya da Ummu Habiba, Allah ya yarda da
su baki xaya.```

Copyright©
*ABU-SINAN*

SAKO ZUWA GA YAN TIJJANIYYA 001

*GAREKU YAN TIJJANIYYA, KU KARE ZANTUKANKU IDAN KUN KASANCE MASU GASKIYA*

*HUJJOJI NA HANKALI DA ZASU KORE QARYAR DA SHEIKH AHMADU TIJJANI (R.A) YA KWANTARA NA CEWA YA HADU DA MANZON ALLAH IDO DA IDO.*

_Fitowa na daya (001)_

```Farkon sabanin da aka fara samu a Musulunci tsakanin sahabbai ya Faru ne bayan rasuwar Manzon Allah s.a.w, a lokacin ne mutanen madina sukace ma mutanen Makkah (muhajirai) mu zamu Nada namu jagora, kuma Ku Nada naku. Haka akayi har tsawon kwana uku kafin a rufe manzon Allah s.a.w.
Tambaya; ya akayi manzon Allah s.a.w bai tashi ya kai karshen wannan cece-kuce da sahabbai keyi ba(ma'ana: yace wane ne Khalifa a baya na)?

Ya akayi manzon Allah s.a.w ya bar wannan al'amari na khalifanci mai girma ba tare da ya tashi yayi bayani ba???

Da ace manzon Allah s.a.w zaiyi magana da wani a farke bayan ya mutu, da sahabbanshi zaiyi magana dasu domin magance musu waccan jayayyar akan ace ya bayyana ga shehu tijjani. Bayan shi Tijjani sai da Manzon Allah s.a.w ya bar duniya da shekara dubu da Dari daya da hamsin(1150AH) ko makamancin haka sannan aka haifeshi. Toh ya akayi hakan ta kasance???

Yan Tijjaniyya muna bukatar amsar wannan tambayar!!!

Allah ka shiryar damu akan hanya madaidaiciya.

Copyright©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU-SINAN)
08064734911```

HUDUBAR JUMA'AH002

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*HUBUDAR JUMA'AH DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABI-HURAIRAH AREA II TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

Taken hudubar: *wajabcin neman Shawara a addinin Musulunci kashi na biyu(002)*

Mai gabatarwa: *_Sheikh Sani Liman (ABU-HURAIRAH) Tsafe._*

Shiga links dake kasa domin saukewa.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://kiwi6.com/file/ij1jswtjn6

Masu matsalar browsing zasu iya bi ta wannan Link
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://k003.kiwi6.com/hotlink/ij1jswtjn6/02h

```wannan itace cigaban hudubar da Shehin Malamin ya gabatar a satin da ya gabata, idan son samu ne ka sauraresu gaba daya domin amfanuwa.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi, Mu kuma Allah ya bamu ikon amfani da wannan hudubah.```

Copyright©
*_MASJID ABI HURAIRAH SOCIAL MEDIA TSAFE_*

HUDUBAR JUMA'AH001

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*HUBUDAR JUMA'AH DAGA MASALLACIN JUMA'AH NA ABI-HURAIRAH AREA II TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

Taken hudubar: *wajabcin neman Shawara a addinin Musulunci*

Mai gabatarwa: *_Sheikh Sani Liman (ABU-HURAIRAH) Tsafe._*

Shiga links dake kasa domin saukewa.
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://kiwi6.com/file/p4cumpwxef

Masu matsalar browsing zasu iya bi ta wannan Link
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

http://k003.kiwi6.com/hotlink/p4cumpwxef/h

```Akwai cigaban wannan hudubah a sati mai zuwa insha Allahu.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi, Mu kuma Allah ya bamu ikon amfani da wannan hudubah.

Copyright©
_Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU-SINAN)_```
atstsamawy@gmail.com
08064734911

ZUMUNTA A MUSULUNCI

🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

*_TATTARAWA:_*

*MALAM SANI LIMAN (ABU HURAIRAH) TSAFE*

_Fitowa Na biyu(002)_

```Bisimillahir-rahmanir-raheem, Alhamdulillah, bayan bayanin da ya gabata na ABUBUWAN DA WANNAN RUBUTU ya kunsa, yanzu zamu fada cikin bayanin Abu na farko.

MECECE ZUMUNTA???

  Ibn athir yana cewa zumunta tana nufin taimakawa yan uwa na bangaren dangantaka da sarakuta da kula da halayen SU koda kuwa suna zaune a wurare masu nisa koda kuma suna munana maka. A daya bangaren kuma, yanke zumunta yana nufin kishiyar abubuwan da aka ambata a baya.

DA WANE ABU AKE SADAR DA ZUMUNTA???

Ana sadar da zumunta da al'amura masu yawa kamar; Ziyartarsu, bibiyar halayensu, tambaya game dasu, aika masu da kyaututtuka da kuma saukar da kowannensu a matsayin da ya dace dashi(wato su yan uwan da ya kamata a sadar da zumunta garesu), sannan kuma ana Sadar da zumunta da bada sadaka ga fakirai daga cikin su da tausasama mawadatan su da girmama manyansu da kuma tausayama kananan su da masu rauninsu da yawan tambayar halin da suke ciki, ziyartar su da kanka ko ka aika wasika ko kayi amfani da wayar salula.

    Mafi girman abunda ake sadar da zumunta dashi shine; mutum yayi kwadayin kiransu((yan uwansa) zuwa ga shiriya ya umurcesu da aiki mai kyau ya kuma hana su aikata miyagun ayyuka.

   Haka nan zumunta bata da wani kayyadadden lokaci da aka kayyade don sadar da ita. Duk abunda al'ada ingantatta ta tabbatar a matsayin Sada zumunta, ana daukarshi a matsayin haka. Haka kuma duk abunda al'ada ingantatta ta tabbatar a matsayin yanke zumunta to ana daukarshi a matsayin haka.

   Zumunta tana bambanta gwargwadon kusanci da matsayi na wadanda ake sadar da zumuntar zuwa garesu, zumuncin da yake tsakanin uba da dansa ya sha bam-ban da Dan uwa na nesa.

   Bugu da kari, zumunta tana banbanta gwargwadon halayen da su wadanda za'a sadarmawa suke ciki, kamar sadar da zumunta ga marar lafiya da mabukaci ta bambanta da sadarwa ga waninsu. Haka kuma sadarwa ga babba ta banbanta da ta karami

    Haka nan sadar da zumunta yana banbanta ta fuskar bagire, Wanda yake zaune a cikin gari ya banbanta da Wanda yake zaune a wani gari wajen ziyartar shi da tambayar halinda yake ciki, da yimasa sallama ko aika mashi da sakonni.

Zamu tsaya a nan, sai wani lokaci idan Allah ya kaimu insha Allahu.

Allah ya bamu ikon sadar da zumunta gwargwadon iko Amiin.

A gaba zamuyi bayani akan FALALAR SADAR DA ZUMUNTA insha Allahu.

Allah yayi mana jagoranci.

Copyright©
MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA```
+2348064734911

BIDI'AR SHAFAR FUSKA BAYAN KAMMALA ADDU'AH


BIDI'AR SHAFAR FUSKA BAYAN KAMMALA ADDU'A🙏
Ibn Rushud yace: an tambayi imamu malik akan mutumin da yake shafar fuska da tafukansa yayin kammala addu'a bayan ya shinfida tafukan kafin hakan?sai imamu Malik yayi inkarin haka,yace bansan wannan ba. nace (Ibn Rushud) Malik (R)yayi inkarin shafar fuska da tafukan hannu bayan addu'a domin yana ganin yin haka badi'a ne, domin babu wani asar daga manzon Allah yake nuna halaccin hakan kuma ra'yi baida mashiga a cikin
📚(albayan wattahsil 49/18)
Imam Abu Daud yace:naji an tambayi imamu Ahmad akan mutumin da ya ke shafar fuskar sa da hannunsa bayan ya kammala wuturi? Sai ya ce "bantaba jin wannan ba" a wani lokacin ma cewa yayi "bantaba jin wani Abu game da shiba". Abu Daud yace banga imamu Ahmad yana aikata hakan ba(ma'ana:babu wani Abu da ya tabbata daga manzaon Allah akan yin haka, kuma babu wani daya daga cikin magabata da ya aikata  haka.
📚(masa'ilah 102).

SIFFOFIN MACE TA GARI

📜📜📜
SIFFOFIN MACE TAGARI📜📜📜
Shaikhul Islam Ibn Taimiyya yace"mace ta gari tana kasancewa tare da miji nagari tsawon shekaru masu yawa.
Ita ce jindadin sa Wanda manzon Allah(saw) ya fada a cikin hadithi yace"ita duniya wani Dan jindadi/amfani ne kuma mafi alkhairin amafani/jindadin ta ita ce mace mumina wadda idan ka kalle ta sai ta  burgeka, idan kabata  umarni sai ta yi maka da'a, idan kafita kabarta zata  kiyaye ka ga kanta(ba zata ci amarnarka ba).

Itace wadda manzon Allah yayi umarni da ita a cikin  zancen sa lokacin da muhajiruna suka tambaye shi:wace dukiya ya kamata murika? Sai yace: "harshe mai yawan ambaton Allah, da zuciya mai yawan godiya, da MACE TAGARI mai taimakon dayanku bisa imani"
(📚Timidhi ya Ruwaito shi saga Salim ibn Abilja'ad daga  Sauban).

Ita ce wadda kauna/soyayya da tausayi yake tabbata da ita kamar yanda Allah (SWT) ya fada a cikin Alqr'an, radadin rabuwa da ita yafi tsanani sama da na mutuwa,wani lakacin ma yafi tsanani sama da kariyar arziki, yafi tsanani sama da barin wurin zama(gida) musamman idan akwai alaqa a tsakanin su (zumunta) ko kuma suna da  'ya 'ya a tsakanin su wadan da rabuwar zata jefasu cikin yanayi na kunci da  tozarta da kuma  gurbacewar dabi'un  su"
(📚majmu'ul fatawa 35/299)

🕌🕌COMMITTEE FOR SOCIAL MEDIA MASJID ABU HURAIRA TSAFE ZAMFARA STATE (07039140450)