HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA
UKKU DAKE TSAFE
ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon
Limamin Massallaci
Jumu'a Na Ukku Dake
Unguwar Area2, Tsafe
Sheik Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #ADALCI Godiya ta
tabbata ga
ALLAH Wanda yayi
umarni Da adalci yayi
hani ga cuta koda kuwa
ga kafurai ne, Na shaida
cewa babu Annabi Muhammad Bawan
ALLAH Ne kuma
manzon sa.
Yan uwa Musulmi muji
tsoron ALLAH Wanda
yayi umarni da ADALCI Yana fada a cikin
suratul nahali ''YANA
UMARNI DA ADALCI
YA HANA ZALUNCI
Hakama ALLAH
Madaukakin sarki yana cewa A cikin suratul
hujirat ''KUYI ADALCI
GA JUNNANKU''
Yaku Yan uwa musulmi
yin adalci tsakanin mu
mafita tare da mafi chan chanta ga rayuwar mu,
A cikin magabatan
malamai wani daga cikin
su yana cewa ADALCI
Shine asa komai dai dai
inda ya dace, Babban malamin tauhidin
nan Ibn taimiyah yace
karshen zalunci shine
tabewa, Karshen
ADALCI Shine aza
komai inda yake tare da aza komai inda
yakamata.
kusani ALLAH Baya
taimakon Azzulumai!
Imam muslim ya ruwaito
a Cikin Wani hadisin yana cewa Manzo
sallallahu Alaihi
wassalam yana cewa
''MASU ADALCI
SUNE A SAMAN
HASUMIYA MAI HASKE A RANAR
KIYAMA''
Yaku yan Uwa musulunci
ku kasance masu adalci
tsakanin matan ku.
Manzo sallallahu alaihi wassalam yace mutun
uku
zasu shiga aljannah
1-Shugaba mai
adalci:Wanda yake
adalci tsakanin
talakawan sa, yake sauke nauyin da ke kansa
yaji
tsoron ALLAH
Madaukakin sarki
2-Mai taushin zuciya
:wanda yake wadata da
abunda ALLAH Ya bashi ya sauke nauyin
iyalin sa, ya shayar da su
halal duk da yana da
matsi
3-Mai kame kai:mai
kame kai daga duk abunda ALLAH Yayi
masa iyaka dashi
Yaku yan Uwa musulmi
manzo tsira ya fada a
cikin hadisi cewa Mutun
Bakwai ALLAH Zai sanya su cikin inuwa
ranar da babu wata sai
ita a ciki akwai
''SHUGABA MAI
ADALCI''
Shi adalci nau'i nau'i ne 1-Adalci ga rayuwa
2-Yima wasu adalci
Kamar yadda ALLAH
Madaukakin sarki ya ce
''LALLAI ALLAH NB
UMARNI KU BADA HAKKI GA MASU
SHI KU TSAIDA
GASKIYA''
Alkali yayi adalci ga
wadanda yake wa shari'a
yayi adalci tsakanin bangori guda biyu
ALLAH Madaukakin
sarki Yana cewa ''KAYI
HUKUNCI
TSAKANIN
MUTANE DA ADALCI KADA KABI SON
RAYUWAR KA.
3-Adalci tsakanin yaya,
sau da yawa zaka ga
wasu na nuna banbanci
tsakanin yan wancan dakin dana wancan
yakamata muji tsoron
ALLAH Yaku yan uwa
musulmi
A wani hadisi wani
mutun yazo wajen Manzo Sallallallahu yace
''WANNAN
DANDANA NE ZAN
BASHI KYAUTA INA
SO KAYI SHAIDA SAI
MANZO SALLALLAHU
ALAIHI WASSALAM
YACE KANA DA
WASU YAYAN YA CE
EH, SAI YACE
KABASU KYAUTAR SAI YACE A'A Daga
nan MANZO
SALLALLAHU
ALAIHI WASSALAM
YACE BANA SHAIDA
AKAN ZALUNCI'' 3-ADALCI Ga magana
ALLAH Yana cewa
''IDAN ZAKUYI
MAGANA KUYI
ADALCI KODA
(ADALCIN) ZATA KASANCE KAN YAN
UWANKU''
4-ADALCI Tsakanin
mata yakamata magida
suyi adalci domin ya
tabbata a hadisi cewa ''RANAR KIYAMA
WANI ZAI TASHI
BANGAREN JIKINSA
YA SHANYE (Wannan
mai nuna son zuciya ne ga
iyalinsa) Hakama ALLAH
Madaukakin sarki yana
cewa ''IN KUNJI
TSORON BAKU
ADALCI TO KU AURI
DAYA'' 5-ADALCI Ga makiya
yin adalci ga makiya
shima nau'i ne na adalci
Yaku yan uwa musulmi
kusani adalci shine ya
tsaida sama da kasa, Hakama Dazarar babu
adalci to za'a shiga
musiba
Musulunci yana cike da
adalci kamar yadda
wannan ayar ke nunawa ''KALMOMIN
UBANGIJI SUN CIKA
DA ADALCI ''
Yaku yan uwa musulmi
tillas ne kuma wajibi
muyi adalci ga kawunan mu, da matanmu da yan
uwa mu, kai harma da
makiyan mu
Ya ALLAH Muna
rokonka da girman ka da
matsayin ka bamu ikon yin adalci
Yaku yan uwa musulmi
kusani ADALCI
Matattarar tsoron
ALLAH Babban Gida a
ADALCI Shine Tauhidi hakama babban zalunci
shine shirka da ALLAH!
Ya ALLAH Muna
rokonka da girman ka da
matsayin ka bamu ikon
yin adalci,Ka daukaka musulunci da musulmai,
ka kaskanta kafurci da
kafurai kayi garin mu
Albarka Ka kyautata
Karshen mv
Subhakalla humma waabiihammdik ash hadu
an la'ila ha illa antta
astagfirka wa'atubu
ilaik
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE
ZAMFARA
19/05/1438
17/02/2017.