FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallacin Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani
Liman(ABU HURAIRA)
Yayi Hudubar Sane Akan
Muhimmancin Rike # ZUMUNTA_KO_KUMA
_SADA_ZUMUNTA
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Haka Kuma ALLAH S.W,T Ya Wajabta Sada
Zumunta Tsakanin Yan Uwa Jini,
Sada ZUMUNTA Dai Bawai Kawai Ya Takaita Ga
Fada Cewa Wane Dan Uwa Nane, A.a, Dole Ne
Anga Wannan Kalma A Zahiri, Da Kuma
Aiwatarwa A Aikace,
Yaku Yan Uwa Musulmi Kusani Ana SADA
ZUMUNTA Ta Hanyoyi, Da Dama, Daga Cikin
Akwai Kyautatawa Ta Hamyar Basu Wani Ihsani,
Sannan Akwai Sakin Fuska, Akwai Jawo Su A
Jiki, Anan Akwai Gagarumar Matsala!
Sau Da Yawa Zakaga Wani Yana Kyautatawa Yan
Uwansa, Amma Baya Son Su Dinga Ziyatar Sa,
Ziyara Kuma Daya Ce, Daga Ciki Ko Kuma Itace
Ginshiki Wato PILLAR, Ta Zumunci!
Yan Uwa Musulmi Mu Jure Mu Yaki Shaidan A
Tsakanin Mu, Domin Shaidani Shine Babban
Wanda Ke Sanya Mana Dogon Lokaci Idan
Mukayi Niyar Zuwa Ziyara, Zakaga Kayi Niyar
Zuwa Ziyara Amma Shaidan L.A Sai Yace Maka
A.a Bari Ka Kara Samun Kudi, Wanda Babu
Ranar Dazaka Same Su, Muddin Kana Sanya
Rana Irin Haka!
Malamai Magada Annabawa Sunyi Mana Nasihohi
Kamar Haka,
1.DUK WANDA YA YANKE ZUMUNCI GAREKA TO
KA SADAR MASA
2.DUK MAI FUSHI DAKAI KAYI MASA MAGANA
KODA BAYA AMSAWA
3.YAWAN ZIYARA YANA KARA DANKON
ZUMUNTA
4.IDAN MA HAR BAKA SAMU DAMAR ZIYARAR
BA, TO KIRAN SU TA WAYA MA ZAI TAIMAKA
AMMA BAI WADATAR BA
5.A KALLA KA KIRA YAN UWANKA KODA SAU
DAYA NE BAYAN KWANAKI GOMA
6.JURIYA TARE DA HAKURI,TARE DA GANI
AMMA KAYI KAMAR BAKA GANI BA
Hadisi Yazo Daga Manzon Tsira Cewa ZUMUNTA
Tana Addu'a Kullun Tana Cewa YA ALLAH DUK
WANDA YASADA NI, KASADA SHI DA
RAHAMARKA, DUK WANDA YA KATSE NI, KA
KATSE SHI DAGA RAHAMARKA
Daga Karshe Muna Fatar Yan Uwa Zamu Gyara
Zumuntar Mu, Tsakanin Mu Dan Yan Uwan Mu.
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
No comments:
Post a Comment