HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Masallacin Jumu'a Na
Ukku Dake Area II Tsafe Sheik Sani
Liman(ABU HURAIRAH)
Yayi Hudubar Sane Akan
Muhimmancin #BIYAYYA_GA_IYAYE
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Hakan Tasa Ya Umurci Bayin Sa , Dayimai
Biyayya,
Sai Kuma Yasanya Biyayya Ga Iyaye Tare Da
Tasa, Yin Biyayya Ga Iyaye Dole Dole Dole Ne,
Ana Yiwa Iyaye Biyayya Akowane Halli in Banda
idan suka umarce ka da Sabon ALLAH''
Ana Fifita yiwa uwa biyayya fiye da uba kamar
yadda daya daga cikin hadisan annabin rahama,
ya nuna mana,
Zakalika annabi rahama yafada a wani hadisin
cewa YAR DAR ALLAH TANA TARE DA YARDAR
IYAYE HAKAMA FUSHIN ALLAH YANA TARE DA
FUSHIN IYAYE''
Akwai Wani nauyi wanda iyaye keda shi kan
mutun idan sun rassu , daga cikin wadannan
nauyin akwai, Yi Masu Addu'a Bayan Basu
duniya, Sada zumuntar da suke sadawa idan su
nan, girmama yan uwansu da abonkasu, da dai
saurasu,
Yaku Yan Uwa Musulmi Ku Sani duk wanda ya
mutu iyayensa basajin dadin sa, to TABBAS
BAYA SHIGA
Yaku yan uwa kunji wata babbar magana!
Daga karshe ina fatar kowa zai kara gyara
zamantakewar sa da iyayens, wanda kuma nasa
basanan zai bi waccan hadisin daya gabata,
muna rokon ALLAH Yagafarta masu gaba daya,
Nima Mahaifina Ya Rassu Ina roko masa gafarar
ALLAH,Game da kurakurar daya gabatar a
rayuwar sa,
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA ALA
ALI MUHAMMADIN WASSALIM
©®DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
11/Safar/1438
11/11/2016.
No comments:
Post a Comment