HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallacin Jumu'a Na
Ukku Dake Area II, Tsafe Sheik Sani
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan
#KAUCEWA_KOYI_DA_YAHUDAWA_TARE
_KAUCEWA_MURNAR_SABUWAR_SHEKARA
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Haka Kuma ALLAH S.W,T
Hakika Addinin Musulunci Shine Cikakken Addini
Kuma Karbarben A Wurin ALLAH Madaukakin
Sarki, Haqiqa Addinin Musulunci Yana Dokoki Da
Kowane Musulmi Yazama Wajibi Yakiyaye Su,
Musulunci Yayi Mana Gata, Ya Bamu Yanci Kuma
Ya Gindiya Mana Sharudda Wadanda Aka
Haramta Mana,
Musulunci Yana Da Watanni Har Guda Goma Sha
Biyu Kamar Yadda ALLAH Yafada Mana, A Cikin
Alqu'arni Mai Tsarki Cewa ''LALLAI WATANNI A
WURIN ALLAH SUNE GUDA GOMA SHA BIYU
DAGA CIKIN SU AKWAI HUDU MAFIYA ALBARKA
KADA KU CUCI KAWUNAN KU A CIKINSU''
Yan Uwa Musulmi Idan Muka Lura Da Wannan
Ayar Ta Nuna Mana Cewa Watanni Musulunci
Sha Biyu Ne, Sun Fara Daga Muharram Zuwa
Zhul Hijja,
Addinin Musulunci Kammalallen Addini Ne Kamar
Yadda Alqur'ani Yafada ''A YAU NA KAMMALA
MAKU ADDININKU NA TABBATAR MAKU DA
NI'IMAR KU(MUSULUNCI) NA WAJABTA MAKU
ADDININ MUSULUNCI YA ZAMA ADDININ''
Mai Ahdari Ya Fada Cewa BAI HALLATA GA
MUTUN YA AIKATA WANI AIKI FACE YASAN
HUKUNCIN ALLAH AKAN WANNAN AIKIN''
Addinin Musulunci Yazo Da Komai Kuskure
Jahilcine Wani Ya Fada Cewa Babu Siyasa A
Addini,
Musulunci Nada Komai,
A Wannan Lokaci Da Muke Ciki Arna Na Shirin
Fara Chrismat!
Wanda Abun Ban Takaici Zakaga Musulmai Wai
Suna Taya Arna Murnar Zagayowa Wannan Rana,
Ita Ranar Christmat Rana Ce Da Aka Haifi Annabi
Isah A.S
Shehul Islam Ibn Taimiyah Yafada Cewa
Hawwariyun Wato Wadanda Suka Taya Annabi
Isah Isar Da Sako Basayin Wannan Bikin, Kunga
Idan Kun Lura Suma Kansu Bidi'a Ce Suka Qago
Wa, Kansu,
Bayan Haka Akwai Wani Kuskure Da Zai
Jagoranci Fitar Mutun Musulunci Wato NEW
YEAR
A Wajen Musulunci Bikin NEW YEAR Haramunne,
A Wajen Arna Kuwa Suna Murna Haihuwar
Annabi Isah, Wanda Suke Dangantawa Wai
Dandan ALLAH A uzu Billahi Iyaza, Ameen,
Kunga Kenan Idan Ka Taya Arna Murnar NEW
YEAR Ko Kuma Christmat Kamar Ka Taya Su
Wancan Shirkar Dana Gaza Sake Rubutawa, A
Uzubillah,
Yaku Yan Uwa Musulmi Idan Muka Girmama
Addinin Mu Hakika Duniya Zata Girmama Shi,
Idan Muka Wofintar Dashi Kazalika Duniya!
Yana Da Kyau Mu Fara Gabatar Da Kwanan Wata
n Musulunci Kafin Nasu,
Yakamata Idan Yazama Wajibi Muyi Amfani Da
Sunayen Watanni Mu Fada Da Hausa, Misali
January Sai Muce Watan Daya,
Bawaye Bane Kuma Ba Gwaninta Bane Wai Ace
Mu Duk Daya, Ai Duk ALLAH Muke Bautawa
Wanda Wannan Kuskure Ne, Basason Mu Kuma
Basason Addinmu Ta Yaya Za'a Ce Mana Wai
Daya Muke?
Baka Tabajin Arne Ya Fadi Hijra Musulunci Ba,
Yaku Yan Uwa Musulmi Duk Abunda Aka Baku
Naci Ko Na Sanyawa Da Sunan Christmat
Haramun Ne,
Ku Tuna Suna Danganta ALLAH Dai Haihuwa Fa
A'uzubillah, ALLAH Kuma Ya Karyatasu A Wajaje
Da Dama Kamar Su Suratul Ikhlas Da Sauransu,
Hakama ALLAH Ya Fada Cewa'' SAMA NA SON
TSAGEWA KASA NA SON TSAGEWA DUWATSU
NA SHIRIN TSEREWA TA DALILIN DANGANTA
WA ALLAH DANDA''
''TA YAYA AKE DANGANTAWA ALLAH DA? BAYA
TABA YIWUWA ALLAH YA RIKI DA'''
'
'
Mu Kiyaye Yan Uwa Idan Kwadai Da Wulakanci,
Hakama Inda Kwadaiyi Akwai Jahannama
Manzo S.A.W Yace ''WANDA YAYI KAMA DA
MUTANE HAKIKA YANA CIKINSU''
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA ALA
ALI MUHAMMADIN WASSALIM
©®DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
+2347064282182
23/Rabi'u Auwal/1438
23/12/2016.
No comments:
Post a Comment