HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #LOKACHIN_SANYI
_DA_ABUBUWAN_DA_YAKAMATA_AKIYA
YE_DA_KULA_DASU
Bayan Sallama Ga Yan Uwa Musulmi, Da Salati
Ga Abul Kasim S.A.W, Da Yabo Ga ALLAH S.W.T,
Sheik Yafara Da Cewa Yaku Yan Uwa Musulmi
Kusani Addini Ya Tanadi Komai, Wanda Yazamo
Jagora Garemu Da Kuma Hanya Wace Idan Muka
Kiyaye Zata Kaimu Ga Hanyar Tsira Gobe
Kiyama,
TSARKI Wani Na'u Ne, Na Addinin Musulunci
Wanda Idan Babu Tsarki Babu Alwallah,
ALWALLAH Kuma Mabudi Ga Ibadah, Musamman
Ibadah Ta Sallah,
Yadda Ake ALWALLAH Shine
Fara Yin Bismilla, Sannan Wake Hannuwa Zuwa
Guiwar Hannu, Sannan Wake Fuska Gaba
Dayanta Tun Daga Mafita Gashin Kai Har Zuwa
Kasan Gemu, Sau Ukku, Sannan Sai Wanke
Hannu Na Dama Zuwa Karshen Guiwar Hannun
Na Dama Sau Ukku, Sannan Kayi Haka Sau Ukku
Ga Hannun Hagu, Sai Shafar Kai Daga Mafitar
Gashi Zuwa Kasan Kai, Jewa Da Dawowa,
Sannan Kwalkwalar Kunne, Daga Karshe Sai
Wanke Kafafu, Farawa Da Kafar Dama, Ka
Tsittsefe ta Gaba Daya, Hakama Kafar Hagu!
MANZO S.A.W YACE DUK WANDA YAYI IRIN
WANNAN ALWALLAR AN GAFARTA MASA
ZUNUBANSA''
ALWALLAH Nada Wani Tasiri A Fuskar Dan
Adam Musulmi, Idan Musulmi Ya Tashi Ranar
Alkiyama Gabobin ALWALLAR Sa Zasu Dinga
Haskakawa, Daga Nesa Zaka Ganesa, ALLAH
Yasanya Mu A Cikin Su,
Yaku Yan Uwa Musulmi Hakika Muna Cikin Wani
Yanayi Na Sanyi, Wanda Amfani Da Ruwa Yana
Da Nauyi Sosai,
''MANZO S.A.W YACE ALWALLAH A LOKACHIN
SANYI TAFI LADA BISA GA LOKACHIN ZAFI''
Haka Zalika ALLAH Madaukakin Sarki Yace
''MUSULUNCI NA NUFIN SAUKI GA AL'UMMA BA
TSANANI BA''
A Wannan Lokachin Akwai Wadanda Idan Sukayi
Amfani Da Ruwan Sanyi Zai Zama Illa Garesu,
A Musulunche Babu Laifi Ka Dafa Ruwan Zafi,
Kayi Amfani Dasu Dan Alwallah, Domin Addini
Sauki Garai,
MANZO S.A.W Yana Amfani Da Wani Kyalle,
Bayan Yayi Alwallah Yana Goge Ruwa,
Kunga Babu Laifi Mu Goge Ruwa Bayan Anyi
Alwallah,
Yan Uwa Musulmi Mu Kyautata Alwallar Mu, A
Wannan Lokachin Dan Samun Karin Lada Ga
ALLAH Madaukakin Sarki,
Mu Daure Kuma Mu Jure Wallahi Idan Muka
Kiyaye Zamuyi Mamaki A Ranar Da Dukiya Da
Yaya Basu Da Amfani!
Idan Akace Kaza Sunnah Ne To Murike Da
Gasken Gasken, Wani Abunda Da Yakara Burgeni
Da Musulunci Shine Zaka Aikata Wani Abun Kai
Kanka Bakasan Yana Da Lada Ba, Amma Idan Ka
Aikata Zaka Samu Lada,
Mu Godewa ALLAH Dayayo Mu Musulmi, Sannan
A cikin Al'ummar Annabi, Da Kuma Yayo Mu
Ahlissunnah,
ALHAMDULILLAH
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA ALA
ALI MUHAMMADIN WASSALIM
©®DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
+2347064282182
30/Rabi'u Auwal/1438
30/12/2016.
ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU. MU KOYI IBADA A SAUKAKE
Friday, 8 December 2017
HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN MAI ZAN AIKATA LOKACIN SANYI.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment