Friday, 8 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN DOGARO GA ALLAH.

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan
Muhimmancin #DOGARO_GA_ALLAH
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Haka Kuma ALLAH S.W,T Ya Halicci Kome Da
Kowa Hakika Shine Maqagin Komai Da Kowa,
ALLAH S.W.T Cikin Hikimar Sa Ya Halicci Dan
Adam, Da Aljani Da Dabbobi Da Tsuntsaye, Da
Ruwa Da Iska, Da Abunda Na Kawo, Da Wanda
Ban Kawo Ba, Ya Halicci Abunda Muka Sani Ya
halicci Wanda Bamu Sani Ba,
ALLAH S.W.T Ya Qagi Wata Abu Da Ake Kira
Dogaro Ga Rai,
Hausawa Na Cewa Dogaro Ga ALLAH Jari,
Kwarai Kuwa Wannan Maganar Haka Take,
''ALLAH S.W.T Yace WANDA YAJI TSORON
ALLAH ZAI BASHI MAFITA KUMA ZAI
ARZIRTASA TA HANYAR DA BAYA TSAMMANI''
Yan Uwa Musulmi DOGARA GA ALLAH Ba Yana
Nufin Wai Kayi Kwance Yajira Wai ALLAH Zai
Kawo Masa Taimako, A'a Katashi Ka Nema Ka
Dogara ALLAH WALLAHI ALLAH Zai Taimakeki,
Akwai Abunda Ake Kira Musabbab, Ma'ana
Sanadi,
Manzo S.A.W Ya Fada Cikin Wani Hadisi Idan
Annabi S.A.W Yace ''TSUNTSAYE ZASU KWANA
BASU DA KOMAI AMMA ZASU KAI MARAICE
CIKIN SU, A CIKE''
Wannan Hadisin Ya Nuna Mana Cewa Tabbas
Idan Ka Dogara Ga ALLAH Zai Baka Mafita,
Kuma Ya Nuna Mana Cewa Ba'a Kwance Ashe
Wai ALLAH Kawo Mani,
Idan Muka Koma Kan Magana Ta Sanadi, Tana
Nufin Ka Tashi Ka Nema, Mai Da Kayanka Ga
ALLAH, Yarda Babu Mai Kawo Hasara Ko Riba
Sai ALLAH,
Kissar Annabi Yunusa Tazo A Cikin Alqur'ani Mai
Girma Cewa Lokachin Da KIFI YA HADEYASA YA
KOMA GA ALLAH INDA YAKAMA FADIN ''TSARKI
YA TABBATA GAREKA KAI KADAI, TSARKI YA
TABBATAR MAKA LALLAI NI NA ZALUNCI
KAINA''
Kunga Wannan Kisar Ta Nuna Mana Yadda
Annabi Yunusa Ya Maida Dogaron ALLAH Kuma
ALLAH Yabasa Mafita Ta Hanyar Fitar Dashi
Daga Bakin Kifin, Amma Duk Da Haka Yana Iya
Kokarinsa,
Yaku Yan Uwa Musulmi Idan Mukayi La'akari Da
Halin Da Muke Ciki A Wannan Zamanin Tabbas
Mafi Yawancin Mu, Mun Rasa Dogaro Ga ALLAH.
Yan Uwa Musulmi Wasu Daga Cikin Mu, Na Dora
Ko Kuma Aza Halin Da Muke Ciki Da Shugaban
Kasa Buhari!
Wanda Wannan Kuskure, Wallahi Sahabban
Annabi Sallallahu Alaihi Wasalam Sun Shiga Hali
Wanda Yafi Nanu Nesa Nesa, Ba Kusa Ba, Amma
Sun Maida Kayansu Ga ALLAH Kuma Yafitar
Dasu A Matsin Da Suka Tsinci Kansu,
A Yakin Badar Musulmi Sun Fito Su Dari Ukku Da
Sitti Wata Ruwaya, Arna Kuma Sun Kai Dubu Da
Wani Abu A Wata Ruwaya, Musulmi Qalilan Ne
Ke Saman Dawakai, Amma ALLAH S.W.T Ya
Basu Nasara Akan Kafurai Suna Ragargazasu
Suka Kore Su,
Duk Irin Hali Na Dadi, Ko Akasin Haka Mu Daina
Dangantawa Ga Mani Mu Maida Lamuran Mu Ga
ALLAH
YAN UWA DA FATAR KUN WUNI LAFIYA
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA ALA
ALI MUHAMMADIN WASSALIM

©®DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA

18/Rabi'u Auwal/1438
18/12/2016.

No comments: