Tuesday, 30 March 2021

05 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA BIYAR (005) DA NA SHIDDA (006)

📒ABU NA BIYAR: SUNNAH NE DANGIN MAMACI DA MAKWABTAN SA SUYI ABINCIN DA KOSAR DA IYALAN MAMACI SU AIKA MASU📒

📌1.Yana daga cikin karantarwar Annabi Muhammad SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM domin tausaya ga iyalan mamaci, dangin sa da makwabtan sa su aika masu abincin da zai Kosar da su. Saboda Hadithin Abdullahi bin Ja'afar da yake cewa: lokacin da labarin mutuwar mahaifin mu (Ja'afar) ya zo, sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM yace: "KUYI ABINCI DON IYALAN GIDAN JA'AFAR (ku aika masu) HAKIKA ABIN DAKE SHAGALTAR DA SU YA ZO MASU". [Abu Dawud da Tirmiziy da bin Majah suka ruwaito sa kuma Hadithi ne ingantacce].

🖋️Haka kuma Imam As-Shafi'iy a cikin littafin sa AL-UMM yana cewa: "INA SO GA DANGI DA MAKWABTAN MAMACI SUYIWA IYALAN MAMACI ABINCI DA ZAI KOSAR DASU A YINI DA DAREN DA YA RASSU, DOMIN SUNNAH NE KUMA YANA DAGA CIKIN AYUKKAN MUTANEN KIRKI A GABANIN MU (Sahabbai da Tabi'ai) DA MA NA BAYAN MU (sauran mabiyan Sunnar Annabi). A karshe sai ya kawo Hadithin Abdullahi bin ja'afar da ya gabata.

📒ABU NA SHIDDA:MUSTAHABBANCIN SHAFA KAN MARAYA DA TAUSAYA MASA📒

📌1. Mustahabbi ne shafa kan maraya da girmama sa, saboda Hadithin Abdullahi bin Ja'afar da yake cewa:.....Manzon Allah ya wuce mu yana kan dabba ni da Qathm da Ubaidullah bin Abbas, sai yace ku miko man shi (wannan yaro) sai aka mika ni ya dora ni a gabansa, sai yacewa Qathm ku miko man shi, sai aka mika masa shi, sai ya dora sa a bayan sa...... a duk lokacin da ya shafi kaina sai yace: "YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA". [Ahmad da Baihaqiy suka ruwaito sa kuma Hadithi ne ingantacce].

Wannan shine abinda Sunnar Annabi Muhammad SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM ta tabbatar dangane da ta'aziyya.

Wallahu a'alamu bissawab.

✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

04 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA HUDU (004)

📒ABU NA HUDU: ABUBUWA UKU DA YA KAMATA A NISANTA A LOKACIN MUTUWA📒

Ya kamata a nisanci al'amurra uku da matane ke yawan yi lokacin da aka yi mutuwa.

📌1. Tururuwar mutane wurin shiga gidan da akayi mutuwa, bai dace ba mutane su dinga shiga gidajen da aka yi mutuwa alhali basu da hurumin shiga gidan da sunan yiwa mata ta'aziyya.

📌2. Taruwa a wani kebantaccen wuri domin karbar gaisuwa (ta'aziyya), kamar Masallaci ko gida ko Makabarta. Musamman yanzu wuraren karbar gaisuwa ya dauki wani sabon salo, wani lokaci kaga kamar buki ake yi an kawo rumfuna da kujeri sai abinci ake kawowa kala-kala, wani lokaci kuma ya zama wurin sharholiya da shaci fadi da giba da aibanta shugabanni da Yan siyasa da masu kudi harma da malaman addini. Kai abin bai tsaya nan ba wasu sun mayar da wurin karbar gaisuwa wani dandalin siyasa da rabawa matasa zauna gari banza kudade.

📌3. Abinci da iyalan mamaci ke tanada domin tarbon masu zuwa ta'aziyya, dalili akan haka shine: Hadithin Abdullahi Albajaliy yace: mu (Sahabbai) "MUN DAUKI TARUWA DON KARBAR GAISUWA (ta'aziyya) DA TANADIN ABINCI DON MASU TA'AZIYYA A MATSAYIN NIYAHAH (wato kururuwa ko kukan mutuwa). [Ahmad da bin Majah suka ruwaito sa, Imam An-Nawawiy ya inganta shi]

🖋️Haka kuma Imam An-Nawawiy a cikin littafin sa AL-MAJMU' sharhin MUHAZZAB na Shayhin Malami Shayraziy cewa yayi: " AMMA ZAMA DOMIN TA'AZIYYA IMAM AS-SAFI'IY DA SHAYRAZIY SUN NASSANTA KARHANCIN SA(kyamar sa)" abinda yake nufi sun karhanta taruwar iyalan mamaci a gida domin mai son yayi masu ta'aziyya ya same su yayi masu ta'aziyya, dai dai abin da ya kamata su tafi wajen bukatun su (na yau da kullum), duk wanda ya ya hadu dasu yayi masu ta'aziyya. Kuma babu bambanci wajen karhanta wannan zama tsakanin maza da mata.

🖋️Abinda Imam An-Nawawiy ya fada yana cikin littafin Imam As-shafi'iy: AL-UMM 1/248, ga kuma abinda yake cewa a cikin littafin: "INA KYAMAR TARON KARBAR TA'AZIYYA KODA BABU KUKA DOMIN YANA SABANTA BAKIN CIKI DA KALLAFA WAHALHALU NA KASHIN DUKIYA".

🖋️Shi kuma bin Humam ya nassanta karhancin a cikin littafin sa SHARHUL HIDAYAH 1/473, kuma yace: BIDI'AH CE MAI MUNI" kuma wannan shine mazhabar Hanabila kamar yadda yake cikin AL-INSWAF 2/565.

Kuma abinda kowa ya sani ne kamar yadda bayani ya gabata wurin karbar gaisuwa ya zama wurin fira, giba, kallon mata, labarin Yan siyasa, Yan kwallo, shugabanni, masu kudi da dai sauran su. Wanda hankali lafiyayye ba zai yarda da wannan ba balantana Shari'ah.

Wallahu a'alamu bissawab

Mu hadu a darasi na biyar (005)insha'allah

✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

03 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA UKU (003)

📒ABU NA UKU: BA'A IYAKANCE TA'AZIYYA DA KWANA UKU BA KAMAR YADDA WASU SUKE RIYAWA 📒

Ita Ta'aziyya ba'a iyakance lokacin yin ta da kwana uku ba, a'a, ana yin ta duk lokacin da aka ga fa'idar yin ta ko kuma lokacin da aka samu haduwa da wanda aka yiwa rassuwa, saboda Hadithin Abdullahi bin ja'afar da ya gabata a darasi na biyu kamar yadda yake cewa: bayan shi ja'afar yayi shahada sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM yayi jinkiri na kwana uku bai je gidan Ja'afar ba, sannan yazo yace: "KADA KU SAKE KUKA GA DAN UWANA DAGA YAU".
Abdullahi yace: sai Annabi yasa aka zo damu, sai muka zama kamar 'ya'yan tsuntsaye (saboda maraici) kuma yasa aka aske muna kawunan mu sannan ya mike hannu na a sama yace: YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA, KA SANYA ALBARKA GA ABDULLAHI (dansa) KUMA KA SANYA ALBARKA GA KASUWANCIN SA". ya fadi haka har dau uku. Daga nan dai mahaifiyar mu ta zo tana ambata masa maraicin mu kuma tana cike da damuwa, sai Annabi ya ce mata: "KINA JI MASU TSORON TALAUCI NE? ALHALI NINE MAJIBINCIN SU DUNIYA DA LAHIRA?".

Wallahu a'alamu bissawab.

Mu hadu a darasi na hudu(004) insha'allah.

✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz juma'at Mosque, Bungudu)

Thursday, 25 March 2021

02 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

DARASI NA BIYU (002)

📒ABU NA BIYU: YIWA IYALAN MAMACI TA'AZIYYA DA KUMA LAFUZZAN DA AKE AMFANI DASU📒

Ana yiwa iyalan mamaci ta'aziyya da duk wadansu kalamai da ake sa ran zasu lallashe su, su rage masu radadi da damuwar wannan rashi tare da sanya su yarda da hukuncin Allah da kuma hakuri, musamman ma lafuzzan da Annabi Muhammad SALAL LAHU ALAIHI WA SALLAM yayi amfani da su, idan mutum ya san su, idan kuwa mutum bai san su ba, to, sai yayi amfani da kyakkyawar kalma domin cimma wannan manufa, kuma kada su sabawa Shari'ah. Dangane da wannan akwai hadithai kamar haka:

📌1. Hadithin Usama bin Zayd (R.A) yace:..... Wata diyar Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ta aika masa cewa danta na dab da mutuwa sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare sa ya aika mata cewa: Yana yi mata sallama kuma yace: "DUK ABINDA ALLAH YA KARBA NASA NE KUMA ABINDA YA BAYAR NASA NE, KO WANE ABU A WURIN SA YANA DA IYAKANTACCEN LOKACI, TAYI HAKURI TA NEMI LADA (a wurin Allah)."  [Bukhariy da Muslim suka ruwaito sa] .

📌2. Hadithin Buraidah bin Husaib (R.A) inda ya nuna cewa:....... Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ya je yiwa wata mata daga cikin matan Madina ta'aziyya sai ya ce mata:" BABU WANI MUTUM KO MACE MUSULMA DAKE DA 'YA' YA UKU (da suka rassu) FACE ALLAH YA SHIGAR DA SU ALJANNA SANADIYAR 'YA' YAN" Sayyidina Umar (R.A) yana gafen dama da Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WA SALLAM, sai yace koda 'ya' ya biyu?, sai Annabi yace: "KODA BIYU" [Bazzar da Hakim suka ruwaito sa, kuma Hadithi ne ingantcce] 

📌3. Ta'aziyyar da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare sa ya yiwa Ummu Salamah a lokacin da mijin ta abu-Salamah ya rassu, sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WA SALLAM ya ce: "YA ALLAH KA GAFARTAWA ABU SALAMAH KA DAUKAKA DARAJAR SA A CIKIN SHIRYAYYU, KA MAYE BAYAN SA, KA GAFARTA MUNA TARE DA SHI, YA UBANGIJIN HALITTU, KA YILWATA MASA KABARIN SA KA HASKAKA MASA". [Muslim ne ya ruwaito sa] 

📌4. Ta'aziyyar da Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM yayiwa Abdullahi bin Ja'afar sai Manzon Allah ya ce:.... "YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA, KA SANYA ALBARKA GA DANSA ABDULLAHI (dansa) KUMA KA (Sanya Albarka ga) KASUWANCI" ya fadi haka sau uku. [Ahmad ya ruwaito sa, kuma hadithi ne ingantcce] 

💡Wasu kenan daga cikin lafuzzan da Annabi Muhammad SALAL LAHU ALAIHI WA SALLAM yayi amfani dasu wurin yiwa Sahabban sa ta'aziyya. 

Wallahu a'alamu bissawab. 

Mu hadu a darasi na uku (003)

✍️Nasiru Bala Bungudu. 
(Chief Imam Salih bin Abdul Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

001 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA FARKO (001)

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai jinkai, Tsira da Amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah. 

Bisa ga la'akari da muhimmancin ta'aziyya da kuma bukatuwar musulmi ga sanin yadda take a Sunnar Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM, domin kaucewa bidi'o'i naga ya dace in tunatar da kaina game da takaitaccen bayani akan ta'aziyya wanda ya kunshi abubuwa guda shidda (6) kamar haka:
👉1. Shar'antuwar Ta'aziyya a Musulunci
👉2. Yiwa iyalan mamaci ta'aziyya da kuma lafuzzan da ake amfani dasu.
👉3. Ba'a iyakance ta'aziyya da kwana uku ba kamar yadda wasu suke riyawa.
👉4. Abubuwa biyu (2) da ya kamata a nisanta a lokacin mutuwa.
👉5. Sunnah ne dangin mamaci da makwabtan sa suyi abincin da zai kosar da iyalan mamacin su aika masu.
👉6. Mustahabbancin shafa kan maraya da tausaya masa.

📒NA FARKO: SHAR'ANTUWAR TA'AZIYYA A MUSULUNCI:📒

An Shar'anta yin ta'aziyya ga iyalai da dangin mamaci, saboda hadithai da suka yi bayanin haka:

📌 1. Hadithin Qurra Al-Muzanniy (R.A), cewa: a lokacin da Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ya samu labarin rassuwar dandan wani daga cikin Sahabban sa, ya je yayi masa ta'aziyya har ma yace masa "MINENE YAFI SOYUWA A GAREKA? SHIN KAJI DADIN RAYUWAR KA TARE DA WANNAN YARO? KO (kafi son) KA ISKO SHI BAKIN KOFAR ALJANNA YANA JIRAN KA, YA BUDE MAKA (don ka shiga)?" sai yace: ya Annabin Allah!, nafi son ya riga ni ya bude mani. Wannan Hadithi [[Nasa'iy ya ruwaito shi da wannan siyaqi, haka kuma ibn Hibban da Hakim da Ahmad duka sun ruwaito sa. Kuma hadithin Sahihi ne.]]

📌 2. Hadithin Anas dan Malik (R.A), yace: Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM yace: "DUK WANDA YAYIWA DAN UWAN SA MUMINI TA'AZIYYA AKAN WATA MUSIBA, (da ta same sa) ALLAH ZAI TUFATAR DA SHI CIKAKKUN TUFAFI A RANAR ALKIYAMA WADANDA MUTANE ZASU YI FATAR SAMUN IRINSU" [Khadeeb Al-Baghdadiy ya fitar da shi da bin Asakir da kuma bin Adiy. Hadithi ne ingantcce] 

Wallahu a'alamu bissawab. 

Mu hadu a darasi na biyu (002) insha'allah. 

✍️ Nasiru Bala Bungudu. 
(Chief Imam Salih bin Abdul Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

Wednesday, 13 January 2021

MUSAN MALAMANMU NA SUNNAH - ALOSAIMI

MUSAN MALAMANMU NA SUNNAH...


Waye Sheikh Salih  Al-Osaimi?

Shine Sheikh Dr. Swalih Bn Abdullahi bn Hamad Al-Osaimi, Al-Otaibi

An haifeshi ne a Birnin Riyadh dake Saudiyya, a watan Safar shekara ta 1391AH kuma yana zaune a garin Riyadh har yanzu.
Malam ya himmatu da neman karatu tun yana ɗan ƙarami, yayi tafiye tafiye zuwa ƙasashe masu yawa domin neman ilimi.
Malam ma'aboci sunnah ne
Yayi karatu a wurin malamai masu tarin yawa daga cikin malaman dake Saudiyya, yana da alaƙar ilimi mai ƙarfi da Sheikh Bukar Abu Zaid (R)
Malaman da yayi karatu a wurin su suna da yawa, daga ci akwai:
1. Sheikh Abdulaziz bn Baaz
2. Sheikh Muhammad bn Salihul Usaimin
3. Sheikh Abdullahi bn Aƙeel
4. Sheikh Abdullahi bn Abdulrahman jibrin
5. Sheikh Bukar Abu Zaid
6. Sheikh Salih bn Fauzan Al-fauzan
7. Sheikh Abdulmuhsin Al'abbad

@ Dr. Osaimi yayi karatu a jami'atu Ummul Ƙura, sannan yayi karatun shi tun daga matakin digiri na farko har digirin digir gir a fannin Ulumul Hadith.

@ Dr. Osaimi Mai Fatawa ne kuma limami ne mai hudubar juma'ah a Masallacin Abubakar Assiddiq dake birnin Riyadh

@ An zaɓi Dr. Osaimi a a matsayin member a majalisar manya manyan malamai dake Saudiyya a ranar 3, Rabi'ul Awwal, 1438H

@ Sheikh Swalihul Osaimi yana da halƙoƙi da yake karantawa a wurare kamar haka:
1. Yana karantarwa a Masallacin Manzon Allah S.A.W, darasin da ake kira:
برنامج مهمات العلم

2. Yana karantawa a birnin Riyadh, yana karantar da:
برنامج أصول العلم
3. Yana karantar da mahajjata kafin fara aikin hajji a Masallacin Harami, darasin da ake kira:
برنامج تعليم الحجاج 
4. Yana karantarwa a lokacin azumi a Masallacin Manzon Allah S.A.W, tun daga 1 har zuwa 20 ga Ramadan, sunan darasin
برنامج السرد المجود

Wannan kaɗan kenan daga cikin wurare da kuma Karatuttukan da yake gabatarwa, wanda adadin su zai kusan kai 18-20

Rubuce rubucen da yayi

@ Dr. Osaimi yayi wallafe-wallafe masu yawan gaske, tsakanin waɗanda ya rubuta da kanshi, da kuma waɗanda yayi ma sharhi da Takhriji suna da yawa, amma ga wasu daga cikin su:

١. ﺗﻌﻈﻴﻢ ﺍﻟﻌﻠﻢ
٢. ﺍﻟﺒﻴِّﻨﺔ ﻓﻲ ﺍﻗﺘﺒﺎﺱ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻭﺍﻟﺤﺬﻕ ﻓﻴﻪ
٣. ﺍﻟﻤﺴﺎﺋﻞ ﺍﻷﺭﺑﻌﻴﻦَ ﻋﻦِ ﺍﻷﺋﻤﺔ ﺍﻷﺭﺑﻌﺔ ﺍﻟﻤُﺘَّﺒﻌﻴﻦ
٤. ﺍﻟﻤُﻌﺠَﻢ ﺍﻟﻤُﺨﺘﺎﺭ ﻣﻦ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﻨَّﺒﻮﻳَّﺔ ﺍﻟﻘِﺼﺎﺭ
٥. ﺍﻟﻘَﺮﻳﺾ ﺍﻟﻤُﺒﺪَﻉ ﻧﻈﻢ ﺍﻟﻘﻮﺍﻋﺪ ﺍﻷﺭﺑﻊ
٦. ﻣﻌﺎﻧﻲ ﺍﻟﻔﺎﺗﺤﺔ ﻭﻗِﺼَﺎﺭ ﺍﻟﻤﻔﺼَّﻞ
٧. ﺍﻟﻄُّﺮْﻓﺔ ﺍﻟﺴَّﻨﻴَّﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﻘﻮﺍﻋﺪ ﺍﻟﻔﻘﻬﻴَّﺔ
٨. ﺧﻼﺻﺔ ﻣﻘﺪِّﻣﺔ ﺃُﺻﻮﻝ ﺍﻟﺘَّﻔﺴﻴﺮ
٩. ﺇﻣﺘﺎﻉ ﺍﻟﻤﺸﻴﺨﺔ ﺍﻷﺣﻤﺪﻳﺔ ﺑﻄﺮﻕ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻀﻞ ﺍﻟﻤﺮﻭﻳﺎﺕ ﺍﻻﺭﺑﻴﻌﻴﺔ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١٠. ﺭﻓﻊ ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ ﻟﻄﺮﻕ ﺣﺪﻳﺚ ﻣﻦ ﺳﺌﻞ ﻋﻦ ﻋﻠﻢ ﻓﻜﺘﻤﻪ ﺍﻟﺠﻢ ﺑﻠﺠﺎﻡ ﻣﻦ ﻧﺎﺭ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١١. ﺍﻟﻔﺼﻞ ﺑﻴﻦ ﺍﻟﻤﺘﻨﺎﺯﻋﻴﻦ ﻓﻲ ﺣﺪﻳﺚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺇﻧﻲ ﺃﺳﺄﻟﻚ ﺑﺤﻖ ﺍﻟﺴﺎﺋﻠﻴﻦ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١٢. ﺍﻟﺪﺭﺀ ﻟﺘﺼﺤﻴﺢ ﺣﺪﻳﺚ ﻣﻦ ﺣﺴﻦ ﺇﺳﻼﻡ ﺍﻟﻤﺮﺀ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١٣. ﻓﻘﻪ ﺍﻟﻮﺍﻗﻊ ﻋﻨﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻭﺍﻟﺠﻤﺎﻋﺔ .
١٤. ﺍﻟﺪﺭﺀ ﺍﻟﻨﻀﻴﺪ ﻓﻲ ﺗﺨﺮﻳﺞ ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ .
١٥. ﻭﺍﻗﻌﻨﺎ ﺍﻟﻤﻌﺎﺻﺮ ﻋﻠﻰ ﺿﻮﺀ ﻣﻨﻬﺞ ﺍﻟﺴﻠﻒ .
١٦. ﻫﺬﻱ ﻫﻲ ﺍﻟﺴﻠﻔﻴﺔ : ﻣﻨﻬﺞ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻭﺍﻟﺠﻤﺎﻋﺔ .
١٧. ﺍﻟﻮﻓﺎﺀ ﺑﺼﺤﻴﺢ ﺍﺫﻛﺎﺭ ﺍﻟﺼﺒﺎﺡ ﻭﺍﻟﻤﺴﺎﺀ .
١٩. ﺍﻟﺸﻜﺎﻳﺔ ﻭﺍﻟﻨﻜﺎﻳﺔ : ﺑﺮﻗﻴﺎﺕ ﻣﻮﺟﻬﺔ ﺇﻟﻰ ﻃﻠﺒﺔ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻭﺍﻟﺪﻋﺎﺓ .
ﺍﻻﻧﺒﺎﻩ ﺇﻟﻰ ﻣﺎ ﻟﻴﺲ ﻣﻦ ﺃﺳﻤﺎﺀ ﺍﻟﻠﻪ .
٢٠. ﺁﺩﺍﺏ ﺍﻟﺼﺤﺒﺔ ﻭﺣﻘﻮﻕ ﺍﻟﻌﺸﺮﺓ ﺑﻴﻦ ﺍﻻﺧﻮﺍﻥ .
٢١. ﺗﺬﻛﺮﺓ ﺍﻟﺤﺪﻳﺜﻲ ﻭﺍﻟﻤﺘﻔﻘﻪ .
ﺍﻻﻧﺘﻤﺎﺀ ﺍﻟﺤﻖ .
٢٢. ﻛﺸﻒ ﺍﻟﻨﻘﺎﺏ ﻋﻦ ﺿﻌﻒ ﺣﺪﻳﺚ ﻋﺎﺋﺸﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﺠﺎﺏ .
٢٣. ﺭﺳﺎﺋﻞ ﺇﻟﻰ ﺷﺒﻞ ﺍﻹﺳﻼﻡ
٢٤. ﺍﻟﻤﻔﺘﺎﺡ ﻓﻲ ﺍﻟﻔﻘﻪ
٢٥. ﺍﻟﻤﻘﺪﻣﺔ ﺍﻟﻔﻘﻬﻴﺔ ﺍﻟﺼﻐﺮﻯ
٢٦. ﺍﻟﻤﻘﺪﻣﺔ ﺍﻟﻔﻘﻬﻴﺔ ﺍﻟﻜﺒﺮﻯ
٢٧. ﺍﻟﻌﺮﻭﺓ ﺍﻟﻮﺛﻘﻰ
٢٨. ﺍﻟﻐﺎﻳﺔ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﺴﻤﺎﻉ ﻭﺍﻟﺮﻭﺍﻳﺔ
٢٩. ﻧﻌﺖ ﺍﻟﺪﺭﺟﺎﺕ ﻟﺘﻠﻘﻲ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻭﺍﻟﻘﺮﺍﺀﺍﺕ
٣٠. ﺗﻔﺴﻴﺮ ﺍﻟﻔﺎﺗﺤﺔ ﻭﻗﺼﺎﺭ ﺍﻟﻤﻔﺼﻞ
٣١. ﻧﺠﻢ ﺍﻟﻤﻨﺒﻬﺎﺕ ﻓﻲ ﻧﺼﺢ ﻃﻼﺏ ﺍﻟﻤﻬﻤﺎﺕ
٣٢. ﺍﻟﺤﻠﺔ ﺍﻟﺴﻴﺮﺍﺀ
٣٣. ﺭﺳﺎﻟﺔ ﺍﻟﻤﺎﺟﺴﺘﻴﺮ : ﺍﻟﻤﺘﺎﺑﻌﺎﺕ ﻭﺍﻟﺸﻮﺍﻫﺪ ﺩﺭﺍﺳﺔ ﻧﻈﺮﻳﺔ ﺗﻄﺒﻴﻘﻴﺔ ﻋﻠﻰ ﺻﺤﻴﺢ ﻣﺴﻠﻢ ﺇﺷﺮﺍﻑ ﺃ . ﺩ . ﻣﻮﻓﻖ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻘﺎﺩﺭ

@ Dr. Osaimi yana da usulubi mai kyau na karantarwa, yana yawan maimaita duk wata jumla mai fa'ida domin ɗalibbai su fahimci inda karatun ya nufa, kamar dai yadda Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (H) yake da irin wannan usulubi mai kyau a nan gida Nigeria

@Na bibiyi wasu daga cikin Karatuttukan da malam ya gabatar kuma ina fa'idantuwa kwarai da gaske, daga Karatuttukan da na bibiya akwai:
١. تفسير سورة الفاتحة وقصار المفصل
٢. الباقيات الصالحات من الأذكار بعد الصلوات لصالح بن عبد الله العصيمي
٣. شرح آداب العشرة
٤. شرح خلاصة الحسناء
٥. شرح خلاصة مقدمة أصول التفسير
٦. شرح الأرجوزة الميئية في ذكر حال أشرف البرية
Waɗannan duk na saurare su daga farko har ƙarshe kuma na fa'idantu sosai.
Haka nan na bibiyi wasu Muhadarori da malam ya gabatar kamar haka:
١. واجب طلاب العلم في النوازل والحوادث المدلهمة

٢. واجب المرأة عند الفتن

٣. الأمر باتباع السنة والتحذير من ردها
Wannan na ƙarshen na saurari muhadarar kuma na sauke littafin saboda muhimmancisa, musamman a wannan lokaci da matsiyata masu ƙaryata hadisan Annabi da sukar maruwaita.

Malam yana nan a raye har yanzu a birnin Riyadh


Allah ya ƙara mashi lafiya da tabbatuwa akan sunnar Annabi Muhammad S.A.W


✍️ Hashim Siraj Uba Ats~tsamawy
29/05/1442AH
13/01/2021AC

Monday, 20 July 2020

WASU DAGA CIKIN AYYUKAN DA AKE SON MUSULMI YA AIKATA A GOMAN FARKO NA ZUL-HIJJAH

*WASU DAGA CIKIN AYYUKAN DA AKE SO MUTUM YA AIKATA A GOMAN FARKO NA WATAN ZUL-HIJJAH*


1. *AIKIN HAJJI:* yazo a cikin bukhari da Muslim, Annabi Muhammad S.A.W yana cewa: (Aikin hajji karbabbe ba yada sakamako sai aljannah).
Abun nufi shine: idan bawa yayi aikin hajji wacce Allah S.W.T ya karba mashi, hajjin da mutum ya tattara ayukan alkhairi, lallai irin wannan baida sakamako, da falala daga wurin Allah sai shigar shi aljannah.

2. *AZUMIN RANAR ARFA:*
 Manzon Allah S.A.W yace: (Azumin ranar arfa yana kankare zunubin shekarar da ta gabata, da wacce zata zo bayanshi.

3. *YANKA ABUN LAYYA DOMIN NEMAN KUSANCI ZUWA GA ALLAH:* Abun nufi a cikin yin layya ba wai kawai cin nama da sadaka da kyauta ne ba kawai, abun nufi shine zubar da jinin dabbar domin neman kusanci ga Allah S.W.T

A karkashin wannan akwai wasu abubuwa kamar haka:
*NA FARKO:*
 Kayi kokarin ganin ka yanka abun layyarka da kanka

*NA BIYU:* idan baka yanka da kanka ba, ka tabbata kana wurin da za'a yanka, a yanka ta a gaban ka.

*NA UKU:* idan baka samu damar yankawa da kanka ba, baka samu damar da zaka tsaya a yanka a gaban ka ba, toh sai kayi umurni, ya zamana cewa an yanka da umurninka cewa a yanka maka

4. *KABBARA, DA GIRMAMA ALLAH S.W.T:*
Ya tabbata daga sahabban Annabi Muhammad S.A.W, Abi hurairah, da Abdullahi dan umar(Allah ya yarda dasu) sun kasance suna kabbarori a kwanaki goma na zul hijja.

5. *AZUMTAR KWANAKI TARA NA FARKON ZUL-HIJJAH:*
Ana son musulmi ya azumci wadannan kwanaki masu daraja, yin ayyukan alkhairi a cikin wadannan kwanaki Yana da falala da lada sosai.


Allah ya datar damu da aikata aiki na kwarai a wadannan kwanaki masu albarka.


https://t.me/muryarsunnah1



✍️ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy ( _ABU SINAN_ )*
atstsamawy@gmail.com