Monday, 22 May 2017

AZUMIN WATAN RAMADHANA

🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉
*AZUMIN WATAN RAMADANA*
🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇

*بسم الله الرحمن الرحيم*

_Rubutawa;_ *HASHIM SURAJO UBA(ABU SINÃN)*

```ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU.

  Godiya ta tabbata ga Allah s.w.t shi kadai Wanda yayi mana umurni da azumtar ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada, Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da ibadar azumi da sauran ibadoji.

Bayan haka;

FALALAR WATAN RAMADANA DA AZUMI A CIKIN WATAN.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan ramadana ya shigo, ana bude kofofin sama, ana kulle kofofin jahannama, ana daure shaidanu.
A wani hadisin kuwa manzon Allah s.a.w cewa yayi" Dukkan wani aiki da dan Adam zaiyi, ana lunka aikin da lada goma irinsa, idan a ramadana ne, ana lunkashi zuwa lunki (700), sai Allah mai girma da daukaka yace ;  banda azumi, domin azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa Wanda yayi shi, yabar matarshi da abubuwan da yakeso, da abinci, da abin sha saboda ni, mai azumi Nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki (shan ruwa) da farin ciki lokacin haduwarshi da Allah, yamin/warin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

ABUBUWAN DA SUKA WAJABA GAREKA A RAMADANA

Ya dan uwa

Kasani cewa Allah ya wajabta mana azumi domin mu bauta masa dashi, sannan kuma ya kasance cewa azuminka ya zamto karbabbe mai amfani.
Dole ne ka kiyaye wadannan abubuwan da zasu zo domin samun cikakkar lada;

1- kiyaye sallah; Da yawa daga cikin masu azumi suna wasa da sallah, bayan kuwa cewa tana daga cikin gimshikan addini, barinta kuma yana kai mutum ga kafurci.

2- Dole ka kasance mai kyawawan dabi'u; Dole ne mu tsoraci kafurci da zagin addini, da aikata muna nan dabi'u a cikin mutane, kafirci yana fitar da musulmi daga addini.

3- Dole ne mu kiyaye halshenmu da sukar juna.
 
Manzon Allah s.a.w yana cewa; "idan dayanku yana azumi, to kada ya fadi maganganun da basu dace ba, idan wani ya zageka ko ya nemi yayi fada da kai, sai kace mashi ni azumi Nike, ni azumi Nike.

4- Ka nisanci zuwa wurin da ake aikata barna! Ko kallon fina-finai na banza, domin hakan zai kai ga bata azuminka.

5- Ka yawaita sadaka ga makusantanka da mabukata, da ziyartar yan uwanka.

6- Ka yawaita zikiri da karatun Qur'ani da saurararshi, da bibiyar ma'anoninsa, da aiki da karantar warshi, sannan da zuwa masallatai domin daukar darussa masu amfani, kamar sauraran tafsirai, yin i'itikafi a masallaci idan goman karshe na ramadana suka kama.

7- karanta takardu akan azumi, domin sanin hukunce- hukuncen da suka shafi azumi, ta yarda zakasan cewa cin abinci ko abin sha da mantuwa baya karya azumi, kasan cewa ita janaba wacce ta sameka da daddare bata hana ka daukar azumi da sauransu.

LADUBBAN DA SUKA SHAFI AZUMI.

1- kiyaye halshe; Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda bai bar zancen karya ba, da aiki da zancen karya, Allah baya da bukatar barin cinsa ko shansa.

2- BUDA BAKI DA SAHUR DA ADDU'AH.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan dayanku zaiyi buda baki, to ya fara da dabino domin akwai albarka a ciki, idan bai samu dabino ba toh sai yayi da ruwa, domin suna tsalkakewa.
Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi buda baki yana fadar;
ذهب الظمأ، وابتلت العروق، وثبت الأجر، إن شاء الله.

Ma'ana: "YUNWA TA TAFI, GABOBI SUN DAI DAI TA, LADA TA TABBATA DA YARDAR ALLAH".
Manzon Allah s.a.w yace; "mutane baza su gushe suna samun alkhairi ba matukar suna gaggauta buda baki.

Anan dole mu gujewa muna nan akeedun shi'ah wadanda basa shan ruwa sai duhu ya shigo sosai, suna kafa hujja da ayar Qur'ani dake cikin suratul bakara, inda Allah s.w.t yake cewa; "...sannan Ku cika azumi zuwa dare. Wanman magana malamai sunyi bayanin me ake nufi tun da dadewa, mai Neman Karin bayani ya duba tafsirin "Aisarat-tafaseer, na jabir jaza'iry."

Manzon Allah s.a.w yace"kuyi sahur, domin a cikin yin sahur akwai albarka."

Manzon Allah s.a.w yace"Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da an rage komai daga ciki ba.

3-  DAGA CIKIN FA'IDOJIN AZUMI

   Duk Wanda yayi azumin ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbansa.

Duk Wanda yayi tsayuwar ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.(ma'ana: tsayuwar tarawihi da kiyamul-laili.)

4- WADANDA AKA YIWA RANGWAMEN AZUMI.

   *Marar lafiya da matafiyi, zasu ranka saboda fadar Allah s.w.t cewa;"Wanda ya kasance a cikinku marar lafiya ko akan hanyar tafiya, zai ranka azumin a kwanakin sauran watanni."
Amma marar lafiya Wanda ba'asa ran warkewa a kusa, toh sai ya rinka ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mai haila, da jinin haihuwa zasu aje azumi, saboda fadar ummuna Aisha R.A; "mun kasance ana umurtanmu da ranka azumi, amma ba'a umurtanmu da ranka sallah.[Bukhari da Muslim].

* Dattijo da dattijiya, wadanda sun tsufa sosai basa iya daukar azumi toh zasu ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mace mai ciki da mai shayarwa idan sunji tsoron rayukansu, toh zasu aje azumi sannan su ranka kawai, amma idan suna jin tsoron yayansu ne kawai, toh zasu ranka kuma su ciyar.

5- ABUBUWAN DAKE BATA AZUMI.

Abubuwan dake bata azumi sun kasu gida biyu:
Na farko; Abunda ke bata azumi Wanda ke wajabta rankawa kawai;

* Cin abinci ko abinsha da gangan.

* Yin amai da gan gan, saboda fadar annabi Muhammad s.a.w cewa: " Duk Wanda yayi amai, toh zai ranka azumi.[Hakim ya ruwaito]

* Mace mai haila da mai haihuwa, koda sauran mintuna kadan ayi buda baki tazo musu, toh zasu ranka azumin.

* Istimna'i(masturbation) wasa da al'aura da hannunka har maniyyi ya fito shima yana bata azumi kuma sai ka ranka.

Abu na biyu dake bata azumi kuma yake wajabta ranko da kaffara shine JIMA'I, akan maganar malamai kaffarar shine yanta baiwa ko azumin kwana sittin(60) a Jere.

6- ABUBUWAN DA BASU BATA AZUMI

* Cin abinci ko abinsha da mantuwa, ko da kuskure ko da tilasci! Babu ranko kuma babu kaffara, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa"Wanda ya manta yana azumi ya ci ko ya sha toh ya cika azuminsa, Allah ne ya ciyar dashi kuma ya shayar dashi.[Bukhari da Muslim]

* Amai ba dagan gan ba.

* Yin aswaki a kowane lokaci ko brush da sauransu.

* Dandana abinci da sharadin kada ka bari ya wuce maka.

* Sumbantar matarka, da sharadin kada akai ga aikata jima'i. Saboda manzon Allah s.a.w ya kasance yana sumbantar Aisha alhali yana azumi[Bukhari da Muslim].

* Cirewar hakori, ko zubar jini daga baki ko hanci.

* idan Alfijir ya keto alhali abunsha na hannunka, kada ka aje har sai ka biya bukatarka.

*jinkirta wankan janaba ko haila ko na haihuwa daga dare zuwa hudowar alfijir. Abunda yafi shine ayi gaugawar yi kafin sallar asuba.

Muna rokon Allah ya amfanar damu da abunda muka rubuta, Allah yasa munyi domin Neman yardar shi, Allah ya sanya ibadojin da zamu gabatar a ramadana su zamo karbabbu, kuma su zamo sanadiyyar tsira garemu duniya da lahira. Inda mukayi kuskure Allah ya shefeshi daga idanun masu karatu ya fahimtar dasu tare damu gabaki daya. Allah ya doramu akan tafarki madaidaici.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.

COPYRIGHT©
Hashim Surajo Uba(ABU SINÃN)```

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.wordpress.com

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

+2348064734911
+2348064734911

AZUMIN WATAN RAMADHANA

🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉
*AZUMIN WATAN RAMADANA*
🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇🍉🍇

*بسم الله الرحمن الرحيم*

_Rubutawa;_ *HASHIM SURAJO UBA(ABU SINÃN)*

```ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU.

  Godiya ta tabbata ga Allah s.w.t shi kadai Wanda yayi mana umurni da azumtar ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada, Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da ibadar azumi da sauran ibadoji.

Bayan haka;

FALALAR WATAN RAMADANA DA AZUMI A CIKIN WATAN.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan ramadana ya shigo, ana bude kofofin sama, ana kulle kofofin jahannama, ana daure shaidanu.
A wani hadisin kuwa manzon Allah s.a.w cewa yayi" Dukkan wani aiki da dan Adam zaiyi, ana lunka aikin da lada goma irinsa, idan a ramadana ne, ana lunkashi zuwa lunki (700), sai Allah mai girma da daukaka yace ;  banda azumi, domin azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa Wanda yayi shi, yabar matarshi da abubuwan da yakeso, da abinci, da abin sha saboda ni, mai azumi Nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki (shan ruwa) da farin ciki lokacin haduwarshi da Allah, yamin/warin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

ABUBUWAN DA SUKA WAJABA GAREKA A RAMADANA

Ya dan uwa

Kasani cewa Allah ya wajabta mana azumi domin mu bauta masa dashi, sannan kuma ya kasance cewa azuminka ya zamto karbabbe mai amfani.
Dole ne ka kiyaye wadannan abubuwan da zasu zo domin samun cikakkar lada;

1- kiyaye sallah; Da yawa daga cikin masu azumi suna wasa da sallah, bayan kuwa cewa tana daga cikin gimshikan addini, barinta kuma yana kai mutum ga kafurci.

2- Dole ka kasance mai kyawawan dabi'u; Dole ne mu tsoraci kafurci da zagin addini, da aikata muna nan dabi'u a cikin mutane, kafirci yana fitar da musulmi daga addini.

3- Dole ne mu kiyaye halshenmu da sukar juna.
 
Manzon Allah s.a.w yana cewa; "idan dayanku yana azumi, to kada ya fadi maganganun da basu dace ba, idan wani ya zageka ko ya nemi yayi fada da kai, sai kace mashi ni azumi Nike, ni azumi Nike.

4- Ka nisanci zuwa wurin da ake aikata barna! Ko kallon fina-finai na banza, domin hakan zai kai ga bata azuminka.

5- Ka yawaita sadaka ga makusantanka da mabukata, da ziyartar yan uwanka.

6- Ka yawaita zikiri da karatun Qur'ani da saurararshi, da bibiyar ma'anoninsa, da aiki da abinda yake karantarwa, sannan da zuwa masallatai domin daukar darussa masu amfani, kamar sauraran tafsirai, yin ittikafi a masallaci idan goman karshe na ramadana suka kama.

7- karanta takardu akan azumi, domin sanin hukunce- hukuncen da suka shafi azumi, ta yarda zakasan cewa cin abinci ko abin sha da mantuwa baya karya azumi, kasan cewa ita janaba wacce ta sameka da daddare bata hana ka daukar azumi da sauransu.

LADUBBAN DA SUKA SHAFI AZUMI.

1- kiyaye halshe; Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda bai bar zancen karya ba, da aiki da zancen karya, Allah baya da bukatar barin cinsa ko shansa.

2- BUDA BAKI DA SAHUR DA ADDU'AH.

Manzon Allah s.a.w yace; "idan dayanku zaiyi buda baki, to ya fara da dabino domin akwai albarka a ciki, idan bai samu dabino ba toh sai yayi da ruwa, domin suna tsalkakewa.
Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zaiyi buda baki yana fadar;
ذهب الظمأ، وابتلت العروق، وثبت الأجر، إن شاء الله.

Ma'ana: "YUNWA TA TAFI, GABOBI SUN DAI DAI TA, LADA TA TABBATA DA YARDAR ALLAH".
Manzon Allah s.a.w yace; "mutane baza su gushe suna samun alkhairi ba matukar suna gaggauta buda baki.

Anan dole mu gujewa muna nan akeedun shi'ah wadanda basa shan ruwa sai duhu ya shigo sosai, suna kafa hujja da ayar Qur'ani dake cikin suratul bakara, inda Allah s.w.t yake cewa; "...sannan Ku cika azumi zuwa dare. Wanman magana malamai sunyi bayanin me ake nufi tun da dadewa, mai Neman Karin bayani ya duba tafsirin "Aisarat-tafaseer, na jabir jaza'iry."

Manzon Allah s.a.w yace"kuyi sahur, domin a cikin yin sahur akwai albarka."

Manzon Allah s.a.w yace"Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da an rage komai daga ciki ba.

3-  DAGA CIKIN FA'IDOJIN AZUMI

   Duk Wanda yayi azumin ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbansa.

Duk Wanda yayi tsayuwar ramadana, yana mai imani da Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.(ma'ana: tsayuwar tarawihi da kiyamul-laili.)

4- WADANDA AKA YIWA RANGWAMEN AZUMI.

   *Marar lafiya da matafiyi, zasu ranka saboda fadar Allah s.w.t cewa;"Wanda ya kasance a cikinku marar lafiya ko akan hanyar tafiya, zai ranka azumin a kwanakin sauran watanni."
Amma marar lafiya Wanda ba'asa ran warkewa a kusa, toh sai ya rinka ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mai haila, da jinin haihuwa zasu aje azumi, saboda fadar ummuna Aisha R.A; "mun kasance ana umurtanmu da ranka azumi, amma ba'a umurtanmu da ranka sallah.[Bukhari da Muslim].

* Dattijo da dattijiya, wadanda sun tsufa sosai basa iya daukar azumi toh zasu ciyar da talaka daya a kowace rana.

* Mace mai ciki da mai shayarwa idan sunji tsoron rayukansu, toh zasu aje azumi sannan su ranka kawai, amma idan suna jin tsoron yayansu ne kawai, toh zasu ranka kuma su ciyar.

5- ABUBUWAN DAKE BATA AZUMI.

Abubuwan dake bata azumi sun kasu gida biyu:
Na farko; Abunda ke bata azumi Wanda ke wajabta rankawa kawai;

* Cin abinci ko abinsha da gangan.

* Yin amai da gan gan, saboda fadar annabi Muhammad s.a.w cewa: " Duk Wanda yayi amai, toh zai ranka azumi.[Hakim ya ruwaito]

* Mace mai haila da mai haihuwa, koda sauran mintuna kadan ayi buda baki tazo musu, toh zasu ranka azumin.

* Istimna'i(masturbation) wasa da al'aura da hannunka har maniyyi ya fito shima yana bata azumi kuma sai ka ranka.

Abu na biyu dake bata azumi kuma yake wajabta ranko da kaffara shine JIMA'I, akan maganar malamai kaffarar shine yanta baiwa ko azumin kwana sittin(60) a Jere.

6- ABUBUWAN DA BASU BATA AZUMI

* Cin abinci ko abinsha da mantuwa, ko da kuskure ko da tilasci! Babu ranko kuma babu kaffara, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa"Wanda ya manta yana azumi ya ci ko ya sha toh ya cika azuminsa, Allah ne ya ciyar dashi kuma ya shayar dashi.[Bukhari da Muslim]

* Amai ba dagan gan ba.

* Yin aswaki a kowane lokaci ko brush da sauransu.

* Dandana abinci da sharadin kada ka bari ya wuce maka.

* Sumbantar matarka, da sharadin kada akai ga aikata jima'i. Saboda manzon Allah s.a.w ya kasance yana sumbantar Aisha alhali yana azumi[Bukhari da Muslim].

* Cirewar hakori, ko zubar jini daga baki ko hanci.

* idan Alfijir ya keto alhali abunsha na hannunka, kada ka aje har sai ka biya bukatarka.

*jinkirta wankan janaba ko haila ko na haihuwa daga dare zuwa hudowar alfijir. Abunda yafi shine ayi gaugawar yi kafin sallar asuba.

Muna rokon Allah ya amfanar damu da abunda muka rubuta, Allah yasa munyi domin Neman yardar shi, Allah ya sanya ibadojin da zamu gabatar a ramadana su zamo karbabbu, kuma su zamo sanadiyyar tsira garemu duniya da lahira. Inda mukayi kuskure Allah ya shefeshi daga idanun masu karatu ya fahimtar dasu tare damu gabaki daya. Allah ya doramu akan tafarki madaidaici.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.

COPYRIGHT©
Hashim Surajo Uba(ABU SINÃN)```

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.wordpress.com

http://shababusunnahtsafe.blogspot.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

+2348064734911
+2348064734911

DABI'UN MAGABATA A CIKIN WATAN RAMADHANA

🍌🍌🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍌🍌
*DABI'UN MAGABATA A CIKIN WATAN RAMADANA*
🍇🍇🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍇🍇

_Rubutawa;_ *Hashim Ibn Surajo Ibn Uba(ABU SINÃN)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

```Assalamu Alaikum warahmatullahi wabarakatuhu.

Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda yayi umurni da azumtar watan ramadana, tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w, Wanda ya koya mana yanda zamu gabatar da azumin.

Bayan haka;

Magabata suna da wasu dabi'u da ayuka da zantuka a cikin ramadana, watan ramadana shine watan da Allah s.w.t ke cewa; "watan ramadana Wanda q cikinshi ne aka saukar da Qurani, domin shiriya ga mutane, da kuma bayanai game da shiriyar....[bakara 185]

Magabata na kwarai suna da ayukan da suke aikatawa a ramadana  fiye da sauran watanni.  Daga cikin magabatan akwai;
*IMAMU MALIK IBN ANAS(imamu darul hijra) ya kasance baya dakatar da karatuka a masallacin Annabi Muhammad s.a.w sai a ramadana, domin yana shagaltuwa da karatun Qurani ne kawai.

*SUFYANUS-THAURY R.H; ya kasance idan Ramadana ya shigo, yana barin dukkan wasu ibadodi, yana shagaltuwa da tilawar Qur'ani.

* MUHAMMAD IBN ISMA'IL AL-BUKHARI(mai sahihul-bukhari): ya kasance a cikin duk yini daya yana sauke Qur'ani, yana tsayuwar tarawihi acikin kwana uku na tqrawihin yana sauke Quran.

*SA'ID IBN JUBAIR: ya kasance yana saukar Qur'an a duk kwana biyu.

* ABU AWANAH yace; naga IMAMU QATADA yana karantar da Qur'an a watan ramadana.

*IMAMU QATADA; ya kasance yana saukar Qur'ani a duk bayan kwana bakwai, idan ramadana ya shigo yana sauka duk kwana uku, idan kwanaki goma na karshe suka shigo yana saukewa a kowane dare.

*RABEEY IBN SULAIMAN(Dalibin imamush-shafi'i) R.H yana cewa; imamush-shafi'i ya kasance yana saukar Qur'ani a ramadana sau sittin (60)[kowace rana sau biyu] a kowane wata yana sauka sau talatin(30) bayan ramadana.

    Kiyamul-laili aikin Annabi Muhammad s.a.w da sahabbansa ne, Aisha R.A take cewa; "kada kubar tsayuwar dare, domin Manzon Allah s.a.w bai taba barinta ba, idan baya lafiya yana yi a zaune.

* Umar Ibn khaddab R.A ya kasance yana sallar dare dai dai gwargwado, idan dare ya raba, said ya tayar da iyalansa domin yin sallar, yana cewa SALLAH! SALLAH!! SALLAH!!! Sannan sai ya karanto aya ta 132 dake cikin suratu Daha, inda Allah madaukakin sarki yake cewa; "Ka umurci iyalanka da yin SALLAH ka kwadaitar dasu akanta, bamu tambayarka wani arziki mine masu azurtaka....

  Wannan shine dabi'un magabata na kwarai a watan ramadana, to mu ya halinmu yake a wannan wata mai albarka???

* Abdullahi Ibn umar(Allah ya kara masu yarda) ya kasance yana yin azumi ba ya buda baki(shan ruwa) sai tare da talakawa, ya kasance idan yana cin abinci sai wani mabukaci yazo ya tambaya sai ya tashi daga abincin ya mika masa, ya wuce da azumi ba tare da yayi sahur ba.

  Wadannan sune magabata na kwarai, kuzo Mani da irinsu a wannan zamanin yã Ku masu da'awar salafiyya da Sunnah!?

*YUNUS IBN YAZEED yake cewa; IBN SHIHAB AZ-ZUHURY ya kasance idan ramadana ya shigo yana cewa; "Wannan watan Qur'ani ne, da kuma ciyar da abinci".

* HAMMAD IBN ABI SULAIMAN ya kasance yana ciyar da mutum dari biyar(500) a watan ramadana. Ya kasance kuma yana ba kowane dayansu dirhami Dari(100).

  Yã yan uwa na masu daraja ya kamata mu kwatanta rabin abunda magabatanmu na kwarai suka aikata na ayukan alkhairi, kada mu shagaltu da abunda bazai amfanemu ba, daga baya mu koma da na sani! Allah madaukakin sarki yana cewa;"ومن أعرض عن ذكري فإن له معيشة ضنكا ونحشره يوم القيامة أعمى، قال رب لم حشرتني أعمى وقد كنت بصيرا، قال كذلك أتتك آياتنا فنسيتها وكذلك اليوم تنسى، وكذلك نجزي من أسرف ولم يؤمن بآيات ربه، ولعذاب الآخرة أشد وأبقى.

Allah yq karemu.

WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.



COPYRIGHT©
Hashim Ibn Surajo Ibn Uba(ABU SINÃN)```

atstsamawy@gmail.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abbansinaan.blogspot.com

http://abbansinan.WordPress.com

http://shababusunnahtsafe.mywapblog.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

+2348064734911
+2349030201868

YA YA ZAMU FUSKANCI RAMADANA???

🍌🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍌
*YA YA ZAMU FUSKANCI RAMADANA???*
🍇🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍉🍇

_Rubutawa:_ *Hashim Ibn Siraj Ibn Uba{ABU SINÃN}*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

```Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda ya wajabta mana yin azumin watan ramadana, Tsira da amincin Allah su tabbata ga farin jekada  Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya koya mana yadda zamu gabatar da azumin ramadana.

Bayan haka;

Allah s.w.t yana fada a cikin suratul bakara aya ta 185 cewa;" watan ramadana Wanda a cikinsa ne aka saukar da Qur'ani domin shiriya ga mutane da kuma bayyanar da shiriyar....."

Ya yan uwa

Allah s.w.t ya kebance watan ramadana da kebantattun abubuwa masu yawa akan waninsa. Daga cikin abubuwan akwai;

* Fadar manzon Allah s.a.w cewa: warin bakin mai azumi, yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.
* Mala'iku na nemawa mai azumi gafara har zuwa lokacin da zaiyi buda baki.
* Ana tsare shaidanu a cikin Ramadana.
* Ana bude kofofin aljanna, ana rufe kofofin wuta.
* A cikin Ramadana ne Daren lailatul kadri yake, wadda tafi wata dubu Alkhairi.
* Allah na gafartawa mai azumi a karshen daren ramadana.

Ya yan uwa
Da wane irin abu zamu tarbi ramadana? Da wasannin banza??? Ko da zuwa kallon kwallo??? Ko da kallon fina finai???
Muna neman Allah ya tsaremu da aikata daya daga cikinsu a wannan wata mai albarka.

Shi bawan Allah na kwarai yana fuskantar ramadana da tuba zuwa ga Allah, yana mika lokuttanshi gaba daya domin yin ayukan kwarai, bawan Allah na kwarai shine mai rokon Allah akan ya karba masa ibadojinsa da addu'oinsa.

1- AZUMI

Manzon Allah s.a.w yana cewa; "Dukkan wani aiki da mutum zai yi, yana da ladar goma irinsa, amma ga azumi ana lunka aikin zuwa lunki dari bakwai(700). Allah mai girma da daukaka yace; banda azumi! Azumi nawa ne, kuma ni zan sakawa masu azumi,(ma'ana babu Wanda yasan adadin ladar mai azumi sai Allah) sun bar abubuwan da suke sha'awa da kauna, sun bar abinci da abin sha saboda ni, mai azumi nada farin ciki biyu, farin ciki lokacin buda baki(shan ruwa), da kuma farin ciki lokacin haduwarsa da ubangijinshi. Warin/yamin bakin mai azumi yafi turaren almiski kamshi a wurin Allah.[Bukhari da Muslim]

Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda ya azumci ramadana, yana mai imani, da kwadayin Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubbanshi.[Bukhari da Muslim]
2- SALLAR TARAWIHI/KIYAMUL-LAILI.

Manzon Allah s.a.w yace; "Duk Wanda yayi tsayuwa a ramadana, yana mai kwadayin Neman lada, an gafarta mashi abunda ya gabata na zunubanshi.[Bukhari da Muslim]

3- SADAKA
Manzon Allah s.a.w ya kasance yafi kowa sadaka a Ramadana da waninsa, manzon Allah kyautarsa tafi iskan dake kadawa yawa, domin tana game kowa da kowa. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana cewa; "Mafificiyar sadaka, itace wacce akayi a cikin Ramadana.

4- CIYAR DA ABINCI

Akwai alkhairai kwarai da gaske a cikin ciyar da abinci, a Ramadana ne ko waninsa. Kamar yadda Allah s.w.t ya ambata siffofin mutanen kirki a cikin suratul insãn aya ta 8-12 saboda suna ciyar da abinci tare da zukatansu na cikin jin dadi da walwala lokacin da suke ciyarwar.
Magabata na kwarai sun kasance suna ciyar da abinci a ramadana kwarai da gaske, manzon Allah s.a.w yana cewa; "yã Ku mutane Ku watsa sallama, Ku ciyar da abinci, Ku sadar da zumunta, kutashi lokacin da mutane ke barci domin kuyi sallah, zaku shiga aljanna da aminci.[imamu Ahmad ya ruwaito da tirmidhi, Albany ya ingantashi].
Manzon Allah s. a.w yace: "Duk Wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatan kwacin ladarsa, ba tare da anrage mashi komai ba.[imamu Ahmad ya fitar, da nasa'i, Albany ya ingantashi.

5- NEMAN LAILATUL-KADRI.
Allah madaukakin sarki yana cewa: "Lallai mu muka saukar dashi (Qur'ani) a daren daraja, wa ya sanar dakai me ake cewa daren daraja, daren daraja yafi Alkhairi fiye da wata dubu.
Manzon Allah s. a.w yace; "Duk Wanda yayi tsayuwar daren lailatul-kadri, yana mai imani da kwadayin Neman lada, an gafarta mashi zunubbansa.[Bukhari da Muslim]

Lailatul-kadari ana nemanta a daren 21,23,25,27 ko 29. Hadisi ya tabbata daga  ummuna Aisha R.A tacewa manzon Allah s.a.w idan na dace da daren lailatul-kadari me zan fada? Sai yace mata kice; اللهم إنك عفو،تحب العفو،فعف أني
Ma'ana; "yã Allah kai mai yafiya ne, kanason masu yafiya, ka yafe mani.[Ahmad ya ruwaito da tirmidhi, Albany ya ingantashi].

6- YAWAITA ZIKIRI DA ADDU'AH DA ISTIGFARI.

Ya yan uwa
  Kwanakin watan ramadana masu tsada ne, mu daure mu ribacesu da yawaita zikiri da addu'ah, musamman a kebantattun lokuta na amsar addu'ah. Daga cikin lokuttan akwai;
* Lokacin da mai azumi zaiyi buda baki, ba'a maida addu'ah a wannan lokacin.

*  Daya bisa ukun dare, lokacin da Allah s.w.t yake saukowa yana cewa: "ina mai rokona in amsa mashi, ina mai neman gafara in gafarta mashi.

Daga karshe ina kwadaitar damu akan mu tsaya mu ribaci wannan wata mai albarka kafin ya wuce! Idan ya wuce bamu da tabbacin zamu kara riskarshi.

Allah ya tabbatar damu akan aikata abubuwan da suka dace da sunnah a cikin wannan wata mai albarka.

        WASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH.



COPYRIGHT©
Hashim ibn Surajo ibn Uba(ABU SINÃN)
ATS~TSAMAWY```

atstsamawy@gmail.com

http://hashimtsamiya.mywapblog.com

http://abbansinaan.mywapblog.com

http://abbansinan.WordPress.com

http://shababusunnahtsafe.mywapblog.com

http://masjiduabihurairatsafe.blogspot.com

https://free.facebook.com/hashimusurajo.tsamiya

+2348064734911
+2349030201868

Wednesday, 19 April 2017

ABUBUWA GUDA ASHIRIN

🌺🌺🌸🌺🌸🌸🌺🌺🌸🌺
```ABUBUWA GUDA (20) DUK WANDA ALLAH YA ALBARKACE SHI DA RAYUWA TARE DA DAYAN MAHAIFANSHI KO DUKAN SU YA KAMATA YA KIYAYE...!!!
🌺🌺🌸🌸🌺🌸🌸🌺🌺🌺

     Dukkan yabo da jin jina da girmamawa sun tabbata ga Allah (S.W.T) wanda ya gwama/hada kadaitashi da biyyaya ga iyaye. Tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta wanda yace “Yardar Allah na tare da yardar iyaye, fushin Allah na tare da fushin iyaye”, da iyalan gidansa da Sahabbansa da wadanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar karshe.

1⃣Yi masu biyayya da da’a ga duk abinda suke so ko suka yi umurni in bai saba ma shari’a ba.

2⃣Nisantar duk abinda zai fusata su ko ya tunzura su.

3⃣Ka tsare mutuncin su da  girmama su a idon jama’a.

4⃣Yi kokari ka yi duk abinda ka san yana faranta ransu koda basu saka ba.

5⃣Ka karba kiransu cikin murmushi, kaje zuwa aikin da suka sanya ka cikin nishadi.

6⃣Kada kayi jayayya dasu ko da a cikin maganar su basu da gaskiya (a maimakon haka ka samu wani lokaci na musamman na lurar dasu kuskuren su a cikin hikima).

7⃣Ka saurare su idan suna Magana kuma kada ka daga masu murya.

8⃣Ka taya su aiki ko da basu neme ka ba.

9⃣Idan dayansu baya da lafiya ka himmatu wajen jinyarsa da kanka.

🔟Bayyana ladabi garesu ko a wurin zama ko tafiya (kada ka saki jiki ko ka mike kafafu ko ka haura sama da su ko kayi tafiya gabansu ta yadda za su ji lallai basu da wani matsayi na girmamawa a gurin ka).

1⃣1⃣Kada ka taba damuwa ko jin ciwon bayyana cewa iyayenka ne (kayi alfahari dasu koda basu da wata daukaka wadda ake kuri da ita).

1⃣2⃣Kada ka bari bukata ta kamasu har su kai ga rokon ka. Ka wadatasu da gwargwado abinda zasu ji dadin rayuwa har su taimaki wani matukar kana da iko.

1⃣3⃣Nuna kulawa da su ta fuskar ziyara koda a wuri daya kuke, idan kuma ba a wuri daya kuke ba to ka ware wani lokaci da zaka rinka tuntubar su, kana samun lokacin fira das u, kana sauraren kokensu da biyan bukatar su.

1⃣4⃣Rinka nuna musu godiya, da cewa duk abinda ka yi musu baka biyasu ba a kan renonka da sukayi.

1⃣5⃣Kada ka bukacesu da abinda basu son baka.

1⃣6⃣Kada ka fifita iyalanka ko ‘ya’yanka akan su.

1⃣7⃣Ka boye masu mafi yawan kyautatawar da ke tsakaninka da iyalanka domin gudun shedan ya sa masu kishi a kan wannan.

1⃣8⃣Idan rashin jituwa ta shiga tsakanin su da iyalinka kada ka taba goyon bayan iyalanka a fili koda su keda gaskiya.

1⃣9⃣Rinka neman addu’arsu kana fada masu bukatunka tare da sanar dasu cewa, addu’arsu tafi  ta kowa kima da saurin karbuwa.

2⃣0⃣Yawaita neman sa albarkarsu a koda yaushe.

COURTESY:
Shababu Ahlissunnah Waljama’ah Tsafe
ZAMFARA STATE
08064607294, 08139348898

P.R.O SHABABUS-SUNNAH TSAFE```

LAA'ILAHA ILALLAH

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*BAYANIN MA'ANAR LAA'ILAHA IL-LALLAHU!!!*
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺

*_001_*

_Rubutawa:_ *Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)*

*بسم الله الرحمن الر حيم*

*الحمد لله رب العالمين، وصلى الله وسلم وبارك على نبينا محمد وعلى آله وصحبه أجمعين.*

```Da farko ya kamata musan cewa ita wannan Kalmar itace ke rabewa tsakanin musulmi da wanda ba musulmi ba!
Wannan Kalmar akan ta aka aiko dukkan Annabawa!
Itace Kalmar dake tabbatar da tsoron Allah na hakika!
Itace igiyar nan mai karfi, wacce duk Wanda ya riketa zata kaishi Aljanna!

Abin lura: Wannan Kalmar ba fadarta a baki ko da halshe tare da jahiltar ma'anarta ke sanya musuluncinka ya inganta ba!

Domin kuwa munafukai suna fadarta a bakunansu, amma kuma Allah yace" suna chan kasan wuta" a suratun nisa'i aya ta 145, tare da cewa suna Sallah suna sadaka, watakila har wurin wa'azi suna halarta.

Abunda ya kamata ga duk wanda ya fadeta, toh ya san ma'anarta har a zuciya ya kudurceta(ma'anarta, sharuddanta, falalarta, da abunda ta kunsa na tauhidi da akeeda) dole ne kaso Kalmar, kaso mai son Kalmar, dole ne ka yaki duk mai adawa da Kalmar ko mai saba mata.

Ita Kalmar LAA'ILAHA- IL-LALLAH! korewa ne da kuma tabbatarwa. Kore ilahantaka ga duk wani wanda ba Allah ba! Koda kuwa Manzo ne, ko Annabi, ko Mala'ika, ko wani mutumin kirki, ko gausi ko waliyyi koma Waye!  Tare da tabbatar da ilahantaka ga Allah shi kadai.

Na daga cikin mas'alolin jahiliyya wanda Annabi Muhammad s.a.w ya saba musu; Bautar mutanen kwarai ta Hanyar Neman biyan bukatunsu da nufin su nema musu ceto a wurin Allah, saboda zatonsu akan cewa Allah na son hakan. Kamar yadda Allah s.w.t yake cewa;
*ويعبدون من دون الله ما لا يضرهم ولا ينفعهم ويقولون هؤلاء شفعؤنا عند الله.* {يونس ١٨}

Ma'ana: "Suna bautar wani wanda ba Allah ba, Wanda bai iya cutar dasu, kuma bai iya amfanar dasu, har ma zakuji suna fada cewa wadancan sune masu cetonmu a wurin Allah"

Wannan ayar in muka lura zatayi aiki ga masu Dariku da yan shi'ah! Saboda suma zakuji suna fadar irin wadannan kalmomin, bari ma, wani lokaci nasu sunfi muni da hadari.

Muna rokon Allah s.w.t ya tabbatar damu akan tauhidi da akeeda Allah ka kara mana Ikhlasi.

Wannan mukaddima ce, amma bayanin zaizo a fitowa ta gaba insha Allahu.

Copyright©
Hashim Suraj Uba Tsamiya(ABU SINÃN)
08064734911```

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???

🌺🍇🍏🌹🌷🌼🌸💐🌺
*AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???*
🌺💐🌸🌼🍇🌷🌹🍏🌺

(001)

Rubutawa: *_Hashim Siraj Uba atstsamawy(ABU SINÃN)_*

بسم الله الرحمن الر حيم

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya chanchanci a bauta masa shi kadai kuma ya hanemu da shirkah, Tsira da Aminci su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad S.A.W wanda ya tsoratar damu daga aikata bidi'ah.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda ganin ya dace mu faɗakar da yan'uwa musamman iyaye da kakanni da ake zalunta da hadisan ƙarya dangane da falalar watan Rajab.

Da farko dai shi watan Rajab yana ɗaya daga cikin watanni masu alfarma wanda aya ta 36 a Suratu taubah tayi bayani.

✏✏✏✏✏✏✏✏
MAGANGANUN MAGABATA AKAN AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI)
✏✏✏✏✏✏✏✏

kai tsaye yanzu ga Wata tambaya da akayi ma Sheikh bin Baaz(R.H) dangane da azumin Rajab(azumin tsofaffi).

An tambayi Sheikh bin Baaz(R.H) akan cewa shin ko yana halatta azumtar watan Rajab (AZUMIN TSOFAFFI) gaba ɗayansa? Domin wasu Malamai suna faɗar cewa: duk wanda ya azumci Rajab, an gafarta mashi zunubbansa koda sun kai yawan kumfar teku, wasu kuma malaman sunyi hani da azumtar watan suna cewa; duk da zamanshi cikin watanni masu alfarma baya halatta a azumce shi baki ɗaya???

Ga amsar da bin Baaz ya bada, yana cewa; " Abun sani kawai shine ba'a shar'anta azumtar watan Rajab ba! Bari ma an karhantashi, abunda ya tabbata shine an shar'anta azumin sha'aban, Manzon Allah S.A.W ya kasance yana yin azumin sha'aban, yana azumtar sha'aban sai kaɗan yake ragewa(Ma'ana, ya a yawaita azumi a Sha'aban), amma Rajab an karhanta yin azumi a cikinsa, azumi a cikinsa yana daga cikin aikin jahiliyya, saboda masu azumtar basu da dalilin azumtar watan!!! 

Hadisan da ake yawo dasu akan falalar watan Rajab basu da asali, bari ma na ƙarya ne waɗanda basu inganta ba, abinda shari'ah ta shar'anta ga musulmai shine suci susha a watan Rajab, sai dai idan ya kasance kana yin azumin nafila tun kafin zuwan watan Rajab wanda su dama shari'ah ta tabbatar dasu, kamar; litinin da Alhamis, Ayyamul-beed da sauransu, wannan yana da kyau kuma babu laifi, amma azumtar watan gaba ɗayansa, ko kuma baka saba yin azumin nafila ba sai da watan ya shigo sai ka fake da azumin nafila ka gabatar da na Rajab wannan shari'ah bata yadda dashi ba.


Wannan itace amsar da sheikh bin Baaz ya bada dangane da azumin tsofaffi na Rajab.

Hadisi ya tabbata daga Aisha matar Annabi Muhammad s.a.w tana cewa:

كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يصوم حتى نقول لايفطر، ويفطر حتى نقول لايصوم، وما رأيته أكثر صياما منه في شعبان.
[صحيح أخرجه البحاري(١٩٦٩)، و مسلم(١١٥٦)].

Ma'ana; Aisha R.A take cewa; "Manzon Allah S.A.W ya kasance yana yin azumi har sai mun ce baya cin abinci! Yana cin abinci har sai munce baya yin azumi(ma'ana yana yin azumi da yawa, haka kuma yana aje azumi ya huta sosai), ban taɓa ganin Manzon Allah S.A.W yana cika azumin wata daya ba sai dai idan ramadhan ne, ban taba ganin watan da yafi azumi a cikinsa ba face sha'aban

[Bukhari da Muslim]

Haka nan Sheikul Islam yqna cewa

ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ " ‏( 25/290 ‏) :
" ﻭﺃﻣﺎ ﺻﻮﻡ ﺭﺟﺐ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ﻓﺄﺣﺎﺩﻳﺜﻪ ﻛﻠﻬﺎ
ﺿﻌﻴﻔﺔ ، ﺑﻞ ﻣﻮﺿﻮﻋﺔ ، ﻻ ﻳﻌﺘﻤﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻋﻠﻰ
ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻬﺎ ، ﻭﻟﻴﺴﺖ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﺮﻭﻯ ﻓﻲ
ﺍﻟﻔﻀﺎﺋﻞ ، ﺑﻞ ﻋﺎﻣﺘﻬﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﺿﻮﻋﺎﺕ ﺍﻟﻤﻜﺬﻭﺑﺎﺕ...

Shaikhul Islam Ibn taimiyyah (RH) y
ace: “Kebance watan rajab da yin azumi,
dukkan hadisan
da su ka zo akan haka da’ifai ne (masu
rauni), bari
ma hadisan karya ne, masu ilimi
basu amfani dasu, domin basu
cikin hadisan
da ake amfani dasu don nuna falalar
aikata abu,  bari ma dukkan su ma
hadisai ne
na karya..”
Duba Majmu’u Fatawa (25/290).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :
" ﻛﻞ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻲ ﺫﻛﺮ ﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻭﺻﻼﺓ ﺑﻌﺾ
ﺍﻟﻠﻴﺎﻟﻲ ﻓﻴﻪ ﻓﻬﻮ ﻛﺬﺏ ﻣﻔﺘﺮﻯ " ﺍﻧﺘﻬﻰ ﻣﻦ " ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ
ﺍﻟﻤﻨﻴﻒ " ‏(ﺹ 96 ‏)

Imam Ibnul Qaiyim (RH) y ace;
“Dukkan hadisan
da suka ambaci azumin watan rajab da
sallatar wasu
darare a cikin sa, hadisai ne na karya kuma
kirkirarru”.
Duba Almanarul Muniif (shafi 96).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺤﺎﻓﻆ ﺍﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﻓﻲ " ﺗﺒﻴﻴﻦ
ﺍﻟﻌﺠﺐ " ‏(ﺹ 11 ‏) :
" ﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ ﻓﻀﻞ ﺷﻬﺮ ﺭﺟﺐ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﺻﻴﺎﻣﻪ
ﻭﻻ ﺻﻴﺎﻡ ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻪ ﻣﻌﻴﻦ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺔ
ﻣﺨﺼﻮﺻﺔ ﻓﻴﻪ ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ﻳﺼﻠﺢ ﻟﻠﺤﺠﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ.

Alhafiz Ibn Hajar Al-Asqalani yake
cewa; “Babu
wani abu da aka ruwaito na falalar
watan Rajab,
ko yin azumi a cikin sa, ko azumtar
wasu adadin
kwanaki ayyanannu, ko tsayuwar
wasu darare
kebantattu”.
Duba Tabyinul Ajab (shafi 11).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺳﻴﺪ ﺳﺎﺑﻖ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ " ﻓﻘﻪ
ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 1/383 ‏) :
" ﻭﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻟﻴﺲ ﻟﻪ ﻓﻀﻞ ﺯﺍﺋﺪ ﻋﻠﻰ ﻏﻴﺮﻩ ﻣﻦ
ﺍﻟﺸﻬﻮﺭ , ﺇﻻ ﺃﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻷﺷﻬﺮ ﺍﻟﺤﺮﻡ , ﻭﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ
ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺃﻥ ﻟﻠﺼﻴﺎﻡ ﻓﻀﻴﻠﺔ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ,
ﻭﺃﻥ ﻣﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻤﺎ ﻻ ﻳﻨﺘﻬﺾ ﻟﻼﺣﺘﺠﺎﺝ ﺑﻪ
" ﺍﻧﺘﻬﻰ

Imam Sayyid Sabiq (RA) yake cewa;
“Azumin
watan rajab bashi da wani fifiko na
falala akan
waninsa cikin watanni, sai dai shi
yana daga cikin
watanni (guda hudu) ma su alfarma,
kuma ba a
samu a cikin sunnah ingatacciya ba cewa
yin azumi a
cikin sa yana da falala kebantacciya,
abunda ya zo
akan haka (ma’ana hadisan da suka
zo) ba a kafa
hujja dasu (domin da’ifai ne)”
Duba Fiqhus-Sunnah (1/383).

ﻭﺳﺌﻞ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻦ ﺻﻴﺎﻡ
ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﻭﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺘﻪ .
ﻓﺄﺟﺎﺏ :
" ﺻﻴﺎﻡ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ
ﻟﻴﻠﺘﻪ ﻭﺗﺨﺼﻴﺺ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺔ , ﻭﻛﻞ ﺑﺪﻋﺔ ﺿﻼﻟﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ " ‏( 20/440 ‏)

An tambayi sheikh Muhammad Salihul Usaimeen
(RH)
dangane da azumi ranar 27 ga watan
rajab da
kuma tsayuwar dararen sa.
Sai ya amsa da cewa:
“Yin azumi ranar 27 ga watan Rajab
da tsayuwar
darensa kebance shi da haka bidi’a
ne, dukkan
bidi’a kuma batace”
Duba Majmu’u fatawa na Usaimeen
(20/440).

   Haka zalika Sayyidina umar R.A ya kasance yana bulala akan wadanda ke kamewa akan azumin Rajab, yana ce musu kuci abinci, wannan watane da ya kasance ake girmamawa a lokacin jahiliyya. [Ibn Abi shaibah ya fitar 3/102] da ibn kathir a cikin musnadil- faruk 1/285]

Haka zalika ibn umar R.A ya kasance idan yaga mutane suna wuce gona da iri akan Rajab, yana kyamar hakan!
[Sahih: ibn abi shaibah ya fitar 3/102]

Ibn Abbas ya kasance yana hani akan azumin Rajab gaba dayansa, saboda kada a maida shi ya zama abunda za'a rinka yi duk shekara, wato a maidashi ya zama idi.
[Sahih; Abdulrazak ya fitar 7854].

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISAN DA SUKA INGANTA AKAN WATAN RAJAB!
✏✏✏✏✏✏✏✏
=  "kuyi axumi a cikinshi kuma kuci abinci a cikinshi.
[Sahih irwa'ul galeel 958]

= Sha'aban yana tsakanin Rajab da Ramadhan, ana shagaltar da mutane akanshi(domin samun saukin Ramadan) a cikin sha'aban ake daukar ayukkan bayi, ina kwadayin/inason kada a daga ayyukana face ina azumi.
[Isnadinsa mai kyau ne, silsilatus-sahiha 1898]

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISSAI DA'IFAI WADANDA MASU AZUMIN RAJAB KE KAFA HUJJA DASU.!!!
✏✏✏✏✏✏✏✏

= A cikin Aljanna akwai wani gulbi, ana kiransa Rajab, ruwansa suna da fari wanda farin yafi na nono, duk wanda yayi azumin Rajab na rana daya, Allah zai shayar dashi daga wannan gulbin.[Silsilatu-dha'ifah 1898]

= Rajab watan Allah, Sha'aban wata na(manzon Allah), Ramadan watan Al'umma ta.
Da'ifi ne, silsilatu-dha'ifah 4400]

= Darare guda biyar ba'a maida Addu'ah: 1. Farkon Daren Rajab. 2. Daren Rabin watan sha'aban. 3. Daren jumu'ah.  4. Daren karamar sallah. 5. Daren babbar sallah.
[Maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 1452]

= Rajab watane mai girma, Allah na lunka lada idan kayi aikin Alkhairi a cikinsa, duk wanda yayi azumin Rajab na kwana daya,kamar yayi azumin shekara. Duk wanda yayi na kwana bakwai, za'a rufe mashi kofofin wutar jahannama bakwai. wanda yayi na kwana takwas, za'a bude mashi kofofin Aljanna takwas. Wanda yayi na kwana sha biyar, mai kira zaiyi kira a sama yace; an gafarta maka abunda ya gabata na laifuka...[maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 5413]

✏✏✏✏✏✏✏✏
RUBABBUN HADISSAN DA YAN SHI'AH KE KAFA HUJJA DASU AKAN FALALAR WATAN RAJAB.
✏✏✏✏✏✏✏✏
Daga Baban hassan (A.S) yace; Annabi Nuhu (A.S) ya tuka jirgin ruwa a farkon watan Rajab, sai ya umurci wadanda ke tare dashi da su azumci wannan ranar, yace; "duk wanda ya azumci wannan ranar Allah zai nisanta shi da wuta na tsawon tafiyar shekara daya.

=Daga Abi Ja'afar, Muhammad ibn Aliyu(A.S) yace; duk wanda yayi azumi a Rajab na rana daya, a farkon Rajab ko tsakiyarsa ko karshensa, Allah ya wajabta mashi shiga Aljanna, kuma Allah zai sanya shi a tare damu a cikin darajojinmu na Ahlul baiti a ranar kiyama, wanda yayi na kwana biyu, Allah zai gafarta mashi duk zunubbanshi da suka gabata, wanda yayi na kwana uku, Allah zai gafarta mashi abunda ya gabatar na zunubi da wanda zaiyi a gaba sannan za'a bashi damar ceton yan uwanshi ma'abota zunubi...

= As-sadik Ja'afar  ibn Muhammad yace; "kada ka bari ranar ashirin da bakwai ga Rajab ta wuce ba tare da ka azumceta ba! Domin a ranar ne aka saukar wa Annabi Muhammad s.a.w Annabta...

Duka wadannan zaka samesu a cikin littafi mai suna FALALAR WATANNI UKU, wanda gingimemen malamin Shi'ah mai suna MUHAMMAD IBN ALIYU IBN HUSSAIN IBN MUSA AL-QUMMY ya rubuta.
Allah ka la'anci qummy.

  A takaice wadannan sune hujjoji na dangane da rashin ingancin azumin Rajab(azumin tsofaffi), duk wanda yake ganin akwai Gyara matukar gyaran nashi ya inganta hadisi ne ko aya ina maraba dashi kwarai da gaske.

Allah ya hadamu dani daku da sauran musulmai a cikin Aljannah.

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH...```


Copyright©
Dalibinku
*_Hashim Suraj Uba Tsamiya {ABU SINÃN}_*
☎08064734911
📞09030201868

http://abbansinan.WordPress.com

http://hashimtsamiya.blogspot.com

http://abusinan.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

17-07-1438AH
15-04-2017AC