Sunday, 25 November 2018

(B) DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪
*وليتذكر ألوا الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

Gabatarwa: *MUKYAUTATA NIYYA*

_PART_ *B*


*KASHI/BAYAN GIDA YAFI MAULIDI A SALI A CIKIN ADDINI...!!!*

*LADUBBAN SHIGA BAYAN GIDA(BIYAN BUKATA)*

Abubuwan da aka so ayi wajen shiga bayan gida don biyan bukata.

*Gasu kamar haka:-*

1. A lokacin shiga, zaka fadi ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺇﻧﻲ ﺃﻋﻮﺫ ﺑﻚ ﻣﻦ ﺍﻟﺨﺒﺚ ﻭﺍﻟﺨﺒﺎﺋﺚ . ```ALLAHUMMA INNI A'UZU BIKA MINAL KHUBSI WAL KHABA ISI```
watau [ALLAH INA NEMAN TSARI DAGA GAREKA, KA KARENI DAGA SHARRIN ALJANNU (SHAIDANU MAZA DA MATA)

2. Shiga bayan gida da kafar hagu.

3.sanya gajeren wando lokacin wanka, domin ka kare tsiraicinka idan a fili ne a wajen wankan

4. Fara yin bisimillah

5. Sanya ruwan wanka a gefen hannun dama

6. Amfani da takaitaccen lokaci a bayan gida(kashi)

7. Fitowa da kafar dama

8. Kebewa daga idanun mutane

9. Tsugunnawa lokacin da ake bayan gida

10. Mayar da nauyin jiki zuwa bangaren hagu

Bai kamata ba a shiga bayan gida da abin da ya ke dauke da sunan Allah s.w.t a jikinsa(sai dai domin gudun kada a sace shi), bayan an gama ana son a wanke hannaye da ruwa, ko da sabulu ko kuma tur6aya ko yashi.

Musulmai ya kamata lokacin da za suyi bayan gida ko wanka, su kebe kansu daga inda mutane zasu iya ganinsu.

An kar6o daga jabir yace; "idan muna tafiya tare da manzon Allah s.a.w, ya kanyi bayan gida idan ya kebe daga mutane (wato ya kan sakaya kansa inda ba mai ganinsa.

*ABUBUWAN DA BA'A SON A AIWATAR DANGANE DA BAYAN GIDA...!!*

1. Fuskantar/juya wa Alkibla baya idan a fili ne.

2. Magana ko kuma wa'ka yayin da ake bayan gida

3. Yin wanka a gaban jama'a

4. Karanta ayoyin alkur'ani a ban daki

5. Yin amfani da ruwa mai yawa.

6. Yin wanka, fitsari, ko bayan gida a wajen da ake ibada, misali;
*MASALLACI, COCI,* ko wani majalisi na al'umma.

7. Wanke can cikin dubura

8. Barin wasu mutane su ga tsiraicin dan uwansu.

9. Yin fitsari a cikin rami.

10. Ta6a azzakari ko dubura da hannun dama.

Yan uwa munji kadan daga cikin ladubban bayan gida(KASHI)
Domin karin bayani, ka duba ﺑﻠﻮﻍ ﺍﻟﻤﺮﺍﻡ -ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻄﻬﺎﺭﺓ - ﺑﺎﺏ ﺁﺩﺍﺏ ﻗﻀﺎﺀ ﺍﻟﺤﺎﺟﺔ

*YAN TA MAULIDE MUNA JIRAN NAKU LADUBBAN NA CASHEWA, DAGA HADISSAI INGANTATTU, DA INDA AKA CIROSU.*

*HAATU BURHAANAKUM INKUNTUM SADIQEEN*

HUJJA MUKE BUKATA BA ZAGI BA


✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy ( _ABBAN-SINAN_ )*
+2348064734911

018 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUPS DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha takwas 018_


Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*MUSTAHABBAN ALWALA:*
Wannan shi ke biye da mataki na sunnoni, kenan sunnoni sun fi mustahabbai karfi,
wadanda suke dukansu biyun farillai na gabansu, babu daya daga cikin sunnoni ko
mustahabbai da mutum zai yi sakaci da su, domin kowannen mu so yake ya yi ibada
cikakkiya kammalalla, to kuwa tunda hakane bai kamata kace ai wannan mustahabbi ne ka daukeshi kamar wani karamin abu. Su mustahabban alwala suna da yawa, amma yanzu ga kadan daga cikinsu:

1⃣ Ambaton Allah kace *Bismillah* a daidai lokacin da zaka fara alwala, amma idan mutum
ya manta saida yake tsakiyar alwalar ya tuna
ba komai sai kayi a lokacin.

2⃣ Addu'a bayan kammala alwala, itace kuma kamar haka:

*ﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥْ ﻻَ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺍَﻟﻠﻪُ ﻭَﺣْﺪَﻩُ ﻻَ ﺷَﺮِﻳﻚَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥَّ ﻣُﺤَﻤَّﺪًﺍ ﻋَﺒْﺪُﻩُ ﻭَﺭَﺳُﻮﻟُﻪُ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺍَﺟْﻌَﻠْﻨِﻲ ﻣِﻦَ ﺍَﻟﺘَّﻮَّﺍﺑِﻴﻦَ، ﻭَﺍﺟْﻌَﻠْﻨِﻲ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﻤُﺘَﻄَﻬِّﺮِﻳﻦَ.*

_Ma'ana:_ ```Ina shaidawa da babu abun bauta da
cancanta sai Allah, kuma shi kadai yake bashi da
abokin tarayya, kuma ina shaidawa lalle (Annabi)
Muhammad bawan Allah ne kuma manzonsa ne,
Ya Allah ! ka sanya ni daga cikin masu yawan tuba, kuma ka sanya ni daga masu neman
tsarkaka.```

3⃣ 'Karanta Ruwa;
   Bawai ana nufin mai alwala ya shashshafa gabbansa bane, a'a, ana bukatar yayi amfani da ruwa amma kada ya malalar dasu, domin yana daga cikin tsarin musulunci
tattali da tsimi da tanadi.

4⃣ Gabatar Da Asuwaki:
Bayani kuma dama ya gabata akan asuwaki, ana yi da danye ko da
busasshe, idan bai samu ba sai ayi da yatsa, amma mu sani asuwaki daban kuskurar baki ma
daban. Hakanan kuma ko da mutum lokacin sallah yayi amma yana da alwala to abinda ake so shine ya yi asuwaki.

5⃣ Wuri Mai Tsarki:
  An so inda zaka yi alwala ya zama wurine mai tsarki.

6⃣ Dama Kafin Hagu:
  Abun nufi shine ka fara wanke hannun dama kafin hannun hagu, hakanan ka fara wanke kafar hagu kafin ta
dama.

7⃣ Jerantawa:
  Wato jeranta kowacce sunnah
tare da 'yar-uwarta, kamar fara gabatar da kuskurar baki kafin shaka ruwa.

8⃣ Wankewa Sau Uku:
  Ma'ana wanke wuraren da ake wankewa sau uku, mu sani wankewa sau uku zai zama mustahabbine idan wankewar farko ta game ko ina, amma idan ta farko bata
game ba to ta biyu tananan amatsayin wajibi, haka idan ta biyun bata game ba
to ta uku tana nan a matsayin wajibi. Ya zama wajibi mai alwala mace ko namiji ya kula sosai
ya cuccuda inda ya kamata ya sa ruwa ba tare da barna ba.
Amma shi kai sau daya ake shafarsa, ba'a shafar kai sau biyu ko uku. Sannan kuma mutum ya tabbata a wadannan wankewa da akace yayi sau uku bai kara akan hakan ba, yayi iya kokarinsa ya ga guda ukun sun kammala.

Wadannan kadan kenan daga cikin
mustahabban alwala, kuma wadannan bayanai
sun shafi mata kamar yadda suka shafi maza, sai dai
mata su sani gashin kansu al'aurane, saboda haka bai
halatta su bayyanar dasu ga maza ba, kenan idan zaki yi alwala sai ki sami wuri ki kebance
kanki.

Wadannan bayanai da suka gabata zasu haskaka mana yadda alwala take, amma hanya mafi sauki shi ne a yi maka ita a aikace ka gani domin haka sahabban ma'aikin Allah suka yi, an
tambayi Usman dan Affan dan gane da alwala sai yasa aka kawo mishi butar alawala yayi musu ita a aikace, yace kuma irinta manzon Allah s.a.w yayi.

A nan nake kira ga dukkanin limamai na juma'a dana sauran masallatai da kuma malamai a
jami'oi da kwalejin ilimi da kuma malamai a sakandare da firamare da malaman islamiyyu da malamai masu karantarwa a masallatai da
masu wa'azi da sauran wadanda abin ya shafa kamar kungiyoyin addini
dasu karantar da mutane alwala a
aikace, yadda kowa zai gani ya kuma yi tambaya, kada kaga kamar kowa ya gane da zarar ka yi ta a aikace zaka ga abin mamaki, ni na taba gwada
hakan a *Federal university birnin kebbi,* ita ibada sai an koyawa mutum ba wai daka akeyi ba, kai da ganin
alwalar wani kasan bai je makaranta ba, Allah ya karba mana ibadummu.

A NAN MUKA KAWO KARSHE DANGANE DA BAYANI AKAN ABUNDA YA SHAFI ALWALA, A GABA ZAMU BAYANIN ABUBUWAN DAKE KARYA ALWALA INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN;
✍ *Hashim Siraj Uba atstsamawy ( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

(A) DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

*وليتذكر ألوا الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*

_Gabatarwa:_ *MUKYAUTATA NIYYA GROUPS*

PART *A*

📌 *WANNAN ITACE HUJJAR MU AKAN CEWA MAULIDI BIDI'AH NE...!!!*

*==============*

▫ Abubakar siddiq(RA) yayi khalifanci tsawon shekara biyu amma baiyi maulidi ba, tare da cewa shi mai gaskiyar wannan al'ummar ne, kuma abokin manzon Allah s.a.w a cikin kogo lokacin hijira..!!
*▪▪▪▪▪▪▪*

🔸 Umar bn khaddab(RA) yayi khalifanci shekaru goma(10), amma ba'a ruwaito cewa yayi maulidi ba, tare da cewa shine FARUQ na wannan al'umma..!

*▪▪▪▪▪▪▪*

🔹Usman bn affan(RA) yayi khalifanci shekaru 13, amma baiyi maulidi ba, kuma baice ayi ba, tare da cewa ya auri yayan annabi guda biyu, kuma yayi hijira guda biyu, Wanda yafi kowa kunya a cikin wannan al'umma..!
*▪▪▪▪▪▪▪*

🔸 Aliyu bn Abi dalib(RA) yayi khalifanci shekaru 4 amma bai aikata maulidi ba, baiyi umurni da ayi ba, kuma shi Dan baffan manzon Allah s.a.w ne, kuma shine ya auri shugabar matan yan aljanna...!
▪▪▪▪▪▪▪

▫Hassan bn Aliyu bn Abi dalib yayi khalifanci wata shida(6) amma baiyi maulidi ba, gashi jikan Manzon Allah s.a.w, kuma shine shugaban samarin aljanna...!
▪▪▪▪▪▪▪

◼ Mu'awiya bn Abu sufyan yayi mulki na adalci a cikin kabilun larabawa, amma baiyi maulidi ba, bai kuma ce ayi ba
▪▪▪▪▪▪▪
◻Daular umawiyya tazo, a cikinta akwai irinsu Umar bn Abdulaziz, daular Abbasiyya tazo, a cikinta akwai misalin Harun Ar-rasheed, amma dukansu basuyi maulidi ba, basu kuma yi umurni da ayi ba..!
▪▪▪▪▪▪▪

🔹 Yanzu ma malaman gaskiya, masoya manzon Allah s.a.w gaskiyar so, basuyi maulidi ba tun daga karnukan nan guda uku, tare da tsananin sanin su akan abunda Allah ya saukar, da kuma girman fahimtarsu ga Qur'ani, ya akayi basuyi ba? Tare da cewa sune suka iso da Qur'ani da hadissai zuwa garemu..?

▪▪▪▪▪▪▪
  Mu dai yanzu zamu ce;  Da maulidi alkhairi ne da sun rigamu aikatashi..!
▪▪▪▪▪▪▪
Zamu fadi Abunda Imamu Malik(RH) ya Fada; ```Duk abunda bai zama addini a lokacin manzon Allah s.a.w da sahabbai ba, ba zai taba zama addini ba har tashin Al-kiyama..!```
▪▪▪▪▪▪▪
➡ Abu sananne kawai shine; Manzon Allah s.a.w bai bar duniya ba sai da ya kammala Isar da sakon da Allah ya aikoshi dashi..!
▪▪▪▪▪▪▪
   ▪ ya tsoratar da sahabbanshi akan kirkirar wani abu a cikin addini, da aikata abunda bai aikata ba..!
▪▪▪▪▪▪▪

▫ Ya kamata kusan cewa; wadancan karnukan masu girma basu San wani biki mai suna Maulidi ba! Shifa Maulidi wata bidi'ah ce da yan shi'ah *(FADIMIYYUNA)* suka kirkira, a karkashin wani shugabansu da suke kira Mai daukaka addinin Allah, sai dai karya suke, shi mai cutar da addini ne..!
▪▪▪▪▪▪▪
🔸 yayi mulki a bisa kafirci, da fasikanci, ta inda ya halasta shangiya, ya halasta kowane  farji na mace, ya tsinewa sahabbai kuma yayi umurni da hakan a saman mimbarorin juma'ah, wannan Dan ta'addan shine ya kirkiri maulidi fa! Ya kasa maulidin gida shida, Na farko; Maulidin Manzon Allah s.a.w, sai na Fadima, Aliyu, Hassan, Hussaini(ALLAH YA YARDA DASU) sai Maulidin kanshi..!
▪▪▪▪▪▪▪

Daga nan sai yan fadimiyyuna suka jahiltar da musulmai akan wannan bidi'ar, ya kamata kusan cewa babu wani dalili a wurin yan tamaulide akan halascin maulidi, kawai hujjarsu wasu nassosi ne suke yim a gurguwar fahimta, ko kuma hadissai na karya koda sun inganta sai ka samu basu nuni akan maulidi amma sai su juyar da ma'anarsu.
▪▪▪▪▪▪▪

◼ *YANZU GA WASU YAN TAMBAYOYI GUDA UKU DA MUKESON MU JEFAWA YAN TAMAULIDE, MUNA NEMAN AMSARSU:*
▪▪▪▪▪▪▪

1⃣ Shin bikin maulidi biyayya ne ga Allah da Manzon Allah s.a.w ko sabon Allah ne??

Idan sunce biyayya ne! Ko kuma sunce Sabo ne, duka akwai tuhuma garesu..!

2⃣ Yawwa, idan sukace biyayya ne ga Allah kuma zasu samu lada akai!
Sai muce Ko Manzon Allah s.a.w yasan da wannan biyayyar?
Ko bai sani ba?

➡ Da zasu ce bai sani ba, da sai muce kaiconku! Yanzu kuna tuhumar Babban malami(Manzon Allah s.a.w) da jahilci, wannan kafurci ne, kuma zindikanci ne..!
▪▪▪▪▪▪▪

🔸 Da zasu ce ya sani, toh sai muje a tambaya ta uku.

3⃣ Kunce biyayya ne, kuma Manzon Allah s. a.w ya sani, shin ya bayyanar dashi ga mutane ko kuwa ya boye???

Idan sunce bai Isar ba, wannan tozarci ne ga Manzon Allah s.a.w, da kuma tuhumar Manzon Allah s.a.w da boye wani Abu na manzanci, bayan a Qur'ani Allah s.w.t ya Fada cewa; ```Yaa kai Manzon Allah ka Isar da abunda ya sauka gareka daga ubangijinka, idan bakayi haka ba, baka Isar da Manzancin ba.```

Idan kuma sunce ya Isar, sai muce; Toh kuzo mana da dalili, ina aikin magabata akai?
Yanzu muna bukatar amsoshi daga gareku.

ALLAH YA NUNA MANA GASKIYA YA BAMU IKON BINTA, YA NUNA MANA BIDI'AH YA BAMU IKON KAUCE MATA

KU WATSA WANNAN A TSAKANIN MUTANE DOMIN AL'UMMA SU GANE GASKIYAR BIDI'AR MAULIDI...

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN;
✍ *Hashim Siraj Uba Tsamiya ( _ABBAN-SINAN_ )*
+2348064734911

Thursday, 15 November 2018

002 DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘
*وليتذكر ألوا الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*
🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶

_Fitowa Na biyu 002_

Gabatarwa: *MUKYAUTATA NIYYA GROUPS*

*ASALIN MAULIDI A MUSULUNCI DA WADANDA SUKA KIRKIRESHI!! KASHI NA BIYU(002)*

HAK’IK’A RAFIDA UBAIDIYYUNA, SUN TILASTA WA DUKKAN MA’AIKATANSU ‘YAN MISRA, DA SU RUNGUMI ADDININSU NA RAFIDANCIN BA’DINIYYA, KAMAR YADDA SUKA WAJABTA WA ALK’ALAI SU ZARTAR DA HUKUNCE – HUKUNCE A BISA DOKOKIN WANNAN ADDINI NASU. KAI, HAR YA KAI GA CEWA; SHARA’DI NE NA SAMUN MATSAYI A DAULAR, SAI MUTUM YA JUYA YA KOMA ADDININ RAFIDANCIN BA’DINIYYA. WANDA HAKAN YA SA DA YAWA DAGA CIKIN KAFIRAN AMANA SUN NUNA SHIGA MUSLUNCI TARE DA RUNGUMAR RAFIDANCI.

*DUBA AL- DAULAR FA’DIMIYYA SHAFI NA 218*.

WA’DANNAN MUTANE ‘YAN SHI’A BA’DINIYYA, WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI, YANA DAGA CIKIN GABARSU DA SUNNAR ANNABI (SAW), DA AHLINTA; AZEEZ SARKIN LOKACIN YA YI UMURNI DA A DENA SALLAR TARAWIHI A DUKKAN K’ASAR MASAR. WATO A SHEKARA TA *372.* SA’ANNAN A SHEKARA *393* AN KAMA WASU MUTANE *13,* AKA YI MUSU DUKA, SA’ANNAN AKA YI YAWO DA SU AKAN RAK’UMA A CIKIN GARI, AKA TSARESU TSAWON KWANA *3,* DUK WANNAN SABODA KAWAI SUN YI SALLAR *WALAHA.* A SHEKARA *381,* AN BUGI WANI MUTUM AKA ZAGAYA A CIKIN GARI DA SHI SABODA KAWAI AN SAMU LITTAFIN *”MUWA’D’DA’A”* TA IMAMU MALIK (R) A WAJENSA.

*TSANANIN GABAR UBAIDIYYUNA (RAFIDA BA’DINIYYA) WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI GA SAHABBAI DA AHLUS SUNNA:*

A SHEKARA TA *395H* A CIKIN WATAN *SAFAR,* AN RUBUTA ZAGIN MAGABATA (SAHABBAI) DA TSINE MUSU A BABBAN MASALLACIN *MISRA ”JAMI’UL ATIK”’* DA MA SAURAN MASALLATAN, TA CIKI DA WAJENSU, DA TA DUKKAN GEFE – DA – GEFENSU, DA K’OFOFIN SHAGUNA DA MAK’ABARTU. AKA ZANA SHI DA ZINARI. HAKA AKA YI A K’OFOFIN GIDAJE DA NA MANYAN ‘DAKUNAN TARO. KUMA AKA TILASTA MUTANE AKAN YIN HAKAN, TSINE MA AHLUS SUNNA ABU NE DA YA WATSU A BAKUNAN MUTANE, AKAN MINBARORI A DUKKAN FA’DIN MASAR TSAWON MULKIN UBAIDIYYUNA. HAR TA KAI GA SHI *ABHID* – SARKINSU NA K’ARSHE- SABODA TSANANIN SHI’ANCINSA, DA GULUWWINSA WAJEN ZAGIN SAHABBAI (RA) – IDAN YA GA MUTUM AHLUS SUNNA SAI YA HALATTA JININSA.

*DUBA AL- KHI’DA’DA NA MAK’RIZIY,* (2/ 341). DA *TARIKHUD DAULATIL FA’DIMIYYA* SHAFI NA (620). DA *WAFIYYATUL A’AYAN* (3/ 110).

*KAFIRCIN UBAIDIYYUNA (RAFIDA BA’DINIYYA) WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI:*

WANI ABU DA YA FI DUKKAN ABIN DA MUKA AMBATA A BAYA SHI NE; *AL- HAKIM* SARKIN DAULAR FA’DIMIYYA, YA YI DA’AWAR CEWA; SHI ALLAH NE. *(SUBHANALLAH)!!*  SAI YA UMURCI MUTANE DA SU TASHI SU TSAYA DA K’AFAFUNSU A CIKIN SAHUN SALLAH A LOKACIN DA MAI HU’DUBA YAKE HU’DUBA IDAN YA KIRA SUNANSA, DON GIRMAMA AMBATONSA DA SUNAN NASA. KUMA HAKA YA SA AYI A DUKKAN MASARAUTAR TASA. HAR A HARAMAINI (MAKKA DA MADINA). AMMA YA WARE MUTANEN MISRA YA UMURCE SU DA SUNA FA’DUWA K’ASA SU YI SUJADA, IDAN AN KIRA SUNAN NASA. HAR YA ZAMA MUTANEN DA SUKE KASUWA MA WA’DANDA BA SA ZUWA JUMA’A SUKAN FA’DIN SU YI SUJADA IN NA CIKIN MASALLACIN SUN FA’DI, IN MAI HU’DUBAN YA AMBACI SUNAN NASA, A RANAR JUMA’A. HAR AN SAMU WASU JAHILAN IDAN SUN GAN SHI SAI SU CE: YA *WAHIDANA,* YA *AHADANA,* YA *MUHYI,* YA *MUMITU.* SA’ANNAN YA UMURCI BAK’AK’E DA SU K’ONA MASAR, SU WAWASHE DUKIYOYINTA, DA KAYAYYAKI, DA MATA. KUMA SUKA BI UMURNIN NASA, SUKA KAMA MATA SUKA YI TA ALFASHA DA MUNANAN AIYUKA DA SU. SUKA K’ONA ‘DAYA BISA 3 NA MISRA SUKA WAWUSHE RABINTA.

DUBA *AL- BIDAYA WAN NIHAYA* (12/ 10 – 11), DA *AL- MUNTAZIM* (7/ 298).

*WANNAN SHINE TARIHIN MAULIDI DA WADANDA SUKA KIRKIRESHI A TAKAICE.*

Note: AKWAI BUKATUWAR DUK WANDA YA KARANTA NA FARKO YAYI KOKARI YA NEMI NA BIYU, IDAN KA KARANTA NA BIYU KADA KAYI HUKUNCI SAI KA NEMI NA DAYA.

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*




✍ *ABBAN_SINAN*

001 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE,
DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na daya 001_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*MUKADDIMA*

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki Wanda ya wajabta mana tsarki, tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya karantar damu yadda zamuyi tsarki.

_Bayan Haka;_
Insha Allahu kamar yadda muka alkawarta muku cewa zamu fara kawo muku karantarwa akan ibada da sauransu, yanzu zamu fara daga yau har zuwa lokacin da muke iyawa insha Allahu.
Mun tsara Abubuwan daki-daki, zamu fara da magana akan tsarki kafin sauran, zamuyi kokarin ganin kullum munyi sau daya, filin tambaya a bude yake insha Allahu.

*TSARKI DA YADDA AKE YINSA A MUSULUNCI*

*Shimfida:*  Mu sani ya 'yan-uwa masu albarka,
wannan addini na musulunci addinine da yake
cikakken addini ta kowane bangare, bai takaitu
ga alwala da sallah ba kawai, ya shafi kowane bangare na rayuwa, kamar tsafta kiwon lafiya
zamantakewa, kasuwanci taimakon juna, tsare-
tsaren gudanarwa dadai sauransu.
A yanzu zamu kawo bayanai da suka shafi tsarki, dame-dame ake yiwa tsarki? Me rashin tsarkin yake jawowa? Ya ladubban yin tsarkin
suke? Ya ake shiga makewayi? Dadai sauran wadansu batutuwa da suke da alaka da wannan
maudu'i, da fatan Allah ya yi mana jagora ya
kuma fahimtar da mu.

*ABUBUWAN DA AKEWA TSARKI:*

Ana yin tsarki ne
daga dukkan abinda ya fito ta daya daga
mafita guda biyu ko ma ta duka inbanda hutu (tusa). Kenan ana yiwa fitsari, bayan gida maniyyi maziyyi jinin al'ada….tsarki, kawai dai idan mutum yana da alwala sai ya yi tusa to
alwalar kawai zai sake ba sai ya dauki buta ya yi tsarki ba.

Insha Allahu zamu dakata anan sai lokaci Na gaba.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim siraj uba ats-tsamawy(ABU-SINAN)*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN:

*MUKYAUTATA NIYYA*
wa.me/+2348064734911

*KARATTUTUKAN MALUMAN SUNNAH*
wa.me/+2349031666613

13 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha biyu 013_

Gabatarwa; *UMMU SINAN*


*MENENE JININ BIKI???*
  Jini ne da yake fitowa daga mahaifa ta sanadiyyar haihuwa.
Kenan shi jinin
biki jini ne da yake da alaka da haihuwa, idan mace taga jini kwana daya ko biyu kafin
haihuwa to shima malamai suna lissafashi cikin
jinin haihuwa.

*MAFI YAWAN KWANAKINSA;*

    Mafi yawan kwanakin da macen da ta haihu zata ga jinin haihuwa malamai sun karawa juna sani, wadansu sukace
kwanaki ar'bain ne (40), wadansu kuma sukace kwanaki sittin ne(60) kamar yadda mai Akhdari
ya bayyana.
Sabanin na al'ada shi kwanaki goma sha-biyar ne.

  Idan mace ta haihu sai jinin bai dauke ba to zata jira kwanaki arba'in, ko sittin, idan ya dauke a kwanakin shikenan sai ta yi wankan tsarki na daukewar jinin haihuwa ta ci gaba da sallah da kuma sauran ayyuka na ibada, idan kuma bai dauke ba to sai a nemi magani ya
zama jinin ciwo sai ta yi wankan tsarki ta ci gaba da ibada, idan kuma jinin ya dauke kafin kwanakin kamar ya dauke ranar da aka yi haihuwar to a nan ma zata yi wanka ne ta cigaba da sallah, laifi ne mai girman gaske mace
jinin haihuwarta ya dauke amma taki yin sallah wai sai ta yi arba'in wannan ba tsari bane na addinin musulunci.

Imam Tirmizi yake cewa: Malamai sun yi ijima'i tun daga Sahabbai da Tabi'ai da wadanda suka zo bayansu (Sun yi ijima'i) akan cewa lalle mace mai haihuwa zata bar salla tsawon kwanaki arba'in sai dai idan ta ga tsarki kafin hakan (kafin kwanaki arba'in din) sai ta yi wanka ta kuma yi sallah.
Idan mace ta yi bari sai ya zama na halittar mutum ta bayyana a barin, kamar ace ga tsarin
halittar ba wai gudan jini bane ya zama na kuma akwai jini daya zuba to anan tana da hukuncin jinin biki(jinin haihuwa), gwargwadon kwanakin da sune  halittar take bayyana a ciki sune
watanni uku galibi amma dai mafi karanci sune kwanaki tamanin (80).
Idan ta yi barin gudan jini ko gudan tsoka ta yadda halittar mutum bata bayyana ba to ba'a
la'akari da wannan jinin da ya zubo, saboda
haka ba zatabar sallah ba kuma ba zatabar
azumi ba saboda jinin domin bata da hukuncin
jinin biki.

Idan jinin haihuwa ya dauke kafin wadancan
kwanakin da aka yi bayaninsu to zata yi
wankane ta kuma yi sallah ko da jinin ya
dauke ne a ranar da aka yi haihuwar.


ZAMU DAKATA A NAN SAI WANI LOKACI NA GABA IDAN ALLAH YA KAIMU INSHA ALLAHU.

DOMIN SHIGA GROUP DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

*وليتذكر أولو الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*

✍ *KO MAULIDI NA DA ASALI A CIKIN ADDINI???*

🍂 *AL-ALLAMA, IMAMUSH SHAUKANY (RAHIMAHULLAH) YACE;*

```Har yanzu ba'a samu dalili a cikin AL-QUR'ANI da SUNNAH, da IJMA'IN MALAMAN MUSULUNCI ko QIYASI da ya nuna tabbatuwar maulidi ba, bari ma Musulmai sun hadu akan cewa ba'a san maulidi a zamanin sahabbai ba ko tabi'ai ko masu bi musu ba.```

📚 *FATHUR-RABBANY(2/1087)*

_GASKIYA DAYA CE, DAGA QINTA SAI..._

#ABBAN_SINAN
http://wa.me+2348064734911
atstsamawy@gmail.com

01DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...

🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘

*وليتذكر أولو الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*
🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶

_Fitowa Na Farko 001_

Gabatarwa: *MUKYAUTATA NIYYA GROUPS*

*ASALIN MAULIDI A MUSULUNCI DA WA’DANDA SUKA K’IRK’IRE SHI!!*

MAGABATAN WANNAR AL’UMMA BA SU YI MAULIDI BA KAMAR YADDA KOWA YA SANI, K’ARNUKAN DA MANZON ALLAH (SAW) YA YABESU WATO K’ARNI NA FARKO DA NA BIYU DA NA UKU DUKA SUN GABATA AMMA LITATTAFAN TARIHI BA SU KIYAYE MANA CEWA AN SAMU WANI DAGA CIKIN SAHABBAI KO TABI’AI KO MABIYA TABI’AI, DA MA WA’DANDA SUKA ZO A BAYANSU DA YA YI MAULIDIN ANNABI (SAW) BA, DUK DA TSANANIN SOYAYYARSU GA MANZON ALLAH S.A.W, KUMA DUK DA CEWA SUN FI KOWA ILIMIN SANIN ADDININ MUSULUNCI, KUMA DUK DA CEWA SUN FI KOWA KWA’DAYIN BIN SHARI’AR ANNABI (SAW).

FARKON WA’DANDA SUKA FARA MAULIDIN ANNABI S.A.W  SUNE :
*BANU UBAID AL-K’ADDAH*, WA’DANDA SUKE KIRAN KANSU DA *FA’DIMIYYUNA*
MA’ANA JIKOKIN FATIMA (R A). SABODA SUNA DANGANTA KANSU ZUWA GA ZURIYYAR ALIYU (R A),
ALHALI A HAK’IK’ANIN GASKIYA WA’DANNAN MUTANE SU NE SUKA ASSASA *DA’AWAR BA’DINIYYA,* WATO ‘YAN BA’DINIYYA MASU CEWA ADDINI YANA DA ZAHIRI YANA DA BA’DINI, KUMA WAI SUNE SUKA SAN BA’DININ.

*ASALIN KAKANSU*
SHI NE *IBNU DISAN,* WANDA AKA FI SANI DA *AL- K’ADDAH,* YA KASANCE MAULA NE NA *JA’AFARUS SADIK’* WATO ‘YANTACCEN BAWANSA, KUMA ‘DAN ASALIN GARIN *AHWAZ* NE, ‘DAYA DAGA CIKIN WA’DANDA SUKA ASSASA MAZHABAR *BA’DINIYYA* A IRAK’I, SANNAN SAI  YA BAR GARIN ZUWA MAGRIB, TO A WANCAN YANKIN NE YA DANGANTA KANSA ZUWA GA *AK’ILU ‘DAN ABI ‘DALIB,* YA RIYA CEWA SHI DAGA TSATSONSA YAKE,  TO A LOKACIN DA *RAFIDA* MASU GULUWI SUKA AMSA DA’AWARSA, SAI YAYI DA’AWAR CEWA WAI SHI ZURIYYAN *MUHAMMAD BIN ISMA’IL BIN JA’AFAR AL- SADIK’* NE, KAWAI SAI SUKA YARDA DA HAKAN DUK DA CEWA SHI *MUHAMMAD BIN ISMA’IL*  YA MUTU BAI BAR *‘DA* BA,
DAGA CIKIN WA’DANDA SUKA BI SHI AKWAI *HAMDAN K’URMU’D*, WANDA *K’ARAMI’DA* SUKE DANGATUWA GARE SHI. DA ZAMANI YA YI NISA SAI *SA’ID BIN HUSAINI BIN AHMAD BIN ABDULLAH BIN MAIMUN BIN DISAN* YA BAYYANA, SAI YA CANZA SUNANSA DA NASABARSA, SAI YACE WA MABIYANSA SHINE *UBAIDULLAHI BIN HASAN BIN MUHAMMAD BIN ISMA’IL BIN JA’AFAR AL- SADIK’*, A HAKA SAI FITINARSA TA BAYYANA A MAGRIB.

DON K’ARIN BAYANI AKAN WANNAN BAYANI, DUBA *WAFIYYATUL A’AYAN*( 3/ 118), *ALBIDAYA WAN NIHAYA* (11/ 202), *FABHA’IHUL BA’DINIYYA* SHAFI NA (11), *ALFARK’U BAINAL FIRAK’ NA BAGDADIY* SHAFI NA (266 – 267).

KHALIFOFIN DAULAR RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA/FA’DIMIYYA DAKE *MISRA* SUNE SUKA FARA DUKKANNIN MAULIDI!

DON HAKA FARKON WA’DANDA SUKA FARA MAULIDI SU NE RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA WA’DANDA SUKA YI NUFIN CANZA WA MUSULMAI ADDININSU, TA HANYAR SHIGAR DA ABIN DA BA YA CIKINSA.
UBAIDIYYUNA SUN SHIGA MISRA NE A *SHEKARA TA 362 BAYAN HIJIRA*, A RANAR *5 GA RAMADAN*, WANNAN NE FARKON LOKACIN DA SUKA FARA MULKINSU A MISRA, WASU SUN CE: RANAR *7 NE GA RAMADAN,* TO DUKKANNIN MAULIDI NA ANNABI (SAW) DA NA WANINSA WA’DANNAN MUTANE UBAIDIYYUNA SUNE SUKA FARASHI,
BABU WANDA YA TA’BA YIN MAULIDI KAFINSU.
*AL- MIK’RIZIY* YACE; KWANAKIN DA KHALIFOFIN FA’DIMIYYA SUKA RIK’A A MATSAYIN RANAKUN IDI, DA RANAKUN TARO WA’DANDA AKE YALWATAWA TALAKAWA DA YAWAITA MUSU NI’IMOMI YA KASANCE KHALIFOFIN FA’DIMIYYA SUNA DA RANAKUN IDI DA NA TARO A TSAWON SHEKARA, GA SU KAMAR HAKA:
*BIKIN DAREN FARKON SHEKARA,* DA, *BIKIN RANAR FARKON SHEKARA,* *RANAR ASHURA,* *RANAR HAIHUWAR ANNABI (SAW),* *RANAR HAIHUWAR ALIYU (RA),* *DA RANAR HAHUWAR HASAN (RA),* *DA RANAR HAHUWAR HUSAINI (RA),* DA RANAR HAIHUWAR *FATIMA AL- ZAHARA’U (RA),* DA RANAR HAIHUWAR *KHALIFA MAI CI A LOKACIN,* DA IDIN DAREN *RAJAB,* DA DAREN TSAKIYAR *RAJAB,* DA DAREN FARKON *SHA’ABAN,* DA TSAKIYAR *SHA’ABAN,* DA TARON IDIN *SALLAR AZUMI,* DA NA IDIN *LAYYAH,* DA IDIN *GADEER,* da sauransu...

SA’ANNAN SAI *AL- MAK’RIZIY* YA ‘DAUKESU ‘DAYA BAYAN ‘DAYA YANA BAYANIN YADDA SUKE YINSU. DUBA *AL- KHI’DA’DUL MIK’RIZIYYA* (1/ 490).

*YANAYIN MULKIN KHALIFOFIN RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA TA DAULAR FA’DIMIYYA, WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI:*

SARAKUNAN DAULAR FA’DIMIYYA TA RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA SUN FUSKANTAR DA SIYASARSU NE ZUWA GA MANUFA GUDA ‘DAYA, ITA CE: YIN DUKKAN IYA K’OK’ARINSU NA TILASTAWA MUTANE AKAN SU BI ADDININSU NA RAFIDANCIN BA’DINIYYA, DA SANYA SHI YA ZAMA SHI NE AWWALU MAA YAJIBU A DUKKAN GARURUWAN MISRA, DA MA SAURAN GARURUWAN DA SUKE MULKI, DA MAK’OBTANSU.
SARAKUNAN WANNAR DAULA SUN YI MATUK’AR MU’AMALA DA YAHUDAWA DA NASARA, TA YADDA SUN NUNA MUSU SOYAYYA SOSAI, SUN BASU MUK’AMAI MASU GIRMA A CIKIN WANNAR DAULA.
DUBA *ALBIDAYA WAN NIHAYA* (11/ 358), *AL- MUNTAZIM* (7/ 190), *ITTI’AZUL HUNAFA* (1/ 297), *AL- DAULAR FA’DIMIYYA* SHAFI NA (202).

HAK’IK’A AL- UBAIDIYYUNA/RAFIDA/‘YAN BA’DINIYYA DA SARAKUNAN DAULAR FA’DIMIYYA, SUN KAI MATUK’A WAJEN YA’DA TSINUWA GA KHALIFOFIN ANNABI (SAW) GUDA 3; *ABUBAKAR* (RA), DA *UMAR* (RA), DA *USMAN* (RA) DA SAURAN SAHABBAI.
SABODA SUNA K’IRGASU A CIKIN MAK’IYA ALIYU (RA). TARE DA WATSA FALALAR ALIYU (RA) DA ‘YA’YANSA TA HANYAR ZANAWA A JIKIN MANYAN K’ARFUNA DA RUBUTAWA A JIKIN KATANGUN MASALLATAI,
KUMA MASU HU’DUBA SUN KASANCE SUNA TSINE MA SAHABBAI AKAN DUKKANNIN MINBARORIN K’ASAR MISRA GABA ‘DAYA.


KADA RUBUTUN YAYI TSAYI, ZAMU DAKATA A NAN SAI LOKACI NA GABA ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*


*ABU-SINAN*

ISTIKHARA

*SALLAR ISTIKHARA(NEMAN ZABIN ALLAH) A MUSULUNCI*
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

Wallafar Dalibinku;
✍ *ABBAN SINAN*

http://darulfikr.com/ebook/41913

KU SAUKE KU KARANTA ZAKU KARU MATUKA

http://wa.me+2348064734911

BINCIKE...

*ANALYSIS*

Assalamu Alaikum warahmatullahi wabarakatuhu

Yan uwa na masu albarka dake group din *MUKYAUTATA NIYYA* both, na *Mata* dana *Maza* ina bukatar taimakonku a wannan shekarar domin Isar da sakon Allah.
Wane irin taimako ne???
Nayi shiri na musamman domin fadakar da yan uwa musulmi cewa *Maulidi* bashi da Asali a cikin addinin Islama, a tare da haka sai nayi wani bincike, *Misali:* Ni ina da Abokai masu WhatsApp mutum 500+, ina da groups 100+, a Facebook ina da abokai 5000, da masu bibiya 1000+ a Facebook ina da groups, Wanda idan aka Tara mutanenshi sun kai 100,000+ bari na tsaya a haka, idan nayi posting duka wadannan zasu gani, abokanansu ma zasu gani, toh abunda Nike bukata a yanzu shine, kaima/kema kuna da WhatsApp friends da groups, me kake/kike tsammani idan kikayi copy na post din ka/kika watsa shi ga abokanka/ki???
Muyi tarayya a wurin yada alkhairi shi yafi domin mu rabauta a wurin Allah, kamar yadda sanarwa ta gabata cewa, salon da'awar a wannan karon zai chanja, taken rubututtukan shine;
ﻭَﻟِﻴَﺘَﺬَﻛَّﺮَ ﺃُﻭﻟُﻮ ﺍﻟْﺄَﻟْﺒَﺎﺏِ...
those of understanding would be reminded...
Domin masu hankali suyi tunani...
Suratu sad aya ta 29

Miye shawararku, ko goyon bayanku akan hakan???

Ina saurare domin karba, ina saran fara rubutu a 29 safar 1440AH insha Allahu

#ABBAN_SINAN
#MAULIDI
#SHAWARA
#MUKYAUTATA NIYYA

http://wa.me+2348064734911

17 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha bakwai 017_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*SUNNONIN ALWALA:*
1⃣ Wanke Hannaye Kafin A Tsoma Su A Ruwa, ta yadda mai alwala zai karkato butar alwala domin ya wanke hannayen sa zuwa  wuyan hannu.

2⃣ *Kuskurar Baki:*    
  Mai alwala ya tabbata ya sanya ruwa a bakinsa sannan kuma ya kuskure bakinsa da
ruwan.

3⃣ *Sha'ka Ruwa:*
  Shine mai alwala ya shaki ruwa ruwan ya shiga hancin sa sosai, sai dai kawai idan yana azumi ne sai yayi kadan. Amma yadda mutane suke shafar hancinsu wai da sunan shaka ruwa wannan bai dace ba, ya kamata mu gyara.

4⃣ *Facewa:*
  Mai alwala zai shaki ruwa ne da
hannun dama sai ya sa hannun hagu akan karan hancin sa, sannan sai ya fyato ruwan da
ya shaka.

5⃣ *Shafar Kunne;*
  Mai alwala ya tabbata ya shafi cikin kunnensa da wajen kunnen, zaka/ki sanya yatsanka manuniya(☝) a cikin kunnen sannan kasa babban yatsa(👍) a wajen kunnen sannan sai ka shafa.

6⃣ *Sake Taba Ruwa:*
A lokacin da zaka shafi kunne shin zaka shafi kunnen ne da ragowar
danshin hannuka da ka yi shafar kai da shi? Ko ko zaka sake taba ruwa na musamman domin
shafar kunne, malamai sun karawa juna sani, ko
wanne ka yi ya yi daidai.

7⃣ *Dawo Da Shafar Kai:*
Ka tsaya ka fahimta, shi shafar kai farilla ne, amma dawo da shafar
kai sunnah ce daga cikin sonnonin alwala.

8⃣ *Jeranto Farillai:*
Ta yadda zaka kawosu daya-bayan-daya kamar yadda aka lissafosu, kada ka dauki na uku ya zama shine na farko
sannan ka biyo shi dana biyar, misali…'.

Wadannan sunnonin matsayinsu bai kai matsayin farillai ba,
amma suna cikin manyan abubuwan da suke cika alwala.


ZAMU DAKATA ANAN SAI LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANIN *MUSTAHABBAN ALWALA* INSHA ALLAHU



WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE;
✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_)*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

16 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha shida 016_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*FARILLAN ALWALA*

1⃣ *Niyyah:*
Domin a bambance wanda ya sa ruwa domin sanyaya jiki, ko domin gusar da
datti, duk wannan ba niyya ce ta alwala ba.

2⃣ *Wanke Fuska:*
  Ita kuma fuska ta bangaren tsawo tana farawa ne daga matsirar gashin kai zuwa karkashin haba(gemu), amma
ta fuskar fadi tana farawa ne daga kunnen dama zuwa kunnen hagu, wannan shine abinda yake amsa fuska, kenan dole mai alwala ya tabbatar ko ina ya samu ruwa kamar kasan haba, gefen
ido da gefan kunne da matsa-matsin karan hanci, ayi hattara sosai domin wasu alwalarsu
kamar alwalar yarace.

3⃣ *Wanke Hannaye Zuwa Gwiwar Hannu;*
Mai alwala mace ko namiji ya tabbata ya wanke hannayensa tun daga saman yatsunsa (farce/kaifa) har zuwa gwiwar hannu ya tabbata gwiwar ta shiga inda ya wanke, anan ma akwai manyan mutane masu alwalar yara.

4⃣ *Shafar Kai:*
Ka tabbata ka hada yatsunka sannan kuma ka fara shafar daga goshi (dai-dai
matsirar gashi) sannan ka shafa zuwa keya.

5⃣ *Wanke Kafa:*
Haka nan mai alwala ya tabbata ya wanke kafarsa har zuwa idon sawu,
wato wadannan kasusuwan guda biyu dake
gefen kafafuwa sun shiga cikin inda aka wanke.

6⃣ *Cudanyawa:*
  Mai alwala ya tabbata ya cudanya duk inda ya wanke ya dirza ruwa ya
shiga ko ina.

7⃣ *Jerantawa:*
  Abinda ake nufi shine a lokacin da ka fara alwala to ka dakatar da komai sai ka kammala, amma kana alwala kana kuma wata sabga daban wannan ba dai dai bane.

Mai alwala ya tabbata ya gabatar da wadannan ayyuka a lokacin da yake alwala ta yadda idan aka rasa daya daga cikin su to alwalarka ta shiga chakwakiya.


ZAMU DAKATA ANAN INSHA ALLAHU SAI WANI LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANI AKAN *SUNNONIN ALWALA*


DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

15 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha biyar 015_

Gabatarwa; *UMMU SINAN*

*FALALAR ALWALA;*
Kasantuwar cewa alwala wajiba ce wannan kadai ya isa ka gane falalar ta a
musulunci domin dukkan abunda akace farillah ne
to wannan matsayi ne mai zaman kanshi, bayan hadisi na 62 a cikin *Muwadda Malik* yana cewa; An karbo daga Abdullahi As-Sunaabihi, lalle ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace:  *''Idan bawa mumini ya yi alwala sai ya yi kuskurar baki dukkanin laifukan dake bakin sun Wanke, idan kuma ya shaqa ruwa sai ya fyace, dukkan laifukan daya shaka sun fice, idan kuma ya wanke fuskarsa laifukan da ke fuskar ta sa sun wanke, har wadanda ke karkashin girar shi, idan ya wanke hannayensa laifukan dake hannayensa sun fice, har wadanda ke karkashin akaifarsa (farce), idan kuma ya shafi kanshi laifukan dake kan nashi sun fice har wadanda ke kunnuwansa, idan kuma ya wanke kafafuwansa duk laifukan dake kafafuwansa sun fice, har wadanda ke karkashin farcen kafafun nashi."*
Sannan kuma
tafiyar da ya yi zuwa masallaci ya zama wani
kari ne da yake da shi na lada''.
Lalle wannan bakamar falala bace da alwala take da shi, domin mai alwala zai kasance yana kammala alwala zunubanshi suna digewa a
kasa, amma wani hanzari ba gudu ba, wannan ladan zai tabbata ne ga wanda ya yi alwala a yadda shari'a ta tabbatar da ita ba wacce ya tsinta a
kan titi ba.

*SHARUDDAN ALWALA*

  Sharuddan alwala sune abubuwan da ake so mai alwala ya cika su kafin ya fara alwalar, sune kamar haka:

1⃣ *Musulunci*
  kenan idan wanda ba musulmi ba ya yi alwala bata yi ba.

2⃣ *Hankali*
Idan mahaukaci ya yi alwala itama bata yi ba.

3⃣ *Wayau*
Idan dan karamin yaro mara dabara
ya yi bata yi ba.

4⃣ *Ruwan ya zama mai tsarki*
Idan ya zama ruwa ne mara tsarki to alwalar bata yi ba, bayanai sun gabata akan hukunce hukuncen ruwa.
5⃣ *Ruwan ya zama na halas*
Idan ruwa ne da
mutum ya sata ko ya same shi bata shar'antacciyar hanya ba to alwalar bata yi ba.

6⃣ *Ya kasance mai tsarki*
  Idan mai alwala ya
kasance ya yi fitsari ko bayan gida misali wato ya kasance mara tsarki kafin alwala to ko ya yi alwalar bata yi ba.

7⃣ *Gusar da duk abinda zai hana ruwa shiga*
Kenan idan mutum ya kasance yana sanye da wani abunda zai hana ruwa ya kai ga fatar jiki to dolene ya cire shi, kamar zobe da sauransu.


ZAMU DAKATA A NAN INSHA ALLAHU SAI WANO LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANI AKAN *FARILLAN ALWALA*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

14 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha hudu 014_

Gabatarwa; *UMMU SINAN*

   Alwala ibadace mai zaman kanta
wacce Allah madaukakin sarki ya shar'anta ta
kafin gabatar da wadansu ibadu musamman ma
sallah, mutum yana samun cikakken ladan alwala idan ya yi ta cikakkiya, Allah madaukakin
sarki ya saukar da hukunce-hukuncen alwala a cikin littafinsa mai girma alkur'ani:

*''Ya ku dukkanin wadanda suka yi imani, idan kuka ta shi za ku yi sallah to ku wanke fuskokin ku da hannayanku zuwa gwiwar hannu ku kuma shafa kawunanku da kafafanku zuwa idon sawu (idon kafa)…''* [Suratu Ma'ida, aya ta: 6].

Tabbas wannan aya ta yi bayanin wajibcin alwala lokacin da za'a yi sallah, kuma ta
bayyana gabban da ya zama wajibi a wanke ko kuma a shafa, sannan kuma ayar ta iya kance
ko wanne mahalli.
       Ma'aikin Allah
–Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya bayyana siffar yadda alwalar take da maganarsa da kuma aikinsa bayanin da yake
gamsasshen bayani.

Ka sani lalle ita wannan alwala tana da falala da kuma sharudda da kuma farillai sannan tana da sunnoni da kuma mustahabbai, sharuddan nan
da farillai tabbas a tabbata mun sansu alokacin gabatar da alwala iya gwargwado domin da sune alwala zata zama karbabbiya, amma su sunnoni da mustahabbai suna cika alwalarne ta inda matsayinsu bai kai matsayin farillai ba.

ZAMU DAKATA A NAN INSHA ALLAHU SAI WANI LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANI AKAN *FALALAR ALWALA*

DOMIN SHIGA GROUP DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613