Thursday, 30 January 2020

004 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_004_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *SABUBBAN DA KE JANYO YANKE ZUMUNTA.*

   Idan kayi nazari akan sabubban dake janyo yanke zumunta zaka samu cewa akwai sabubba masu yawa. Ga kadan daga cikinsu
1. *JAHILCI:* Jahiltar mummunan sakamakon da mai yanke zumunta yake samu anan duniya da lahira, ko kuma rashin yin aiki da abin da mutum ya sani. An karbo daga Umar (R) ya kasance akan mimbari yana cewa: ku nemi sanin dangantakarku, sannan ku sadar da zumuntarku wallahi! Lallai zai kasance tsakanin mutum da dan uwansa wata rigima ta hadasu saboda rashin sanin juna, da yasan akwai zumunta tsakaninsu da wannan dalilin na alakar zumunta ya hanashi cin mutuncinsa *(Bukhari, Adabul mufrad 73)*

2. *KARANCIN TSORON ALLAH;*
  Idan tsoron Allah yayi rauni sannan addini yayi saku-saku ba zai damu ba idan ya yanke abin da Allah yayi umarnin asadar, kuma baya kwadayin ladar da ake samu idan an sadar da zumunta kuma baya tsoran mummunan sakamakon da zai same shi a dalilin yanke zumunta.
An karbo daga sa’id bn sam’an, yace: Naji Abu Hurairah yana neman tsarin Allah daga shugabancin yara da wawaye (jahilai) sai aka ce masa mine ne alamar yin haka? sai yace dan za’a dinga yanke zumunta a kuma dinga yin da’a ga mai halakarwa a saba ma mai shiryarwa *(Adabul-mufad 66)*

3. *GIRMAN KAI;*
  Sashen mutane idan mutum ya samu wani matsayi babba ko ya samu wata daukaka ko kuma ya zama babban dan kasuwa sai yayi girman kai ga yan'uwanshi, ya kyamaci ziyartarsu, kuma ya kyamaci zuwa garesu, yana ganin shi ke kan gaskiya kuma shi ya can-canta a ziyarta.

4. *YANKEWA MAI TSAWO;*
A nan akwai wanda yake yanke ma yan'uwansa lokaci mai tsawo al’amarin ya dore akan haka har ya kai ga yanke zumuntarshi dasu gaba daya, har ya saba da yankewa sai yayi nesa dasu. An karbo daga Mikdam, lallai yaji manzon Allah (SAW) yana cewa lallai Allah yana maku wasiyya da iyayenku mata sannan yana maku wasiyya da iyayenku maza, sannan yana maku wasiyya da yan'uwanku *(Adabul mufrad 60)*

5. *AIBANTAWA MAI TSANANI;*
Sashen wasu mutane idan dan'uwansu ya ziyarcesu bayan a baya ya yanke zumuntarshi dasu lokaci mai tsawo sai su yawaita zar ginshi har zargin yayi tsanani wanda wannan sai yasa shi kaurace masu saboda tsoron mummunan zargi da suke mashi.

6. *DORA MA RAI NAUYIN DAYA WUCE QA’IDA;*
A nan akwai wanda idan dan'uwansu ya ziyarcesu sai su dora ma kansu yin hidindimu da suka wuce karfinsu domin su ga cewa sun karrama dan'uwan nasu sama da karfinsu ko karancin abun hannunsu, wannan shi ke sanya yan'uwan nasu su dinga takaitawa da ziyartarsu domin tsoron kada su dora masu ire-iren wadannan nauye-nauyen. Saboda Annabi yace mafi karancin sadar da zumunci shine sallama mafi girman zumunta shine  sadarma wanda ya yanke maka.

7. *KARANCIN KULA DA WADANDA SUKA KAWO MAKA ZIYARA;*
  Akwai daga cikin mutane wanda idan yan'uwanshi suka ziyarceshi baya bayyanar da farin cikinsa akan ziyarar, bai tsayawa ya tattauna dasu ko ya sakar masu fuska, sai dai za ka ga yana bata rai yana kyamarsu, wannan yana zama sanadin yan'uwa ba zasu kara ziyartarshi ba dan tsoron irin wannan wulakancin.
Manzon Allah yace, kada ku wulakanta wani abu na alkhairi ko da sakin fuskane idan ka hadu da dan'uwanka.

8. *TSANANIN ROWA;*
  Wasu daga cikin mutane idan Allah ya azurtasu da dukiya mai yawa ko wani matsayi zaka same su suna gudun yan'uwansu, ba wai dan girman kai ba a'ah! Domin jin tsoron kada yan'uwan suyi amfani da wannan damar domin bayyanar da bukatunsu zuwa garesu, ko kuma domin kada ya temakesu. Maimakon ya basu dama idan sun ziyarceshi yakarbi bakuncinsu, ya yalwata masu, yayi masu hidima gwargwadon halinsa,ko kuma ya basu uzuri akan abin da ba ya da ikon yi masu amma sai kaga yana kauda kansa, yana kaurace masu domin kada su rokeshi kamar yadda yake riyawa. Mine ne amfanin dukiya ko matsayi da mutum zai samu idan har zai haramta ma yan'uwansa amfana da ita.
9. *JINKIRIN RABON GADO;*
Hakika zaka samu wasu daga cikin mutane suna jinkirta rabon gado kodai  domin kasala, ko kuma wani daga cikin magadan yana da wani mummunan kuduri game da yan'uwansa ko makamacin haka.
Duk lokacin da aka jinkirta rabon gado to kiyayya da adawa zata watsu tsakaninsu domin idan wannan yana da hali ko yafi karfin gadon wani shi kuma yana bukatar raba gadon domin bashi na shi kason ya samu ya bude kasuwanci ko makamanci haka.

10. *MUTUWAR AUREN ZUMUNCI;*
  Hakika mutuwar auren zumunci yana haifar da matsaloli a tsakanin yan'uwa na bangaren miji dana bangaren mata musamman in akwai 'ya'ya a tsakaninsu ko kuma saboda wasu matsaloli da suka shafi sakin auren.

A NAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI CIGABAN *SABUBBAN DAKE JANYO YANKE ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN
https://fb.me/abbansinan

003 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_003_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *HADARIN  DA KE CIKIN YANKE ZUMUNTA*

Hakika Allah (SWT) da manzonsa (SAW) sun tsoratar dangane da hadarin yanke zumunci, suka sanya matsayin yanke zumunci dai dai da Fasadi/barna a bayan kasa.
Allah (SWT) yace to shin kuna fatan idan kun juya daga (umarnin) zakuyi barna a cikin kasa, kuma ku yanke zumuntarku? Wadannan sune wadanda Allah ya la'anesu, kuma ya kurmantar dasu, kuma ya makantar da ganinsu. *(Suratu Muhammad 22-23)*

An karbo hadisi daga Aisha (R) manzon Allah (SAW) yace zumunta tana rataye da al’arshin Allah. Tana cewa wanda ya sadar dani Allah ya sadar dashi, wanda ya yanke ni Allah ya yankeshi *(Muslim 2555)*
An karbo daga MUD’IM (R) manzon Allah (SWA) yace mai yanke zumunta baya shiga Aljanna *(Muslim 2556)*
Haka nan kuma, an karbo  daga Abubakrata, Manzon Allah yace, Babu wani laifi daya can-canta Allah ya gaggauta ma ma'abocin sa uquba tun anan duniya tare da  cewa yayi mashi tanadin uqubar a lahira kamar wanda ya yanke zumunta da kuma azzalimi *(Bukhari adabul mufrad 67)*
An karbo daga Abu Huraira; lallai wani mutum yace ya manzon Allah lallai ni ina da yan'uwa kuma ina sadar da zumuntarsu amman suna yanke mani, ina kyautata masu amma suna munana mani, ina yin hakuri dasu amma suna jahiltata? Sai Annabi yace, idan har ka kasance kamar yadda ka fada to lallai kamar kana zuba masu toka ce mai zafi, Allah ba zai gushe ba yana taimakonka akansu matukar ka dauwwama akan haka *(Muslim 2558)* Ma’ana: kamar kana ciyar dasu toka mai zafi saboda abin da suke haduwa dashi na laifi.
Haka nan kuma an karbo daga Abdullahi ibn Amru binul As, Manzon Allah (SAW) yace, bai zama mai sadar da zumunta ba wanda yake so aranka mashi, sai dai mai sadar da zumunta shine wanda idan an yanke mashi, shi yana sadarwa *(Bukhari 541)*
An karbo daga salmanu ibn Amir, Manzon Allah yace, yin sadaka ga miskinai sadakace kamar sauran sadakoki, amma yin sadaka ga dan'uwa tana da darajoji biyu (2) ladar sadaka da kuma ladar sadar da zumunci *(Abu Dawud 2555 da Tirmidhi 658)*
An karbo daga Abu Hurairah yace, lokacin da wannan ayar ta sauka,,, kayi gargadi ga yan'uwanka makusanta, Annabi (SAW) ya kira Quraishawa, suka hadu gaba dayansu, yayi musu wa’azi gaba dayansu kuma yayi ma dai-dai kunsu yace ya Fatima ki tsamar da kanki daga wuta, lallai ni bani wadatar daku a wurin Allah da komai sai dai lallai kuna da wata zumunta da sannu zan sadar da ita *(Muslim)*

ANAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI *SABUBBAN DAKE JANYO YANKE ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868
DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN
https://fb.me/abbansinan

KARATUTTUKAN MASALLACIN ABU HURAIRAH TSAFE

*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE*

Wannan Masallaci karkashin kwamitin social media na masallacin sunyi kokarin tattara karatuttukan da *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)* yake gabatarwa a wannan Masallaci har kusan littafai *36* gasu kamar haka:

1. *Aqeedatud dahawiyya*

2. *Ahkamul idaini*

3. *Alfurqan baina auliya'allahi wa'auliya'ish-shaidan*

4. *Ahkamul uduhiyya*

5. *Al'imamu wa'af'alihi*

6. *Al'ilmam, bi'ahkami wadabus siyam*

7. *Aljawabul khafi*

8. *Alwajibatul mutahattimatul ma'arifah.*

9. *Bugyatul mushtak*

10. *Bulugul maram*

11. *Daura- akan Magunguna da ruqya*

12. *Daura- akan Maulidi*

13. *Hisnul Muslim*

14. *Hiqbatun minat-tarikh*

15. *Hudubobi guda 166*

16. *Imani haske*

17. *La'ilaha ilallah*

18. *Manasikul hajji*

19. *Mayatamayyazu bihil muslimu anil mushrik*

20. *Mu'amalatul hukkam*

21. *Muhadarori*

22. *Nabiyur Rahma*

23. *Qa'idatul jalila*

24. *Ru'usul aqlam*

25. *Riyadus saliheen*

26. *Ramadhan Tafseer, 2007,10,13,16,17,18, da 2019*

27. *Salatut Tarawih*

28. *Sahihul bukhari*

29. *Shama'ilul Muhammadiyya*

30. *Sifatu saumun Nabiyy, kala biyu*

31. *Tarbiyatul aulad, kala 3*

32. *Tafseer weekly na ibn Katheer*

33. *Tuhfatul iraqiyya*

34. *Usulul iman*

35. *Usulus salasa*

36. *Wasiyyatul kubrah*

37. *Aqeedatul wasidiyya na (ibn taimiyya).*

38. *Adabuzzifaf na (Albany)*

39. *Fadlul Islam na (Muhammad bn abdulwahab)*

40. *Nawaqidul Islam na(Muhammad bn Abdulwahab)*

41. *kitabuttauhid na (Muhammad bn abdulwahab)*

42. *kitabuttauhid na (sheikh salhul fauzan)*

43. *Albida'ah*

44. *Sharhin sunnah na (Barbahary)*

45. *Kama takunu yuwalla alaikum na (dr. Ramadani)*

46. *Jilbabul m ar'atil Muslima na (Albany)*

47. *Huququn da'at ilaiha fidra waqarrarat'ha shari'a na(sheikh uthaimin)*

48. *Siyamu Ramadan*

49. *Qiyamu Raman.*

50. *Ahkamul jana'iz na (Albany)*

51. *Tafsirul kalimatul shahada.*

52. *Sifatus salatin nabiyy na (Albany)*

53. *Sharhi masa'ilil  jahiliyya na (Muhammad bn Abdul wahab)*

54. *Auradu ahlussunah.*

55. *Tabyini kazibul muftary bima nusiba ila ibn taimiyya na (M Kabir Maru).*

zamu cigaba da kawo wadan da muka tuna  daga baya insha Allahu

Wannan kwamiti na Nan na kokari kafin zuwa Ramadan za'a gabatar maku da 16GB memory card Mai dauke da Wadannan karatuttukan da ma wasu wadanda bamu shigar ba a Nan.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi

#MABUHURAIRAHTSAFE_SOCIAL_MEDIA

005 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_005_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *CIGABA DA BAYANI AKAN SABUBBAN DA KE JANYO YANKE ZUMUNTA.*

11. *NISAN WURIN ZAMA DA KUMA KASALAR ZUWA ZIYARA*
Akwai daga cikin mutane wadanda idan gidan su ko garin su yana nesa sai a dinga jin kasalar zuwa ziyartarsu, wanda wannan sai ya nisantasu da yan'uwansu.
Nisan wuri bai kamata ba ya zama dalili na yanke zumunta, musamman wannan zamanin da ake da hanyoyin sadarwa daban daban, Allah ya bamu ikon kulawa da zumunta.

12. *MAKWABTAKA A TSAKANIN YAN UWA*
Da yawa Makwabtaka tana gadar da yankewar zumunta a tsakanin yan'uwa. Umar Dan khaddab yace ku umurci yan'uwanku su dinga ziyartar yan'uwansu amma kada suyi makwabtaka da juna a gidajensu, sannan sau dayawa kusanci a tsakanin gidajen yan'uwa yana haifar da sashen wasu matsaloli wadanda suke haifar da fada a tsakanin 'ya'yansu wanda wannan yakan zarce har zuwa ga iyayensu sai wannan ya haifar da gaba da yanke zumunci a tsakaninsu.

13. *KARANCIN KAUDA KAI DA HAKURI A KANSU:*
Sashen wasu mutane suna da karancin kauda kai da kuma hakuri akan abin da yan'uwansu suka yi masu. Wasu yan'uwan da an samu sabani tsakaninsu ko wani kuskure da ya afku sai su yanke zumunta, su kaurace ma yan'uwansu.

14. *HASSADA:*
   Akwai daga cikin yan’uwa wanda Allah yake azirtawa da ilimi ko wani babban matsayi ko dukiya mai yawa sai ka same shi yana yima yan'uwansa hidima yana kyautata ma su, sannan ka samu sashen yan'uwansa suna nuna masa hassada da kiyayya da haifar da rikici tsakanin shi da su, suna cewa duk abin da yake yi masu ba domin Allah yake yi ba.

15. *YAWAN WASA:*
Lallai yawan wasa (da sunan wai abokin wasa) yana haifar da mummunan abu a tsakanin yan'uwa domin wani yana iya fadar kalma mai muni ga dan'uwansa ba tare da ya kula da hadarinta ba agare shi, wannan sai ya gadar da kiyayya da gaba a tsakaninsu a sanadiyyar wannan Kalmar.

16. *ANNAMIMANCI DA KARBAR GULMA:*
Akwai da yawa daga cikin yan'uwa wadanda dabi'arsu shine yawo da annamimanci a tsakanin yan'uwa domin su kawo rabuwar kai da gurbata tsakanin yan’uwa wanda wannan yana gadar da yanke zumunta, sai dai abu mafi muni shine karbar gulma da yadda da ita shi ke haifar da yankewar zumunta.

17. *SHAGALTUWA DA DUNIYA:* Shagaltuwa da duniya da son yawan tara abin duniya yana hana mutun sadar da zumunta, da kuma samun lokacin ziyartar yan'uwansa da nuna soyayyar shi zuwa gare su.

18. *MIYAGUN HALAYE NA MATAR SHI:*
Wasu daga cikin mutane ana jarabtarsu da muguwar mata mai mummunan dabi’a mai yawan sukar yan'uwansa, bata son yayi mu’amala da yan'uwansa ko wasu, tana dogewa wajan ganin ta raba shi da yan'uwansa tana hana shi ziyartarsu, da sadar da zumunta zuwa garesu, idan yan uwan sa suka ziyarceshi sai tayi ta fushi tana murtike fuska. Bugu da kari akwai mazajen da suke mika ragamar zumuncinsu ga matarsu sai wanda ta yarda dashi yake sadarmawa, wanda bata yarda da shi ba sai ya yanke ma sa.

19. *MANTAWA DA WASU YAN'UWA A LOKACIN WALIMA KO WATA HIDIMA:*            Hakika wani daga cikin yan'uwa yakan shirya walima ko wata hidima ya gayyaci yan'uwansa sai ya manta da wani ko wasu, sai su da ba’a gayyata ba su munana masa zato, su nuna kamar an wulakantasu an zabi wasu wadanda suka fisu, wannan  nasa ya kaurace masu da yanke zumunta a tsakaninsu.
Wadannan sune  kadan daga cikin abubuwan dake janyo kauracewa juna da kuma yanke zumunta. Ya kamata a basu kulawa ta musamman da hattara da fadawa cikinsu.

A NAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI *ABUBUWAN DA SUKE TAIMAKAWA WAJAN SADAR DA ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN

https://fb.me/abbansinan

LADUBBAN NEMAN ILIMI DA BADA ILIMI

*KWAMITIN HARKOKIN ADDINI DA ZAMANTAKEWA NA MASALLACIN ABU HURAIRAH TSAFE*

*LADUBBAN NEMAN ILIMI DA BADA ILIMI*

✅ *IKHLASI:*
yi don Allah, mai neman ilimi da malamin dake bada ilimi ya zama dukan su sunayi don Allah, domin neman yaddar Allah. Rasulullahi (S.A.W) yace "Duk wanda ya nemi ilimi don neman yaddar Allah, daga baya ya canza niyarsa don neman duniya, ba zaiji kanshin Al-Janna ba" *(Abu Dawuud: 3664)*

✅ *NIYYAR DAUKE JAHILCI:*
  Duk wanda zai nemi ilimi ko zai bada ilimi ya zamanto don ya dauke ma kansa jahilci da waninisa. Imam Ahmad Bin Hambali Yace "Shi ilimi babu abun dake dai-dai dashi ga daraja musamman ga wanda ya kyautata niyar sa". Dalibansa sukace kamar yaya? Yace "Wanda yayi da manufa (Niyar) ya dauke makansa jahilci ko waninsa"

✅ *NEMAN ILIMI DA MANUFAR KARE ADDINI:*
  Ya kamata ga mai bada ilimi ko dalibi ya kasance da manufar ba addini kariya ya keyi, Rasulullahi (S.A.W) yace: "Yaku wanda sukayi imani ku kasance masu taimakon addinin Allah, *Q: Suratul Saffi;14".*

✅ *AIKI DA ILIMI:* Na daga cikin ladubban ilimi ga malami da dalibi aiki da  ilimi Rasulullahi (S.A.W) yace Alqur'ani hujjane gareka ko akan ka” *(Muslim: 223)* hujjane gare ka in kayi aiki dashi kashiga Aljanna. Akan ka in bakayi aiki dashi ba ka shiga wuta.

✅ *HAKURI:*
Dole ne malami da mai neman ilimi suyi hakuri: malami yayi hakuri wajen bada ilimi, dalibi yayi hakuri wajen neman ilimi. Hakuri kan neman ilimi ya kasu gida ukku (3):

1. Hakuri da talauci da yinwa

2. Hakuri akan dagewa har sai ka samu

3. Rashin yanke kauna ga abin da kake nema

Imam Ahmad bin Hambali yace Na shekara tara (9) ina karatun *Kitabul Haid* har saida na gane shi

✅ *TAWALIU DA NISANTAR GIRMAN KAI:*
Ana son malami da dalibi su sanya tawali'u da nisantar girman kai ga abin da suke nema. Imam Mujahid yace Mai girman kai ko mai kunya baya samun ilimi.

✅ *TAFIYA DON NEMAN ILIMI:*
Wajibi ne ga malami ko dalibin ilimi da suyi tafiya don neman ilimi musamman ilimin da babu a  inda suke. Rasulullahi (S.A.W) yace Neman ilimi wajibine ga dukkan musulmi” *(Muslim)*

✅ *RASHIN KARBAR ILIMI GA DAN BIDI'AH:*
Bai halitta ga dalibi ya nemi ilimi ga dan bidi'ah, yan bidi'ah sune wadanda suke saba ma gaskiya kuma suka kirkira abubuwan da musulunci bai zo dasu ba, kamar: Yan shi'ah, Khawarij, da sauran darikun Sufaye.
Muhd Bin Sirin yace: Kada ku kuskura ku zauna da yan bidi'ah kada kuyi karatu garesu kar ku sauraresu domin Ahlis-sunnah sunyi ittifaki a kaurace masu da kuma nesa dasu”.

Allah ya bamu ilimi Mai amfani Kuma Mai albarka 🤲🤲🤲

*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA COMMITTEE*
+2348064734911
https://fb.me/masjidabuhurairahtsafe

Friday, 10 January 2020

021 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_021_

RASHIN LAFIYA (CIWO)

Ciwo daga Allah ya ke babu wanda ya fi qarfin Allah ya jarrabe shi da ciwo ko wane iri ne, in muka bibiyi tarihi za mu ga bayin Allah da dama sun yi fama da rashin lafiya ba don kome ba sai dai don Allah ya daukaka darajarsu da kuma kankare ma su zunubansu. Gwargwadon imanin mutum gwargwadon yadda Allah zai jarraba shi. Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya gaya mana cewa girman lada na tare da girman jarrabawar da Allah ya jarrabe ka da ita, haqiqa idan Allah ya so wasu mutane sai ya jarraba su (da wata cuta), wanda ya yarda da hukuncin Allah to yana da yarda, wanda ya yi hushi to yana da sakamakon fushinsa.
[Tirmidhi ya ruwaito]

Don haka ciwo ba abin zargi ba ne domin akwai wani sakamako wanda Allah ya ke bai wa wanda ya yi ciwo,
haka ma’aiki sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya fada mana a wani hadisi da aka samo daga Anas Allah ya qara masa yarda ya ce, “Manzon Allah sallal Lahu Alayhi wa alihi wa sallam ya ce, ‘Idan Allah ya so bawansa da alheri sai ya sa masa wata cuta (uquba) a nan duniya, amma idan Allah ya nufi bawansa da sharri sai ya qyale shi da zunubinsa har ya cika masa da shi ranar qiyama.’”
[Tirmidhi ya ruwaito]

Wannan magana ta manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ta nuna mana ashe duk wanda ciwo ya same shi ya yi haquri ba kansa ne farau ba, manyan mutane su ma sun yi ciwo na tsawon lokaci mai tsawo, misali kamar Annabi Ayyub da Allah ya gaya mana ya yi ciwo na tsawon lokaci wanda har ya kai na shekara 18 ba ya fita saboda ciwo, wanda har ya kai ga gaba dayan dukiyarsa ta qare ‘ya’yansa duk suka mutu baki dayansu saboda tsananin ciwo, sai da ta kai gaba dayan jikinsa ba ya amfani sai zuciyarsa kawai, wasu malaman tafsirin ma cewa suka yi sai da ya kai jikinsa ya kasance yana yankewa yana faduwa qasa. Wata rana matarsa ta ce masa ya roqi Allah ya ba shi lafiya mana, sai ya ce shekarata saba’in lafiyata lau amma in kasa haquri da rashin lafiya ta shekara sha bakwai? [IBN KATHER]

ﺍﻟﻠﻪ ﺃَﻛْﺒَﺮُ
Bayin Allah ke nan shekara da shekaru suna fama da rashin lafiya amma suka yi haquri, haka aka san bayin Allah cikin haquri ko da yaushe.

Kusan idan muka bibiyi tarihi zamu ga yadda Allah Ya ke jarraba bayinsa da cututtuka ba don komai ba sai don Ya qara masu daraja da daukaka. Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa salam ya yi ciwo, haka shi ma babban sahabinsa Abubakar shi ma haka, haka shi ma Imam Malik ya yi rashin lafiya har ya kai ba ya zuwa masallaci sai a gidansa yake yin sallah,haka ya mutu cikin wannan rashin lafiya. Allah Ya rahamshe shi amin. Shi ma dalibinsa Imamu Shafi’i ya yi rashin lafiyar da ta kai in ya hau doki jini na zuba a duburarsa, har ya cika masa huffinsa (takalminsa). A qarshe dai ina mai cewa ciwo ko rashin lafiya daga Allah ne kuma ba abin zargi ba (ba aibu ba ne) ne domin jarrabawa ce daga Allah, kuma akwai sakamako mai yawa ga wanda ya yi haquri kuma ya miqa al’amarinsa ga Allah. Imam Ahmad shi ma ya yi ciwo mai tsanani har ta kai ga yana nishi da qyar, kuma a cikin wannan ciwon ya rasu Allah Ya rahamshe shi amin.
Ana so mara lafiya ya yi haquri da cutar da ta same shi ya miqa lamarinsa ga Allah kuma ya yi haquri, babu abu mafi tsada fiye da Allah Ya ba ka haquri, kuma Allah Ya yabi masu haquri a cikin littafinsa kuma Ya yi ma su bushara da lada mai yawa kuma Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya fadi irin falalar haquri, shi mumini duk abin da ya same shi lada ne.
Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya ce, “Abin sha’awa ga al’amarin mumini komai nashi lada ne. Idan abin farin ciki ya same shi ya gode wa Allah alkhairi ne a gare shi, in kuma abin baqin ciki ko damuwa ya same shi ko ciwo ne ya yi haquri alkhairi ne a gare shi.” [Muslim]
Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce wanda Allah ya nufe shi da alkhairi sai ya sanya ma shi wata cuta. [Bukhari da Muslim]
Babu wata damuwa ko baqin ciki ko ciwo ko wani abu mai cuta da zai sami mumini face lada ne a gare shi. Har qaya idan ya taka face Allah Ya kankare masa kurakuransa. [Bukhari da Muslim]
Ibn Mas’ud ya shiga wajen Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya taras da shi yana zazzabi, sai ya ce ma shi, “ Ashe kai ma kana zazzabi zazzabi mai tsanani haka?” Sai Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce, “Haka ne abin yake, ni ciwon mutane biyu nake yi.” Sai Ibn Mas’ud ya ce, “Kana nufin kana da lada biyu ke nan?” Sai Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce, “Na’am.” Sannan
sai ya ce, “Babu wani ciwo ko qaya da zai sami musulmi face Allah ya kankare masa munanan ayyukansa kamar yadda itaciya take kakkabe ganyayen ta. [Bukhari da Muslim]

Zamu dakata anan, idan Allah ya kaimu wani sati zamu cigaba Insha Allahu.

Wannan duka yana zuwa muku ne a cikin littafin: *HUKUNCE HUKUNCEN JANAZA A MUSULUNCI* Wallafar: _Malam Haruna Abubakar Shika._

MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA* SAI SU TURA CIKAKKEN SUNA DA GARI ZUWA GA
+2349030201868 A WHATSAPP

Https://fb.me/abbansinan

022 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_022_

*LADDUBAN ZIYARAR MARA LAFIYA DA ABIN DA KE KAN MAI JINYA DA LIKITA DA AN GUWAR ZOMA.*

Kamar yadda muka gani a baya cewa ciwo daga Allah yake kuma ciwo kaffara ne na zunubai, kuma mun ga cewa hatta
manya-manya daga cikin bayin Allah
sun yi ciwo. Musulunci ya koyar da komai domin hatta yadda a ke zuwa ziyarar/gaida mara lafiya manzon sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya koyar da mu ladubban zuwa ziyarar/gaida da mara lafiya. Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa aihi wa sallam ya kasance yakan je gaida mara lafiya kuma hadisi ya tabbata daga manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam da ya ke nuna mana idan mutun ba shi da lafiya yana da haqqi a kanka na ka je ka gaishe shi, muddin ba ka je ba ka tauye masa haqqinsa. *[Muslim]* Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya ce, “Ku gaishe da mara lafiya Musulmi, ku ciyar da abinci,ku ‘yanta wuyaye.” *[Bukhari]*
Hakqin Musulmi ga Musulmi guda shida ne: Idan ya haxu da shi ya yi masa Sallama, idan ya kira ka ka amsa ma shi, in ya nemi ka yi masa nasiha ka yi ma shi, in ya yi atishawa ya kuma ce Alhamdu lil Lah, ka gasshe shi, in ya yi rashin lafiya ka je ka gasshe shi. Ya ce mai gaida Mara lafiya yana tafiya a gavar
Aljanna ne har ya je ya dawo. *[Bukhari]*

Ga ladubban kamar haka;

*NIYYA  KYAKKYAWA:*

Domin dukkan ayukka ba sa ingantuwa sai da niyya. Ana so niyyar ta zamanto kyakkyawa koda yaushe, mai zuwa ziyarar mara lafiya ana so ya yi niyyar zuwa gasshe da mara lafiya domin Allah ba wai don wani abu ba, a’a ya je ne domin samun lada wajen Allah, haka Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ambaci lada mai yawa ga wanda ya je gasshe da mara lafiya domin Allah. *[Muslim 268 da Abu Daud 3569]*

*NEMAN IZINI:*
Ana so ka nemi izinin mara lafiyan kafin ka shiga wajensa kamar yadda ya zo cikin Sahihul Bukhari Ibn Abbas ya nemi izinin shiga wajen Nana A’isha Allah ya qara mata yarda lokacin da ba ta da lafiya kafin ya shiga.  *_(Yana da kyau ‘yan‘uwa su kiyaye shiga gidajen jama’a, wannan bala’i ne kuma laifi ne shiga gidajen jama’a ba tare da izini ba, ko da ka yi sallama sai ka jira an ba ka izini kafin ka shiga, haka Annabi sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya koyar da mu. Haka nan ma haramun ne qanin miji ya shiga xakin matar wansa sai da izinin yayan nasa, idan kuma baya nan to haramun ne kai qaninsa ka shiga xakin matar. Allah ya ba mu ikon gyarawa amin)._*
Kai ma ana so ka nemi izinin mara lafiya kafin ka shiga wajensa ko da kuwa a asibiti, yayin da Ibn Abbas ya je gaishe da Nana A’ishatu Allah ya qara mata yarda, da ya je ya nemi izinin shiga sai ta ce kada ya shigo, sai aka gaya mata Ibn Abbas ne fa dan baffan Annabi sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam, sai ta ce kada dai ya shigo, da aka matsa mata sai ta ce, “Ina tsoron in ya shigo zai yabe ni, amma ya shigo. Da ya shigo sai ya ce mata, “yaya jiki?” kamar dai yadda a ka koyar da su, sai ta amsa da cewa, “Muna fatar rahamar Allah kuma muna tsoron azabarsa.” Sai Ibn Abbas ya ce, Haba ke da kike matar Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam! Ke ce fa wadda Annabi ya fi so, kuma ke ce wadda aka saukar da aya kaza da kaza saboda ita.” Ya yi ta gaya mata kyawawan ayyukanta. sai ta ce, “Da ma abin da na ke tsoro ke nan na ce kada ka shigo, da ma na san sai ka yabe ni sai ka yi ma ni Kirari.” *[Bukhari]*
Shi Ibn Abbas ya yi abin da Annabi
sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya yi umurni ne da a yi wa mara lafiya, ita kuma ta yi tawali’u ne kuma da ma tawali’u hali ne na mutanen kirki, don haka babu kyau a rinqa tuna wa mara lafiya munanan ayyukansa, haramun ne a je ziyarar mara lafiya kana a riqa tuna masa munanan ayyukansa.
Abdullahi ibn Umar lokacin da ya ke ciwon ajali Hajjaj ibn Yusuf As Saqafi ya nemi izinin ya shiga ya gaishe shi, sai
Abdullahi ibn Umar ya ce a ce masa ba ya so, ya taqura sai ya shiga, da ya shiga ya yi sallama Abdullahi bn Umar ya yi banza da shi. *_(Hajjaj bn Yusuf saqafi shi ne ya sa aka soki Sahabi mai daraja Abdullahi bn Umar Allah ya qara masa yarda da wani masoki mai dafi, ba don komai ba sai don zalunci da mugunta, Abdullahi bn Umar ya yi wa Hajjaj magana ne ranar juma’a a kan ya tsananta wa jama'a wajen huduba har la’asar, sai ya sa aka soke shi. Wannan sukar ce ta zama sanadiyyar Rasuwar sa. Bayan an soke shi ne daga baya ya zo gaishe shi don yaudara, sai shi kuma Abdullahi bn Umar ya ce ba ya so, shi ya sanya Shamsudden Zahabi a cikin littafinsa Siyar ya fadi miyagun maganganu a kansa ba don komai ba sai don ya kashe sahabai da bayin Allah nagari har a qarshe yake cewa, “Muna qin sa ne saboda Allah ya ce ’’ mugu dan ta’adda azzalumi dan kama karya jabberi’’ ya dai sossoke shi. Mai karatu yana da kyau ya karanta tarihinsa a cikin SIYAR A’ALAMUN NUBALA shafi 343/4)._*
Bukhari ma ya kawo magana mai kama da wannan da ke nuna ladabin zuwa
ziyarar mara lafiya.
Dattijon arziqi mafifici mai daraja a bayan qasa bayan manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam
Abubakar Siddiq, shi ma ya nemi izinin shiga ya gaishe da Nana Fatimatu Allah ya qara ma ta yarda lokacin da ba ta da lafiya, ya yi sallama Sayyina Ali dan Abi Dalib Allah ya qara ma sa yarda ya fito sai ya ce masa ya nema ma sa izinin shiga ya gaishe da Nana Fatimah, sai Ali ya shiga ya gaya ma ta Abubakar yana neman izinin ya shigo ya gaishe ta, sai ta ce ya shigo, shi kuma ya shiga ya gasshe ta.
Ana so mai zuwa ziyarar mara lafiya ya nemi izinin shiga kafin ya shiga wajen mara lafiya.

ANAN ZAMU DAKATA, A GABA ZAMU CIGABA DA BAYANI AKAN LADDUBAN ZIYARAR MARA LAFIYA INSHA ALLAHU.

Wannan duka yana zuwa maku ne a cikin littafin: *HUKUNCE HUKUNCEN JANAZA A MUSULUNCI* Wallafar: _Malam Haruna Abubakar Shika_

MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA* SAI SU TURA CIKAKKEN SUNA DA GARI ZUWA GA +23430201868 A WHATSAPP

https://fb.me/abbansinan

022 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

Monday, 6 January 2020

JILSATIL ISTIRAHAH DA HUKUNCIN TA A CIKIN SALLAH

🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*JILSATIL ISTIRAHA  DA HUKUNCIN TA A CIKIN SALLAH*
💐💐💐💐💐💐💐💐💐💐

Rubutawa: *ABBAN SINAN ATS~TSAMAWY*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, muna gode masa, muna neman taimakonsa, muna neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk Wanda Allah ya shiryar babu Mai batar dashi, Wanda Kuma ya batar babu Mai shiryar dashi. Kuma na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya, Kuma na shaida cewa Annabi Muhammad S.A.W bawan Allah ne Kuma Manzonsa ne.

Bayan haka:

Yaa Kai Dan uwana Kuma masoyina:

Wannan matsalar tana daga cikin mats'aloli Wadanda keda ala'ka da Sallah, wato(jilsatil istirahah), malamai sunyi sabani(Allah yayi masu rahama 👏) akan hukuncinta, da hukuncin wasu mas'aloli dake da ala'ka da ita.
Kowanne daga cikin malaman yana da dalilai akan abin da ya tafi akan shi.

Saboda haka a Matsayin ka na musulmi kayi addini da addinin Allah madaukakin sarki akan abin da yake na dai dai, kada ka dauki Ta'assubanci da ta'kalidanci don kawai kana son kayi sabani da yan uwanka musulmi akan abin da ijtihadinsu ya lurar dasu Kuma zuciyarsu ta natsu dashi.

*MI AKE CEWA JILSATIL ISTIRAHAH?*

*Jilsatil istirahah:* Wani zama ne gajere da Mai Sallah keyi bayan ya dago daga sujada ta biyu a Raka'ar farko kafin yayi yunkurin tashi zuwa ga Raka'a ta biyu da kuma bayan dagowa daga sujada ta biyu a Raka'a ta uku kafin yunkurin tashi zuwa Raka'a ta hudu, babu wani zikiri kebantacce da ake yi a lokacin zaman.

Abin da ake nufi shine; idan Mai Sallah ya kare Raka'a ta farko, yayi nufin tashi domin kawo Raka'a ta biyu, kafin ya tashi zai zauna zama dan kadan Sannan ya tashi, haka idan ya kare Raka'a ta uku yayi nufin tashi domin kawo Raka'a ta hudu, sai ya zauna zama dan kadan Sannan ya tashi.

Ana Kiran wannan zaman: *جلسة الأوتار* wato zaman wutiri, saboda Yana kasancewa bayan Raka'o'in wutiri(Ta farko da ta uku) a cikin Sallah.

*HUKUNCIN JILSATIL ISTIRAHAH*

Malamai sunyi ittifaqi akan cewa jilsatil istirahah ba ta daga cikin abubuwan da suke wajibi a cikin Sallah.
Sai dai sunyi sabani akan hukuncinta, shin Sunnah ce ko kuwa? Wannan har ya kaisu ga maganganu guda uku.

*NA FARKO:*
Sun tafi akan cewa Sunnah ce mustahabbiya, wannan shine mazhabin shafi'iyyah akan zance Wanda yafi shahara.
Imamun nawawy(R) yake cewa: Da wannan ne Malik bnul huwairith da Abu Humaid da Abu Qatada, da wasu jama'ah daga cikin sahabbai(ALLAH YA YARDA DASU) suka tafi akanshi, haka Abu Qilabah da waninshi a cikin tabi'ai duk suna akan wannan fahimta.
المجموع، شرح المهذب(3/443)

*DALILIN SU AKAN HAKA*

1. Hadisin Malik bnul huwairith (R.A) cewa: ya ga Annabi Muhammad (S.A.W) Yana Sallah, idan ya kasance a wutiri a cikin sallar shi baya yunkurin tashi har sai ya dai daita a zaune
[Bukhari 823]

Da yace a (wutiri a cikin sallar shi) Yana nufin Raka'a ta farko kafin yaje ta biyu, da Raka'a ta uku kafin yaje ta hudu

Akwai wata riwayar daban da bukhari ya riwaito a hadisi Mai lamba ta 824, daga Abi Qilabah yace: Malik ibnul huwairith ya zo mana, sai yayi Sallah a tare damu a masallacin mu wannan, sai yace: Ni wallahi zanyi Sallah a tare daku Amma ba ina nufin zanyi Sallah bane, sai dai ina nufin in ganar daku yadda Naga Annabi Muhammad (S.A.W) Yana Sallah? Sai Ayyub yace: sai muka ce da Abi Qilabah: To ta ya ya sallar shi take? Sai yace: irin sallar wannan dattijon namu Yana nufin (Amru bn salamah) sai Ayyub yace: wannan dattijon ya kasance "Yana cika kabbara, idan ya dago kanshi daga sujada ta biyu sai ya zauna, ya dai daita akan kasa Sannan sai ya tashi.

Abu Daud ma ya riwaito a hadisi Mai lamba ta 842, Kuma Albany ya inganta a sahihu Abi Daud, hadisi Mai lamba ta 748 cewa Amru bn salamah (Limamin su) ya kasance idan ya dago kanshi daga sujada ta karshe a Raka'a ta farko sai ya zauna, Sannan ya tashi.

Akwai wata riwayar a wurin Ahmad, a hadisi Mai lamba ta 20558 daga Abi Qilabah yace: (Abu Sulaiman, Malik bnul huwairith yazo a masallacin mu, sai yace: Wallahi ni zanyi Sallah, ba ina nufin Sallah bane, sai dai ina nufin in ganar daku yadda Naga  Annabi Muhammad (S.A.W) Yana Sallah? Sai yace: sai ya zauna a Raka'a ta farko bayan ya dago kanshi daga sujada ta karshe, Sannan ya tashi.
Akwai wata riwayar daban wacce ita ma Imamu Ahmad ya riwaito a hadisi Mai lamba ta 20539

Malaman da suke ganin Sunnah ce mustahabbiya suka ce: daga cikin abin da zai kara karfafa mustahabbancin yin ta shine, shi Malik ibnul huwairith shine Wanda ya riwaito hadisin dake cikin bukhari Mai lamba ta 631cewa Manzon Allah (S.A.W) yace:
صلوا كما رأيتموني أصلي
Babban Malami, Alhafiz ibn hajar(R) a cikin fatahul bary, sharhin Sahihul bukhari (2/302) a inda yake sharhin hadisin Malik bnul huwairith sai yace: a cikin shi akwai shar'ancin yin jilsatil istirahah, Kuma imamush shafi'i yana akan hakan, da wani yanki na manyan Malaman hadisi, haka a Musnad Ahmad akwai riwayoyi guda biyu....

2. Hadisin Abi Humaid Assa'idy, a inda yake siffanta sallar Annabi Muhammad (S.A.W), yace: *_"Sannan yayi sujada, Sannan yace: ALLAHU AKBAR, Sannan ya kafa 'kafar shi, ya zauna, ya dai daita har sai da kowane 'kashi ya koma mazaunin shi, Sannan ya Mike.
[ Tirmidhi ya riwaito a hadisi Mai lamba ta 304, da ibn khuzaimah a hadisi Mai lamba ta 685, da Ahmad a hadisi Mai lamba ta 23647, Kuma Albany ya inganta shi a cikin
إرواء الغليل في تخريج أحاديث منار السبيل(2/14)
Kuma babban malami Mai fatawa, Sheikh bin baaz ya rinjayar da wannan zancen. A inda yake cewa: jilsatil istirahah Sunnah ce, ba wajiba ba, wannan shi yafi inganci, wasu daga cikin malamai suna cewa Sunnah ce ga masu rauni da gajiyayyu,  kamar mara lafiya da tsoho, da sauran masu rauni, abin da yafi rinjaye shine Sunnah ce kawai ga kowa, idan mutum bai yiba a wasu lokutta babu laifi.
فتاوى نور على الدرب (2/327)

*NA BIYU*
Sun tafi akan cewa ba Sunnah bace, wannan shine mazhabin malikiyyah, da hanafiyyah, sufyan Athauri da Abu yazeed da ishaq ibn rahwiyyah, duk sun tafi akan cewa ba Sunnah bace.

*DALILIN SU AKAN HAKA*
1. Hadisin Nan na مسيء صلاة suka ce: Manzon Allah (S.A.W) bai ambaci wannan zaman ba a lokacin da yake karantar da wannan Wanda baiyi Sallah dai dai ba, da ace an shar'anta ta da ya ambata mashi ita.

*ABIN DA ZAMU CE AKAN WANNAN*
Manzon Allah (S.A.W) Yana karantar dashi wajibi ne kawai👌 ba tare da sunnoni ba(idan ka koma cikin hadisin za kaga hakan).

2. Hadisin Abi Humaid Assa'idy: inda yake cewa: sai yayi kabbara, yayi sujada, Sannan yayi kabbara, sai ya Mike bai zauna ba. [Abu Daud ya riwaito a hadisi Mai lamba ta 733 da imamul Baihaqy a hadisi Mai lamba ta 2749 da Ibn hibban a hadisi Mai lamba ta 1866.

*ABIN DA ZAMU CE AKAN WANNAN*

Shi wannan hadisin Dha'ifi ne, Albany a cikinضعيف أبي داود 171 yace: hadisin Dha'ifi ne da wannan siyaqin da suka kawo, saboda a cikin isnadin akwai wani Wanda ake Kira Isah bn Abdullah, Ibnul madeeny yace: Majhul ne(ba'a sanshi ba)

3. Hadisin Nu'uman bn Abi Ayyash, yace: na riski ba mutum guda kadai ba daga cikin sahabban Annabi Muhammad (S.A.W) sun kasance idan suka dago kansu daga sujadar karshe ta Raka'a ta farko da Raka'a ta uku suna mikewa basu zaunawa. [Ibn Abi Shaibah ya riwaito a hadisi Mai lamba ta 3989]

*ABIN DA ZAMU CE AKAN WANNAN*

Rashin yin jilsatil istirahah ga wasu daga cikin sahabbai ba zai sa ta zamo ba Sunnah ba, saboda barin abin da ba wajibi ba ya halasta.

Daga karshe, ni a Matsayi na na dalibi, dogarona da hadisan da suka a cikin bukhari da Abu Dauda ingantattu, ina akan fatawar malamai na farko akan cewa Sunnah ce mustahabbiya, Wanda yayi zai samu ladar koyi, Wanda baiyi ba sallar shi ta cika shi ma.

ALLAH YA QARA HADA KAWUNANMU AKAN KARANTARWAR ANNABI MUHAMMAD S.A.W, YAYI MANA JAGORA A CIKIN AL'AMURRAN MU NA YAU DA KULLUM.

✍ *Hashim Siraj Uba ats~tsamawy _(ABU SINAN)_*
+2349030201868

Https://fb.me/abbansinan

Saturday, 4 January 2020

HALASCIN SHAFA AKAN SAFA

*SHIN KO YANA HALASTA YIN SHAFA AKAN SAFA*

MALAMAI SUN KASU GIDA UKU AKAN MATSALAR SHAFA AKAN SAFA

*NA FARKO:* MALIK, SHAFI'I DA ABI HANIFA SUN TAFI AKAN BAYA HALASTA, HUJJARSU SHINE
لأن الجورب لا يسمى خفا، فلا يأخذ حكمه.
SABODA ITA SAFA BA'A KIRATA DA SUNAN HUFFI BA, SABODA HAKA BA ZATA DAUKI HUKUNCIN HUFFI BA.

*NA BIYU:* HASANUL BASRY, IBNUL MUSAYYIB, IMAMU AHMAD BN HAMBAL(Imamu AHLIS-SUNNAH WALJAMA'AH) DA WASUNSU, SUN TAFI AKAN YA HALASTA DA SHARA'DIN SAFAR TA KASANCE MAI KAURI, KUMA MAI TSAWO WACCE ZATA IYA RUFE WURIN DA FARILLA NE A WANKE IDAN ANXO ALWALA

*NA UKU:* YANA HALASTA SHAFA AKAN SAFA KO WACE IRI CE, KODA SHARARA CE(Ba tada kauri), WANNAN SHINE MAZHABIN IBN HAZAM, KUMA SHEIKHUL ISLAM IBN TAIMIYYA YA ZABI WANNAN, QARAMIN IBN TAIMIYYA NA WANNAN ZAMANIN, WATO IBN UTHAIMIN YA RINJAYAR DA WANNAN MAGANA TA IBN HAZAM, HAKA IBN BAAZ DA IMAMUSH SHANQIDY DUK SUNA AKAN WANNAN FATAWA TA IBN HAZAMIN

IBN UTHAIMIN (RH) YAYI WATA MAGANA MAI QAYATARWA, GA ABIN DA YACE:

SHAFA AKAN SAFA HADISAI SUNXO AKAN HAKAN, YA INGANTA CEWA SAHABBAI DA DAMA SUNYI SHAFA AKAN SAFA, DA ACE ZAMU QADDARA CEWA MA BA SUNNAH BANE DAGA MANZON ALLAH S.A.W, KUMA BABU ATHAR DAGA SAHABBAI, YACE QIYASI TSAFTATACCE YAYI NUNI DA HALASCIN SHAFA AKAN SAFA,YA CIGABA DA CEWA: SABODA MU MUN SAN HIKIMAR DA TA SA AKA HALASTA SHAFA AKAN HUFFI SHINE SABODA TSANANI DA KUMA TAKURA A WURIN ALWALA(ace duk zakayi alwala sai ka cire)......... HAR ZUWA INDA YACE: SABODA HAKA MUKE GANIN NASSI DA KUMA DUBO(Qiyasi) DUKKANIN SU SUNA NUNI AKAN HALASCIN SHAFA AKAN SAFA

MUGEERA DAN SHU'UBA (RA) YA RUWAITO DAGA MANZON ALLAH S.A.W: YAYI ALWALA SAI YAYI SHAFA AKAN SAFA DA KUMA TAKALMA
(ABU DAUD, KUMA ALBANY YA INGANTA SHI)

YA TABBATA CEWA SAHABBAI DA DAMA SUNA AIKATA SHAFA AKAN SAFA, A CIKIN *SUNAN ABU DAUD* YA KAWO CEWA SAHABBAI DA DAMA SUNYI SHAFA AKAN SAFA, DAGA CIKINSU AKWAI: ALIYU DAN ABI DALIB YAYI SHAFA AKAN SAFA, HAKA IBN MAS'UD, DA BARRA' BN AaZIB, DA ANAS DAN MALIKU, DA ABU AMAMA ALBAHILY, DA SAHAL BN SA'AD ASSA'IDY DA AMRU IBN HAREETH, HAKA AN RUWAITO CEWA UMAR BN KHADDAB DA ABDULLAHI DAN ABBAS SUNA AIKATA SHAFA AKAN SAFA

ABU HANIFA YA KASANCE YANA HANA SHAFA AKAN SAFA, SAI A QARSHEN RAYUWAR SHI YA DAWO AKAN WACCAN FATAWAR,  YACE: YANA HALASTA SHAFA AKAN SAFA, BAI FI KWANA UKU KO BAKWAI BA KAFIN YA RASU YA BADA FATAWAR HALASCIN HAKAN

IMAMUT TIRMIDHI YACE: DA WANNAN FATAWAR TA HALASCIN SHAFA AKAN SAFA SU SUFYAN ATHAURY DA IBNUL MUBARAK DA AHMAD DA ISHAQ SUKA TAFI

انتهى

*ليهلك من هلك عن بينة ويحي من حي عن بينة*

#ABU_SINAN
+2348064734911

Https://fb.me/abbansinan

HUKUNCIN HADE SALLOLI A LOKACIN SANYI

*MINENE GASKIYAR MAGANA AKAN HADE SALLOLIN AZHR DA LA'ASAR KO MAGRIB DA ISHA'I A LOKACIN SANYI MAI TSANANI???*

Rubutawa: *ABU_SINAN ATS~TSAMAWY*

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad S.A.W da iyalan gidansa da sahabbansa baki daya.

Bayan Haka:

Yan uwa Yana da kyau mu fahimci cewa ita fa shari'ah tazo mana da sauki a lokacin da aka shiga cikin tsanani, haka tazo mana da saukakawa a cikin ibada a kowane al'amari Wanda a cikinsa akwai wahala da takura wacce take a bayyane. Kamar yadda Allah madaukakin sarki yake cewa:
*يريد الله بكم اليسر ولا يريد بكم العسر...*
Da Kuma inda Allah madaukakin sarki yake cewa:
*وما جعل عليكم في الدين من حرج...*
Duka Wadannan suna nuna Mana cewa addinin Allah sauki ne dashi.
Yazo a cikin sahihul bukhari, Hadisin da Abi Hurairah ya ruwaito, Manzon Allah S.A.W yace: *_"Lallai shi addini sauki ne, babu Wanda zai dauki addini da tsanani face sai addinin ya rinjayeshi...."_*

Allah madaukakin sarki Yana son mu karbi sauki daga gareshi a lokacin da ya saukaka Mana, ko a cikin abubuwan da ya saukaka Mana.
Ya tabbata a Sunnah, saukakawa a cikin ibada a lokacin da ake zaune gida da lokacin tafiya a wani yanayi kebantacce. Daga cikin abin da ya tabbata na saukakawa akwai *sanyi Mai tsanani ga mutane.*

Dalilin hakan shine saboda gudun kada mutum ya kamu da rashin lafiya a rayuwarsa.
Amma sanyi Wanda baya cutarwa baya halasta, hukuncinsa kamar hukuncin sauran sanyi ne na jin dadi da more rayuwa.

*AN RANGWANTA YIN SALLAH A GIDA KAMAR YADDA AKA RANGWANTA HADE SALLOLI A LOKACIN SANYI MAI TSANANI*

An rangwanta ma Wanda sanyi Mai tsanani ya shafa da yayi Sallah a gidansa, ya bar jama'ah a masallaci. Dalilin hakan shine abin da Nafi' ya ruwaito cewa: *_"ibn Umar ya kira Sallah a wani dare Mai sanyi a wani gari ko wuri da ake Kira DHAJNAN, Sannan yace: kuyi Sallah a cikin gidajenku, sai ya bamu labari cewa: Manzon Allah S.A.W Yana umurtar  ladan ya kira Sallah Sannan ya sashi ya fadi cewa: KUYI SALLAR KU A DAKUNAN KU. A dare Mai sanyi, ko lokacin da sukayi doguwar tafiya."_*[Bukhari da Muslim]
Haka Abu Daud yayi babi a cikin littafin shi, sunan babin: *_BABIN DAKE MAGANA AKAN RABUWA DA JAMA'AH A DARE MAI SANYI._*
Haka Babban Malami *Ibn Qudama* a cikin littafin shi Mai suna: المغني yace: *_Anyi uzuri ga barin jama'ah saboda tsananin iska a dare Mai duhu Kuma Mai sanyi._*

Haka Muslim ya fitar a cikin littafin shi, daga Ibn Abbas (R.A) yace: *_"Manzon Allah S.A.W yayi sallar azhr da la'asar a lokaci guda, magrib da isha'i a lokaci guda ba tare da akwai tsoro ba, ba tare da yayi tafiya ba, ba Kuma ruwan sama akayi ba. An tambayi Ibn Abbas: me yasa yayi hakan toh? Sai yace: Yana nufin kada ya tsananta ma al'ummarshi ne."_*

Saboda haka abin da yake ingantacce shine, ana hade sallolin azhr da la'asar ko magrib da isha'i a lokacin da sanyi ya tsananta.

Haka imamu Ahmad ya ruwaito cewa: *_"Abdullahi Dan Umar ya kasance yana hada salloli a daren da ake tsananin sanyi."_*

Abin da yake na dai dai ga musulmi shine ya saukaka ma kanshi da saukakawar mahaliccinshi, kada ya tsananta ma kanshi ko al'ummarshi.

Akwai maganganun malaman mazhabobin Malikiyya da Shafi'iyya da Ahmad da Abu hanifa akan wannan matsalar. Mazhabin Abu Hanifa kadai ne ya sabawa sauran mazhabobin, shi Abu Hanifa ma yana ganin cewa baya halasta a hade wata Sallah idan ba a arfa ba(Azhr da la'asar) ko muzdhalifa(Magrib da isha'i)

Amma sauran mazhabobin guda uku duk sun yarda a hade salloli saboda tsananin sanyi, inda suka danyi sabani shine wasu na ganin cewa ba za'a hade azhr da la'asar ba wasu Kuma sunce har su za'a hade matukar sanyin da ake ya tsananta.

ALLAH MADAUKAKIN SARKI SHINE MASANI.

#ABU_SINAN
+2349030201868

https://fb.me/abbansinan

Wednesday, 1 January 2020

002 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_002_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *FALALAR SADA ZUMUNTA*

  Sadar da zumunta yana da tarin falala mai yawa kadan daga ciki sun hada da: 
Sadar da zumunta alama ce dake nuna cewar bawa yayi imani da Allah da kuma ranar lahira.  kamar yadda hadithin  da Abu Huraira ya riwaito daga manzon Allah (SAW) yace: ''Duk wanda  yayi imani da Allah da kuma Ranar Lahira to ya  Karrama Bakonsa, haka nan wanda yayi imani da Allah da ranar lahira to ya sadar da zumuntarsa (Buhari ya riwaito shi 6138”).
Lallai sadar da zumunta sababine na yalwar arziki da kuma tsawon rayuwar dan adam da kuma samun albarka a cikin su.
  An karbo hadithi daga Anas (R) yace manzon Allah, yace:''Duk wanda yake so a shimfida arzikinsa a kuma jinkirta masa rayuwarsa to ya sadar da zumuntarsa" *(Buhari 5986- Muslim 2557).*
Abdullahi dan Umar (R) yace ''Duk wanda ya kiyaye  ubangijinsa, ya sadar da zumuntar sa to za’a jinkirata masa ajalinsa, kuma dukiyarsa zata yalwata, sannan iyalansa zasu so shi.”
*(Tirmizi-1979- Buhari  adabul mufrad-58).*
3. Sadar da zumunta yana janyo sadarwar Allah ga wanda ya sadar da ita.
   Abu Huraira ya ruwaito hadithi daga manzon Allah (S.A.W) yace ''Lallai Allah ya hallicci dukkan halitta bayan ya kammala sai zumunta ta tashi sai tace nan ne matsayin da zan nemi tsari daga wanda ya yanke ni?  Sai Allah (S.W.T) yace eh; shin ko kin yarda in sadar ma wanda ya sadar dake in kuma  yanke ma wanda ya yanke ki? Sai tace eh, sai Allah yace haka zai kasance gareki''.
*(Bukhari -5987- muslim 2554).*
4.  Sadar da zumunta yana daya daga cikin manyan sabubban da ke shigar da mutun Aljanna. Abu Ayubal Ansari yace ''Lallai wani mutum; yace  ya manzon Allah ka ba ni labarin aikin da zai shigar dani aljanna kuma ya nisanta ni daga shiga wuta, sai manzon  Allah yace ''ka bauta ma Allah kada ka hadashi da komai a wajan bauta, ka tsaida  sallah, ka bada zakka, ka sadar da zumunta.
*(Bukhari 1396-muslim 13)*
5. sadar da zumunta yin da'a ne  ga Allah da Manzonsa, Allah (S.W.T) ya fada a cikin Alqur’ani yana mai yabon masu sadarda zumunta  “sune wadanda suke sadar da abin da Allah yace a sadar dashi (Zumunci) suna jin tsoron ubanginsu kuma suna tsoron mummunan hisabi"
*(Suratul Ra’ad 21)*
An karbo hadisi daga Abu sufyan a cikin hadisinsa mai tsawo a cikin kissar *Hirkala* yace ma Abu sufyan mine ne Manzon Allah yake umurtar ku dashi sai Abu sufyan yace: yana cewa ku bauta ma Allah shi kadai kada ku hadashi da komai a wajen bauta, kubar ababen da iyayenku ke fada,kuma yana umartarmu da yin Sallah da riko da gaskiya da kamewa, da kuma sadar da zumunta
*(Muslim 1883)*
6. Sadar da zumunta yana daya daga cikin kyawawan ayyuka a cikin addinin musulunci, Allah (SWT) yana cewa: ''kuba ma’aboci kusanci hakkinsa (ana nufin dan'uwa) *(Isra’i 26)*
Haka nan a wani wurin yace, kuji tsoron Allah wanda kuke rokon juna dashi kuma ku sadar da zumunta *(Suratul Nisa’i 1).* Ya kuma kara cewa ku bauta ma Allah kada ku hadashi da komai a wajen bauta, ku kyautata ma iyayenku da makusantanku (yan'uwanku na zumunta) da marayu da miskinai da makwabci na kusa.

A NAN ZAMUYI BURKI SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI *HADARIN  DA KE CIKIN YANKE ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN
https://fb.me/abbansinan