Wednesday, 6 December 2017

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 007

*GORON SALLAH*1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na takwas(008)_

``` √ AKIDATUL BADA’A.

Akidatul Bada’a rukuni ce daga cikin rukunnan
addinin Shi’a, akidatul bada’a tana nufin Allah
yana yin kuskure a cikin ayyukansa da
maganganunsa. Sai daga baya ya gano kuskure
ne, sai ya canza. Sun sanya ta a cikin rukunnan
addinin su domin su watsar da nassosa na
shari’ar musulunci da nuna duk abunda musulmi
ya yarda da shi to Allah ya canzashi bayan ya
gano kuskurene. A takaice dai a wajen su Allah
yana jahiltar wasu ayyuka da magan-ganunsa,
wanna akidar tana daga cikin mafi munin akidar
su domin suna nuna tozarci da kasawa da jahilci
ga Allah wadanda duk sunkoru ga reshi (SWT).
Shi kuma Mahadin sunnah, ingantacciyar ruwaya
ta zo game da shi cewa yana daga cikin tsatson
Hassan bin Aliyu
(R.A).
Daga karshe yaku bayin Allah, wannan yar
takaitattar nasiha ce da tayi bayani akan micece
Shi’a da miyagun akidunta saboda haka ne
malamai sun yi hukunci cewa ‘Yan Shi’a kafirai
ne, kuma zindikai ne.
Imamu Malik yace “Wanda yake zagin sahabban
Manzon Allah ba shi da rabon muslunci” (Wato
ba musulmi bane)
Imamu Ahmad bin Hambal yana cewa “ba’a
auren mata ‘Yan Shi’a, kuma ba’a cin yankansu
domin sunyi ridda sun bar musulunci. Kaga anan
Imamu Ahmad yana nufin idan har baya halatta a
auri diyan su mata to min babi aula kenan mu
musulmai baya halatta mu basu aure, duk da
cewa addinin muslunci ya halatta auren
ahlulkitabi, wannan yana nuna munin Shi’a sama
da Yahudu da Nasara.
Manufar wannan bayanin bayana nuna karanta
darajar Aliyu ko ahlulbaiti bane, lallai
ahlussunnah suna son Aliyu da ahlulbaiti da
sauran sahabbai. Shi’a ita ce kungiya mafi hadari
ga addinin muslunci, domin suna kashe musulmai
suna kyale masu bautar gumaka, suna zagin
Sahabbai amma a hakika Annabi suke zagi
Imamu San’ani yana cewa “al-ummar musulmi ta
hadu akan kafircin Shi’a Imamiyya
Sheikh bin Baz yace “Shi’a Rafida da kumaini
suna kan shirka babba
Sheikh Albani yace “Lallai abun da kumaini yake
kira akan shi na cewa sahabbai sun juyar da
Qur’ani wannan kafirci ne babu shakka
Don haka babu wadanda sukafi ahlussunnah son
ahlulbaiti da sauran sahabbai da magabata gaba
daya
Kamar yadda Imamu Shafii ya kawo a cikin
diwaninsa
Ya ku ahlulbait Rasulullah, lallai Allah ya farlanta
sonku kamar yadda ya saukar a cikin Qur’anin sa
Ya isheku girman alfahari duk wanda yayi salati
ga Manzon Allah bai sanya kuba to bashi da
salati.

DA WANNAN NE MUKA KAWO KARSHEN
WANNAN RUBUTU, MUNA GODIYA GA MASU
BIBIYARMU A KODA YAUSHE, ALLAH YA
AMFANAR DAMU DA ABUNDA MUKA KARANTA,
YA KARA TSAREMU DAGA MIYAGUN AKEEDU.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 006

*GORON SALLAH* 1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na shida(006)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA IMAMA.

Imama a wajen ‘Yan Shi’a tana dai-dai da
Annabawa a wajen musulmi, don haka ma suka
ce imamansu (12) ma’asumaine (Basu yin laifi)
“Yan Shi’a sun kudurce cewa lallai Imama baza
ta kasan ce ga kowaba sai ga Aliyu da diyan sa
(12) kuma sun sanya wannan a cikin rukunnan
imani suka ce duk wanda yayi kudurin Imama ba
ga Aliyu ko diyansa ba to ya kafirta kafirci mai
girma.
Hakika malaman sunnah sun hadu akan cewa
wadanda suka can-canta da halifanci bayan
Manzon Allah gasu kamar yanda suke a jere: -
Abubakar, Umar, Usman, sannan Aliyu, kuma
haka suke a wajen falala.
Ma’ana: Abubakar shine mafifici, sannan Umar,
sannan Usman, sannan Aliyu. Malaman suka ce
duk wanda yace Aliyu yafi Abubakar da Umar
falala to shi dan bidi’a ne.

√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA ILIMIN FIQIHU.
‘Yan Shi’a sun sabama ahlussunah dangane da
ilimin Fiqihu saboda basu karbar hadisai
ingantattu da sunnoni da aka ruwaito a cikin
littafan sunnah.
‘Yan Shi’a mabukata ne ta bangaren fahimtar
sunnah.
Sun kir-kiri bidi’o’i a cikin kiran sallah kamar
haka:
Suna karawa da Ash-hadu anna Aliyu
Waliyuullah, Madadin Ash-hadu anna
Muhammadarrasulullah
Sun kir-kiri bidi’o’i ta bangaren sallah kamar
haka:
Suna hada sallah ba tare da wani uzuriba
Basu yarda da sallar juma’a ba ko da a zahiri
anga sunayi.
Sun haramta cin zomo
Sun halatta auren mutu’a
Duk wadannan haramunne ga Ijma’in malamai.
ALLAH YA KARA TABBATAR DAMU AKAN
HANYA MADAIDAICIYA.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 005

*GORON SALLAH*1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_*  *Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na biyar(005)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA TAUHIDI.

‘Yan Shi’a mushrikai ne ta bangaren tauhidi
domin suna rokon Aliyu, da Hussaini da Zainab
da Fatima, dare da rana, lokacin tsanani da
jindadi. A wurin ‘Yan Shi’a ziyartar kabarin
Hussaini yana daga cikin manya-manyan
sabubban samun waraka daga rashin lafiya, da
wadatar arziki da samun taimako da biyan
bukata.
Babban malamin Shi’ar nan Jafar Ibn Muhammad
Kaulawaihi ya kawo a cikin littafinsa mai suna
“Kamilizziyarat” wato kammalallar ziyara
Babin da ke Magana akan ziyarar Hussaini kamar
ya ziyarci Allah a alarshin sa
Babin da ke Magana akan wanda ya ziyarci
Hussaini tana kore dukkan bakin ciki
Babin da ke Magana akan ziyartar Hussaini tana
dai-dai da aikin Hajji da Umra
‘Yan Shi’a sun kudurce cewa lallai ziyartar
kabarin Hussaini yafi tsayiwur Arfa falala kuma
lallai Allah yana kallon wadanda suka ziyarci
Hussaini kafin ya kalli wadanda suka tsaya a
Arfa. Haka nan kuma ‘Yan Shi’a sun kudurce
lallai limaman su sha biyu (12) daga cikin diyan
Aliyu ma’asumai ne kuma sunfi Annabawa da
Mala’iku falala, kuma basu mutuwa, kuma sun
san gaibu kuma su ke kula da halittun Allah gaba
daya.
Yazo acikin littafin su “Alkafi”
babi da ke Magana akan lallai limamai (12)
hasken Allah ne
Babi da ke Magana akan lallai limamai (12) sun
san abun daya kasance da abun da zai kasance
nan gaba, babu wani abu da ke boyuwa a kan su
Babban mawakin nan na Shi’a Aliyu Sulaiman
Almazidi Allabanani (Libenon) ya fadi a cikin
wakar sa yayin da ya ke yabon Aliyu
Baban Hassan kaine ainihin abun bauta, kuma
kaine ikon Allah baki daya
Ilimin ka ya kewaye dukkan gaibi, ko akwai wani
abu da zai boye maka?
Baban Hassan kaine mijin Batula, kuma kaine
abun bauta kuma kaine ma Manzon Allah
Kaine cikakken wata, kuma kaine ranar hankulla
mamallakin ubangiji kaine mai mulki
Zuwa gareka makomar komai take, kuma kaine
masanin abunda ke cikin zukata
Kaine mai tayar da wadanda ke cikin kabari,
kuma nassi ya nuna kai ne mai hukunci a ranar
kiyama
Kai ne mai-ji kuma mai gani, kai ne mai iko akan
dukkan komai
Badon kai ba da tauraro baiyi tafiya ba badon kai
ba da falaki bai zagayaba
Kai ne masanin dukkan sarari, kai ne magana da
Ahlulrakim
Ba don kai ba da Musa bai zama kalimi ba, tsarki
ya tabbata gareka da kai ne yayi Magana
Badon kai ba da Annabawa basu zamoba
Badon kai ba da Manzanni basu zamoba
Badon kai ba da alkalami bai rubuta a alloba
Badon kai ba da talikai basu zamoba, dukkan su
bayinka ne kuma mallakar kane.
Tambaya ita ce miya rage ma Allah idan har
Aliyu ya zama haka? Allah ya nisanta Aliyu ya
ksanace yana da siffa ta rububiyya. Wannan ita
ce tsantsar akidar Kiristoci ga Annabi Isah da
suka ce masa Allah, kaga wannan yayi dai-dai da
akidar Shi’a ga Aliyu (R).
ALLAH YA TABBATAR DAMU AKAN SUNNAH.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 004

*GORON SALLAH*1438/2017

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_* *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na Hudu(004)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA SUNNAH.
‘Yan Shi’a sune mafi jahiltar Hadisai da Sunnoni
da ruwayoyi daga Manzon Allah. Ba zaka samu a
cikin zancan su ba cewa daga Manzon Allah,
abun da zakaji kawai shine. Aliyu yace, ko Jafar
yace ko Hussaini yace mafi yawan ruwayoyin su
karya ce suka kirkira suka jingina ga Aliyu da
Ahlulbait musamman Ja’afarus-sadiq
‘Yan Shi’a basu yarda da littafin Bukhari, da
Muslim da sauran littafan Hadisan nan guda hudu
ba, suna cewa *kirkiren karya ne, kuma
tatsunniya ce a cikin su.
Suna da wani littafi wanda a wajen su yayi dai-
dai da bukhari da Muslim da sauran littafan
hadisi mai suna “Alkafi” wanda malamin su
Kulaini ya rubuta cike yake da karai-rayi da
tatsuniyoyi.

√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA SAHABBAI.
Sahabbai sune mafifitan halitta bayan Manzon
Allah (SAW). Allah (SWT) ya fada a cikin
littafinsa mai tsarki yana mai yabon su
“Muhammad Manzon Allah ne, kuma wadannan
da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai,
masu rahama ne a tsakanin su, kana ganin su
suna masu ruku’i masu sujada, suna neman
falala daga ubangijin su da yardarsa, alamarsu
tana a cikin fuskokin su daga kufar sujuda.
Wannan shine siffar su a cikin Attaura. Kuma
siffarsu a cikin Injila, itace kamar tsiron shuka
wanda ya fitar da reshen sa, sa’an nan ya
karfafa shi, yayi kauri, sa’annan ya dai-daita a
kan kafafunsa, yana bayar da sha’awa ga masu
shukar domin (Allah) ya fusatar da Kafirai game
da su, kuma Allah yayi alkawari ga wadanda
sukayi imani, kuma suka aikata ayyukan kwarai
daga cikin su da gafara da lada mai girma
(Suratul Fat’h – 29)
Duk wanda ya soki Sahabban Manzon Allah
hakika ya soki Manzon Allah domin zagin
Sahabbai gaba dayansu kafirci ne kuma ridda ne.
Kulaini ya fada a cikin littafin sa “Alkafi” cewa
“Lallai sahabbai gaba dayansu sunyi ridda bayan
rasuwar Manzon Allah in banda mutum ukku.
‘Yan Shi’a sunayin addu’a ta la’anci zuwaga
sahabban Manzon Allah a cikin salla, kamar
yanda Majiisi ya ambata a cikin littafinsa “Al-
anwar”. Suna cewa ‘Allah ka la’anci gumakan
Quraishawa guda biyu da makaryatansu guda
biyu da diyansu guda biyu’.
Gumakan sune Abubakar da Umar
Makaryatan sune Abubakar da Umar
Diyansu kuma sune Aisha da Hafsat
Kumaini (Batacce) ya fada a cikin littafinsa
“Hukumatil Islamiyya” cewa: Lallai Abubakar da
Umar fasikaine kuma wawaye ne.
Yan Shi’a suna da’awar cewa Usman munafukine,
Abubakar fasikine, Aisha mazinaciyace da dai
sauran miyagun maganganu da suka fada ga
sahabbai wanda da suna nan cike da littafan su.
ALLAH YA TABBATAR DAMU AKAN
INGANTACCIYAR AKEEDA.
ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 003

*GORON SALLAH*

*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*

*_WALLAFAR:_* *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_Fitowa Na uku(003)_

```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA MUSULMI DA DAULAR MUSULUNCI.

      Yana daga cikin akidar Shi’a shine tsananin adawa ga musulunci da daulolin musulunci tun daga zamanin halifofi har zuwa wannan zamanin. Ga kadan daga cikin misalan da suka faru: -
Abu Lu’uluatal Majusi (Mai bautar wuta) shi ya kashe Umar dan Khattab
Wanda ya kashe Usman bin Affan daya ne daga cikin mabiyan Abdullahi bin Saba Alyahudi
Ashe ba Ibn Alkami da Dusii bane suka shigo da tattara a bagdad, suka kashe miliyoyin musulmai ba?
Ashe basu bane a (2003) suka shigo da mayakan America a Bagdad suka kashe dubban mutane ba?
Ashe ba ‘Yan Shi’a bane a (1885) suka hada kai da Yahudawa suka kashe daruruwan Falasdinawa?
Bugu da kari, ‘Yan Shi’a ne suka kai hari a Makka suka kashe Alhazai, suka sace Hajarul Aswad ya cigaba da zama a hannun su tsawon shekara (20). ‘Yan Shi’a Fadimiyya ne suka kafa daula sukayi mulkin Misra da Yammacin Africa suka kashe malaman Fiqihu wadanda suka hana zagin Abubakar da Umar
Wadannan sune kadan daga cikin misalai dake nuna irin yanda Shi’a ke kiyayya ga daulolin musulunci da musulmai.

√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA QUR’ANI.

       ‘Yan Shi’a sun qudurce cewa lallai Qur’ani karkatacce ne, suka ce Abubakar da Umar ne suka juyar da shi, suka shafe wasu surori da wasu ayoyi da ke nuna Aliyu shine Halifa bayan rasuwar manzon Allah. Suka ce Abubakar da Umar sun shafe Suratul Wilaya, ma’ana surar da ta nuna Aliyu ne Halifa bayan Manzon Allah, ga yan da surar take a wajen ‘Yan Shi’a
‘Yaku wadanda sukayi imani da Annabi da waliyyi (Aliyu) wadannan da muka aiko domin su shiryar da ku zuwa ga hanya madai-daiciya’
‘Yan Shi’a sun ce Abubakar da Umar sun juyar da Suratul Sharhi daga asalin ta wai asalinta shine:
‘Ashe bamu muka bude kirjin ka ba? Muka sanya Aliyu ya zama surukinka?
A shekara ta (1877) wani babban malamin Shi’a wanda ke zaune a garin Najib mai suna Alhaji Maimizan Hassan ibn Muhammad Takiyuddaini Addabaristi ya wallafa littafi mai suna:
“Rarrabe zance domin bayani akan juyar da littafin Ubangijin Halittu”. A cikin littafin yayi bayanin yanda Abubakar da Umar suka juyar da Qur’ani!
To mi ya rage ga musulmi? Idan har alqur’ani ya kasance anjuyar dashi a wajen wadan can bataccin? (Yan Shi’a) Ibn Hazm yayi jayayya da Kiristoci akan juyar da Bible sai suke ce shima Qur’ani ai anjuyar da shi kamar yadda Shi’a tace. Sai Ibn Hazm ya maida masu da raddi cewa lallai Shi’a ba musulunci bane a wurin mu ballantana har a kafa hujja da maganar su.

ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.

ALLAH YA SHIRYAR DAMU HANYA MADAIDAICIYA.

HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)
08064734911```

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 002

*GORON SALLAH 1438/2017*

*_SHI’AH DA AKEEDOJINTA_*


_Wallafar:_  *_Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)_*

*Fitowa Na biyu(00)2*



“`√ ASALIN SHI’ANCI.

     Shi’anci ya bayyana ne a lokacin
halifancin Usman bin Affan ta hanyar
Abdullahi bn Saba’a alyahudi alyamani
mai tsananin kiyayya da musulunci.
Hakika ya watsa a tsakanin musulmai
cewa Aliyu shine yafi cancanta da
halifanci kuma Abubakar da Umar zalunci
sukayi domin Aliyu ne Manzon Allah yayi
ma wasiyya kamar yanda annabi Musa
yayi ga Yusha’u bin Nun. Wannan
mummunar Magana ta watsu a tsakanin
sashen wasu jahilai, har suka wuce wuri
game da Aliyu har suka qudurce cewa
Aliyu Allah ne.
Malaman tarihi sun ambata cewa Aliyu ya
dinga kona su da wuta
Aliyu ya fada a cikin diwanin sa na
wakoki yace”
“Yayin da naga al-amarin al-amarine mai
muni sai na hura wuta na kira yarana”
Ma’ana: ya hura wuta ya kira yaransa ya
umurcesu dasu dinga sanya yan Shi’a a
ciki sai suka ce ai babu mai kona mutane
da wuta sai ubangijin wuta. Malamai sun
fada cewa daga cikin sabubban bayyanar
shi’anci shine keta da kiyayya da
kabilanci da farisawa (Mutanen Iran)
masu bautar wuta sukayi akan Larabawa
da Abubakar da Umar saboda sun karya
daular Farisawa
Yana daga cikin abun daya kamata mu
sani cewa Abu lu’uluata Majusin nan duk
da cewa ba musulmi bane bautar wuta
ya keyi mutanen Iran sun samar da wata
hubbare a kasar Iran a garin Kashan suna
yi masa dawafi domin girmamawa zuwa
gareshi akan abun da yayi masu na
kashe Umar. Wannan yana nunawa karara
cewa shi’anci kabilanci ne tsantsa ba
musulunci ba.
Shi’anci ya cigaba da yaduwa a lokacin
halifancin Aliyu bayan kashe Hussaini (R)
shi’anci bai gusheba yana girmama har
ya zama wata mazhaba da miliyoyan
mutane suke bi a matsayin addini, wajibi
ne muyi hattara da yaduwar shi’anci a
cikin duniya.


√ AKIDOJIN SHI’A.

Shi’a tana da akidu masu yawa zamu fadi
kadan daga cikin su domin takaitawa

1. KAMANCECENIYAR SHI’A DA
YAHUDAWA DA KIRISTOCI.

Akidar shi’a tayi kama da ta yahudawa da
kiristoci domin duk musibar da take a
cikin Shi’anci itace musibar da take a
cikin Yahudanci.

* YAHUDAWA; sun ce baza’ayi jihadi
domin daukaka kalmar Allah ba har sai
Dujal ya bayyana.

* YAN SHI’AH; su ma ‘Yan Shi’a su na
cewa baza’ayi jihadi domin daukaka
kalmar Allah ba har sai mahadi ya fito Ma’ana: a wajen yan Shi’a duk jihadin da
Manzon Allah yayi da Sahabbansa har
zuwa Sheik Usman bin Fodiyo duk
wahalar banza ce kuma shirme ne.

* YAHUDAWA;  suna jinkirta sallah har
zuwa fitowar taurari.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a suna
jinkirta sallar Magariba har zuwa lokacin
sallar Isha’i.

* YAHUDAWA; suna karkacewa daga
alqibla suma.

* YAN SHI’AH; ‘Yan Shi’a suna karkata
kansu daga alqibla.

* YAHUDAWA; sun juyar da Attaura.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a sun juyar
da Alqur’ani.

* YAHUDAWA; sun haramtawa kansu cin
kifi.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a sun
haramtawa kansu cin zomo.

* YAHUDAWA; basu yin shafa akan huffi.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a basu yin
shafa akan huffi.

*YAHUDAWA; suna kiyayya da Mala’ika
Jibril.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a suna
kiyayya da Mala’ika Jibril suka ce yayi
kuskuren kawo wahayi maimakon ya kai
shi ga Aliyu sai ya kai shi ga Annabi
Muhammad kaga anan suna tuhumar
manzancin Manzon Allah (SAW).

*KIRISTOCI; suna halatta auren mata ba
tare da sadaki ba.

* YAN SHI’AH; suma ‘Yan Shi’a sunayin
auren mutu’a.

Yahudawa da Kiristoci sunfi ‘Yan Shi’a da
dabi’o’i guda biyu.

* YAHUDAWA;  An tambayi yahudawa
suwa nene mafifita a cikin addinin ku?
Suka amsa da cewa sahabban Annabi
Musa.

* KIRISTOCI; suma kiristoci da aka
tambayesu suwaye mafifita a cikin
addinin ku? Sun amsa da cewa sahabban
Annabi Isah.

* YAN SHI’AH; Da aka tambayi ‘Yan Shi’a
suwa nene mafi sharri a cikin addinin ku?
sai suka amsa da cewa Sahabban Annabi
Muhammad(S.A.W).

An umurce su suyima sahabban Annabi
Istiqfari amma sai suka zage su.

Wannan yana nuna Yahudawa da kiristoci sunfi
‘Yan Shi’a girmama Annabawansu da
Sahabban su, kuma yana nuna irin yanda Shi’a ke nuna kiyayya ga Sahabban Annabi karara.

Wannan yana nuna cewa akidar Shi’a dai-
dai take da ta Yahudawa da Kiristoci.

ALLAH YA KARA SHIRYAR DAMU AKAN
HANYA MADAIDAICIYA, WADANDA KE
CIKIN WANCAN BATA KUMA ALLAH YA
SHIRYESU IDAN MASU SHIYUWA NE.

ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.“`

HAKKIN MALLAKA©
*_Hashim Sirajo Uba Tsamiya
(ABU~SINÃN)_*
+2348064734911

SHI'AH DA AKEEDOJINTA 001


*SHI’AH DA AKEEDOJINTA*

WALLAFAR;  *_Malam Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)_*

*GABATARWA*

“`Godiya ta tabbata ga Allah, muna
godemasa, muna neman taimakonsa,
muna neman gafararsa, muna neman
tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da
munanan ayyukan mu, wanda Allah ya
shiryar babu mai batar dashi, wanda
kuma Allah ya batar babu mai shiryar da
shi.
Na shaida babu abun bauta na gaskiya
sai Allah, shi kadai yake baya da abokin
tarayya, kuma na shaida Annabi
Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa
ne
Bayan haka, mafi gaskiyar zance shine
littafin Allah, fiyayyar shiriya ita ce
shiriyar Manzon Allah, mafi sharrin
alamurra sune wadan da aka kir-kiro a
cikin addini, dukkan abunda aka kirkiro a
cikin addini bidi’a ce dukkan bidi’a bata
ce, dukkan bata makomarta ita ce wuta.
Dalilin rubuta wannan ‘Yar takaitacciyar
nasiha shine na gabatar da huduba a
Masallacin Juma’a na Abu Huraira dake
Area 2 a Garin Tsafe mai taken Shi’a da
Hadarorinta, sakamakon haka ne wasu
‘yan uwa suka nemi da in fassara ta
zuwa harshen Hausa domin amfanin yan
uwa musulmi
Ina rokon Allah (SWT) ya azurta ni da
ikhlasi a cikin wannan aiki, kuma ya
amfanar dashi ga yan uwa musulmi.
√ MICECE SHI’A???
Shi’a daya ce daga cikin kungiyoyin bata,
da ake kira da sunaye daban-daban, ana
cemata Rafida, ko Ja’afariyya, ko Isna
Ashariyya.
√ SUWAYE ‘YAN SHI’A???
‘Yan Shi’a sune masu kokarin jingina
kansu zuwa ga Aliyu bin Abi Dalib, suna
kudurce cewa, Halifanci da Imama suna
tabbata ne kadai ga Aliyu bin Abu Dalib
bayan Manzon Allah, basu yarda da
Halifancin Abubakar da Umar da Usman
ba. Cibiyoyin su ta duniya a yanzu tana
kasar Iran da Lebenon, da Iraki da Syria
da Afganistan, tana da rassa a wasu
kasashen Africa musamman Nigeria inda
Alzakzaki ke jagorancin ta.


Zamu cigaba insha Allahu.


HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya
(ABU SINAN)“`
+2348064734911