*GORON SALLAH*1438/2017
*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*
*_WALLAFAR:_* *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*
_Fitowa Na takwas(008)_
``` √ AKIDATUL BADA’A.
Akidatul Bada’a rukuni ce daga cikin rukunnan
addinin Shi’a, akidatul bada’a tana nufin Allah
yana yin kuskure a cikin ayyukansa da
maganganunsa. Sai daga baya ya gano kuskure
ne, sai ya canza. Sun sanya ta a cikin rukunnan
addinin su domin su watsar da nassosa na
shari’ar musulunci da nuna duk abunda musulmi
ya yarda da shi to Allah ya canzashi bayan ya
gano kuskurene. A takaice dai a wajen su Allah
yana jahiltar wasu ayyuka da magan-ganunsa,
wanna akidar tana daga cikin mafi munin akidar
su domin suna nuna tozarci da kasawa da jahilci
ga Allah wadanda duk sunkoru ga reshi (SWT).
Shi kuma Mahadin sunnah, ingantacciyar ruwaya
ta zo game da shi cewa yana daga cikin tsatson
Hassan bin Aliyu
(R.A).
Daga karshe yaku bayin Allah, wannan yar
takaitattar nasiha ce da tayi bayani akan micece
Shi’a da miyagun akidunta saboda haka ne
malamai sun yi hukunci cewa ‘Yan Shi’a kafirai
ne, kuma zindikai ne.
Imamu Malik yace “Wanda yake zagin sahabban
Manzon Allah ba shi da rabon muslunci” (Wato
ba musulmi bane)
Imamu Ahmad bin Hambal yana cewa “ba’a
auren mata ‘Yan Shi’a, kuma ba’a cin yankansu
domin sunyi ridda sun bar musulunci. Kaga anan
Imamu Ahmad yana nufin idan har baya halatta a
auri diyan su mata to min babi aula kenan mu
musulmai baya halatta mu basu aure, duk da
cewa addinin muslunci ya halatta auren
ahlulkitabi, wannan yana nuna munin Shi’a sama
da Yahudu da Nasara.
Manufar wannan bayanin bayana nuna karanta
darajar Aliyu ko ahlulbaiti bane, lallai
ahlussunnah suna son Aliyu da ahlulbaiti da
sauran sahabbai. Shi’a ita ce kungiya mafi hadari
ga addinin muslunci, domin suna kashe musulmai
suna kyale masu bautar gumaka, suna zagin
Sahabbai amma a hakika Annabi suke zagi
Imamu San’ani yana cewa “al-ummar musulmi ta
hadu akan kafircin Shi’a Imamiyya
Sheikh bin Baz yace “Shi’a Rafida da kumaini
suna kan shirka babba
Sheikh Albani yace “Lallai abun da kumaini yake
kira akan shi na cewa sahabbai sun juyar da
Qur’ani wannan kafirci ne babu shakka
Don haka babu wadanda sukafi ahlussunnah son
ahlulbaiti da sauran sahabbai da magabata gaba
daya
Kamar yadda Imamu Shafii ya kawo a cikin
diwaninsa
Ya ku ahlulbait Rasulullah, lallai Allah ya farlanta
sonku kamar yadda ya saukar a cikin Qur’anin sa
Ya isheku girman alfahari duk wanda yayi salati
ga Manzon Allah bai sanya kuba to bashi da
salati.
DA WANNAN NE MUKA KAWO KARSHEN
WANNAN RUBUTU, MUNA GODIYA GA MASU
BIBIYARMU A KODA YAUSHE, ALLAH YA
AMFANAR DAMU DA ABUNDA MUKA KARANTA,
YA KARA TSAREMU DAGA MIYAGUN AKEEDU.
HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya(ABU SINAN)
08064734911```