*GORON SALLAH*1438/2017
*SHI'AH DA AKEEDOJINTA*
*_WALLAFAR:_* *Malam Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*
_Fitowa Na Hudu(004)_
```√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA SUNNAH.
‘Yan Shi’a sune mafi jahiltar Hadisai da Sunnoni
da ruwayoyi daga Manzon Allah. Ba zaka samu a
cikin zancan su ba cewa daga Manzon Allah,
abun da zakaji kawai shine. Aliyu yace, ko Jafar
yace ko Hussaini yace mafi yawan ruwayoyin su
karya ce suka kirkira suka jingina ga Aliyu da
Ahlulbait musamman Ja’afarus-sadiq
‘Yan Shi’a basu yarda da littafin Bukhari, da
Muslim da sauran littafan Hadisan nan guda hudu
ba, suna cewa *kirkiren karya ne, kuma
tatsunniya ce a cikin su.
Suna da wani littafi wanda a wajen su yayi dai-
dai da bukhari da Muslim da sauran littafan
hadisi mai suna “Alkafi” wanda malamin su
Kulaini ya rubuta cike yake da karai-rayi da
tatsuniyoyi.
√ AKIDAR SHI’A DANGANE DA SAHABBAI.
Sahabbai sune mafifitan halitta bayan Manzon
Allah (SAW). Allah (SWT) ya fada a cikin
littafinsa mai tsarki yana mai yabon su
“Muhammad Manzon Allah ne, kuma wadannan
da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai,
masu rahama ne a tsakanin su, kana ganin su
suna masu ruku’i masu sujada, suna neman
falala daga ubangijin su da yardarsa, alamarsu
tana a cikin fuskokin su daga kufar sujuda.
Wannan shine siffar su a cikin Attaura. Kuma
siffarsu a cikin Injila, itace kamar tsiron shuka
wanda ya fitar da reshen sa, sa’an nan ya
karfafa shi, yayi kauri, sa’annan ya dai-daita a
kan kafafunsa, yana bayar da sha’awa ga masu
shukar domin (Allah) ya fusatar da Kafirai game
da su, kuma Allah yayi alkawari ga wadanda
sukayi imani, kuma suka aikata ayyukan kwarai
daga cikin su da gafara da lada mai girma
(Suratul Fat’h – 29)
Duk wanda ya soki Sahabban Manzon Allah
hakika ya soki Manzon Allah domin zagin
Sahabbai gaba dayansu kafirci ne kuma ridda ne.
Kulaini ya fada a cikin littafin sa “Alkafi” cewa
“Lallai sahabbai gaba dayansu sunyi ridda bayan
rasuwar Manzon Allah in banda mutum ukku.
‘Yan Shi’a sunayin addu’a ta la’anci zuwaga
sahabban Manzon Allah a cikin salla, kamar
yanda Majiisi ya ambata a cikin littafinsa “Al-
anwar”. Suna cewa ‘Allah ka la’anci gumakan
Quraishawa guda biyu da makaryatansu guda
biyu da diyansu guda biyu’.
Gumakan sune Abubakar da Umar
Makaryatan sune Abubakar da Umar
Diyansu kuma sune Aisha da Hafsat
Kumaini (Batacce) ya fada a cikin littafinsa
“Hukumatil Islamiyya” cewa: Lallai Abubakar da
Umar fasikaine kuma wawaye ne.
Yan Shi’a suna da’awar cewa Usman munafukine,
Abubakar fasikine, Aisha mazinaciyace da dai
sauran miyagun maganganu da suka fada ga
sahabbai wanda da suna nan cike da littafan su.
ALLAH YA TABBATAR DAMU AKAN
INGANTACCIYAR AKEEDA.
ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.
HAKKIN MALLAKA©
Hashim Sirajo Uba Tsamiya (ABU SINAN)
08064734911```
No comments:
Post a Comment